Sashe 2
African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals · about 8 min read
Cikin murya irin na wacce ta sha kwaya,Hibba ta tambayeta. Ta kauda kai tana fesar da hayak'i,kafin ta sanya hannu ta cire tufkar da ta yiwa kitsonta na gashin doki,ya zubo har kafad'unta.
"Uban waye ne? Ina zan sake samun damar cin karo da mai motar nan?"
Hibba ta dubi Manal wacce tayi filo da cinyar abokin watsewarta,Manal ta tabe baki inda ta juyar da kanta gefe don kuwa zuwa yanzu kishin Baby fal cike a zuciyarta. Wani d'an karambanin aka samu ya kai hannu da niyyar tab'a fuskar Baby,batayi wata wata ba ta mik'e ta wankeshi da mari gami da nunashi da yatsa.
"Ba kowane tsami ne yake da damar tab'a jikina ba! Daga yau ina mai gargad'inka ka nisantar da kanka daga gareni if not..."
Tayi kwafa ba tare data k'arasa ba ta dauki mukullin mota da jakarta ta haye sama.
Dariya gayun suka sanya mishi,wani dake can gefe yana kokarin jona socket jikin TV ya d'ago mishi hannu
"Sorry Baaba,wannan fa babban goro kake gani sai magogin k'arfe. Ka kiyaye a zauna lafiya."
Wanda aka kira da baaba ya shafa kumatunsa yana murmushin takaicin marin da Baby tayimishi kafin yayi kissing hannunshi
"Me takeji dashi? Kud'i ko kyau?"
"Babu wanda bata ji dashi,kasan babu abunda zaka nuna mata don ubanka.Da kud'inka tsohonka kake tutiya,ita kuwa harkarta har da sa'annin ubanka da gayu irinmu da suka dame tsoffinmu a kud'i da komai Baby gogayya take dasu."
Baaba ya jinjina kanshi yana murmushin da shi kad'ai yasan manufarsa kafin yayi wuf yabar wajen. Suka k'ara sanya dariya,banda Manal wacce takeji tamkar ta tashi da kifawa Musty mari yanda yake ta kod'a Baby. A fusace ta mike zaune zatayi magana saidai ta fasa sakamakon kid'an da ya cika ko'ina na gidan. Nan wasu suka mik'e suka hau casu alhalin ga kiran sallah can na magrib yana tashi a masallatan unguwa.(Allah Ya shiryemu,amin.)
Baby tasleem kuwa tana shiga d'akinta wanka tayi na musamman ta fito ta k'ara mulke jikinta da mayuka da turarukanta tsadaddu kafin ta shirya cikin wata gown mai tsaga a gefe gefenta,tun daga gwuiwa har k'asa. Ta k'ara gyara gashinta,ta fesheshi da Hairsprays kala kala. Kafin tayi zaman shafa jan farce a yatsunta kalar skyblue(wato kalar gown dinta). Ta kwashi awa kusan uku gaba daya yayin wankan da komai nata na shiri. A lokacin da take jiran bushewar faratan nata ne,Dalal ta turo k'ofa ta shigo. Itama ta had'e cikin riga da wando matsastsu masu bin jiki. Sai taunar cingam takeyi na yan bariki ta rike k'ugu tana duban Tasleem wacce kallo d'aya tayi mata ta madubi bata k'ara dubanta ba.
"Zaki gidan Momi ne ko muyi gaba?"
Kamar bazatayi magana ba,har ta k'ular da Dalal.
"Kuje,zan biyoku. Hibba ta jirani mu wuce tare."
Harararta Dalal tayi kafin tayi gaba tana jan tsaki yanda Baby bazata jiyota ba. Ta iske Hibba cikin shiri zaune a saman mota
"Hakimar tace kiyi jiranta ku taho tare. Munyi gaba,kinsan Momi batason a b'ata lokaci."
Hibba tayi murmushi domin tasan yanda Momi ke ji da Baby ko don masu gidan ranar da take kai mata a kowane sati,domin nata kyautar ga Momi yafi na dukkansu yawa.
"Kada ku damu kuyi gaba."
