← Book details African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals Local reading mode
READING PART 27 OF 35

Sashe 27

African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals · about 8 min read

Zufa ta karyowa Tasleem,gabanta ya hau dukan uku uku. Shigowar Nura da sallama itace ta ceceta

"Anti kizo inji dad."

Mamma tayi azamar mikewa

"Ina zuwa."

Tayi gaba wanda hakan yasa tasleem sauke ajiyar zuciya. Amma rashin gaskiya ma baiyi ba.

Hawayenta suka kwaranyo,wannan wane irin bala'i ne haka? Ita kam ko za'a kasheta bazata fadi komai ba ko don gargadin yayan nata ala barshi shi da bakinsa ya fad'a d'in. Waya ce ta soma k'ara,ta duba taga mai kiran. "Abdullah1"

Bata d'aga ma ta ajiye. Har yayi ya katse. Haka ya jera kira har uku shiru sannan ya hakura. Tana nan zaune tana tunane tunane har Mamma ta k'ara shigowa tare da Humaira. Ganin wayarta na blinking ya fahimtar da ita anyi kiranta ne. Ta dauka ta duba,murmushi tayi mai ma'anoni tana duban Tasleem wacce ganinta yasa ta d'agowa daga kwanciyar da tayi idanunta bai bar fidda ruwan hawayen ba.

"Ko yanzu kadai maganata ta fito."

Ta zauna tana mai daure fuskarta tamau ta zauna kan gadon

"Humaira tafi wajen gwaggo kuyi hira."

Ba musu yarinyar ta fice a guje,tasleem kallo daya ta yiwa mahaifiyarta tasan babu wasa a tattare da ita

"Baki da wacce ta fini duk duniyar nan,baki da wacce zaki kaiwa kukanta a duniya ta baki shawara wacce ni bazan iya baki ba. Tun rabuwata daku bana bacci mai dadi tasleem. Ga yawan mafarkai da nakeyi da lamuranki,haka kawai hankalina bai kwanta ba akan irin rufeni da Abdullah ke yawan yi idan na tambayeki. Ki fito ki gayamin hakikanin halin da rayuwarki ke ciki,naso na dauko ki alokacin da RALIYA ta rasu saidai kuma hakan bai samu ba sakamakon Abdullah daya cemin karatu kikeyi nima kuma alokacin Allah baiyi zanje gaisuwar ba. Wai menene ainahin abunda ke tafiya dangane dake?"

"Raliya ta rasu?!! Ta maimaita a fili cike da tsananin mamaki. Tuni hawaye sun wanke fuskar Mamma

"Baki kyautamin ba keda yayanki Tasleem,tambayarki ta kara fad'armin da gabana. Mutuwar Raliya baki da masaniya akai,rashin lafiyar abbanki baki sani ba,haihuwar yayanki da takwarar daya samar maki nan ba baki da labarinsa. Wannan wane irin al'amari ne mai d'aure kai? Tasleem ko guduwa kikayi daga gidan mahaifinki kika kasa hakuri har komai ya wuce??"

Kawai sai baby ta fashe da kuka,toh ya ta iya? Mahaifiyarta ce fa.

"Bazakiji komai daga bakina ba wallahi sai kinyi kiran yaya abdullah garin nan. Sai mun hadu mu uku sannan zanyi maganar dake bakina."

Mamma tayi shiru tana kallonta har na tsawon mintuna kafin tayi azamar daukar wayarta tayi kiran Abdullah. Ya dauka ya soma gaisheta gami da tambayar ko lafiya ya kira ba'a d'aga ba?

"Bana dakin,kanwarka ce a ciki."

Bai taba kawo tasleem take nufi ba,a zatonsa ma Humaira ce. Mamma ta katseshi

"Duk abunda kakeyi inaso ka ajiyeshi abdullah,gobe kazo kazaure inason ganinka."

Yayi tsai kamar mai tunani sai kuma a sanyaye yace

"Lafiya dai mamma?"

"Lafiya lau,kazo dai nace."

"Shikenan,in sha Allah ina nan tafe goben."

Sukayi sallama. Mamma ta mike bata kara cewa komai ba ta fita. Ranar basuyi wata hirar arziki da diyarta ba kamar a farko ba itace ke d'okin ganinta ba......

*****

Gaba daya sun hadu a babban falon Daddy ciki kuwa harda Kb.....!

'YAR BARIKI

©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)

(51)

Abba ne ya soma magana cikin nutsuwa

"Kabir."

Cikin sussunne kai ya amsa

"Na'am Abba."

