Sashe 8
African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals · about 8 min read
Tayi shiru tana sharar kwallah,kowannensu jiki yayi sanyi na tuno abubuwan daya shud'e a rayuwarsu. Baby daga kwance itama hankalinta taji ya tashi,babu wacce ta tsaya a ranta kamar mahaifiyarta. Taji gaba daya tanason taje duba lafiyarta. Manal ta share hawaye ta mike
"Yan iska zaku tunomin bakin labarin rayuwata,ku tashi muje shan ice cream. Yau jakata a cike take."
Sukayi murmushi don babu wacce keda kuzarin dariya,Manal ta dubi Baby.
"Zakije ne?"
Baby ta girgiza kai
"Banajin fita ne."
Sun lura jikinta yayi sanyi, tausayinta ya mamayesu musamman ma Manal wacce anan duniya ita kadai tasan wacece Baby Tasneem. Ita kadai tasan tarihin rayuwarta. Don kafin ta hadu da kowacce cikinsu,Baby tasleem ta soma haduwa da ita harma ta sauketa a gidanta. Haka suka fice suka barta a gidan. A ranar Baby taci kuka sosai,ba don komai ba sai don rashin sanin halin da mahaifiyarta ke ciki. Karshe ta mike ta shiga daki ta kwanta ba don tanajin bacci ba. Sai don kawai tunanin rayuwarta.
*****
KWANA HUDU BAYAN HAKA
Tafiya takeyi da baya da baya tana kallonta,yayinda ita kuwa ke kwance duk fuskarta ya baci da kuraje,hannu take miko mata alamun tsayar da ita tana ihun kuka
"Ya d'iyata,kada ki gujeni! Karki barni cikin wannan halin! Ki dawo gareni!"
Maimakon ta dawo,sai ta juya a guje zata tafi, karar da taji uwar tayi ya sanyata itama kwala ihu kafin tayi wuf ta fada wata rijiya a wajen."
A tsananin firgici Baby ta tashi sakamakon wannan mafarki mai rud'arwa,gumi ya wanke fuskarta duk da Ac dake a kunne. Sai haki takeyi tamkar wacce tayi gudu. Ta sanya hannu ta dafe kirjinta dake dukan uku uku. Can kuma tayi wuf ta sauko daga gadon. Wani d'an karamin akwati ta dauko ta bud'e. Hoto ne a cikin (envelope),nan da nan ta zaro tana duba. Dattijuwa ce tare da yarinya mai shekaru uku,sai dan saurayi mai kimanin shekaru goma sha daya a hoton. Dukkansu suna dariya.
Ta rungume hoton a kirjinta yayinda hawayenta suka karu. Tausayin kanta ya dabaibayeta,taji nan duniya bata sha'awar komai daya wuce na zuwa kauye ganin Mahaifiyarta. Tun hirar da sukayi tare dasu Manal,hankalinta yake a tashe. Ta amince bazata taba samun nutsuwa ba har sai ta dangana ga duba lafiyar mahaifiyarta.
******
Karfe goma na safiyar Asabar,ya shirya tsaf cikin kananun kaya ya feshe jikinsa da turaruka. Bai dauki komai ba sai karamin trolley dinsa inda ya shirya kayan sawarsa. Saida ya soma zuwa gidansu yayi sallama da Daddy,kafin yaje gidan Abba. Nan ma yayi musu sallama,mahaifiyarsa ta bashi sako a kaiwa uwarta,wato kakarsa. Daga haka ya kama hanya.
******
Zaune suke suna karyawa,basu ankara ba suka ganta ta fito tana jan akwati. Ba jan akwatin ne yafi basu mamaki ba,tunda sun saba tafiye tafiyensu. Shigar dake jikinta ne ya burgesu kuma ya basu mamaki. Doguwar rigar atamfa ce, anyi mata dogon hannu three quarter,maimakon ta dora dankwalin saita yafa karamin mayafin (pashmina) a kanta. Saida tazo kusa dasu sannan ta dubesu fuskarta babu wata kwalliya ta daukar ido sai hoda da jan baki mai kalar ruwan hoda(pink).
"Zanyi 'yar tafiya ne,amma in sha Allah bazata wuce kwana uku ba. Amanar gidana yana hannunki sister."
Ta dubi Manal. Murmushi manal tayi kafin tace
"Karki samu damuwa baby,shigarki tayi mana kyau,tamkar bake ba."