Manal ta bud'e wutar hon,da azama Dalal ta shiga suka tafi. Basuyi mintuna da barin gidan ba,Baby ta fito cikin takunta na jin ita d'in ta isa tana tafe ko'inanta yana rawa,tana amsa waya tamkar bataso. Hibba dai kallon ikon Allah takeyi,har ta soma zargin kodai Baby 'yar wata basaraken ce? Haka tayi ta kallonta ita kuwa batasan ma tana yi ba,mota ta bud'e ta shiga ba tare da ta cewa Hibba uffan ba. Don kanta itama ta bud'e gidan gaba ta shiga. Minti uku da soma tafiyarsu,Hibba ta fahimci da shahararren mai kud'in nan Baby take waya, wato Alhaji Ridwan Naira. Gudu takeyi kasancewar dare ne,hakan yasa tafiyar mintuna talatin,sai gashi minti goma sha biyar ya kawosu gidan MOMI......!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(04)
Falo ne babba,cike yake da matasan mata da manyansu. Kowacce tana ji da kanta da ganin tafi 'yar uwarta. Wacce aka kira fa Momi tana hakimce a saman kujera mai zaman mutum biyu ta kishingid'a tana cin tuffa. Kallonsu takeyi d'aya bayan d'aya fuskarta dauke da murmushi. Kowaccensu tasha shiga ta alfarma,saika rantse wani shagalin akeyi. Daidai lokacin Baby ta sanyo kai,a bayanta Hibba. Matasa da yawa dake mutanenta ne,suka hau jinjina da ihu
"Shegiya Baby,manya a baku naku daban."
Ta sakar musu murmushi mai bayyana hak'ora tare da mimmik'a musu hannu suna cafkewa. Manyan kuwa gaisheshu tayi kafin ta isa ga Momi wacce ta zuba mata ido tana murmushi. Hannu ta dunkule,alamun jinjina
"Na gaida uwata,ranki ya dade tuba nake."
Momi ta ja hannunta ta zauna da ita gefanta tana dariya ga hakoran Makkah farare a hakoranta biyu na gefe da gefe.
"Bakya laifi gareni baby."
Daga haka Momi ta juya don soma abunda ya tarasu. Magana ce aka cigabansu a harkokinsa. Ta kara gargad'insu akan su kiyaye kada su bari ciki ya shiga jikinsu koda wasa. A karshe ta dubesu sosai
"Maganata ta karshe ku sani, babu aure a tsarinmu. Nasha sanar maku koda ya kasance zakuyi auren,toh fa baifi na wata uku ba kin fito. Auren ba talaka ba,mai hannu da shuni,ki tabbatar kin tatso mana mai yawa kafin ki datse igiyar auren naki. Wannan shine jawabina. Batun balance kuma,ina jiranku babu wacce batasan acc.no. dina ba."
Haka suka jima suna tattaunawa kafin taro ya watse,Momi ta dubi Baby wacce tayi haramar tafiya. Lokacin karfe sha biyu da mintoci
"Baby baby,kodayaushe tauraruwarki kara haskawa takeyi. Ba daga kananun ba,daidai da manyan suna son mu'amala dake. Ina kuma ga an lek'a ga Hajiyoyinmu duk da dai kin nuna wannan baya kanki yanzu."
Baby tayi murmushi ta girgiza kanta
"Momina kenan,me zanyi da jinsi irin nawa? Wannan babbar kazanta ce, wannan dinma da nakeyi fatana nan gaba na daina."
Momi ta kyalkyale da dariya tana mai dafa kafad'ar Baby
"Babu ranar da wannan fatan naki zai tabbata kuwa,zan maki uzuri da alama bakisan alfanun jinsi ba sai nan gaba."
Baby tayi murmushi mai had'e da jan numfashi
"Ba halina bane,baya daga abunda nake sha'awar aikatawa. So,in sha Allah bazan tab'a bin wannan hanyar ba."
"Ja'irar kaya,ashe har yanzu kinsan da sunan Allah? Toh ba laifi muje zuwa."
Abun sai ya bawa baby dariya,ta d'an dara kafin ta mik'e tayi hanyar fita
"Momi kenan,na barki lafiya."
