Sashe 31
Auren Fari Part 1 Complete Hausa Novel · about 10 min read
..... Tana hango shi tayi saurin cire glasses din ta dan ja baya tare da dan bata fuska.
Ya dalla mata harara malama ba taba ki zanyi ba kwantas, ta danyi murmushi ganin har ya karanto abinda take nufi ya ruko mamee tayi saurin janye hannunta ganin yana niyyar dan shafowa.
Ta harareshi *Ni zakayima wayau?*
Zaku fara? .... Zaku fara ko sababbu?
Mamee ta fada
Yarinyar nan mamee muguwar bagidajiya ce wallahi ji yanda ta yankwana ni,
Da ta maka me?
Ya kara hararar ta ba sai ta rugo ta dan rikeni ba ko ba arzikin *Hug*....... Tooo lallai kunnenka na kashi ne, to bazatayi hakan ba.
Ya kyalkyace da dariya wasa nakeyi...... Bakinsa ya rufe ganin yan jaridu kamar an ingizo su.
Ya daga masu hannu da sauri kada su ballo mishi ruwa, *Kada Wanda ya ce wani abu* bani da wannan lokacin suka wuce.
mamee ta fara salati da sallallami. Ganin yanda gida ya koma, suna shiga falo ta yi turus!!, daman bai shigo ba ya dan tsaya waje da wasu baki.
Aka fara shigowa da jakunkunan su ana wucewa dasu daki.
Ya shigo da sauri mamee wai wadannan iyayen jakun kunan na menene kuka kwaso?
Ta nuna umaimah gata nan bacin na mata magana kilan da ta rungumo makka ko madina wannan da kake gani.
Ya tun tsure da dariya abu yazo ga ma iya.
An dawo lafiya?
Darling welcome....... Mamee ta wuce ciki tana kwakwazo, wai duk yaushe aka yi aikin?sati ukun da bama nan?
Umaimah ta dan zauna ya zo gaban ta ya zukunna. Wallahi kin canza kinyi kyau umaimah anya zan zauna da ke Nigeria? Wannan fatar bata nan kasar ce ba..... Ta danyi murmushi , mun sameku lafiya?
Ya mike ya zauna kusa da ita, ke ba lafiya lau ba na galabaita wallahi.
Ta danyi dariya, a hakan?
Ya harareta kawai. Ina tsarabata?
Kai ciwon ciki ..... Ka daiyi hakuri ko ruwa in sha ko?
Ya kyalkyace da dariya ni ne ciwon cikin? Gaskiya je ki kawon tsarabata.
Ta ce hummm,
Kinji?
Wai baka bari na in huta?
Aikin me kikayi?
Wallahi kamar an mun tsinannen duka,
Yayi yar dariya wane hutu gareki yanzu?
Bani da shi? Ta bukata tana murmushi. Ya mike tsaye don idan ya saki bai tashi ba sai yayi halin, nidai jeki dauko mun ina jiranki sama.
Zatayi magana kawai ya wuce yana fadin *Ina jiranki*
Kai *Rigimar duniya* ta fada tare da mikewa tayi ciki.
Ta iske mamee tsaye, itama tayi turus!
Uwani kinga gyara?
Ta washe baki, wallahi mamee gidan nan yayi kyau kamar ba shi ba.
Kin dai gani, ai idan madaki yasa kansa abu baya shawara, kina tunanin idan ina nan zan bari yayi wannan almubazzarancin, shine ya koramu yayi bikin kansa.
Umaimah tayi dariya kuma gyaran ya tsaru,
Ta dan kalleta ya yi kyau ma sosai. Ya na ina?
Gashi can ya hau sama wai lallai in kai mishi tsarabar sa.
Sai ki hanzarta ai, neman rigima ce kawai mamin ta shige toilet.
Jakun kuna 3 ne nashi biyu turaruka daya jallabiyoyi da agoguna.
