← Book details Auren Fari Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 5 OF 37

Sashe 5

Auren Fari Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Eh wallahi fitar uwani gidan nan fita fita yau, ya dafe kai wayyoooo mamee kar kija in saba miki yau ki kori yarinyar nan kada inyi kisa.....kisa????
Umaimah tayi sama da numfashi wayyo na shiga uku so takeyi ta kwace mamee ta riketa gamm, ya runtse ido da karfi,
Me ye ya hada ka da ita?
Duk barin miyar da nake zuwa miki dashi 'yar iskar yarinyar nan ce, ita ce.......dazun.... Umaimah ta zaro ido jin zai fadi ta yanka shi tace wallahi mamee shine ya fara watsa man ajiki ni bansan wanene shi ba.... Don ubanki sai kinsan wanene ni zaki mutuntani?
Ta juyo ta bayan mamee ta motsa baki yana kallo *badai ubana ba* sarai ya karanto me ta fada ya zaro ido ya yunkuro ubanme kike cewa?
Kai tsaya yaushe tayi magana?
Wai mamee menene haka yarinyar nan munafuka ce yau sai naji Wanda ya turo ta wurina.... Wazai turo ta umar?
Jikin mamee har ya fara ciwo wannan rigima, kawai sai dubara ta fado mata. Ta fara layi da kai.
Mamee calm down ki zauna karki shiga abinda babu ruwanki.
Na fita ciki kayi abinda kaga dama tunda baza ka saurari abinda zan fada maka ba, kuruciya ce kayi hakuri........ Kawai sai ya yashi fuuuu yayi sama.
Umaimah na ganin haka ta shiga neman takalmi, ina zaki je?
Kiyi hakuri mamah amma bani iya wannan aikin. Saboda baki kaunata uwani? Don kinga na kwallafa rai akanki bani da 'ya mace ganin ki nake tamkar diyata. Ni na haifi umar kina ganin duk sabanin da kuka samu zan yarda ya cuta miki ina kallo? Duk zuciyar sa dole yabi umarnin maganata.
Ki dubi girman Allah ki zauna dani kina debe mani kewa.
Idan aka wayi gari kuma na 6ace wa zai nemo ni? Ta fada a zuci, a zahiri sai kawai ta fashe da kuka wallahi mama kuskure ne.
Na sani uwani nice shaida.
Ki kwantar da hankalin ki zan lallashe shi.
Haka dai ta wuni sukuku, karfe biyar zata tafi tana ta dube duben takalmi dagowar da zatayi daga mutum tsaye kanta. Tayi saurin ja da baya, ya dalla mata harara, zuwa nayi in gargade ki , na rantse da Allah zakiyi ma mamee aiki gidan nan kamar yanda ta bukata idan kika saki ko da gigi na ganki kusa dani sai dai uwarki ta haifi wata haka zalika Qala idan kika ce dani sai kin raina kanki banson ganin ki banson jin maganar ki......ta na gama ji taci gaba da dube dube.
Ya fincikota ko bakiji ina magana?
Ta kalleshi shekeke ikon Allah ina ce kunne keji ko? Ka ce baka son in maka magana to amsar me zan baka. Ka fada naji sai ka shafan lafiya. Ko kuwa yanzu da kazo kiranka nayi nida kai waya tarad da wani..... Ya makaro wuyanta gidana kike hattara....... Yi maza kasheni inyi shahada kai kuma ka karawa kanka bala'i gata dukiya gata kisan kai... Ya ingijeta ta fadi tana tari *mugu kawai* Wanda bai iya fada da katti sai yarinya..... Ya zaburo...kai kai...... Wai umar menene haka?
Zaiyi magana umaimah ta rigashi ina duba takalmi kawai yazo yana ta zagina hada makuremun wuya ya faffalla mun mari....ban mareki ba amma yanzu.....
Ina ce mun gama maganar nan da kai ko? Na lura kafi kaunar bacin raina fiye da farin ciki don haka tunda ka nunawa duniya ban isa dakai ba kaje kayi abinda kaga dama. Ta na fadar ta juya.
Umaimah na ganin ta shige ciki ta buga tsalle ahayye a taba ni asha tsinuwar uwa ta yi mishi gwalo ta ruga.
Duk iyakar bincike yayi ya kuma sanya an mishi akan umaimah amma tabbas babu alamar abinda takeyi wani ne ya aiko ta hasali ma tatihin yarinyar mamaki ya bashi ganin wauta da kasada yarinya marar galihu haka take da *gut* na ja dashi.
Satinsa uku baya zama kullum yana yawon meeting wani ma cikin jirgi akeyin sa.
Hakan yasa umaimah ta saki jiki sosai da mamee ita kadai ke gyara mata bed room da toilet sai ta hana kowa shiga, idan ta gama malamin dake kara ta karatu yazo sai Suyi tare umaimar tafi ganewa don haka idan ya tafi ita ce ke dagewa har sai taga mamee din ta haddace, sannan suci abinci tare kafin a zauna ana labari umaimar na basu dariya da iyashegen ta.
Kowa ya fara sabawa da ita.
