← Book details Bakar Izaya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 28

Sashe 3

Bakar Izaya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

harda cewa indai harbaije yadawo da wannan dukiyarba to babasu bashi

shidai shiru yai yaqalesu baice uffanba har suka gama zage zagensu saka tafi da amshe raquminshi daya dayarage

Allah yaso basuji cewa yanada milyan daya ahannunshi ba dan bankai ga fada masuba suka fars zage zage

nasan da har ita saisun amshe nandai nabashi haquri da abinda yan uwanshi sukaimai

yace bakomi ai abinda yasa yasaida raquman bawai dan dije na diyar shi daya ba jiyai suna shawarar xasu kasheshi inya fita kiwo

shiyasa yai maza yaje yasayar naji tausayinshi sosai sukatashi suka tafi suma hakadai

rayuwa taita tafiya yayinda cikin dije yakai wata tara haihuwa yau ko gobe
[3/8, 1:05 AM] ‪+234 703 962 5239‬: 😭BAQAR IZAYA😭 10

😘Ansholly😘

ranar asabar da asuba dije tasauka ta haifi kyaikyauwar yarta wace hatta unguwar xoman data wanketa saida yarinyarnan tabata tsoro

dan kyan yarinyar yayi yawa amma datai wani tunani taga daga uwar har uban kyawawane shiyasa yarinyar tazama maikyau haka

da akaba iro karkiso kiga murnar dayayi yana godiya ga Allah dan kyan yarinyar firgitashi yayi

To aqa idar garinnan inhar matar mutum tahaihu dole yaje masallaci yafada haka yai alwalla yatafi masallaci cikin farin ciki

bayan angama sallah yace matarshi ta haihu tahaifi diya mace kamin yagama rife baki

Wani yace kace annoba tafito duniya wadda in akace uwarta nada ciki mutum yanayin asara ina ace anhaifeta

shima kamin yarife baki wani yaro yashigo massalacin dagudu yace adamu babanka ya mutu kamin yaran ya ida magnar nan adamu ya fece daga

Masallacin da gudu kamin mi wani yinquri wasu yaran suka kaqara zowa suka fadamana mutuwar mutum ukku hadda kakanki
mlm amadu

da gananfa mutane suka fara tsanar dije da iro haka akakai matattu har hudu gidansu na gaskiya yayinda mahaifiyarki dije har suma tai

hakadai akaita zaman gaisuwa yayinda mutane ko kallanki basuyi daga dije sai iro saikuma kakaninki matake daukarki wani abin mamaki tunda

aka haifeki baki taba koda rintse idankiba koda cikin dare idanki abude suke ranar da su mlm amadu suka cika sati guda aranar

tun cikin dare kike bacci kema aranar satinki guda aduniya abin yayima dije dadi dataga kina bacci danda duk atuna nunsu kobaki lfy

har anfara neman maki magani shiyasa duk yan rugarnan suka sani tunda aka haifeki kwana shidda baki taba bacci ba

wanda ansan jariri da bacci

to aqa idar rugarnan inhar mutum ya mutu to ranar daya cika kwana bakwai aranar zakiga

anata abin ciccika kamar anayin biki kuma har yanxu

ba adaina ba haka mata dayawa suketa kai abincin gidan mlm amadu

wani fura wani tuwo wani nono hakadai mutane keta shiga da qwarya an aje da anyi sallah la asar za ai addu,a lokacin bai ida karasawa ba

mukaji wuta takama agidan mlm amadu ga mata dayawa aciki dan aqalla matan dake ciki zasukai ashirin

muka tashi dankai dauki amma da mutum yatin kari wutar zakaga kamar ta biyushi haka munaji muna gani wutarnan tacinye mutanan ciki kaf ciki harda mahaifiyarki da matar mlm sule da matar marigayi mlm amadu da matar liman

saida mangariba tai kana wutarnan tatsaya batare da ankasheta ba gurin yayi sanyi qalau kamar bawurin akai gobara ba

haka mutane sukaita shiga cikin gidan amma inba tukaba ba abinda kake gani

Kakanki mlm sule sumewa yayi dan tashin hankali daman ga mutuwar amininshi bata sake shiba yanzu gashi matarshi

ta mutu wani abun mamaki ke kina kwance ba abinda yasa meki dan wasanki kawai kike da hannu wanki