Ta kirawo sadisu ya taimaka mata da na turarukan ita kuma taja na jallabiyoyin.
Yana zaune falo. Yanzu ya daina bari su hadu bedroom din sa, ya bita da kallo, yana ajiyewa ya juya ta dan karasa dana hannunta gabanshi gasu nan.
Ya kalleta lefe kika hado man?
Ta kyalkyace da dariya a'a ka manta *Aure* ya tashi da sauri ya janyo jakunkuna ya fara budawa.
Yayi shiruuuuu , ya kalleta don Allah zauna umaimah. Sannan ya janyo wacce ta riko ya buda jallabiyoyin ma basu da yawa don basu wuce kwara goma ba agogunan ne suka dauki hankalinsa fiye da turarukan.
Ya durkusa gabanta, umaimah: *This gift you gave me was more than perfect in each and every way. Thank you so much for it. I will always preserve and keep it with me forever.* thank you so much my love.
Kun ya ta baibayeta ni dai tashi don Allah.
Ya akayi kika San duniya nafi kaunar turare da agogo?
Na sani mana, ta fada tana wasa da yatsun hannunta. Umaimah ka kira sunanta duk ya rikice, kina azumi? Gabanta ya fadi *Nashiga uku* ko ya gane banayi?
Me zai hanani azumi? Ta harareshi, yayi murmushi in tambayeki zaki ban amsa?
Um, idan ina da amsar zan baka, ta dan kalleshi kadan duk ya diririce,
Ki taimaka man ki aureni umaimah wallahi bani iya hakurin rashin ki, a duk lokacin da kike kusa dani sai inji ina neman fita hayyacina, ranar da duk na wuni ban ganki ba kuwa zan kasa sarrafa kaina in nemi haukacewa.......
Haba dai, Allah na amince da kai kasan haka kuma,
Ki tausaya man, na miki alkawari wallahi zan barki ki karasa karatun ki believe me,
Shi kenan, ta ce a takaice.
Ya mike zo muje ki gani..... Ya fara zagayawa da ita tsarin duk ya canza banda dakin sa ya kara gyara wani an zuba sabbin kayan daki masu launin *White and pink* ta dan saci kallon sa taga ya zuba mata ido...... Ta dan sunkuyar da kai.
Ko bai miki kyau ba?
Ya yi mana!, suka zagaya ta baya dakuna biyu ne na yara daya komai da ke cikin dakin sky blue and white ne,
Daya kuma komai na dakin dark and light pupple.
Ga dakin yaran mu maza daban....... Ta fice kawai ya biyota kin fito ko bai miki ba a canza tsarin?
Ta kalleshi da kyau *Yau me ke damunka ?*
Kaunar ki, umaimah sonki me Neman zautani .
Ka barni na je na huta na gaji........... Ya langabe kai anya kinyi missing dina umaimah? Tayi murmushi nayi mana........ Maganar mamee yajiyo tana kwala mishi kira itama ta hawk saman.
Ta gansu tsaitsaye, kai kuwa akwai fitinannen yaro bazaka barta ta huta ba?
Zaiyi magana idanunta suka kai ga jakunkunan tsarabar umaimah.Ta rike baki *Au daman duk kai ta jibgowa wadannan turarukan?*
Sai kawai umaimar tayi kasa da gudu.
Ta bita da kallo kya gudu ja'ira. Uwani taki ci taki tsinana ma kanta uwar komai kullum ta fita sai ta dawo da turaruka ko agogo.
Ya yi murmushi miji ake ma tsaraba mamee, ta dalla mishi harara kai dai wallahi baka San annabi ya faku ba.
Ya kyalkyace da dariya, suka fara zagayawa, mamee kamar ta goya shi.
Suka dawo falon sa, naga akwatuna dakina set biyu.
Ya ce au zo muje kiga lefe.
Wancen naki ne...... Nawa ne me? Kana hauka nima lefen zakayi mun? Zata fara fada ya rungumota haba mamee love haka zaki ci bikin ba dinkuna?
