← Book details Bakar Izaya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 28

Sashe 7

Bakar Izaya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da sauri yafito daga cikin hospital har yana hada hanya duk yadda yake cikin tashin hankali bai hana kyanshi fitowa ba sujojine barjet a hospital din da sauri suka taho suka Saramai kana suka bude mota yashiga

Sukansu sunsan ogansu yana cikin tashin hankali koda suka iso bai jira sun bude maiba yafito da Sauri haryana cin tuntube

hafsa ke hafsa dan uwarki kina ina da sauri tafito domin kiran yabata maki baisaba yimata irin wannan kiranba

karo sukaci shima yana quqarin shiga bedroom din nata duka taji ko ina ajikinta dan ubanki nizaki cuta nixakiha inta miye ban maki wane haqqine naki bana saukewa

amma kirasa dami zaki sakaman saiki dauko cuta kisaka man wallahi kincuceni hafsa saida yayi mata lilis kana yace kije nasakeke saki ukku

duk da jikinta baqarfi amma saida tabude baki tai mgn

ni kasaka haisham cikin xafin xuciya yace wallahi hafsa dada abinda yafi saki da saina makishi tunda nake bantaba zinaba amma gashi na aure mata mazina ciya

wurin naiman maxanki kingoga man cuta banjiba banganiba wallahi Allah ya isa tsakani dake

tunda yafara maganar hafsa ke kuka yanzu haisham sharrin daxa kaiman kenan aizansa ko wani yace maka ina hulda da maxa zaka qaryata amma kai da bakinka

kake fada kamar yadda kace baka taba xinaba haka nima dan kokai shedane kaine kafara sanina aya'mace amma kaje nabarka da Allah sharrin dakaiman

kuma insha Allah tundaga nan duniya zaka fara ganin sakaiyata mari yakai mata wanda saida komi nata ya tsaya cak natsawan minti 30 taga dai bakinshi yanata mgn amma batasan miyake cewa ba

saida yajeho mata wata farar takarda kana tadawo hankalinta kiken isa naja maki sharri saiki bude wannan takardar ki karanta da sauri tadauka tana gama karanta wa taja jiki tafi daki domin bata iya tashi saida tashiga bathroom tahada hot water

tagasa jikinta sosai kana tafito tana kuka tana tunanin haisham sam bashida adalci

hakadai tagama shiryawa abaya kawai tasa light blue tadauki dan qarimin gyale tayafa wanda tunda ta aure haisham yahanata sa qaramin mayafi kuma tadaina amma gashi yanzu yasaka mata da abu mafi muni

awurin ya'mace wato saki kuma sakinma nawula qanci saki uku gasharrin zina wai harda H I V wai itake da h i v aidolema kamin taje gida saita biya hospital anmata gwaji itama indai hartana da ita to haisham ne yagoga mata domin ita bata taba

Mu amala dawani da mijiba inba haisham ba hakadai tafito daga ita sai handbag dan baxata iya daukar komiva inba jikarba

yana zaune abisa daya daga kujirin da suka kawata falo harta taxo fita yadaka mata tsawar datasa yan cikinta juyawa

ubanwa kikeso ya kaimaki shedar takardar sakin naki da hanxari tajuyo taga wata takarda kan center table kobai fadaba tasan itace ta dauka tajuya

tana fita sojoji sukayo gunta kaminsu qaraso tada katar dasu kuma wurin aikinku nikade nakeso natafi

wani cikinsu zaiyi magn kawai tajuya tabarsu tsaye ba yarda suka iya haka suka koma wurin dasuke

get aka wanga memata tafice daga gidan kamar walqiya saida tahau titi kana taji xuciyarta namata daci

Miyasa haisham zaiman haka miyasa lokaci guda yacanxa daga yadda nasanshi kuka tasa mai tsuma zuciya wani prvt hospital data gani shiyasa tatsaya

