← Book details Bakar Izaya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 13 OF 28

Sashe 13

Bakar Izaya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

tuwa tazubo yanada yawa sosai gashi yayi wani irin sanyi dan yanxu lokacin sanyi suke amma bata damu da sanyin dayiba haka taketa turashi saida taji taqoshi kana tatashi ruwa tasha kana tadauki buta tayi alwala tana gama sallar daba tasan mitake cewaba

takama shara dan mlm iro yana masallaci

uwale nashiga rugarsu bata zarce ko inaba sai gidan wanda aka kira mahaifinta

lokacin anfito daga masallaci duk yan uwanshi suna zaune za araba gadan aba kowa hakkinshi kamar yadda addini yatsara

ganin mutum sukai tsaye bako sallama kowa yadago yana kallanta lfy mlm kikazo kikai mana tsaye aka kindai san baki da gadan mamacin nan kowa kuma yasani dan haka kama hanya kikoma inda kika fito

A,a illiya baza ai hakaba ke uwale miyaka woki nan uwale datun dazo take tsaye tamkar damisi dan maganganin illiya sunbata mata rai badan bokanya tace kartai wata magana ba bayan taraban gado to aradu da maikwatar illiya sai Allah

illiyan ne yakara magn waibake akema mgnb banxar mata kawai inhar kinsan baki da abincewa ubanmi kikazo yimana nan aradu koki wuce konazo natatta kaki

cikin isa uwale tai mgn gadona nazo amsa tsit kaji kowa yayi illiya yanaso yayi mata mgn amma yakasa samun wuritai tazauna sai wani cika take tana batsewa

haka sunaji suna gani sukaba uwale dukiyar gaba daya dan ba abunda tarage masu inba raqumi daya ba kuma kosuce mata basu yarda ba wanda duk sbd dukiyar suka kashe yayan nasu amma gawata arana tsaka tazo tatafi da ita

sunajin gidan nan kawai suka qaru dashi sai raqumi daya

kallan illiya tayi tashi muje karakani wajan da shanin suke ba musu yatashi yabita yana gaba tana biye dashi har sukaje wurin tsaye yayi yanama uwale kallan tsana domin shima yaci buri akan wa innan shanun

to mlm sai akara gaba ko jinjina kanshi yayi kana yafice daga wurin domin wani kuka yaji yataho mashi

tana dukawa xata fara kwancewa taji mgnr bokanya wanda yasata zabura dan tsanin tsoro saura kadan tasaki goyan dake kan bayanta

karkiji tsoro nice bokanya ina tare dake tun tahowarki kibarsu anan zamu dauki abunmu ke kingama aikinki

to uwale tace cikin qermar jiki dan har fitsari tasaki ficewa tayi daga wurin da sauri bata tsaya ko inaba hanyar rugarsu tayi

gidan yalwa tashiga taci Sa,a tana nan sauke goyan mai kudi tayi buta tadauka tayi bayi da gudu

chan saigata tafito yalwa yau naji tsoro aradu bantaba jin tsoro hakaba sai ranar danaga Hainan cikin dakina baccin nasan naya data rafi sai kuma yau

ya akaine uwale har kinje rugar taku kindawo ko biyoki sukai yan rugar taku

ke yalwa duk wannan mai saukine to miyafaru

wai ina cikin kwance shanin dana samu kawai sainaji mgnr bokanya nan dai tagaya mata yadda sukai da bokanya

ke uwale ashe abin bokanya harya kai haka

kedai bari shiyasafa bana wasa da al amarinta yanxu dai tashi mutafi wurinta muji mizatace

uwale da yalwa zube gaban bokanya bayan sungama kirarata dan yau har kirarin dabasu taba yimataba sunyi mata

kallansu tayi daya bayan daya kana tafara mgn

aljanin daxai maki aiki akan kisan hainan shine akaba dukka shanun da raqumma

kubashi nanda wata bakwai xai baki mgnin da zaki zuba mata abinci tanaci ko sharawa bazatai ba zata mutu

cikin firgici uwale tadago kanta bokanya wata bakwai yayi yawa nida nakeso yanzu dana koma gidata mutu

tsawarda bokanya tayice yasa dan uwale firgita yasa kuka

Ansholly😘
😭BAKAR IZAYA😭
48_49

😘Ansholly😘

*wannan pagen sadaukarwace ga dukkan masoya bakar ixaya ngd d kaunard kuke nunama littafina*