"Jiya yarinyar nan muka ganta kwatsam ta dawo a motar kasuwa,koda muka tambayeta tace kaine kace ta dawo ba tare da ita kanta tasan dalilinka ba,gashi mun taru munason jin hakikanin matsalar data had'aku. Me tayi maka da zafi har haka?"

Kabir ya saci kallon Yasmeen wacce akaci sa'a ita d'inma kallonsa takeyi. Kauda kai tayi gefe,jikinsa ya k'ara sanyi, ga kunya data dabaibayeshi. Toh me zaice? Lallai Yasmeen ta barshi a tsaka.

"Wai bakaji ne ana magana sakaran banza da wofi!"

Cewar Daddy cikin fusata. Yasmeen cikin kuka ta tare

"Wallahi Daddy laifina ne,fad'a yayimin ni kuma nayi fushi nayi tahowa wata. Don Allah kayi hakuri Yaya kabir,ka gafarceni bazan k'ara ba don Allah."

Haris ya runtse ido kansa a k'asa idanunsa sunyi jazur kirjinsa har d'agawa yakeyi saboda bacin rai. Ya saci kallon Kabir,duk alamun rashin gaskiya ya bayyana a fuskarsa.

"Daman nasan kece marar gaskiya Yasmeen. Ni nasan d'ana bazai wulakantaki ba.." Cewar Abba.

"Kada kayi saurin shaidar mutum mana Aliyu,idan anbi ta b'arawo abi ta mabi sahu. Alamun wannan shashashan sun nuna bashi da gaskiya. Idan ba haka ba kayi magana mana."

Kabir ya daure kansa a k'asa yace

"Gaskiyane Daddy,laifi tayimin nayi mata fad'a saidai banyi tsammanin zai mata ciwo har haka ba ta taho Kano bada sanina ba. Na yafemaki kema kuma ina fatan komai daya faru ya wuce,kuskure ne."

Haris ya wurga mishi kallon raini,saidai baice komai ba.

Abba yace komai ya wuce,nan ya k'ara yi musu fad'a akan hakuri da juna daga karshe yace su bari zuwa gobe su juya Abuja.

"Na dawo kanka kai kuma,ya zancenka ya kwana?" Cewar Daddy.

Haris ya k'ara russunar da kansa

"Kamar yanda na fad'awa Daddy ne,Malam yace muje daku karshem sati yanason ganinmu ne."

Daddy da Abba suka dubi juna,kafin Abba ya jinjina kai

"Shikenan,Allah Ya kaimu asabar d'in."

Aka amsa da amin kafin su sallamesu.

Da sassarfa ya nufi wajen motarsa

"Haris!!"

Muryar KB ta dakatar dashi. Kamar bazai tsaya ba sai kuma ya tsaya ba tare da ya juyo ba. Ya karaso ya jingina da motar yana fuskantar Haris.

"Nasan koda yasmeen ta boyewa kowa abunda ya had'amu,toh bazata boyemaka ba. Nayi laifi,please ka tayani bata hakuri."

Haris yayi mai wani irin duba yana d'aga girarsa kadan

"Ka kwantar da hankalinka dan uwana,yanda kaima ka shaidi Yasmeen da nuna maka soyayya tsantsa wacce ba algus hakika bazaka samu wata mishkila ba daga gareta..."

Jin taku a d'an nesa dasu ya sanya Haris juyawa kafin ya dubi Kabir yana murmushi wanda tuni KB ya fahimci can k'asan nurmushin nan bacin rai da haushinsa ne tsantsa.

"As i said,bazatayi fushi dakai ba koda kuwa zata kamaku turmi da tab'arya,ita d'in mai rufa asirinka ce. Sai kayi hattara KB,ba'a cutar irin wadannan matan a zauna lafiya."

Daga haka ya kama handle na motarsa zai bud'e,KB fuska daure ya matsa,daidai lokacin Yasmeen ta k'araso.

"Yayana tafiyarce?"

Haris wanda ke kokarin sanya key ya dubeta yana murmushi cike yake da tausayinta

"Tafiyarce kanwata,kada ki damu zan b'ullo kafin ku wuce. Hope bada wuri zaku tafi ba?"

Ya maida akalar tambayar zuwa ga KB,KB ya d'an tab'e baki

"Banajin da wuri zamu tafi, watakil ma sai zuwa jibi.."

"Meyasa? Kaga fa ban taho da wasu kaya ba sosai,kuma Abba yace lallai gobe mu wuce."

Ya watsa mata kallo kamar yayi magana sai kuma ya fasa, shi fa so yake ya nemi inda baby take. Ganin kallon da yayi mata yasa ta tsoraci fad'ansa tayi azamar cewa

"Yayana saida safen."