Cikin asibitin tashiga tasai kati layi yana zuwa kanta tashiga taima likita bayanin tanaso aimata gwajin aids

wata nurse yakira yabata wata takarda yacema hafsa tabita

haisham tunda hafsa tafita yaji duniyar taimashi qunci jiyake inama yakashe kanshi yahuta ya tabbata

hafsa tagama cutarshi kamarshi ace yanada h i v ya duniya zatace shida yake shugaban sojoji yanxu inyaranshi sukaji anya zasu qara girma mashi

kuka kawai yasa duk da ansan soja da dauriya amma shi yakasa daure wa

waye haisham haisham dane gurin alhaji hamxa wanda subiyu ne iyayanshi suka haifa shida qananshi Ameen

haisham tunya dan shekara biyar aduniya yakesan sojoji to da mahaifinshi yaga haka bai taiyeshi ba yasashi makarantar sojoji yana gama secondary yatafi America dan qarasa karatunshi

yagama karatunshi cikin nasara yafito da babban matsayi

lokacin daya dawo gida hutu lokacin ne yahadu da hafsa sunsha soyayya cikin wata daya domin hutunshi na wata biyune ya yarda da ita itama tayarda tadashi

aka daura masu auransu amarya tatare agidanta cikin farin ciki suke zaune domin haisham yasa meta yadda yakeso

Wata daya dayin auran yatattara ya koma bakin aikinshi hafsa harda kuka

Shima duk yadamu domin yana san hafsat dinshi nan yaymata alqawarin inya dawo da ita zai koma dominshi abuja yake aiki gidan iyayanshi kuma yana kaduna

haka ko akai yana dawo wa y dauketa sukatafi abuja soyayya suke mai tsabta yana mata abinda takeso itama haka shiyasa suke San junansu

Sunada shekara ukku amma haryanxu Allah bai basu haihuwa ba lokacin kuma aka qarama haisham

girma yazam mana shine shugaban sojojin Nigeria

abinya mashi dadi dagashi har ma soyanshi alokacin wanda baisanshi ba yasanshi dan dinne masoyan shi suka hada mai duk gidan TV dake garin abuja saida sukaxo wajan dinner nan anci ansha antashi wuraran 2 kowa yakama hanyar gidanshi cikin jin dadi

yayinda haisham yagina wani qatan gida cikin asok ba abinda babu inkashi cikin gidan zaka dauka ba aduniya kakeba dan tsarowar gidan get gomane acikin gidan kana kowane get akwai sojoji guda goma

Inkashiga cikin gidan titine yatafi har bakin wata kofar glass wadda zata sadaka da shiga gidan koda halibin bindiga baxai fasa wannan kofarba bare atara qarti goma saida suyi bugun sugaji bazata taiko motsiba

Sanna inkaje gurin dole saika fadi sunanka kana na urar tafa dama yan gidan sunanka da hotanka insun amince kofa tabude kashiga

cikin falon kanshi abin kallone kujeru saiti biyar ne kowani kuma akwai taxara sosai atsakaninsu

kana daga bedroom dinsu zaka iya hango duk abinda ke faruwa waje domin kofar ta glass ce

gurin kayan motsa jiki ko babu abinda babu fans ku ida yima kanku imagen din gidan

kowa yaga gida saiyace yayi kyau yayinda alhaji hamxa yaimai fada sosai dan yana ganin yayi almubaxxaranci

nafisa yanaji kinyi shiru ne hmm kedai bari sadi tun jiya danaga birgediya general naji yatafi da imanina sadi ina sanshi San aure bawai san shashanci ba

hmm nafi kekina ganin zai aureki yanada wannan tsaleliyar matar

😘Ansholly😘
[3/8, 1:07 AM] ‪+234 703 962 5239‬: 😭BAKAR IZAYA😭25

😘Ansholly😘

saida nafi tayima sadi wata irin harara tamkar idanuwanta zasu fado kasa

kana tarafa magana tabbas sadi komin munina sai birgediya general ya aureni wallahi kuma yaxauna dani ni daya domin ni banida kishiya agidan haisham

suduka shiru sukai chan sadi tace bance bazaki iyaba amma tayaya

zokiji akunnanta tarada mata wata mgn wacce bansan mitace mataba

dariya sukai kana suka tafa wallahi kawata kina wuta

amma kuma yaza aiki hada wannan plan din

murmushi tayi miyasa ke sadi kinada saurin mantuwa kinmanta waye likitan da akaba haisham

