Sashe 15
African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals · about 7 min read
"Na dawo sashen Raliya,dakinsu Hamidah. Saidai na gwammace inama ban dawo Kano ba. Aikin sashenta tsaf ni nakeyi,ta sallami 'yar aikinta daya,dayar kuwa tace iyakarta kicin da baranda. Amma komai ni nakeyi. Bana k'in yi mata aiki,saidai idan ina aikin kallo daya zakayimin ka gane rashin sabo. Nan da nan nake gajiya. Abun kona ran bai wuce tarewar dasu Nura da Usman da kuma matansu,Bilkisu da Meena sukeyi ba. Kodayaushe suna nan suna kallo da hira tare dasu Hamida da Raliya tamkar zasu fasa falon. Ni ce zanyita zirga zirgar kaiwa da komowa wajen kawo musu abinci da abin sha. Bilkisu ce mai yaro daya,Junaid. Ya zamana ni na zama yar raino matukar tana sashen. Cire mishi pampers,goyashi,bashi ceralac da sauran ayyuka masu cimin rai. Ga wannan shegen kallon dana tsana a wajen Usman,duk sadda muka hada ido sai ya hau yimin murmushi yana kashemin ido,harararsa nakeyi alokacin saidai wai an tsikari kakkausa ko a jikinsa. Hindatu kadai ke tausayamin.
Bana kwanciya bacci saina kammala ayyukana. Abu daya naki yarda da gyarawa,dakin kwananmu,rantsuwa na yiwa Raliya a gabanta akan cewar bazan gyara ba tunda nikam shimfidata,Kafet ne. Sune masu kwanan gadon,bandaki kuma duk sadda zanyi amfani dashi zan gyara idan ta kama. Zata mareni naja baya nace wallahi ta mareni saina gayawa Abba. Nasan ba tsorata tayi ba,saidai bansan dalilinta nayin kwafa ta fice ta kyaleni ba. Hamida tayi wuf ta taso zatamin fitsara,ta juyo ta daka mata tsawa. Wai ita saita mareni din taga abunda zanyi,ganin uwarta ta hanata nayi murmushi nace "Kinci sa'a domin wallahi sai kin gane kurenki muddin kika tab'a jikina."
Jin haka ta harzuka ta daga hannu zata mareni,Raliya ta daka mata tsawa,ni kuwa na rike hannun na murdeshi ta fasa k'ara. Raliya ta iso ta hankadani ta janye Hamida sukayi gaba. Na rasa dalilinta nak'in daukar mataki akan hakan,saidai gaba mai tsanani ta shiga tsakanina da Hamida babu maganar dake had'ani da ita.
Ranar da zamuyi Graduation kuwa,ban nemi komai daga Abba ba hakanan ban gayyaci kowa daga bangarena ba. Yaya abdullah kadai na shaidawa ta waya, duk da har lokacin baisan Mamma bata gidan ba. Ya tayani murna yace inama yana nan dashi za'ayi. Yayimin alkawarin tahomin da kyauta ta musamman idan zaizo. Murmushi kawai nayi. Sauran kudadena na hada na biya komai da makaranta ta bukata. Ranar kuwa da sassafe na shirya,Hamida sunsan da maganar saidai basu cewa kowa uffan ba,hindatu ma ta shirya cikin uniform kamar yanda dokar makarantar tace dalibanta suyi a ranar. Ta dubeni"Zaki rigamu tafiya ko Tasleem?" Murmushi nayi mata na amsa da eh. Daga haka na dauki yar karamar handbag dana zuba kayan amfanina na fito sanye da rigar T-shirt na school da jeans na gida. Mukayi arba da Raliya,ta daure fuska "Ke kuma ina zaki? Kodayake wannan ba matsalata bace bazan hanaki yawon banzanki,aikina fa? Wa zaiyimin? Kada ki sake kibar gidan nan batare da kinyisu ba." Daga haka tayi dakinta,tsaki naja bana tsoron dukanta balle na Hamza,yau ranata ce babu wanda ya isa ya hanani zuwa makaranta. Ina waige waigen neman direba naji hon,ina dubawa naga Usman zaune a motarsa yana dagomin hannu yana murmushi. "Dan iska." Na fada a fili na kauda kaina.....