Ta harareshi kana dai son kara janyo mun zagi gurin su yaya ko?
Kin San kuwa tazo..... Ya fada mata wulakancin da ta zazzaga. Tayi murmushi kawai ta ce *Uhumm*
Kai Allah ya saka ma da alkhairi *madaki* Allah ya baku zuri'a dayyiba. Wallahi duk abinda kayi ma uwani ta cancanci fiye da haka ta bashi labarin kyautatawar da tayi mata saudiyya tana kara fada mishi kyawawan dabi'un ta.
Addu'a takeyi yana ta faman *Amin mamee*
Ta kalleshi don Allah na sanka da saurin daukar zafi kamar wutar murhu madaki ka sanya ma ranka hakuri ga zaman aurenku.
Har yanzu uwani yarinya ce kada ka biye mata kuyi ta yarinta don Allah ka bada mamaki.
Zanyi mamee trust me.
Kamata yayi tunda saura sati daya gobe ta shirya ta koma gida saboda suma a basu daman shirye shirye kuma can su sanar da ita.
Nidai mamee da kin kyaleta nan sai ana gobe daurin aure?
Ta mike saboda kana mahaukaci ko?
Ya marairaice don Allah kitaimaka man mamee , ta wuce ma tabarshi wurin tana fadin abin naka ya wuce mizani.
Ta iske daki tana da yan gyare gyare , to agogo aikin ne?
Ta danyi dariya kai mamee.
Ta zauna bakin gado.
Na wuto su Mansurah nata tsalle kin cika su da tsaraba. Allah ya biya.
Amin mamee, ta fada tana mamakin Yanda suke mata godiya kuma fa duk abinnan daga garesu ya fito.
Kaii samun mutane irin su mamee yanzu wallahi sai anyi da gaske, shi madakin duk ya rikice wai saboda tsaraba, shi fa ya biya mana, kaii wadannan mutane hoo.
Uwani na ce zuwa gobe sai ki tafi gida ki kai masu tasu tsarabar kidan kwana biyu sai ki dawo ko kuwa?
Ta fadada fara'ar ta eh wallahi mamee.
Ta kalleta uwani kenan? Duk muzgunawar da ake miki gidan Ku Har yau baki taba gajiya dasu ba baki taba gudun su ba. Kai halinki na da wahalar samu.
Ta danyi dariya kai mamee.
Kusan yanzu idan suna magana kusan amsarta kenan tace *Kai mamee*
Saboda gajiya da wuri ta kwanta shi kuwa har kusan biyu saura yana tare da mamee suna ta tsara yanda za ayi.
Da safe ta shirya wajen karfe goma mamee ta kara mata tsaraba sosai.
Kamar mamee ta sani ta ce kinga uwani ki sadada *Haruna* ya kaiki kawai don madaki na fitowa wallahi baki tafiya yanzu.
Ta mike tana dariya. Har sai da taga sun tafi sannan ta shigo tana tausayin umaimar saboda zata dawo gidan a matsayin *Mata*
Tana shiga yana kokarin saukowa ya kalleta cikin zolaya ina aka fito hajiya mamee?
Ya dora hannu bisa kai *Qalu innalillahi wa'inna ilaihi raji'un* amma mamee kin gama dani yau.
Ya zauna da karfi idanun sa sun kada sunyi jawur, yarinyar tayi sati uku bata nan jiya kiri kiri kika ce na kyaleta ta huta kuma yau tunda safe ki harba ta gida?
Au harbata ma nayi?
Yayi shiru, ya fiddo waya ya kira Haruna, amma yace mishi har ya ajiyeta ya juyo, ya dafe kai, duk sai jikin mamin yayi sanyi kuma don ransa ya baci sosai.
Kai da sati mai zuwa za a maido maka ita a baka har abada?