*Ansholly*
[3/8, 1:06 AM] ‪+234 703 962 5239‬: 😭BAQAR IZAYA😭 11

😘Ansholly😘

sadaukarwa g limsy🌺 ina godiya da addu,arki

haka mutane sukaita magan ganu akanki wasu suna cewa keba mutum bace qilan diyar aljannuce domin kuta kyanki aka duba ansanke ba diyar mutane bane

haka dai mutane suketa magan ganunsu wani mai zafin zuciya abbashe dan gidan jamo shiya daukeki ya samu karmami ya kunna wuta

yaje zai sakaki ciki alokacin muna chan wajan qokarin ibu tokar mutanan da suka qune ihun mutum kawai mukaji muduka da sauri muka fito daga inda muke

Abbashe ne muka gani cikin wutar yanata ihu wuta tana cinshi muduka kamar anriqe mana qafa muka kasa zuwa inda yake harsai da yacinye wutar tamutu

kana muka iya zuwa wurin yadda muka ganki acikin gida kina gefe haka yanzuma muka sameki sai wasa kike da hannunki

tan bayar mutane mukai cewa miya kawoki anan kida keki cikin gida nansuka fara bamu lbr abbashe ne yadauko ki zai sakaki awuta yazo dai dai wutar

sai yayi kamar anjefashi ciki muza musama harda yarinyar taqone hakadai muka sallaci tuka muka tai muka rife aka dawo da wata saban xaman

ke kuma babanki iro yadauke ki yatafi dake gida domin duk dacewa mutum ukku ya mutu agurinsu to ba wanda yakoma qofar gidan anadawo wa

daga maqabartar kowa yakama hanyar gidanshi dan atunanin mutane yanxu kuma maza xa akashe tunda bida bine abun andauki maza sai kuma aka dauki mata to

Insuka qara zama suza aqara dauka shiyasa da aka dawo maqabarta mlm sule yagaba wanda yabiyo su saiyaja iro cikin gida

yafaramai nasiha domin yaga yafara yadda da abinda mutane kecewa akanki shin iro ka yarda diyarka yar aljannuce kamar yadda mutane ke fada

iro saida yaqara sinkuyar da kai domin jiyake shima kamarya hadi zuciya ya mutu dan rasa matarshi dayayi da mahaifiyarshi

kana yafara magana to baffa zata iya kasan cewa haka domin daga yadda mutane sukace ba ataba

haifar mai kyantaba duk rugarnan ni kaina yanzu tsoranta nake

dan kyanta kanshi abin tsorone ballantana yadda kuma taxa mamma mutane annoba ciki hardani dan nima nayarda annobace aka haifa man kawai yasa kuka

*Ansholly*

*08136195038*
[3/8, 1:06 AM] ‪+234 703 962 5239‬: 😭BAQAR IZAYA😭 12

😘Ansholly😘

Mlm sule zubama iro ido kawai yayi yana kallanshi saida yayi mai isarshi kana yaishiru

kana mlm sule yafara mgn iro kaban mamaki dahar dakai ake cema diyar daka haifa annoba kuma wai yar aljannu to inajin jinina ajikin yarka kuma nasan wannan

yarinya yarkace domin jini baya qarya da yarka bace da baxanji jininta ajikina ba kawai dai nasan da abinda Allah yabuye akan wannan yarinya

hakadai mlm sule yaitaima iro nasiha ta dai dai iliminshi cikin ikon Allah iro yasa duda yayda dake yarshice danda

da gaske kallan yar aljannu yake maki nan suka samaki suna hainan dan ba asa maki sunaba kuma yasan yanxu inyace atara mutane asa maki suna ba wanda zai iya

zuwa mlm sule ne yace iro ya dauko shanuwa guda cikin shanunshi ukku yanka maki na sunanki dan alqawari yai indai dija ta haihu saniya zai yanka mata dan haka kuda bata da rai bazai fasa wannan al qawarin daya dauka ba saida aka gama yankan shanuwar