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(32)
Kai tsaye wajen Baba Maigadi na nufa. Na tambayeshi ko direba yazo saidai ya sanar dani cewar matarsa ke nakuda yaje kaita asibiti ba lallai ne ya dawo nan kusa ba. Bakin ciki ya turnukeni,da ace na iya mota da duk hakan bata faru ba,gashi kuma koda yazo dole ne sai na amso mishi mukulli wajen Raliya domin shaf ina manta cewar mukullayen motar gidan a hannunta yake. Daidai nan Usman ya iso acikin motarsa,baba Maigadi ya tafi don budemishi gate.
"Zaki makara fa my sister,zo ki hau na saukeki."
Kamar nace bazan hau ba,saidai tunawa da nayi Abba kansa baya gari ballantana nasa ran dakewa zuciyata na amso kudin mota yasa banyi musu ba na shiga don kuwa bani da ko ficika. Ai daman kudin ubanmu ne suke takama dashi,babu laifi don alokacin Abba dayake am shanyeshi a rubutu ya k'ara bude musu shaguna kowanne da nashi a kantin kwari suna d'an maida hankali. Na shiga gidan gaba na zauna fuska a daure. Bai damu Usman ba ko kadan,sai bayan mun soma tafiya naji yace"Ba gaisuwa ko?"
Ni wallahi mamaki ma yake bani har lokacin ganin yanda yake yimim sanyi sanyi a yanzu. Banda niyyar gaisheshi,na dauke kaina ma. Yayi dariya"Ke kam don kinsan kin hadu shiyasa kike yiwa mutane yanga Tasleem. Hakane dalilin dayasa kike wulakanta masu zuwa gidan nan da sunan sunzo zance wajenki ko?"
Na watsa mishi harara,ko a jikinsa na kauda kaina bance uffan ba.
"Tasleem kina da kyau sosai kamar mominki ko ince kinma fita. Gashi Allah Yayi maki baiwar diri ko ta ina ke macece. Dole ki dunga yiwa maza yanga."
Na dauki surutan Usman a matsayin wofi,banko kara dubansa. Har muka iso yana zazzaga shirmensa don shirme na dauki zantukansa. Na soma hango take takensa,akwai abunda yake nufi a kaina saidai ko kusa ban nuna alamar na fahimci komai ba. Muna isowa na yunkura zan bude kofar ya dakatar dani ta hanyar cewa na tsaya. Na dakata,kudi ya mikomin har dubu uku ba musu na karb'e ai kudin na ubana ne. Ko godiya banyi ba na fice.
Anan muka shirya,sannan muka nufi inda ake taron,Afficent. Waje ya cika makil da iyayen yara da sauran yan makaranta. Tausayin kaina ya kamani sanin cewa bani da wanda zaizo mini cikin yan uwana gashi ko abun rabo banyiba. Haka na kutsa na zauna,saidai a ranar nayi hotuna da kawayena,Munnira da Jamila, da yan ajinmu maza da mata. Saida akayi kirana domin amsar certificate na mike a nutse naje. Nayi mamakin ganin wanda ban taba zato ba yazo da niyyar daukata a hoto. Yaya Musty(dominka,yaya mustyna..love u forever..miss you:ur bloodsis..rufaida) ne,d'an gidan Gwaggo Hafsatu yayar Mamma dake Kazaure. Na saki fuska sosai,ina karba na nufeshi bakina a washe
"Yaya mustyna kai dawa kuke tafe? Ya akayi kukasan da wannan ranar?"
Ya harareni
"Bayan da kika k'i kiranmu a waya ki sanar damu sai Abdullah dake a wata k'asar ne zai gayamana?"
Nayi dariya a shagwabance nace
"Afuwan yayana,yanzu kai da waye kuke tafe?"
Yana dariya yaja hannuna yana fadin
"Muje ki ganewa idonki."