Ya daiyi shiru,
Yarinyar nan ta tsargu wallahi bana son ta gane nafi son iyayenta su fada mata..... Na sani mamee amma da sai ki tausaya mun ko kirana kiyi muyi bankwana.
Yanzu idan aka sanar da ita ta birkice fa? Ko zan shawo kanta fa sai idan ta zo gidan nan kin sani.
In shaa Allah hakan bazata faru ba ka kwantar da hankalinka.
Ya mike ya fice yana kumbure kumbure.
Abu yazo ga ma'iya ni *Rabi* ta fada tana rike baki.
Umaimah kuwa Sam bata gane gidan su ba, hada *Gate* sai da ta kalla sosai ta runtse ido ta bude tabbas ba gizo idanun ke mata ba,
Murna tsalle, gida ya rikice yan unguwa kafin kace me, sun cika gida ana kallon umaimah.
Ita dai sai dariya takeyi. Abinda yake daure mata kai kowa ya shigo amarya amarya.
Sai da komai ya lafa ta fiddo ma kowa tsaraba sannan aka kukkulla ta makota.
Malam bawa ya shigo yana ta washe baki ya shige dakin sa ya ce a kira mishi umaimar.
Ta dauki ledojin tsarabar sa ta tafi.
Suka gaisa ta dan bashi labari da wasu abubuwan da suka faru na kyautatawar.
Ya ce Alhamdulillah, Ai Alhajin yazo munje har kauye. Tayi murmushi ai haka naji, ta fada mishi yanda akayi lokacin.
Ya danyi dariya ai ya ce yana tsoron kada ki tayar da hankalinki.
Kin tabbatar kina son sa umaimah kada kisa kwadayi da son abin duniya ki dubi maraicin ki da mutuncin ki. Kina son sa?
Ta danyi murmushi.
Ya kara cewa kada kiji kunya ko nauyi idan bai miki ba kiyi magana.
Ta kara murmushi.
Ya fadada fara'ar sa masha Allah.
To abinda nake so da ke don girman Allah ki sanya ma ranki hakuri kada ki tayar da hankalinki, yayi alkawarin zai barki kiyi karatun da kike so...... Gabanta ya fadi . Wai ya akayi ,ne? Ta tambayi zuciyarta.
Kamar ya karanto tambayar sai ya ce, Ya turo iyayen sa, munje kauye an yi magana kinga dai dawainiyar da yake tayi kinga gida kinga dakunan iyayenki jibi nawa, don Allah kada ki bamu kunya.
Ranar sallah za a daura auren ki dashi.......ta dago ido cikin tsoro baba ranar sallah kuma? Sai ta fashe da kuka.
Ya bata fuska to uwaki za a jira? Au na baki hakuri shine zaki tayar da hankalin naki?
Ni dai baba a bari sai nan gaba duka nawa nake....... Yaro ba mutum ba . amma umaimah kin tabbata sakarai.
Yayi kasa da murya ni zaki kunyata ki tona ma asiri saboda ko habaici ya isheni gidan nan ga shi kinzo kuma zaki kara janyo mun wata maganar. Dama suna fadin asiri akayi daman tallar ki muka kai sun manta lokacin da kika sami aikin ma bakin su na ji.
Ta ci gaba da kuka kawai duk hankalinta ya tashi, sallamar hajiya ta jiyo har zata mike ya ce zauna ta shigo nan.
Hakan kuwa akayi suka taru suna kwatanta mata tare da kwantar mata da hankali saboda ita kanta hajiyar madakin yaje har gida ya sameta.
Ta wuni kwance daki tana kuka saboda shi kanshi dakin an gyara masu shi sosai don yasan zata dan zauna na kwana biyu.
Karfe takwas yazo, har ciki ya shigo ta dan tashi zaune kanta kasa, fuskarta tayi jawur tasha kuka har ta bani.
Hankalin sa ya tashi ya karasa kusa da ita ya zauna *Umaimah kuka kikayi haka?* ..... Kamar ya zugata wasu hawayen suka zubo *Sharrrrrrrrr*...............