******
Mutum ne matsakaici,mai dogon fuska,yana da matsakaicin hanci saidai akwai magana(idanu). Girarsa a cike kuma bak'i wuluk,kamar dai yanda sajensa da gashin kansa yake. Fari sol,zubin Fulani.
Zaune yake a ofis yana aiki akan Laptop. Hankalinsa gaba d'aya ya tafi ga aikinsa,kallo d'aya zakayi mishi kasan yana hutawa. Daidai lokacin aka bud'e kofar gami da yin sallama. Ba tare daya kalli mai sallamar ba ya amsa ciki ciki kasancewar ransa a b'ace yake dashi. Ya k'araso da fara'a ya zauna
"An gaida mutumina,ba fad'a mai ya kawo gaba kuma? Ace har ka iso garin nan saidai don rashin mutunci ko waya bakayi domin sanar dani ba sai a bakin kanwarka na tsinci labarin."
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(05)
Har ya gama maganarsa baice mishi komai ba. Ganin haka ya buga tebur wannan yasa shi watsa mishi wani irin kallo kafin ya karkato yayi juyi da kujerarsa yana fuskantarshi. Fuska a daure yace
"Kana da kunyar takowa ofishina bayan wulakancin kayimin?"
Cikin rashin fahimta,KB ya zuba mishi ido kafin ya tambayeshi
"Me kake nufi wai Haris? Nifa bansan takamaiman laifin dana aikata ba."
Ya dubeshi kadan kafin ya girgiza kai
"Jiya,(around 6:00pm),na had'u dakai anan wajejan sultan road. Saidai abun mamaki nayita hon baka tsaya ba saida kyar,karshe ma don rainin hankali kak'i fitowa daga motar. Saidai a yanda ka nuna yanzu ya tabbatar min ba kaine cikin motar ba saidai tabbas lambar motarka ce. Na soma tunanin direbanka ne,toh a gaskiya ka chanja direba,domin bakayi dace ba wallahi da zan ganshi zai sha mari ne...."
Kb ya katseshi
"Tsaya don Allah,gayamin menene ya faru?"
Haris ya labarta mishi,ya k'arashe da cewa
"Mercedes Benz dinka ce, kada kaso kaga gudun da direbanka ke...."
KB ya katseshi a kunyace
"Oh,Baby ce a ciki fa."
Haris ya yamutsa fuska
"Who the hell is Baby?"
Kb yayi murmushin basarwa
"Wata cousin d'in Mamina ce,ta ari motata ne tun kusan (last two days.)"
Haris ba don ya yarda ba,sai don kawai bai fiye bin kwakkwafin abunda bai shafeshi bane,ya gyada kanshi
"Ok."
Daga haka suka bar zancen suka fad'a hirarsu.
*****
Kabir Idris Babangida da Haris Aliyu Kazaure. Aminan juna ne,wadanda amintarsu ta samo asali tun daga iyayensu maza wadanda suma a baya can makwaftaka ta had'asu tun suna kauyensu na Kazaure kafin Allah Ya azurtasu a garin Kano. Kowannensu yayi gini na gani na fad'a ya dawo birnin Kano da zama.
Makaranta d'aya Haris da Kabir sukayi. Har ya zamana sun karanci course d'aya,wato business.
Kabir shi kad'ai ne d'a a wajen mahaifinsa Alhaji Idris. Shi kuwa Haris,su biyar ne. Saboda zumunta dake tsakanin iyayensu wadda bata wasa ba,ya sanya Alhaji Aliyu daukar Haris tun yana d'an shekara biyu ya damk'awa Alhaji Idris da matarsa Hajiya Jamila. Sunyi murna matuk'a domin Allah Ya sani,tun Haris na jariri suna matukar kaunarsa,kai bama su kad'ai ba. Mutane da yawa suna kaunar Haris saboda kyawu da farin jinin da Allah Ya bashi. Hajiya Aisha kuwa,mahaifiyar Haris mace ce mai alkunya wannan yasa ko kusa bata nuna damuwarta akan wannan kyautar ba tunda ga YASMEEN da sauran yaranta uku a gabanta.