kana suka kama tunanin waye xai soya mlm sule ne yace iro yaje gida zai bada akawo mashi shi yasamu wadda zaya turo tasuya

yana tafiya ahanya yagamu da uwale ita uwale ba yar rugarmu bace rugarsu nagaba datamu

uwartace ke aure anan shine tatahu da ita agolanci to uwale tunda taga iro taji tana sanshi amma shi alokacin baya takanta domin

dijen shice abun sanshi gaisawa sukai kana taimai gaisuwa yaji dadin gaisuwar da taimai domin tunda akaimai mutuwar ba
wanda yaimai gaisuwa

wasuma harararshi kawai suke yai mata godiya harzata wuce yatsaida ta

dan Allah uwale wani tai mako nakesan kiman

to Allah yasa zan iya dama baffane ya yankama hainan shanuwa to narasa wanda

zai suya man yancikin koxaki iya taima kaman ki suya man kamin gobe nasamu mai suyaman gangar jikin

saida tara zana dataji ance saniya aka yanka maki domin koni aka haihu gidana tumakai nake yankawa dan kinsan fullatani da shaninshi gwara

yaga tafadi ta mutu da ace anyankata uwale cikin saurin murya tace ta amince amma saitaje ta gayama innarta

bakomi saikin dawo dannasan lokacin har ankawo naman

kuda taje tagayama mahaifiyarta bata hanata ba itama dauko gyaletai tabiyo yar tata domin sunada san banza sosai

koda yaran da mlm sule ya aiko kawo naman yazo sai iro yace yafa dama mlm sule yasamu mai mashi soyen

haka uwale da mahaifiyarta sukaxo suka kama soye bayan angama sallah magarib iro yafadi

ansa maki suna hainan ba wanda yace mashi ko uffan

hakasu uwale suka gama soyansu suka tafi da alqarin gobema zasu dawo su ida sauran

haka kowa yake jininshi bisa akaifa har kika kai sati daya lokacin satin mahaifiyarki daya bata raye

kekuma satinki biyu aduniya amma tun bayan baccin dakikai kina sati daya aduniya baki kuma wni baccin ba

😘Ansholly😘
[3/8, 1:06 AM] ‪+234 703 962 5239‬: 😭BAQAR IZAYA😭 13

😘Ansholly😘

To abinda yasa mutane suka saki jiki shine da sukaga harkinyi wata ukku ba abinda yaqara faruwa

yayinda uwale tashi gema iro sosai tunyana shareta har yake yafara kulata domin yadda take kula dake

yanxu kuma yafara jin saukin yan rugar dan sun fara rage tsanar da suke mashi shida yarshi

haka baffanshi yaje ya neman mashi auran uwale ba asa bikin da nisaba domin uwale ta jima gida dan xata kai shekara 20

dan duk rugarnan ba tsaranta danmu yarinya nada shekara 13 muke aurar da ita

ansha biki lfy ankawo uwale gidan mijinta

ya yinda kike da wata tara kina tafiyarki ko ina

alokacin uwale tadaina kula dake saiki kashinki harya bushe ajikinki bata wanke ba har sai iro yadawo shi zaya wanke maki

ranar dazaki ciki shekara daya aranar kikai bacci

hankalin iro yatashi dan gani yake kamar abinda yafaru abaya zai kuma faruwa da assuba yatashi yai alwalla yatafi masallaci

dan sadda yaje ko liman bai samuba haka yatsaya har liman yazo iro lfy naganka haka cikin tashin hankali

bai iya boyewa limanba yafada mashi abinda ke faruwa

wanda yaci ace ya boye wannan abun acikin xuciyarshi danda bai fadaba ba wanda xaice

dan kincika shekara daya wani bala,i yafada mashi hakadai aka kira sallah

bayan angama sallah liman yatashi yafara gayama mutane abinda iro yafada mai

kana yace nafada makune dan kusan da zanchan dan kar abar mutane cikin duhu

nan akaita surutu kamar ba masallaci akeba wani cayake wallahi inhar tasake tataba mani wani nawa aradun Allah saina bajeta

hakadai iro yatashi yatafi gida jikinshi duk ba dadi domin saiyanxu yake dana sanin fadar dayai
Chapter 3 · 0% Book details