Ya dalla mata harara malama ba taba ki zanyi ba kwantas, ta danyi murmushi ganin har ya karanto abinda take nufi ya ruko mamee tayi saurin janye hannunta ganin yana niyyar dan shafowa.
Ta harareshi *Ni zakayima wayau?*
Zaku fara? .... Zaku fara ko sababbu?
Mamee ta fada
Yarinyar nan mamee muguwar bagidajiya ce wallahi ji yanda ta yankwana ni,
Da ta maka me?
Ya kara hararar ta ba sai ta rugo ta dan rikeni ba ko ba arzikin *Hug*....... Tooo lallai kunnenka na kashi ne, to bazatayi hakan ba.
Ya kyalkyace da dariya wasa nakeyi...... Bakinsa ya rufe ganin yan jaridu kamar an ingizo su.
Ya daga masu hannu da sauri kada su ballo mishi ruwa, *Kada Wanda ya ce wani abu* bani da wannan lokacin suka wuce.
mamee ta fara salati da sallallami. Ganin yanda gida ya koma, suna shiga falo ta yi turus!!, daman bai shigo ba ya dan tsaya waje da wasu baki.
Aka fara shigowa da jakunkunan su ana wucewa dasu daki.
Ya shigo da sauri mamee wai wadannan iyayen jakun kunan na menene kuka kwaso?
Ta nuna umaimah gata nan bacin na mata magana kilan da ta rungumo makka ko madina wannan da kake gani.
Ya tun tsure da dariya abu yazo ga ma iya.
An dawo lafiya?
Darling welcome....... Mamee ta wuce ciki tana kwakwazo, wai duk yaushe aka yi aikin?sati ukun da bama nan?
Umaimah ta dan zauna ya zo gaban ta ya zukunna. Wallahi kin canza kinyi kyau umaimah anya zan zauna da ke Nigeria? Wannan fatar bata nan kasar ce ba..... Ta danyi murmushi , mun sameku lafiya?
Ya mike ya zauna kusa da ita, ke ba lafiya lau ba na galabaita wallahi.
Ta danyi dariya, a hakan?
Ya harareta kawai. Ina tsarabata?
Kai ciwon ciki ..... Ka daiyi hakuri ko ruwa in sha ko?
Ya kyalkyace da dariya ni ne ciwon cikin? Gaskiya je ki kawon tsarabata.
Ta ce hummm,
Kinji?
Wai baka bari na in huta?
Aikin me kikayi?
Wallahi kamar an mun tsinannen duka,
Yayi yar dariya wane hutu gareki yanzu?
Bani da shi? Ta bukata tana murmushi. Ya mike tsaye don idan ya saki bai tashi ba sai yayi halin, nidai jeki dauko mun ina jiranki sama.
Zatayi magana kawai ya wuce yana fadin *Ina jiranki*
Kai *Rigimar duniya* ta fada tare da mikewa tayi ciki.
Ta iske mamee tsaye, itama tayi turus!
Uwani kinga gyara?
Ta washe baki, wallahi mamee gidan nan yayi kyau kamar ba shi ba.
Kin dai gani, ai idan madaki yasa kansa abu baya shawara, kina tunanin idan ina nan zan bari yayi wannan almubazzarancin, shine ya koramu yayi bikin kansa.
Umaimah tayi dariya kuma gyaran ya tsaru,
Ta dan kalleta ya yi kyau ma sosai. Ya na ina?
Gashi can ya hau sama wai lallai in kai mishi tsarabar sa.
Sai ki hanzarta ai, neman rigima ce kawai mamin ta shige toilet.
Jakun kuna 3 ne nashi biyu turaruka daya jallabiyoyi da agoguna.
Ta kirawo sadisu ya taimaka mata da na turarukan ita kuma taja na jallabiyoyin.