Haka Kabir da Haris suka taso cikin kaunar juna da tsananin gatan da ake nuna musu. Rayuwarsu saita burgeka na yanda suka shak'u.
"Uban waye ne? Ina zan sake samun damar cin karo da mai motar nan?"
Hibba ta dubi Manal wacce tayi filo da cinyar abokin watsewarta,Manal ta tabe baki inda ta juyar da kanta gefe don kuwa zuwa yanzu kishin Baby fal cike a zuciyarta. Wani d'an karambanin aka samu ya kai hannu da niyyar tab'a fuskar Baby,batayi wata wata ba ta mik'e ta wankeshi da mari gami da nunashi da yatsa.
"Ba kowane tsami ne yake da damar tab'a jikina ba! Daga yau ina mai gargad'inka ka nisantar da kanka daga gareni if not..."
Tayi kwafa ba tare data k'arasa ba ta dauki mukullin mota da jakarta ta haye sama.
Dariya gayun suka sanya mishi,wani dake can gefe yana kokarin jona socket jikin TV ya d'ago mishi hannu
"Sorry Baaba,wannan fa babban goro kake gani sai magogin k'arfe. Ka kiyaye a zauna lafiya."
Wanda aka kira da baaba ya shafa kumatunsa yana murmushin takaicin marin da Baby tayimishi kafin yayi kissing hannunshi
"Me takeji dashi? Kud'i ko kyau?"
"Babu wanda bata ji dashi,kasan babu abunda zaka nuna mata don ubanka.Da kud'inka tsohonka kake tutiya,ita kuwa harkarta har da sa'annin ubanka da gayu irinmu da suka dame tsoffinmu a kud'i da komai Baby gogayya take dasu."
Baaba ya jinjina kanshi yana murmushin da shi kad'ai yasan manufarsa kafin yayi wuf yabar wajen. Suka k'ara sanya dariya,banda Manal wacce takeji tamkar ta tashi da kifawa Musty mari yanda yake ta kod'a Baby. A fusace ta mike zaune zatayi magana saidai ta fasa sakamakon kid'an da ya cika ko'ina na gidan. Nan wasu suka mik'e suka hau casu alhalin ga kiran sallah can na magrib yana tashi a masallatan unguwa.(Allah Ya shiryemu,amin.)
Baby tasleem kuwa tana shiga d'akinta wanka tayi na musamman ta fito ta k'ara mulke jikinta da mayuka da turarukanta tsadaddu kafin ta shirya cikin wata gown mai tsaga a gefe gefenta,tun daga gwuiwa har k'asa. Ta k'ara gyara gashinta,ta fesheshi da Hairsprays kala kala. Kafin tayi zaman shafa jan farce a yatsunta kalar skyblue(wato kalar gown dinta). Ta kwashi awa kusan uku gaba daya yayin wankan da komai nata na shiri. A lokacin da take jiran bushewar faratan nata ne,Dalal ta turo k'ofa ta shigo. Itama ta had'e cikin riga da wando matsastsu masu bin jiki. Sai taunar cingam takeyi na yan bariki ta rike k'ugu tana duban Tasleem wacce kallo d'aya tayi mata ta madubi bata k'ara dubanta ba.
"Zaki gidan Momi ne ko muyi gaba?"
Kamar bazatayi magana ba,har ta k'ular da Dalal.
"Kuje,zan biyoku. Hibba ta jirani mu wuce tare."
Harararta Dalal tayi kafin tayi gaba tana jan tsaki yanda Baby bazata jiyota ba. Ta iske Hibba cikin shiri zaune a saman mota
"Hakimar tace kiyi jiranta ku taho tare. Munyi gaba,kinsan Momi batason a b'ata lokaci."
Hibba tayi murmushi domin tasan yanda Momi ke ji da Baby ko don masu gidan ranar da take kai mata a kowane sati,domin nata kyautar ga Momi yafi na dukkansu yawa.
"Kada ku damu kuyi gaba."