Mamee ta kalleta wannan sarkin rashin yardan da zaki je ki gyara mishi daki kafin ya dawo tunda ya tafi da mika'ilu ina da spare mukulli a hannu na tunda bazai gane ba sai muyi shiru da bakin mu saboda cikin sharudan da ya kindaya man ciki hada kada ki kuskura ko matattakalan benen sa kije.
Mamah tunda har yace haka yanzu idan ya dawo kwatsam fa? Daga saman zai tulloni kafin ki zo na zama gari.
Mamee ta tuntsure da dariya kai uwani hoo wai gari. Tayi murmushi Allah kuwa.
Ki barshi da kayanshi idan yazo sa gyara abinsa.
Bazaiji dadin zama nan din ba don mafi yawa idan yayi kwanaki haka to anan yake sauka baya hawa saman sai an gama gyarawa.
Da zaki fara yau zuwa gobe duk kin kammala, shiru kawai tayi ta rasa yanda zata nuna rashin amincewar ta, ungo mukullin ta karba kawai.
Dukan tara tara kirjinta ya ringa yi.
Makeken falo ta tarar daga gefen sa matattakala ce tana lekawa taga swimming pool ne zata kaika da wurin shakatawa wurin kansa abin kallo ne kujeru kala kala group group group. Ta duba dama tabi wata hanya daki ne karo kamar hall da kujeru ta tabe baki meeting akeyi anan ko? Ta dawo baya ta shiga wani daki makeken bedroom yasha kayan alatuta hango kofa ta bude tayi ma kewayen wani kallo ganin jaridu da TV ta zaro ido iyayi..... Watan idan ana kashi ana karatu ko kallo ta tuntsure da dariya tabar dakin, ai wallahi sai naga kwaf kwaf, ta fada wata hanya kayan motsa jiki ta gani ta kale wani keke Tabb ai sai nasha banza Ashe auto ne taji ankwasa da ita guje ana jijjigawa timmmm ta wuntsulo tana haki cike da tsoro ta baro wurin.
Sai kuma ta kama dariya,
Umm bari dai inyi abinda ya kawo ni. Ta shiga gyara ta dunga canza tsarin komi tana kimtsawa gyaran da ya kaita har magariba abinda ya bata tsoro bedroom dinsa durowowi ta ringa gani da kudi shirye , kasan kafet kudi wasu jakunkuna data bude kudi, tana shirin fadawa kitchen taji kiran sallah tayo kasa da sauri. Mama kada dare yayi Gobe na karasa, tana tsaya tsaya amma ina tayi gida.
Washe gari sauri sauri ta gama aikin mamee ta haye saman don ta gama da wuri, ta gyara sosai ko ina ta na yi tana korafi. Musamman kitchen da gani mugun ci gareshi ko ina ka gani kitchen da kewaye an ci ai dole ayi kashi ta bushe da dariya ta gama tsaf ta sa abin kamshi kenan hanne ta hawo da gudu uwani kiyi Sauri ga Alhaji nan inji hajiya........nan tabarta tsaye ta watsa da gudu. Tana isa gaban hajiya yana turo kofa tayi ciki da sauri bai ganta ba, hanne yabi da ido tana saukowa ya daka mata tsawa ke ubanwa kikayo sama? Ni na aiketa mamee ta katse shi.
Ya dade falon har mika'il yagama hawa da kayan ya dawo yallabai an gama. Har ka kimtsa ko ina?
Ai na tarar da kamar ma yanzu aka gama gyara wurin,
Ya watsa hannuwa mamee kenan ya haye sama, gyaran yasha ban ban da Wanda ake masa. Yayi suka bisa gado ya runtse ido yana shakar kamshin dake tashi,
Umaimah kuwa sauri sauri ta bar gidan mamee na tsaya ki taya ni kwance tsaraba tana gobe na gani har takai bakin kofa tace af ke gafa waya dazun na bada aka siyo miki saboda tsaren lalura ta buga tsalle toh tayi waje.
Tana fita ya sauko mamee wa kika sanya yayi mun gyara haka?
Ta zaro ido an maka barna ne?
Da a makaranta ne yanda nayi tambayar nan kika tambayeni punishing din ki za ayi. Kai sai kayi yanzu don kaniyarka, ya kyalkyace da dariya ban isa ba my love.
Yayi kyau kwarai naga abin wani sabo an kara gyara man dressing mirror an shirya flowers an canza ma komai tsari yayi kyau.
To madallah zan ringa sa Wanda nasa yau tunda ya maka. Ya tuno hanne tana saukowa watan ita mamee tasanya.
Ta sauya zancen da ina maganar matar da mukayi kace sai karshen watan nan? To ai yau sha hudu ga, zata kara magana wayarsa tayi kara yace ina zuwa ya haye sama.
Yau ta makara sakamakon wanki da tayi zaune suke bisa table suna kalaci ta shigo gabanta yayi mugun faduwa, ta shigo sukuku mamah ina kwana..... Ya daka mata tsawa mamar ubanwa baki ce mata hajiya yanda kowa ke fadi? .....ina ruwanka da ita? Mamee ta katse shi rai bace,
ta balla mishi harara ta wuce, ya mike wakike yiwa wannan kallo? Tayi ciki da gudu.........

*UWAR ABDALLAH*

💑 *AUREN FARI* 💑

0⃣0⃣6⃣
Chapter 5 · 0% Book details