Yana zaune falo. Yanzu ya daina bari su hadu bedroom din sa, ya bita da kallo, yana ajiyewa ya juya ta dan karasa dana hannunta gabanshi gasu nan.
Ya kalleta lefe kika hado man?
Ta kyalkyace da dariya a'a ka manta *Aure* ya tashi da sauri ya janyo jakunkuna ya fara budawa.
Yayi shiruuuuu , ya kalleta don Allah zauna umaimah. Sannan ya janyo wacce ta riko ya buda jallabiyoyin ma basu da yawa don basu wuce kwara goma ba agogunan ne suka dauki hankalinsa fiye da turarukan.
Ya durkusa gabanta, umaimah: *This gift you gave me was more than perfect in each and every way. Thank you so much for it. I will always preserve and keep it with me forever.* thank you so much my love.
Kun ya ta baibayeta ni dai tashi don Allah.
Ya akayi kika San duniya nafi kaunar turare da agogo?
Na sani mana, ta fada tana wasa da yatsun hannunta. Umaimah ka kira sunanta duk ya rikice, kina azumi? Gabanta ya fadi *Nashiga uku* ko ya gane banayi?
Me zai hanani azumi? Ta harareshi, yayi murmushi in tambayeki zaki ban amsa?
Um, idan ina da amsar zan baka, ta dan kalleshi kadan duk ya diririce,
Ki taimaka man ki aureni umaimah wallahi bani iya hakurin rashin ki, a duk lokacin da kike kusa dani sai inji ina neman fita hayyacina, ranar da duk na wuni ban ganki ba kuwa zan kasa sarrafa kaina in nemi haukacewa.......
Haba dai, Allah na amince da kai kasan haka kuma,
Ki tausaya man, na miki alkawari wallahi zan barki ki karasa karatun ki believe me,
Shi kenan, ta ce a takaice.
Ya mike zo muje ki gani..... Ya fara zagayawa da ita tsarin duk ya canza banda dakin sa ya kara gyara wani an zuba sabbin kayan daki masu launin *White and pink* ta dan saci kallon sa taga ya zuba mata ido...... Ta dan sunkuyar da kai.
Ko bai miki kyau ba?
Ya yi mana!, suka zagaya ta baya dakuna biyu ne na yara daya komai da ke cikin dakin sky blue and white ne,
Daya kuma komai na dakin dark and light pupple.
Ga dakin yaran mu maza daban....... Ta fice kawai ya biyota kin fito ko bai miki ba a canza tsarin?
Ta kalleshi da kyau *Yau me ke damunka ?*
Kaunar ki, umaimah sonki me Neman zautani .
Ka barni na je na huta na gaji........... Ya langabe kai anya kinyi missing dina umaimah? Tayi murmushi nayi mana........ Maganar mamee yajiyo tana kwala mishi kira itama ta hawk saman.
Ta gansu tsaitsaye, kai kuwa akwai fitinannen yaro bazaka barta ta huta ba?
Zaiyi magana idanunta suka kai ga jakunkunan tsarabar umaimah.Ta rike baki *Au daman duk kai ta jibgowa wadannan turarukan?*
Sai kawai umaimar tayi kasa da gudu.
Ta bita da kallo kya gudu ja'ira. Uwani taki ci taki tsinana ma kanta uwar komai kullum ta fita sai ta dawo da turaruka ko agogo.
Ya yi murmushi miji ake ma tsaraba mamee, ta dalla mishi harara kai dai wallahi baka San annabi ya faku ba.
Ya kyalkyace da dariya, suka fara zagayawa, mamee kamar ta goya shi.
Suka dawo falon sa, naga akwatuna dakina set biyu.
Ya ce au zo muje kiga lefe.
Wancen naki ne...... Nawa ne me? Kana hauka nima lefen zakayi mun? Zata fara fada ya rungumota haba mamee love haka zaki ci bikin ba dinkuna?