Haka mukayita kutsawa taron jama'a bai tsaidani gaban kowa ba sai Mamma da gwaggo Hajara. Ihun murna na saki ban damu da wadanda suka kalloni ba. Na rukunkume Mamma kafin na saketa na rungumi Gwaggo Hajara. Bansan ya akayi ba kawai sai na fashe da kuka sosai,har wani malamin Chemistry dinmu sarkin shishshigi ya matso wai bai taba ganin kukan Headgirl ba(kasancewar mukamin dana rike kenan a makaranta)sai a yau. Su mamma sukayi dariya,nikam na harareshi dariya kawai yayi ya kara gaba bayan yace"Madam,your daughter is one of my best students,very talented." Mamma murmushi tayi kawai. Kirana da aka karayi ne naje nayi speech a matsayina na headgirl na mike na tashi bayan na damkawa Mamma certificate dina. Tiryan tiryan nayi na gama na yiwa manyan bak'i fatan komawa gida lafiya sannan na bada shawara ga juniors dinmu nan aka hau tafi raf raf akarshe na koma gasu Mamma mukayi ta daukar hotuna. Munnira da Jamila suma suka iso suka gaida Mamma.
Ina zaune kawai sai naga yaya musty ya shigo da kwalaye,nayi mamakin ganin jakunkunan rabo dauke da memo fa handfan a ciki. Na kalleshi idona taf da kwalla,yace
"Zaki soma kuma dai? Muddin kikayi kuka zan fasa baki."
Gwaggo Hajara tayi dariya
"Wannan hukunci yayi."
Nayi azamar share fuskata
"Kaga nabar kuka yayana."
Mukayi dariya,ashe tun sadda na sanarwa Yaya abdullah ya gayamusu. Shine Mamma ta bayar ayimin memo,anan shima Malam ya k'ara mata kud'i. Don farin ciki na rasa inda zansa raina.
"Hamida,hindatu."
Hamida ta kalleta ta tabe baki tayi gaba,hindatu ce ta tako ta gaishesu. Mamma ta dafa kanta tana murmushi bayan sun amsa. "Ina maminku? Ku gaisheta."
Kusan lokaci daya muka dubi Mamma nida gwaggo Hajara,gwaggo Hajara harararta tayi. Nikam mamakin rashin zuciya irin na Mamma nakeyi,bata fushi. Da hindatu kadai na dauki hotuna,a karshe yaya musty ya amshi camera dita da zummar zaisa a wankemin hotunan harda na tasa wayar. Naji dadi sosai.
Har kusan azahar muna tare kafin a watse suma su soma shirin komawa Kazaure. Anan ne idona ya raina fata,gwaggo Hajara ta dafani
"Haba 'yata,menene abun kukan? Kiyi hakuri,tunda kunyi hutu saiki tambayi Abbanki idan ya amince sai kizo mana koda sati kiyi kinji? Kukanki sai ya karyar da zuciyoyinmu."
Suka lallabani suka tafi.
Bana kwanciya bacci saina kammala ayyukana. Abu daya naki yarda da gyarawa,dakin kwananmu,rantsuwa na yiwa Raliya a gabanta akan cewar bazan gyara ba tunda nikam shimfidata,Kafet ne. Sune masu kwanan gadon,bandaki kuma duk sadda zanyi amfani dashi zan gyara idan ta kama. Zata mareni naja baya nace wallahi ta mareni saina gayawa Abba. Nasan ba tsorata tayi ba,saidai bansan dalilinta nayin kwafa ta fice ta kyaleni ba. Hamida tayi wuf ta taso zatamin fitsara,ta juyo ta daka mata tsawa. Wai ita saita mareni din taga abunda zanyi,ganin uwarta ta hanata nayi murmushi nace "Kinci sa'a domin wallahi sai kin gane kurenki muddin kika tab'a jikina."
Jin haka ta harzuka ta daga hannu zata mareni,Raliya ta daka mata tsawa,ni kuwa na rike hannun na murdeshi ta fasa k'ara. Raliya ta iso ta hankadani ta janye Hamida sukayi gaba. Na rasa dalilinta nak'in daukar mataki akan hakan,saidai gaba mai tsanani ta shiga tsakanina da Hamida babu maganar dake had'ani da ita.