Tayi murmushi batace komai ba ta nufi waje. Babu wata wata,ta fada motarta ta shiga. Duk da dai bata taba karambanin tuk'i mai nisa ba,yau kam tanason yi. Dole taje ga mahaifiyarta ta duba lafiyarta. Tsananin kewarta yana neman hanata sukuni,ga fargabar abunda zata tarar sskamakon mafarkin da tayi a daren jiya......!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(19)
Tafe take kawai saidai dukkan hankali da tunaninta yana ga zantukan karshe da tayi da mahaifiyarta kafin su rabu.
"Na sanki,yarinya kike mai basira da kula dakai. Kada ki sake ki bari shaidan yayi maki hud'uba Tasleem. Kibi matar ubanki sau da k'afa,kiyi biyayya ga mahaifinki kada ki sanya damuwar komai a ranki. Allah Yana tare dake."
Hawayenta suka k'aru,yayin data k'ara karfin gudunta.
"Fitarmin daga gida,yar iskar yarinya! Kin bata wayonki! Bazaki zo ki b'atamin tarbiyyar yarana ba! Shegiya! Kedai kam ina kwakwanto akanki! Anya nine ubanki?!"
A zuciye ta kuma k'ara karfin speed dinta,hawaye bai bar kwaranyo mata ba.
"Kin bani mamaki kanwata,kin bata wayonki. Har da kanki ki dunga kai kanki dakin namiji?!! Tirr da wannan d'abi'a taki. Toh wallahi ki barmin gidana,kuma kika kuskura kikaje ga mahaifiyarmu kika kashe aurenta,wallahi saikin raina kanki! Kije duniya ce! Daidai take da kowa!"
A fusace take tafiya,bata ankara ba,motar ta kufce mata, ta rasa yanda zatayi ta tsayar da ita. Taka burki takeyi saidai batasan dalilin cijewar burkin ba,haka tayita wala wala har ta k'umu da bishiya. Bata k'ara sanin duniyar da take ba.
******
Farkawa tayi ta ganta kwance a gadon da yafi kama dana asibiti,ta tsurawa rub'abb'en kwanon silin din ido tana duba,hannunta tayi kokarin d'agawa da niyyar tab'a goshinta wanda ke sarawa tamkar zai fad'o saidai wani irin azaba da hannunta yayi ya sanyata cije lebbanta tana 'yar k'ara kad'an.
Wannan ya jawo hankalinsa,yana zaune saman gadon dake fuskantarta yana danne wayarsa a kokarinsa na kiran gida domin kada a jishi shiru ayi tsammanin ko babu lafiya. Ya dubeta,nan da nan zuciyarsa tayi sanyi ya mike ya karaso wajen kanta
"Sannu,ya jikin?"
Ta waiwayo dakyar sakamakon ciwon kan da takeji ya addabeta,ido kawai ta zuba mishi ba tare da tace komai ba. A zuciyarta mamaki kawai takeyi,meyasa Allah Yake yawan kawo mata shi aduk lokacin da take da buk'atar taimako? Abun tambayar ma shine,ya akayi yazo nan?
Kafin ta kammala tunaninta tuni ya juya ya fita. Minti daya sai gashi da likita,likitan ya karaso yayi mata gwaje gwaje kafin ya dubeta yana murmushi
"Sannu fa madam,yanzu meke damunki bayan hannunki? Kina jin wani ciwo daban ne?"
Baby ta k'ak'alo murmushi kafin ta d'aga hannu ta dafe kanta.
"Oh sorry,bari na sanya nos ta k'ara baki magungunanki. A sannu zai daina. Saidai kafin nan..."
Ya juya yana dubansa
"A samo mata abunda zata ci don bana zaton taci wani abu a yau."
Ya dubi Baby wacce tayi tsai da ido tana kallonsa,fuskarta babu yabo ba fallasa kamar dai wani tunanin na daban takeyi. Ya dauke kansa ya maida ga likita yana mai gyada mishi kai.
Likitan yana fita yabi bayanshi ba tare da yace mata uffan ba. Ta bishi da kallo sannan ta kauda kanta tana tuna abunda ya janyo mata hatsarin. Hawaye suka gangaro saman kuncinta,ko kusa batayi yunkurin sharesu ba,saima ta barsu suka cigaba da shatata.