*garin abuja*

hannu yasa yadafe zuciyarshi danjiyai tana wani irin bugu amma yana ganin tamkar arba dayi da abinda yaji nantake yanaso ne domin yana ganin tunda yake baitaba san wataba sama dawannan baiwar Allah wace ko sunanta baisani ba

nafi tasowa tayi daga wurin datake zaune dan tanasan yaji kamshin turaran da boka yabata sosai taba kafadarshi tayi firgigit yadawo daga tunanin daya tafi

ido takashe mai yadai my haisham kodai ban makaba ne

haisham da tunda yashaqi kamshin Nafi ya ida birkicewa yafara magna cikin voice dinshi mai saka yan mata surude irinsu halima Lol

tunda nake bantaba samun macen danaji tashiga zuciyata irinki inajinma yanxu dana fita daga nan kd zani dan inaso ayi auran nan cikin kankanin lokaci dan baxan iya jure rashinkiba akusa dani

dadin danafi taji Allah kadai yasani dan jitai tamkar tazuba ruwa akasa tasha amma tayi alkawari da haisham yatafi zata hada wani qwarya qwaryar party

kallanta haisham yayi yaga tatafi tunani tabata yayi lfy naganki cikin tunani

murmushi taimai kana tafara mgn ina tunanin Sa ar da Allah yabani nasamun qwarxan namiji irinka haisham ina sanka tunda naganka naji narasa sukuni harsai yau daka firta man kallamar so

kallanta yayi cikin murmushin shi dama kintaba sanina ne baby

sai yanxu tagane katobarar datasoyi girgixa kanta tayi a,a kasan dai inso yana azabar da mutum baima san miyake fitowa daga bakinshi ba

fira sukaci gaba dayi tamkar sunkai shekara yayinda haisham ma yamanta yana dauke da wata cuta mai suna aids yana ganin tamkar yanxu zaifara
aure kuma auran saurayi da budurwa

saida akayi sallah azahar kana yai shirin miqewa

baby nah baqo zaiyi halinsa zantafi badan nagaji dake ba saida i haquri ne domin inda xani danna sameki ne amma dazaki yarda kibini mutafi tare dana tafi dake saidai nasan baxaki iyaba

cikin kisisina irintasu ta yan bariki tafara mgn nima haka nakeji my haisham jinake tamkar karmu rabu amma yaxanyi tunda tafiyar taka takasance wacce xamu xama abu dayane saidai kawai naimaka addu,a

shafo fuskarta yayi baby kintafar man da xuciyata gabaki dayanta inama ganan gaba

amma kinman laifi m kallanshitai alamar firgici afuskarta laifin minai ma my haisham

murmushi yayi kwantar da hankalinki baby bawani laifi kikaiman mai yawaba

sunanki ne baki fadaman kinaso naje gida dad dina yatambaye ni nakasa fada dakuma garinku kifada man komi

sunana nafisa mubiyu ne wajan iyayenmu nida yar uwata sadi mahaifina Allah yaimashi rasuwa shekara goma data gabata wani hawayan muna firci tashare daga fuskarta

ayya sry Nafisa Allah yajikan baba

amin tace kana tafara mgn sunan qyauyan mu sulaja
mahaifina kamin yarasu yanada rifin asirin shi amma tunda ya mutu yan uwanshi

suka kwace mana komi yazam mana abincin dazamuci yana gagararmu to lokacin Dr bashir yaje qyauyanmu domin duba asibitin cikin qyauyan ko wa inda aka turo suna aiki yadda yakama to anan yaga yayata yace yanasan ta

kamin takara mgn wayar haisham tadauki qara da sauri yadauki wayar assalama alaikum chan dayan bangaran akace

wa alaikumussalam dad ina wuni lfy dama cemaka xanyi inbaka samo matarba toni nasamo ma yarinyar mutinci diyar alhaji Ahmad aikasan irin tarbiyar dayake ba yaranshi ko

murmushi yayi dad karka damu nasamu wata yarinya mai tarbiya gani nanma wurinta tace nagaida ka duk mgnr dayake idanshi nakan Nafi