Ranar da zamuyi Graduation kuwa,ban nemi komai daga Abba ba hakanan ban gayyaci kowa daga bangarena ba. Yaya abdullah kadai na shaidawa ta waya, duk da har lokacin baisan Mamma bata gidan ba. Ya tayani murna yace inama yana nan dashi za'ayi. Yayimin alkawarin tahomin da kyauta ta musamman idan zaizo. Murmushi kawai nayi. Sauran kudadena na hada na biya komai da makaranta ta bukata. Ranar kuwa da sassafe na shirya,Hamida sunsan da maganar saidai basu cewa kowa uffan ba,hindatu ma ta shirya cikin uniform kamar yanda dokar makarantar tace dalibanta suyi a ranar. Ta dubeni"Zaki rigamu tafiya ko Tasleem?" Murmushi nayi mata na amsa da eh. Daga haka na dauki yar karamar handbag dana zuba kayan amfanina na fito sanye da rigar T-shirt na school da jeans na gida. Mukayi arba da Raliya,ta daure fuska "Ke kuma ina zaki? Kodayake wannan ba matsalata bace bazan hanaki yawon banzanki,aikina fa? Wa zaiyimin? Kada ki sake kibar gidan nan batare da kinyisu ba." Daga haka tayi dakinta,tsaki naja bana tsoron dukanta balle na Hamza,yau ranata ce babu wanda ya isa ya hanani zuwa makaranta. Ina waige waigen neman direba naji hon,ina dubawa naga Usman zaune a motarsa yana dagomin hannu yana murmushi. "Dan iska." Na fada a fili na kauda kaina.....
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(32)
Kai tsaye wajen Baba Maigadi na nufa. Na tambayeshi ko direba yazo saidai ya sanar dani cewar matarsa ke nakuda yaje kaita asibiti ba lallai ne ya dawo nan kusa ba. Bakin ciki ya turnukeni,da ace na iya mota da duk hakan bata faru ba,gashi kuma koda yazo dole ne sai na amso mishi mukulli wajen Raliya domin shaf ina manta cewar mukullayen motar gidan a hannunta yake. Daidai nan Usman ya iso acikin motarsa,baba Maigadi ya tafi don budemishi gate.
"Zaki makara fa my sister,zo ki hau na saukeki."
Kamar nace bazan hau ba,saidai tunawa da nayi Abba kansa baya gari ballantana nasa ran dakewa zuciyata na amso kudin mota yasa banyi musu ba na shiga don kuwa bani da ko ficika. Ai daman kudin ubanmu ne suke takama dashi,babu laifi don alokacin Abba dayake am shanyeshi a rubutu ya k'ara bude musu shaguna kowanne da nashi a kantin kwari suna d'an maida hankali. Na shiga gidan gaba na zauna fuska a daure. Bai damu Usman ba ko kadan,sai bayan mun soma tafiya naji yace"Ba gaisuwa ko?"
Ni wallahi mamaki ma yake bani har lokacin ganin yanda yake yimim sanyi sanyi a yanzu. Banda niyyar gaisheshi,na dauke kaina ma. Yayi dariya"Ke kam don kinsan kin hadu shiyasa kike yiwa mutane yanga Tasleem. Hakane dalilin dayasa kike wulakanta masu zuwa gidan nan da sunan sunzo zance wajenki ko?"
Na watsa mishi harara,ko a jikinsa na kauda kaina bance uffan ba.
"Tasleem kina da kyau sosai kamar mominki ko ince kinma fita. Gashi Allah Yayi maki baiwar diri ko ta ina ke macece. Dole ki dunga yiwa maza yanga."
Na dauki surutan Usman a matsayin wofi,banko kara dubansa. Har muka iso yana zazzaga shirmensa don shirme na dauki zantukansa. Na soma hango take takensa,akwai abunda yake nufi a kaina saidai ko kusa ban nuna alamar na fahimci komai ba. Muna isowa na yunkura zan bude kofar ya dakatar dani ta hanyar cewa na tsaya. Na dakata,kudi ya mikomin har dubu uku ba musu na karb'e ai kudin na ubana ne. Ko godiya banyi ba na fice.