auhaka fane natuna mutumin kine domin in bandama ta dalilinshi baxakiga haisham din bama harkice kina sanshi

saida tayi fari da idanuwa kana tace to dashi xan hada plan dina

amma sainan da 1months kinga lokacin ya yadda dashi saimu fara plan dinmu koya kikace

hakanma yayi qawata kina wuta muna binki da gas dariya suka fashe da ita

nafi yar kauyan cikin garin abuja ce sulaja iyayanta talakawa wane sosai wanda insukaci nayau ba lallai susamu nagobe ba

😭Bakar ixaya😭26

😘Ansholly😘

haka suke rayuwarsu cikin rufin asirin Allah yayinda nafisa take bakin cikin zowarta tatsatsunsu domin tana gani tamkar baban nata malalacine shiyasa suke zaune cikin talauci har yanxu

tanada shekara sha biyu tafara bin maza duk iyayanta basu sani ba

lokacin da tanada shekara sha biyar lokacin tayi ciki

mahaifinta wannan bakin cikinne sanadin mutuwar shi ya yinda mahaifiyarta tace baxata zauna mata agida ba

ko dar batajiba dama tagaji daxama cikin talauci tattara kayanta taqarama rigarta iska dama wanda yaimata cikin yana taso tadawo gurinshi

dazama domin aganinshi qaramar yarinya da ita bai dace tana zaune cikin talauciba

koda tagama gayamai yarda sukai da innarta

dariya yayi karkiji komi nafi nizan riqeki tamkar yayanki
kuma wannan cikin yau baxaki kwana dashiba

kallanshi taicikin mamaki to yaxa ai dashi

dariya yasa kana yace karfa kimanta nafi nifa likitane

haka yaxubar da cikin nafi tare dayi mata alqawarin gobe xaitafi da ita cikin garin abuja dominshi

ba anan yake aikiba yaxone yaga ya mutanan da aka turu suke aikinsu to nan yaga nafi

safiya nayi nafi da Dr bashir suka kama hanyar cikin garin abuja kotaje tanemi yafiyar innarta

koda suka shigo baixarce da ita ako inaba sai gidan magajiyar karuwai

hannu biyu tatar besu domin tasan dr bashir sosai
lbrn komi yabata jawo nafi tayi jikinta kisaki jikinki sosai nafi nan gidan kune bamai korarki inbake kisake wani gidan ba

nafi taji dadi har acikin ranta domin gani take yanxu xatai rayuwar yanci

saida magajiya tayi wata biyu tana goge nafi kana tahadata dawani alhajin birni wanda saida yasauke ma magajiya dubu dari biyar

kana yatafi da nafi hakadai nafi tazama gogargiyar yar bariki domin ko magajiyar tana sara mata

duk cikin gidan da sadiya kawai suke shiri shiyasa koda dr bashir yabata gida suka dawo tare

to dinner da akai dr bashir yagai yaceta taje danta samo masu wani mai kudin amma ita ganin

birgediya general yabirkita mata lissafi dan tunda taganshi takasa sukuni

yau watan birgediya general daya yana aki lfy domin bawani matsalar dayake samu da sauri yashigo office din domin yana gani yayi latti sosai dan

yanada meeting around 10:30 gashi kuma yanxu har 9:30

yana xama PA dinshi yana shigowa kallanshi yayi da mamaki yace lfy

domin yayi mamakin ganin PA dinshi dan yace kar wanda akabari yashigo

domin yanaso yahada wasu takardune baiso ayi disturbing dinshi

saida yaqame tamkar gunki kana yace sry sir

wanine yace nakawo maka wannan takardar yanxu dan saboda akwai important abinda yakamata kasani ciki

amsa kawai yayi ya aje ya yinda PA nashi yajuya yafita

harxai aje saiya tuna da ance important ne budewa yayi yafara karantawa kamar haka
Chapter 7 · 0% Book details