Tayi gaba da sauri saurinta,Haris ya dubeta kafin ya watsawa Kb kallo a wulakance,tuni idanunsa sun sauya

"Baby ce ke neman shiga rayuwar aurenka kb,right?"

Kb ya dubeshi a sanyaye,ya numfasa

"Hakane Haris, saidai wallahi bansan meyasa na tsinci kaina da mugun kaunar yarinyar nan ba ni kaina bazance maka ga...."

Figar motar da Haris yayi ne ya sanya Kb ja baya da sauri hakanan hon ya shigayi da karfinsa har Maigadi ya kammala bud'ewa ya fita. Yayi daidai da zuwan Abba da daddy. Abba ne zai shiga gidansa.
Ganin yanda Haris ya fita,Abba yace

"Kai Kabiru,menene ya faru?"

Kb wanda tunani da mamakin yanda akan yasmeen amintarsa da dan uwansa ke neman samun mishkila duk ta hanashi motsi,jin maganar Abba ne yasa ya juyo.

"Bansani ba Abba."

"Allah Ya tsare hanya toh. Matarka nace ta shirya kuje can gidanka idan yaso zuwa gobe saiku wuce Abujan."

Baiji dadin wannan hukuncin ba,saidai yasmeen ta biyashi data boye sirrinsa,tabbas idan yayi mata wani rashin adalcin bai kyauta ba. Ya amsa da toh kawai. Jimawa kadan ta fito suka wuce a mota sai janta yakeyi da hira ta basar dashi bisa hud'ubar mami da ta nuna mata ya dace ta d'an ja ajinta.

****
Da sallama ya shigo gidan,humaira aguje ta rukunkumeshi tana ihu

"Ga yaya! Ga Yaya!!"

Wannan yayi sanadin tashin tasleem dake bacci a falon sakamakon damuwa ta haneta bacci daren jiya da kuma shariyar da Mamma tayi mata tabar wani d'okin ganinta gaba daya ma ta chanja mata fuska.

Cak ya tsaya ita kuwa ta daure fuskarta tamau tayi azamar mikewa zata nufi falon sama,a guje yasha gabanta. Bakinsa na rawa,ya kasa gaskata cewar ita d'ince tsaye a gaban idonsa. Dakyar ya iya tab'a hannunta jin cewar ita d'ince yasa ya riko hannun hawaye sun wanke fuskarsa. Kawai sai ta soma kukan itama kafin ta warce hannunta tayi sama a guje har zuwa d'akin mamma da batanan tana dakin mijinta. Gadonta ta fad'a tana kukan tunowa da yanda yayan nata yayi mata korar kare daga gidansa. Muryarsa taji cikin kuka a kusa da ita

"Na rasa kalar godiyar da zan yiwa Ubangiji,da ace kin kara shekara baki dawo ba wallahi mutuwa zanyi ko nima a nemeni a rasa. Tasleem kin jefa yayanki cikin tashin hankali,nayi magana cikin fushi na zartar da hukunci ban tab'a zaton zakiyimin haka ba. Tasleem ina kika shiga? Ya za'ayi ni Abdullah na yankewa kanwata abar kaunata wannan hukunci mai tsauri. Ina sunan 'yan uwantakanmu? Wallahi kusan zaucewa nayi dana wayi gari naga da gaske kin gujeni...."

Mamma ya gani tsaye ta harde hannuwanta a saman kirjinta,hakanan ta zuba musu ido. Jin da tasleem tayi Abdullah yayi shiru yasa ta dago kai,taji k'arar rufe k'ofa wannan yasa itama ta dubi k'ofar. Mukulli mamma ta saka daman mijinta ya fita zuwa aiki,humaira tayi umarni ga gwaggo mai aikinta ta mik'ata gidan liman. Nura kuwa makaranta yake zuwa baya dawowa sai yamma sakamakon shirin jarabawar karshe na sakandire da yakeyi.
Gidan ya zamana daga Mamma sai yaranta mafi soyuwa azuciyarta. Fuska a daure ta zauna yayin data dubesu

"Ku zauna sosai."
Tasleem ta mike zaune daga kwanciyar da tayi,shima abdullah ya zauna gefenta a saman gadon,yayinda mamma taja kujerar gaban madubinta ta zauna idanunta a kansu. Ta dubi tasleem

"Kince sai yayanki yazo zaki fadamin abunda ya afku a rayuwarki ko? Yau kuma gani gaki,gashi muna sauraronki duka."

''YAR BARIKI
Chapter 27 · 0% Book details