Anan muka shirya,sannan muka nufi inda ake taron,Afficent. Waje ya cika makil da iyayen yara da sauran yan makaranta. Tausayin kaina ya kamani sanin cewa bani da wanda zaizo mini cikin yan uwana gashi ko abun rabo banyiba. Haka na kutsa na zauna,saidai a ranar nayi hotuna da kawayena,Munnira da Jamila, da yan ajinmu maza da mata. Saida akayi kirana domin amsar certificate na mike a nutse naje. Nayi mamakin ganin wanda ban taba zato ba yazo da niyyar daukata a hoto. Yaya Musty(dominka,yaya mustyna..love u forever..miss you:ur bloodsis..rufaida) ne,d'an gidan Gwaggo Hafsatu yayar Mamma dake Kazaure. Na saki fuska sosai,ina karba na nufeshi bakina a washe
"Yaya mustyna kai dawa kuke tafe? Ya akayi kukasan da wannan ranar?"
Ya harareni
"Bayan da kika k'i kiranmu a waya ki sanar damu sai Abdullah dake a wata k'asar ne zai gayamana?"
Nayi dariya a shagwabance nace
"Afuwan yayana,yanzu kai da waye kuke tafe?"
Yana dariya yaja hannuna yana fadin
"Muje ki ganewa idonki."
Haka mukayita kutsawa taron jama'a bai tsaidani gaban kowa ba sai Mamma da gwaggo Hajara. Ihun murna na saki ban damu da wadanda suka kalloni ba. Na rukunkume Mamma kafin na saketa na rungumi Gwaggo Hajara. Bansan ya akayi ba kawai sai na fashe da kuka sosai,har wani malamin Chemistry dinmu sarkin shishshigi ya matso wai bai taba ganin kukan Headgirl ba(kasancewar mukamin dana rike kenan a makaranta)sai a yau. Su mamma sukayi dariya,nikam na harareshi dariya kawai yayi ya kara gaba bayan yace"Madam,your daughter is one of my best students,very talented." Mamma murmushi tayi kawai. Kirana da aka karayi ne naje nayi speech a matsayina na headgirl na mike na tashi bayan na damkawa Mamma certificate dina. Tiryan tiryan nayi na gama na yiwa manyan bak'i fatan komawa gida lafiya sannan na bada shawara ga juniors dinmu nan aka hau tafi raf raf akarshe na koma gasu Mamma mukayi ta daukar hotuna. Munnira da Jamila suma suka iso suka gaida Mamma.
Ina zaune kawai sai naga yaya musty ya shigo da kwalaye,nayi mamakin ganin jakunkunan rabo dauke da memo fa handfan a ciki. Na kalleshi idona taf da kwalla,yace
"Zaki soma kuma dai? Muddin kikayi kuka zan fasa baki."
Gwaggo Hajara tayi dariya
"Wannan hukunci yayi."
Nayi azamar share fuskata
"Kaga nabar kuka yayana."
Mukayi dariya,ashe tun sadda na sanarwa Yaya abdullah ya gayamusu. Shine Mamma ta bayar ayimin memo,anan shima Malam ya k'ara mata kud'i. Don farin ciki na rasa inda zansa raina.
"Hamida,hindatu."
Hamida ta kalleta ta tabe baki tayi gaba,hindatu ce ta tako ta gaishesu. Mamma ta dafa kanta tana murmushi bayan sun amsa. "Ina maminku? Ku gaisheta."
Kusan lokaci daya muka dubi Mamma nida gwaggo Hajara,gwaggo Hajara harararta tayi. Nikam mamakin rashin zuciya irin na Mamma nakeyi,bata fushi. Da hindatu kadai na dauki hotuna,a karshe yaya musty ya amshi camera dita da zummar zaisa a wankemin hotunan harda na tasa wayar. Naji dadi sosai.
Har kusan azahar muna tare kafin a watse suma su soma shirin komawa Kazaure. Anan ne idona ya raina fata,gwaggo Hajara ta dafani
"Haba 'yata,menene abun kukan? Kiyi hakuri,tunda kunyi hutu saiki tambayi Abbanki idan ya amince sai kizo mana koda sati kiyi kinji? Kukanki sai ya karyar da zuciyoyinmu."
Suka lallabani suka tafi.