Ta harareshi kana dai son kara janyo mun zagi gurin su yaya ko?
Kin San kuwa tazo..... Ya fada mata wulakancin da ta zazzaga. Tayi murmushi kawai ta ce *Uhumm*
Kai Allah ya saka ma da alkhairi *madaki* Allah ya baku zuri'a dayyiba. Wallahi duk abinda kayi ma uwani ta cancanci fiye da haka ta bashi labarin kyautatawar da tayi mata saudiyya tana kara fada mishi kyawawan dabi'un ta.
Addu'a takeyi yana ta faman *Amin mamee*
Ta kalleshi don Allah na sanka da saurin daukar zafi kamar wutar murhu madaki ka sanya ma ranka hakuri ga zaman aurenku.
Har yanzu uwani yarinya ce kada ka biye mata kuyi ta yarinta don Allah ka bada mamaki.
Zanyi mamee trust me.
Kamata yayi tunda saura sati daya gobe ta shirya ta koma gida saboda suma a basu daman shirye shirye kuma can su sanar da ita.
Nidai mamee da kin kyaleta nan sai ana gobe daurin aure?
Ta mike saboda kana mahaukaci ko?
Ya marairaice don Allah kitaimaka man mamee , ta wuce ma tabarshi wurin tana fadin abin naka ya wuce mizani.
Ta iske daki tana da yan gyare gyare , to agogo aikin ne?
Ta danyi dariya kai mamee.
Ta zauna bakin gado.
Na wuto su Mansurah nata tsalle kin cika su da tsaraba. Allah ya biya.
Amin mamee, ta fada tana mamakin Yanda suke mata godiya kuma fa duk abinnan daga garesu ya fito.
Kaii samun mutane irin su mamee yanzu wallahi sai anyi da gaske, shi madakin duk ya rikice wai saboda tsaraba, shi fa ya biya mana, kaii wadannan mutane hoo.
Uwani na ce zuwa gobe sai ki tafi gida ki kai masu tasu tsarabar kidan kwana biyu sai ki dawo ko kuwa?
Ta fadada fara'ar ta eh wallahi mamee.
Ta kalleta uwani kenan? Duk muzgunawar da ake miki gidan Ku Har yau baki taba gajiya dasu ba baki taba gudun su ba. Kai halinki na da wahalar samu.
Ta danyi dariya kai mamee.
Kusan yanzu idan suna magana kusan amsarta kenan tace *Kai mamee*
Saboda gajiya da wuri ta kwanta shi kuwa har kusan biyu saura yana tare da mamee suna ta tsara yanda za ayi.
Da safe ta shirya wajen karfe goma mamee ta kara mata tsaraba sosai.
Kamar mamee ta sani ta ce kinga uwani ki sadada *Haruna* ya kaiki kawai don madaki na fitowa wallahi baki tafiya yanzu.
Ta mike tana dariya. Har sai da taga sun tafi sannan ta shigo tana tausayin umaimar saboda zata dawo gidan a matsayin *Mata*
Tana shiga yana kokarin saukowa ya kalleta cikin zolaya ina aka fito hajiya mamee?
Ya dora hannu bisa kai *Qalu innalillahi wa'inna ilaihi raji'un* amma mamee kin gama dani yau.
Ya zauna da karfi idanun sa sun kada sunyi jawur, yarinyar tayi sati uku bata nan jiya kiri kiri kika ce na kyaleta ta huta kuma yau tunda safe ki harba ta gida?
Au harbata ma nayi?
Yayi shiru, ya fiddo waya ya kira Haruna, amma yace mishi har ya ajiyeta ya juyo, ya dafe kai, duk sai jikin mamin yayi sanyi kuma don ransa ya baci sosai.
Kai da sati mai zuwa za a maido maka ita a baka har abada?
Ya daiyi shiru,
Yarinyar nan ta tsargu wallahi bana son ta gane nafi son iyayenta su fada mata..... Na sani mamee amma da sai ki tausaya mun ko kirana kiyi muyi bankwana.
