← Book details Fulanin Daji Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 25

Sashe 7

Fulanin Daji Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

🎄 FULANIN DAJI 🎄
🎄 🎄 🎄 🎄 🎄
🎄 🎄 🎄 🎄
🎄 🎄 🎄
🎄 🎄
🎄
N@ B Aleeyu 💕 page 6⃣9⃣
Hafsa da joda ne tafe suna fiarar yanda bikinsu zai kasance, Sega amina tazo wucewa takira hafsa zo muyi mgn, hafsa taja hannun joda suka tafi, amina tace ke kuma ubanwa yakiraki nagadai yar uwata nakira bakeba, joda tace hafsa idan kungama kyasameni aciki, hafsa tace to shikenan Dan Allah kiyi hakuri, amina tace iyye wato ma hakuri kike bata, yanxun dae bama wann ba, Allah kada kije mana da ita abikin bruhh in bahakaba wlh se in diz gata a bainar jama'a

Hafsa tace akanme nagadai itama ta zama tamkar yar gida, amina tace to shikenan zaki gane wann shegiyar yarinyar dakyau kamar aljana ay se gabaki daya hankalin samarin yakoma kanta, hafsa ta kyalkyale da dariya, to kindaiji abunda zakije jealously kawai, amina tace wlh zan jimiki ciyo mezanyi wa wann banxar kishi akai, hafsa tace ay sedai kiyi amma joda kamar taje biki ne ashobe bawanda ban mata ba , hakama head ba abunda zaki nuna mata inmadai bakiyi hankali ba tafiki haduwa domin make up artist zan dauka har agama biki, amina tace bura'uba wlh se in gayawa bruhh nasan shi baxai bari aje da ita gurin bikinsa ba

Hafsa tajuya tareda Jan tsaki tayi gurin joda, koda taje tasameta suna dama fura da gwaggo, joda tace hafsa zoga fura ke nake damawa, hafsa tace kai my joda naji dadi wlh, joda tace hafsa plss kirakani gidansu khalthum inkaimata ankon nan , kartayi fushi dani, hafsa tace ok yaushe zamuje, joda tace bayan sallah magrib driver nakaimu seya dawo damu, hafsa tace toh shikenan Allah yakaimu lokacin joda tace ameen " gwaggo tace hafsa ungo wann ta abbanmu ce kije dakinshi kisaka masa a fridge amma fa karkibari yayi kankara zai lalace, hafsa tace lallae ma dad, yazarce da shan furar gwaggo, joda tace kinsan me, allah duk randa ba'a masa wann furar ba dakanshi yake xua tanbaya kuma wae duk wann plastic din kafun gobe yakare, hafsa tace uhm aikam dad zai iya yanaso fura ne sosae

Agidansu khalthum se tsokanar joda take tana cewa matar abdallah, hafsa tace nifa banganeba wane abdallan, khalthum tace yayanki mana shiyake son joda harda ciyon so yayi, hafsa tace iyye shine ba'a gayamun matar yayana ashe zamusha liki jibi , joda tace kinga hafsa banaso ki dena, hafsa tace tab aikuwa yanxun ma nafara kice munada shagali agaba mune yan amarya mune yan ango, kaiiiii abun zai bada ma'ana......shiru tayi ganin joda na hawaye, khalthum tace lfy joda? In dae kan wann mgnr ne to mun daina tinda bakyaso, joda tace a'a khalthum bashine abunda yasakani kuka ba,

Hafsa tada fata to menene joda, hawaye dake fuskarta tagoge sann tace hafsa wlh inason ya abdallah kodan shiruwar da yayi aka ina amma nasan niba matar bace inaji ajikina kamar ankusa rabamu dashi, hafsa tace wakuwa zai rabaku bayan da kunason junanku, joda tace a'a hafsa hjyr abdallah tayiwa gwaggo dani kaina garfadi akan danta, gwaggo ita kanta ta gayamun bata son ganina da abdallah takaras he zancen cikin kuka