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(20)
Haka har ya dawo ya sameta cikin wannan yanayin. Shigowar baisa ta sharesu ba,a zahiri ma sam batasan da wanzuwarsa ba. Lura da cewar ko kusa batasan da shigowarsa bane da kuma sallamarsa,yasa shi yin magana
"Tasleem."
Batasan lokacin data dubeshi ba,haka kawai sanyi ya ratsa zuciyarta domin tunda take bata tab'a jin wanda ya iya kiran sunanta ba kamarsa. Ya kauda kansa yana mai bude ledojin,fuskarsa a daure
"Tashi ki d'an ci wannan."
Ta mike dakyar ta zauna bayan ta sauke kafafuwanta dake ciwo kadan kadan a k'asa. Batace dashi komai ba ta mike tana dafe gado,band'aki ta zagaya. Can kuma sai gata ta fito.
"Ko zaka taimakamin da brush da maclean please?"
Ya mike ya fita, sai gashi ya dawo dauke dasu sabbi. Saida ta tabbatar da tsaftar bakinta sannan ta fito. Maimakon ta iskeshi saita iske nos. Da taimakonta ta ci abincin kadan ta sha yoghurt din da yawa kafin daga bisani tasha magungunan. Bayan nan tayi mata godiya,nos din tana shirin fita ta tsaidata
"Don Allah karfe nawa ne? Inason gabatar da sallar dake kaina."
Ta bata amsa
"Ai Hajiya yanzu haka ma isha'i ta kusa."
Cikin mamaki Baby ta mike tayo alwala ta fito, rarraba idanuwa ta tsaya yi ganin babu wani darduma ko abunda zata rufe jikinta dashi. Turo k'ofar da akayi ta sanyata waigawa. Sukayi ido hud'u dashi,ta sakar mishi murmushi ya kauda kai.
"Sannu HARIS,don Allah inason yin sallah ne."
Wani irin kallo yayi mata,ta kauda kanta. Ya jinjina kai baice uffan ba ya fita. Sai gashi dauke da akwatin kayanta da kuma dardumar dake cikin motarsa. Ajiyewa yayi kawai ya koma gefe ya tsaya domin son ganin ikon Allah. Ga mamakinsa sai yaga ta fiddo Hijab zunb'ulele ta sanya. Baki ya saki har lokacin bai bar jifanta da kallon mamaki ba. Ta lura da hakan,murmushin dai ta k'ara yi mishi a karo na ba adadi. Batace komai ba ta soma kokarin shimfid'a dardumar da hannunta na hagu wanda baya ciwo,saidai ta kasa. Ba zato taga hannuwansa sun kama mata. Ta dubeshi,bai ko kalleta ba. Yana gama shimfid'a mata ya kauce.
"Nagode."
Ta furta a sanyaye. Salloli uku dake kanta ta rama,kafin ta zauna ta kwararo addu'o'i tana hawaye. A karshe ta shafa. Tana shirin mikewa,aka soma kiraye kirayen sallar Isha'i,wannan yasa Haris ficewa zuwa masallaci.
Itama ta gabatar da sallar isha,ta had'a da shafa'i da wutri. Nan ma addu'ar tayi ta shafa duk da irin radadin da hannunta keyi bata k'i d'agashi ba yayin addu'a.
Anan kan darduman ta zauna,kafafuwanta a mik'e tana mai jingina kanta da bango. Bata fi mintuna ba,Haris ya dawo da sallamarsa. Bakinta ya motsa alamun amsawa. Ya zauna a gefen gadon kafin ya soma magana
"Nayi iyakar taimakon da nake ga ya dace nayi gareki a matsayinki na 'yar uwa a musulunci dana sameki rai a hannun Allah na kawoki asibiti. Alhamdulillah,tunda har sauki ya soma samuwa zan tafi. Ga wayoyinki nan..."
Ya sanya hannu a aljihu ya fiddo mata su gami da ajiyewa a gefenta.
"Kina iya kiran d'aya cikin abokan harkarki,anan babban asibitin kauyen danbatta kike. Batun motarki kuma,gaskiya ta samu matsala,amma tana nan a police station na nan gefen asibitin(inji ni.. Lol)idan yaso idan kun tashi saiku janyeta ku koma. Na barki lafiya."