Yanzu idan aka sanar da ita ta birkice fa? Ko zan shawo kanta fa sai idan ta zo gidan nan kin sani.
In shaa Allah hakan bazata faru ba ka kwantar da hankalinka.
Ya mike ya fice yana kumbure kumbure.
Abu yazo ga ma'iya ni *Rabi* ta fada tana rike baki.
Umaimah kuwa Sam bata gane gidan su ba, hada *Gate* sai da ta kalla sosai ta runtse ido ta bude tabbas ba gizo idanun ke mata ba,
Murna tsalle, gida ya rikice yan unguwa kafin kace me, sun cika gida ana kallon umaimah.
Ita dai sai dariya takeyi. Abinda yake daure mata kai kowa ya shigo amarya amarya.
Sai da komai ya lafa ta fiddo ma kowa tsaraba sannan aka kukkulla ta makota.
Malam bawa ya shigo yana ta washe baki ya shige dakin sa ya ce a kira mishi umaimar.
Ta dauki ledojin tsarabar sa ta tafi.
Suka gaisa ta dan bashi labari da wasu abubuwan da suka faru na kyautatawar.
Ya ce Alhamdulillah, Ai Alhajin yazo munje har kauye. Tayi murmushi ai haka naji, ta fada mishi yanda akayi lokacin.
Ya danyi dariya ai ya ce yana tsoron kada ki tayar da hankalinki.
Kin tabbatar kina son sa umaimah kada kisa kwadayi da son abin duniya ki dubi maraicin ki da mutuncin ki. Kina son sa?
Ta danyi murmushi.
Ya kara cewa kada kiji kunya ko nauyi idan bai miki ba kiyi magana.
Ta kara murmushi.
Ya fadada fara'ar sa masha Allah.
To abinda nake so da ke don girman Allah ki sanya ma ranki hakuri kada ki tayar da hankalinki, yayi alkawarin zai barki kiyi karatun da kike so...... Gabanta ya fadi . Wai ya akayi ,ne? Ta tambayi zuciyarta.
Kamar ya karanto tambayar sai ya ce, Ya turo iyayen sa, munje kauye an yi magana kinga dai dawainiyar da yake tayi kinga gida kinga dakunan iyayenki jibi nawa, don Allah kada ki bamu kunya.
Ranar sallah za a daura auren ki dashi.......ta dago ido cikin tsoro baba ranar sallah kuma? Sai ta fashe da kuka.
Ya bata fuska to uwaki za a jira? Au na baki hakuri shine zaki tayar da hankalin naki?
Ni dai baba a bari sai nan gaba duka nawa nake....... Yaro ba mutum ba . amma umaimah kin tabbata sakarai.
Yayi kasa da murya ni zaki kunyata ki tona ma asiri saboda ko habaici ya isheni gidan nan ga shi kinzo kuma zaki kara janyo mun wata maganar. Dama suna fadin asiri akayi daman tallar ki muka kai sun manta lokacin da kika sami aikin ma bakin su na ji.
Ta ci gaba da kuka kawai duk hankalinta ya tashi, sallamar hajiya ta jiyo har zata mike ya ce zauna ta shigo nan.
Hakan kuwa akayi suka taru suna kwatanta mata tare da kwantar mata da hankali saboda ita kanta hajiyar madakin yaje har gida ya sameta.
Ta wuni kwance daki tana kuka saboda shi kanshi dakin an gyara masu shi sosai don yasan zata dan zauna na kwana biyu.
Karfe takwas yazo, har ciki ya shigo ta dan tashi zaune kanta kasa, fuskarta tayi jawur tasha kuka har ta bani.
Hankalin sa ya tashi ya karasa kusa da ita ya zauna *Umaimah kuka kikayi haka?* ..... Kamar ya zugata wasu hawayen suka zubo *Sharrrrrrrrr*...............