Manal ta bud'e wutar hon,da azama Dalal ta shiga suka tafi. Basuyi mintuna da barin gidan ba,Baby ta fito cikin takunta na jin ita d'in ta isa tana tafe ko'inanta yana rawa,tana amsa waya tamkar bataso. Hibba dai kallon ikon Allah takeyi,har ta soma zargin kodai Baby 'yar wata basaraken ce? Haka tayi ta kallonta ita kuwa batasan ma tana yi ba,mota ta bud'e ta shiga ba tare da ta cewa Hibba uffan ba. Don kanta itama ta bud'e gidan gaba ta shiga. Minti uku da soma tafiyarsu,Hibba ta fahimci da shahararren mai kud'in nan Baby take waya, wato Alhaji Ridwan Naira. Gudu takeyi kasancewar dare ne,hakan yasa tafiyar mintuna talatin,sai gashi minti goma sha biyar ya kawosu gidan MOMI......!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(04)
Falo ne babba,cike yake da matasan mata da manyansu. Kowacce tana ji da kanta da ganin tafi 'yar uwarta. Wacce aka kira fa Momi tana hakimce a saman kujera mai zaman mutum biyu ta kishingid'a tana cin tuffa. Kallonsu takeyi d'aya bayan d'aya fuskarta dauke da murmushi. Kowaccensu tasha shiga ta alfarma,saika rantse wani shagalin akeyi. Daidai lokacin Baby ta sanyo kai,a bayanta Hibba. Matasa da yawa dake mutanenta ne,suka hau jinjina da ihu
"Shegiya Baby,manya a baku naku daban."
Ta sakar musu murmushi mai bayyana hak'ora tare da mimmik'a musu hannu suna cafkewa. Manyan kuwa gaisheshu tayi kafin ta isa ga Momi wacce ta zuba mata ido tana murmushi. Hannu ta dunkule,alamun jinjina
"Na gaida uwata,ranki ya dade tuba nake."
Momi ta ja hannunta ta zauna da ita gefanta tana dariya ga hakoran Makkah farare a hakoranta biyu na gefe da gefe.
"Bakya laifi gareni baby."
Daga haka Momi ta juya don soma abunda ya tarasu. Magana ce aka cigabansu a harkokinsa. Ta kara gargad'insu akan su kiyaye kada su bari ciki ya shiga jikinsu koda wasa. A karshe ta dubesu sosai
"Maganata ta karshe ku sani, babu aure a tsarinmu. Nasha sanar maku koda ya kasance zakuyi auren,toh fa baifi na wata uku ba kin fito. Auren ba talaka ba,mai hannu da shuni,ki tabbatar kin tatso mana mai yawa kafin ki datse igiyar auren naki. Wannan shine jawabina. Batun balance kuma,ina jiranku babu wacce batasan acc.no. dina ba."
Haka suka jima suna tattaunawa kafin taro ya watse,Momi ta dubi Baby wacce tayi haramar tafiya. Lokacin karfe sha biyu da mintoci
"Baby baby,kodayaushe tauraruwarki kara haskawa takeyi. Ba daga kananun ba,daidai da manyan suna son mu'amala dake. Ina kuma ga an lek'a ga Hajiyoyinmu duk da dai kin nuna wannan baya kanki yanzu."
Baby tayi murmushi ta girgiza kanta
"Momina kenan,me zanyi da jinsi irin nawa? Wannan babbar kazanta ce, wannan dinma da nakeyi fatana nan gaba na daina."
Momi ta kyalkyale da dariya tana mai dafa kafad'ar Baby
"Babu ranar da wannan fatan naki zai tabbata kuwa,zan maki uzuri da alama bakisan alfanun jinsi ba sai nan gaba."
Baby tayi murmushi mai had'e da jan numfashi
"Ba halina bane,baya daga abunda nake sha'awar aikatawa. So,in sha Allah bazan tab'a bin wannan hanyar ba."
"Ja'irar kaya,ashe har yanzu kinsan da sunan Allah? Toh ba laifi muje zuwa."
Abun sai ya bawa baby dariya,ta d'an dara kafin ta mik'e tayi hanyar fita
"Momi kenan,na barki lafiya."
******
Mutum ne matsakaici,mai dogon fuska,yana da matsakaicin hanci saidai akwai magana(idanu). Girarsa a cike kuma bak'i wuluk,kamar dai yanda sajensa da gashin kansa yake. Fari sol,zubin Fulani.