Ya sanya hannu ya fiddo bandirin kud'i na 'yan d'ari biyar biyar ya ajiye mata. Caraf ta riko hannunsa,da sauri ya dubeta. Hawayen da yaga tana fitarwa ne ya sanyaya mishi jiki. Ta narkar da fuskarta tana mai marairaice murya
"Yan iska zaku tunomin bakin labarin rayuwata,ku tashi muje shan ice cream. Yau jakata a cike take."
Sukayi murmushi don babu wacce keda kuzarin dariya,Manal ta dubi Baby.
"Zakije ne?"
Baby ta girgiza kai
"Banajin fita ne."
Sun lura jikinta yayi sanyi, tausayinta ya mamayesu musamman ma Manal wacce anan duniya ita kadai tasan wacece Baby Tasneem. Ita kadai tasan tarihin rayuwarta. Don kafin ta hadu da kowacce cikinsu,Baby tasleem ta soma haduwa da ita harma ta sauketa a gidanta. Haka suka fice suka barta a gidan. A ranar Baby taci kuka sosai,ba don komai ba sai don rashin sanin halin da mahaifiyarta ke ciki. Karshe ta mike ta shiga daki ta kwanta ba don tanajin bacci ba. Sai don kawai tunanin rayuwarta.
*****
KWANA HUDU BAYAN HAKA
Tafiya takeyi da baya da baya tana kallonta,yayinda ita kuwa ke kwance duk fuskarta ya baci da kuraje,hannu take miko mata alamun tsayar da ita tana ihun kuka
"Ya d'iyata,kada ki gujeni! Karki barni cikin wannan halin! Ki dawo gareni!"
Maimakon ta dawo,sai ta juya a guje zata tafi, karar da taji uwar tayi ya sanyata itama kwala ihu kafin tayi wuf ta fada wata rijiya a wajen."
A tsananin firgici Baby ta tashi sakamakon wannan mafarki mai rud'arwa,gumi ya wanke fuskarta duk da Ac dake a kunne. Sai haki takeyi tamkar wacce tayi gudu. Ta sanya hannu ta dafe kirjinta dake dukan uku uku. Can kuma tayi wuf ta sauko daga gadon. Wani d'an karamin akwati ta dauko ta bud'e. Hoto ne a cikin (envelope),nan da nan ta zaro tana duba. Dattijuwa ce tare da yarinya mai shekaru uku,sai dan saurayi mai kimanin shekaru goma sha daya a hoton. Dukkansu suna dariya.
Ta rungume hoton a kirjinta yayinda hawayenta suka karu. Tausayin kanta ya dabaibayeta,taji nan duniya bata sha'awar komai daya wuce na zuwa kauye ganin Mahaifiyarta. Tun hirar da sukayi tare dasu Manal,hankalinta yake a tashe. Ta amince bazata taba samun nutsuwa ba har sai ta dangana ga duba lafiyar mahaifiyarta.
******
Karfe goma na safiyar Asabar,ya shirya tsaf cikin kananun kaya ya feshe jikinsa da turaruka. Bai dauki komai ba sai karamin trolley dinsa inda ya shirya kayan sawarsa. Saida ya soma zuwa gidansu yayi sallama da Daddy,kafin yaje gidan Abba. Nan ma yayi musu sallama,mahaifiyarsa ta bashi sako a kaiwa uwarta,wato kakarsa. Daga haka ya kama hanya.
******
Zaune suke suna karyawa,basu ankara ba suka ganta ta fito tana jan akwati. Ba jan akwatin ne yafi basu mamaki ba,tunda sun saba tafiye tafiyensu. Shigar dake jikinta ne ya burgesu kuma ya basu mamaki. Doguwar rigar atamfa ce, anyi mata dogon hannu three quarter,maimakon ta dora dankwalin saita yafa karamin mayafin (pashmina) a kanta. Saida tazo kusa dasu sannan ta dubesu fuskarta babu wata kwalliya ta daukar ido sai hoda da jan baki mai kalar ruwan hoda(pink).
"Zanyi 'yar tafiya ne,amma in sha Allah bazata wuce kwana uku ba. Amanar gidana yana hannunki sister."
Ta dubi Manal. Murmushi manal tayi kafin tace
"Karki samu damuwa baby,shigarki tayi mana kyau,tamkar bake ba."