Hafsa tace clm dwn, joda addua zakiyi kowane aure se yaxo datashi gaddama wani yaxo dasauki wani kuma yazo da tsauri addua itace magani kiyita tsayuwar dare kina kaiwa Allah kukanki akan yazaba miki mafi alkhairi muma kuma zamu tayaki da addua amma kisani duk abunda kika ga Allah. Yayi toshine dae2 mafi alkhairi agareki, gara kisakawa zuciyar ki salama tin yanxu, kikoyi yanda ake danne so ayi biyayya ga u waye, joda tace hmm Allah shigemana gaba ameen

Tin randa hafsa tamata wadann maganganun seta kara Jin kamar zata rasa abdallah ah yan kwanakin nan, shikanshi abdallah yana yawan Jin faduwar gaba a duk lokacin daya tuna joda , yaukam yashirya fadamata komai, zaune suke a garden kowannensu yayi shiru da abunda yake sakawa aranshi, abdallah yafara dacewa joda bansan meke faruwa ba se intajin faduwar gaba aduk lokacin dana tunaki, joda tace nikuma jinake kamar sanadin rabuwarmu natare damu, abdallah yace kamarya kenan

Joda tace abdallah ji nake ajikina yan kwanaki kalilan suka rage mana murabu da Juna, abdallah yace hava joda yakike irin wann zancen ay seki saka narasa dayan side din jikina, domin ke rabin jikina ce , joda kam fashewa tayi da kuka, abdallah yakaraso kusanta yadan janyota ajikinshi yana lallashinta ana haka Sega gwaggo tazo wucewa tsananin bacin rai taji lokacin data hangesu rungeme da Juna , jodaaaaa takirata da murya mai karfi, dasauri joda tadago tareda janye jikinta abdallah kuwa zare ido yayi, gwaggo tace wlh baxan taba yafe maka ba idan ka lalatamun "ya , abdallah yace Dan Allah gwaggo kidena mun kallon ma yaudari wlh son tsakani da Allah ne

🎄 FULANIN DAJI 🎄
N@ B Aleeyu 💕 page 7⃣0⃣
Gwaggo tajuya afusace danko zuciyarta takawo baxata jure tsayuwa ba , joda tamike aguje zata bita abdallah yarike mata hannu joda ta girgiza masa kae , abdallah yace karki bata hakuri yanxu ki bari harta huce joda tace koma yane yanxun kasakeni hankalina at ashe yake inajin tsoro, abdallah yace shikenan ,tana wucewa yadafe kanshi omg ya Allah kamun gata a wann lamarin

Gwaggo kam share joda tayi gabaki daya tadena shiga lamarin ta, joda tin tana hakuri har tafara kuka da rashin cin abinci, hafsa talura da halin da halin datake ciki, tayi2 da ita taki gaya mata komai, dole tasamu gwaggo itama din cewa tayi kibarni da ita hafsa dole badan tasoma tafidda kanta a lamarin, daga lokacin tafara tsoron tsayuwa da abdallah shima haka dukda cewa kuwa tana missing

dinshi sosae da sasae, yau sundawo islamiyya itada hafsa tafe suke suna firar bikinsu joda tace nidae hafsa inajin tsoron xua bikinku kinsan yanda yayanki yatsaneni hakama su hjy barema amaryar inkinga yanda take hantarana ma basauki , hafsa tace hava joda bruhh batsanarki yayi ba rayuwar shi hakanan kowa yana iya yiwa hakan Dan Allah kiyi hakuri kicirewa ranki hakan, bashida sabo ne barema nacemiki idan kun saba zai bari, joda tace hmm bakisan wasu abubuwan dasuka faru ba bayan tafiyarki, acikin ranta take wann zancen

ganin abdallah yasaka ta manta duk wani bacin rai, dasauri ta isa gareshi , ya abdallah shine kagujeni koh " abdallah yace joda bana son naja miki matsala ne tsakaninki da mahaifiyarki, hafsa ta karaso tace zanshiga ciki kisameni, joda tace toh ganinan xua fiarar su suke gwanin sha'awa kowannensu yana nunawa Juna irin son da yake yiwa Dan uwansa, joda tabuka sgegiyar kara sakamakon bulala dataji a bayan ta haka adinga zuba mata dorina,

abdallah yaturata da karfi mamma kashe ta zakiyi ne kome? Hjy tace abdallah wlh zan kashe ta matukar bata rabu dakai ba, abdallah yace niyakamata ki kashe ba itaba domin ni nake biyar ta ba itaba, hjy tayi tsalle tasake bugawa joda dorina joda tazube kasa, hafsa tafito aguje tareda sauran masu aykin gidan , gwaggo tafito tayi tsaye tana kallon su, abdallah yace wlh hjy idan kika jimata ciyo agidan nan kowa bazaiji dadi ba wlh zan to tonawa kowa asiri sekuma yafashe da kuka jikin hajiya yayi sanyi gwaggo kanta ya bata tausayi