Zaune yake a ofis yana aiki akan Laptop. Hankalinsa gaba d'aya ya tafi ga aikinsa,kallo d'aya zakayi mishi kasan yana hutawa. Daidai lokacin aka bud'e kofar gami da yin sallama. Ba tare daya kalli mai sallamar ba ya amsa ciki ciki kasancewar ransa a b'ace yake dashi. Ya k'araso da fara'a ya zauna
"An gaida mutumina,ba fad'a mai ya kawo gaba kuma? Ace har ka iso garin nan saidai don rashin mutunci ko waya bakayi domin sanar dani ba sai a bakin kanwarka na tsinci labarin."
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(05)
Har ya gama maganarsa baice mishi komai ba. Ganin haka ya buga tebur wannan yasa shi watsa mishi wani irin kallo kafin ya karkato yayi juyi da kujerarsa yana fuskantarshi. Fuska a daure yace
"Kana da kunyar takowa ofishina bayan wulakancin kayimin?"
Cikin rashin fahimta,KB ya zuba mishi ido kafin ya tambayeshi
"Me kake nufi wai Haris? Nifa bansan takamaiman laifin dana aikata ba."
Ya dubeshi kadan kafin ya girgiza kai
"Jiya,(around 6:00pm),na had'u dakai anan wajejan sultan road. Saidai abun mamaki nayita hon baka tsaya ba saida kyar,karshe ma don rainin hankali kak'i fitowa daga motar. Saidai a yanda ka nuna yanzu ya tabbatar min ba kaine cikin motar ba saidai tabbas lambar motarka ce. Na soma tunanin direbanka ne,toh a gaskiya ka chanja direba,domin bakayi dace ba wallahi da zan ganshi zai sha mari ne...."
Kb ya katseshi
"Tsaya don Allah,gayamin menene ya faru?"
Haris ya labarta mishi,ya k'arashe da cewa
"Mercedes Benz dinka ce, kada kaso kaga gudun da direbanka ke...."
KB ya katseshi a kunyace
"Oh,Baby ce a ciki fa."
Haris ya yamutsa fuska
"Who the hell is Baby?"
Kb yayi murmushin basarwa
"Wata cousin d'in Mamina ce,ta ari motata ne tun kusan (last two days.)"
Haris ba don ya yarda ba,sai don kawai bai fiye bin kwakkwafin abunda bai shafeshi bane,ya gyada kanshi
"Ok."
Daga haka suka bar zancen suka fad'a hirarsu.
*****
Kabir Idris Babangida da Haris Aliyu Kazaure. Aminan juna ne,wadanda amintarsu ta samo asali tun daga iyayensu maza wadanda suma a baya can makwaftaka ta had'asu tun suna kauyensu na Kazaure kafin Allah Ya azurtasu a garin Kano. Kowannensu yayi gini na gani na fad'a ya dawo birnin Kano da zama.
Makaranta d'aya Haris da Kabir sukayi. Har ya zamana sun karanci course d'aya,wato business.
Kabir shi kad'ai ne d'a a wajen mahaifinsa Alhaji Idris. Shi kuwa Haris,su biyar ne. Saboda zumunta dake tsakanin iyayensu wadda bata wasa ba,ya sanya Alhaji Aliyu daukar Haris tun yana d'an shekara biyu ya damk'awa Alhaji Idris da matarsa Hajiya Jamila. Sunyi murna matuk'a domin Allah Ya sani,tun Haris na jariri suna matukar kaunarsa,kai bama su kad'ai ba. Mutane da yawa suna kaunar Haris saboda kyawu da farin jinin da Allah Ya bashi. Hajiya Aisha kuwa,mahaifiyar Haris mace ce mai alkunya wannan yasa ko kusa bata nuna damuwarta akan wannan kyautar ba tunda ga YASMEEN da sauran yaranta uku a gabanta.
Haka Kabir da Haris suka taso cikin kaunar juna da tsananin gatan da ake nuna musu. Rayuwarsu saita burgeka na yanda suka shak'u.