Tayi murmushi batace komai ba ta nufi waje. Babu wata wata,ta fada motarta ta shiga. Duk da dai bata taba karambanin tuk'i mai nisa ba,yau kam tanason yi. Dole taje ga mahaifiyarta ta duba lafiyarta. Tsananin kewarta yana neman hanata sukuni,ga fargabar abunda zata tarar sskamakon mafarkin da tayi a daren jiya......!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(19)
Tafe take kawai saidai dukkan hankali da tunaninta yana ga zantukan karshe da tayi da mahaifiyarta kafin su rabu.
"Na sanki,yarinya kike mai basira da kula dakai. Kada ki sake ki bari shaidan yayi maki hud'uba Tasleem. Kibi matar ubanki sau da k'afa,kiyi biyayya ga mahaifinki kada ki sanya damuwar komai a ranki. Allah Yana tare dake."
Hawayenta suka k'aru,yayin data k'ara karfin gudunta.
"Fitarmin daga gida,yar iskar yarinya! Kin bata wayonki! Bazaki zo ki b'atamin tarbiyyar yarana ba! Shegiya! Kedai kam ina kwakwanto akanki! Anya nine ubanki?!"
A zuciye ta kuma k'ara karfin speed dinta,hawaye bai bar kwaranyo mata ba.
"Kin bani mamaki kanwata,kin bata wayonki. Har da kanki ki dunga kai kanki dakin namiji?!! Tirr da wannan d'abi'a taki. Toh wallahi ki barmin gidana,kuma kika kuskura kikaje ga mahaifiyarmu kika kashe aurenta,wallahi saikin raina kanki! Kije duniya ce! Daidai take da kowa!"
A fusace take tafiya,bata ankara ba,motar ta kufce mata, ta rasa yanda zatayi ta tsayar da ita. Taka burki takeyi saidai batasan dalilin cijewar burkin ba,haka tayita wala wala har ta k'umu da bishiya. Bata k'ara sanin duniyar da take ba.
******
Farkawa tayi ta ganta kwance a gadon da yafi kama dana asibiti,ta tsurawa rub'abb'en kwanon silin din ido tana duba,hannunta tayi kokarin d'agawa da niyyar tab'a goshinta wanda ke sarawa tamkar zai fad'o saidai wani irin azaba da hannunta yayi ya sanyata cije lebbanta tana 'yar k'ara kad'an.
Wannan ya jawo hankalinsa,yana zaune saman gadon dake fuskantarta yana danne wayarsa a kokarinsa na kiran gida domin kada a jishi shiru ayi tsammanin ko babu lafiya. Ya dubeta,nan da nan zuciyarsa tayi sanyi ya mike ya karaso wajen kanta
"Sannu,ya jikin?"
Ta waiwayo dakyar sakamakon ciwon kan da takeji ya addabeta,ido kawai ta zuba mishi ba tare da tace komai ba. A zuciyarta mamaki kawai takeyi,meyasa Allah Yake yawan kawo mata shi aduk lokacin da take da buk'atar taimako? Abun tambayar ma shine,ya akayi yazo nan?
Kafin ta kammala tunaninta tuni ya juya ya fita. Minti daya sai gashi da likita,likitan ya karaso yayi mata gwaje gwaje kafin ya dubeta yana murmushi
"Sannu fa madam,yanzu meke damunki bayan hannunki? Kina jin wani ciwo daban ne?"
Baby ta k'ak'alo murmushi kafin ta d'aga hannu ta dafe kanta.
"Oh sorry,bari na sanya nos ta k'ara baki magungunanki. A sannu zai daina. Saidai kafin nan..."
Ya juya yana dubansa
"A samo mata abunda zata ci don bana zaton taci wani abu a yau."
Ya dubi Baby wacce tayi tsai da ido tana kallonsa,fuskarta babu yabo ba fallasa kamar dai wani tunanin na daban takeyi. Ya dauke kansa ya maida ga likita yana mai gyada mishi kai.
Likitan yana fita yabi bayanshi ba tare da yace mata uffan ba. Ta bishi da kallo sannan ta kauda kanta tana tuna abunda ya janyo mata hatsarin. Hawaye suka gangaro saman kuncinta,ko kusa batayi yunkurin sharesu ba,saima ta barsu suka cigaba da shatata.
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(20)
Haka har ya dawo ya sameta cikin wannan yanayin. Shigowar baisa ta sharesu ba,a zahiri ma sam batasan da wanzuwarsa ba. Lura da cewar ko kusa batasan da shigowarsa bane da kuma sallamarsa,yasa shi yin magana
"Tasleem."