A yanda taso zata karawa joda wani dukan amma kuma ganin yanda abdallah yake kuka da sanbatu yasaka jikinta sanyi, joda takara fashewa da kuka saka makon jinin data gani akafarta hjy tayi fuuu tawuce tareda yada dorinar hafsa tazo dasauri tajanyota abdallah kuwa yabisu har daki yana dada basu hakuri, a hanyar garden ya hadu da gwaggo dasauri yaduka yana bata hakuri tareda zayyane mata yanda sukayi da dad dinshi, yakara dacewa zan dena kula joda har se randa aka mana baiko,

Gwaggo tace tashi bakomai Allah zaba mana mafi alkhairi ameen " Joda kam kuka take kamar me badan komai ba sedan in ta tuna kiyayyar da hjy ke mata, dakyar aka samu tayi shiru, abdallah kuwa doctor yadauko yadubata aka mata dress din gurin, kulawa yake bata kamar me abu kadan zaice me, me kikeso, hafsa kanta tana tausayin yayanta yanda duk yawani canzawa lokaci guda yazama silent fiyeda tunaninka

Bayan kwana uku tawarware har takoma islamiyya , iyakacin su gaisawa da abdallah joda najin tsoron tasake cin wani dukan , abdallah kuwa bayaso yasake jamata wani abin , gamida gwaggo kuma bayaso tasake kamasa da wani laifin baya da abin Kare kansa , joda takira doctor dinta tace wai nikam se yaushe zamuje gurin matarka ne " dariya yayi sann yace kefa kin cika azarbabi , ba nagaya miki cewa dakaina xanxo muje tare ba, idan nasamu chance. joda tabata fuska tamkar tana ganinsa nidai idan aka wuce wann tym din banaso I mean cikin wann satin...........

🎄 FULANIN DAJI 🎄
N@ B Aleeyu 💕 page 7⃣1⃣
Yau Saturday yaune Ahmed zai dawo, kuma yaune za'a fara biki, hafsa tazo tacewa joda Dan Allah zoki rakani mugyara dakin bruhh Ahmed, joda tace aza hannu aka, tace wah ni tufa mun asiri wlh ba inda zanje mezanyi a parlor dinku kuma har dakinshi sokike yakasheni tabb kedai Allah kiyaye hanya , bayan da hafsa batayi ba amma firr taki xua dole taje ita kadai

Bayan tagama ne tazo ta kawowa joda kayan da zasu saka, English wear ne riga da skit sekuma Dan kwali fari riga baka skit pink, da talkami farare da baki komai iri daya, khalthum kam kamar tasan abunda zasu saka itama tasaka nata amma ita shigar marron colour da milk bakaramun kyau tayi ba , hakama joda yaran kamar "yayan turawa khalthum ce tanada musu dankwalin kamar head.

A motar hafsa sukaje basu bari angansu ba "nice day" ce saboda haka kowa irin shigar yayi barinma amarya abun basauki, hotel suka dauka babba a nata ciye ciye ga lemuka kamar ruwan panpo, duk inda sukayi idanun jama'a na kansu, musamman joda ana son sanin ko yar waye yanda suke kama da hafsa dakuma Ahmed, mansura tadauki loudspeaker tafara godiya ga kawayenta yan uwa da abokan arziki sann takara da yan gayyar sodi, khalthum tace kaddai dani take billahillazi bana daukar kaniya ba shegiyar data isa , hafsa tace clm dwn mana khalthum bada ke take ba mutun nawa yake gurin nan taya zaki gane hakan
Chapter 7 · 0% Book details