shima alhaji hamxan fadada fara,arshi yayi to ina amsawa yaushe xakazo gidan dan xaman dakake ba mata yana damuna

dad yau ina nan tafe to saikazo kashe wayar yayi yakalli Nafi to nidai xan tafi baby inajin sai gobe xandawo inna dawo xaki idaban lbrn

dariya tayi tace saidai muhadu asilaja dan gobe muma zamu tafi dan afada masu dawuri to xanm sameku achan din kiran orderly dinshi yayi da waya kakawo man 2milyan yanxu ok sir

ai Nafi mutuwar tsaye tayi 2 milyan to itaxaiba koko tsaye kawai take amma xuciyarta taruga wani wuri zata iyacewa duk karuwancinta bata taba rike koda 1milyan ba amma yau gata harda 2

ba afi 3mnt ba yashigo dauke da kudin ahannunshi amsar jikar haisham yayi gashi baby kiyi manaiji kamin nadawo inkuma bakisan wannan kinfisan kifiddo da kanki to kifada man

girgixa Kai tashigayi uwa kadan garu murmushi yayi mata kana yajuya yatafi dan yaga tamkar batasan inda take ba

itakuma tayi shirune domin tasan inhar tabude baki to ihu zata saki dan tsananin murna to bataso tabada kantane

Ansholly
😭BAKAR IZAYA😭
53_54

😘Ansholly😘

*wannan page nakini Aisha*

kd
haisham ne xaune shida mahaifiyarshi kasha hanya dan nan dayake baka safe take fadin sunanshi ba

murmushi yayi haba hajiya wace hanya ga mutuman da yaxo ajirgi

duk da hakanan akwai gajiya yanzu katashi kaje kadan watsa ruwa kana kaci abincin

to yace mata dan yanasan hajiyar tashi ganin yadda take tattalinshi tamkar karamin yaro dayazo wurinta jiyake duk wata damuwarshi takau

yana shiga bedroom din wani kamshi yadakeshi yasan aikin hajiyarshi ne wani tausayinta yaji tabbas inba uwaba bawanda zaima haka dan yasan ita tagyara dakin dakanta tunda tasan bayasan na house girl

cire kayanshi yayi yafada bathroom

Nafi tanajin qarar fitar motarsu haisham tabuga wani irin ihu nafarin ciki da gudu Dr bashir suka shigo palon dama suna kusa da wurin dan tunda sukaji alamar haisham yatafi suka fito daga cikin gidan

tana ganinsu tarungume Dr bashir yayana mafarkina ya kusa zama gaske kaduba kaga irin kyautar da haisham yayi man alokaci daya to inama ga abu yayi nisa

nandai sukaita murna Nafi ce tai mgn aiyau akwai party dan dolene achashe

dole kudi suyi kuka sadi taba hannu suka tafa

shidai Dr bashir yana xaune yana kallansu yayana yanaga kai shuru ina tunanin wani abune Nafi

bai kamata ataba kudin nanba gwara kitashi mubi hanyar kauyanku yanxu dan mugaya gidanku yake kinsan tunda bawani gidan kirki bane ko qyaure babu ballantana yyanxu

wannan kudin chan yakamata suyi kuka banan ba kinsan matsayin haisham kodashi baiga aibun gidanba tunda yana sanki wasufa zasu gani yakamata muje mugaya gidan yake kana

amma inkinga shawar batayiba shikenan

tashi tayi da sauri haba yayana wanama irin shawararka batayiba tabbas kakawo shawara mai amfani kawai tashi muje

bawani bata lokaci suka dauki hanya bayan tayi amfani da mgnin da boka yabata

muntoci kadanne yakaisu cikin kauyan dan bawani nisa daga cikin gari zuwa kauyan

yadda gidan yake haka yake saima kara lalacewar dayayi

shiga cikin gidan sukai itada sadi sai wani irin warinne ketashi tamkar ba mutane aciki sadice takalli Nafi anya nafi akwai mutane cikin gidan nan jibafa kiga gidan duk kazanta aini wallahi ko yawo bana iya hadawa

Nafi tajuyo zatai mata mgn sbd tadanji haushin abinda sadi tace kamin tace wani abu wata mata tafito daga cikin wani daki wanda yake bara xanar xubewa koda yaushe
Chapter 13 · 0% Book details