Batasan lokacin data dubeshi ba,haka kawai sanyi ya ratsa zuciyarta domin tunda take bata tab'a jin wanda ya iya kiran sunanta ba kamarsa. Ya kauda kansa yana mai bude ledojin,fuskarsa a daure
"Tashi ki d'an ci wannan."
Ta mike dakyar ta zauna bayan ta sauke kafafuwanta dake ciwo kadan kadan a k'asa. Batace dashi komai ba ta mike tana dafe gado,band'aki ta zagaya. Can kuma sai gata ta fito.
"Ko zaka taimakamin da brush da maclean please?"
Ya mike ya fita, sai gashi ya dawo dauke dasu sabbi. Saida ta tabbatar da tsaftar bakinta sannan ta fito. Maimakon ta iskeshi saita iske nos. Da taimakonta ta ci abincin kadan ta sha yoghurt din da yawa kafin daga bisani tasha magungunan. Bayan nan tayi mata godiya,nos din tana shirin fita ta tsaidata
"Don Allah karfe nawa ne? Inason gabatar da sallar dake kaina."
Ta bata amsa
"Ai Hajiya yanzu haka ma isha'i ta kusa."
Cikin mamaki Baby ta mike tayo alwala ta fito, rarraba idanuwa ta tsaya yi ganin babu wani darduma ko abunda zata rufe jikinta dashi. Turo k'ofar da akayi ta sanyata waigawa. Sukayi ido hud'u dashi,ta sakar mishi murmushi ya kauda kai.
"Sannu HARIS,don Allah inason yin sallah ne."
Wani irin kallo yayi mata,ta kauda kanta. Ya jinjina kai baice uffan ba ya fita. Sai gashi dauke da akwatin kayanta da kuma dardumar dake cikin motarsa. Ajiyewa yayi kawai ya koma gefe ya tsaya domin son ganin ikon Allah. Ga mamakinsa sai yaga ta fiddo Hijab zunb'ulele ta sanya. Baki ya saki har lokacin bai bar jifanta da kallon mamaki ba. Ta lura da hakan,murmushin dai ta k'ara yi mishi a karo na ba adadi. Batace komai ba ta soma kokarin shimfid'a dardumar da hannunta na hagu wanda baya ciwo,saidai ta kasa. Ba zato taga hannuwansa sun kama mata. Ta dubeshi,bai ko kalleta ba. Yana gama shimfid'a mata ya kauce.
"Nagode."
Ta furta a sanyaye. Salloli uku dake kanta ta rama,kafin ta zauna ta kwararo addu'o'i tana hawaye. A karshe ta shafa. Tana shirin mikewa,aka soma kiraye kirayen sallar Isha'i,wannan yasa Haris ficewa zuwa masallaci.
Itama ta gabatar da sallar isha,ta had'a da shafa'i da wutri. Nan ma addu'ar tayi ta shafa duk da irin radadin da hannunta keyi bata k'i d'agashi ba yayin addu'a.
Anan kan darduman ta zauna,kafafuwanta a mik'e tana mai jingina kanta da bango. Bata fi mintuna ba,Haris ya dawo da sallamarsa. Bakinta ya motsa alamun amsawa. Ya zauna a gefen gadon kafin ya soma magana
"Nayi iyakar taimakon da nake ga ya dace nayi gareki a matsayinki na 'yar uwa a musulunci dana sameki rai a hannun Allah na kawoki asibiti. Alhamdulillah,tunda har sauki ya soma samuwa zan tafi. Ga wayoyinki nan..."
Ya sanya hannu a aljihu ya fiddo mata su gami da ajiyewa a gefenta.
"Kina iya kiran d'aya cikin abokan harkarki,anan babban asibitin kauyen danbatta kike. Batun motarki kuma,gaskiya ta samu matsala,amma tana nan a police station na nan gefen asibitin(inji ni.. Lol)idan yaso idan kun tashi saiku janyeta ku koma. Na barki lafiya."
Ya sanya hannu ya fiddo bandirin kud'i na 'yan d'ari biyar biyar ya ajiye mata. Caraf ta riko hannunsa,da sauri ya dubeta. Hawayen da yaga tana fitarwa ne ya sanyaya mishi jiki. Ta narkar da fuskarta tana mai marairaice murya