← Book details African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals Local reading mode
READING PART 18 OF 35

Sashe 18

African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals · about 4 min read

*****
Baby ta dakata tana mai sheshshekar kuka sosai,Haris cike da tausayawa ya daure yace

"Kiyi hakuri Tasleem."

Kamar bazatayi shiru ba,har ta soma rikita mishi tunani don hakikanin gaskiya ya tsani kukan mace. Dakyar ta nutsu ta goge fuskarta da (handkerchief) din daya bata. Kafin ta zubamishi jajayen idanunta wadanda sukayi kusan kwana uku suna zubar da ruwan hawaye.[2/3, 21:29] Rufy: 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(35) "Haris a wannan ranar Usman ya ketamin haddina.
Yayi amfani dani ba a hayyacina ba." Ta numfasa kafin
ta cigaba "Baccin nan bai sakeni ba sai wajen magriba.
Nayi mamakin irin radadin da naji a gabana. Na yunkura
da zummar mikewa daga shimfidar da nake kwana na
katifa a karamin dakin yar aikin meena wacce zuwana
yasa ta koma sashen raliya da aiki,saidai ko kalilan ban
iya motsawa ba. Kawai sai na fashe da matsanancin
kuka,a hankali kuma tunanina ya dawo da lemun dana
sha hakanan cikin magagin bacci na hango fuskar
Usman lokacin daya kwasheni zuwa dakina. Nayi
azamar duba pant dina,jinin dana gani ba karamin
dagamin hankali yayi ba. Ihu nasa hadi da fashewa da
kuka. Yayi daidai da shigowar Meena da Gwaggonta,wuf
suka fado dakin. Meena na fadin "Wane irin iskancin
banza ne zaki...." Sauran maganarta ta makale ganin
halin da nake ciki,gwaggo ta matso tana buga salati
"Mun shiga uku,Aminatu kinga abunda nake gani? Yau
tsinanniyar nan ta janyo mana abun magana." Meena ta
dubi Gwaggo tace"Wa?! Wallahi badai dani ba! Kanta ta
janyowa,karuwae banza da wofi. Bazaki janyomin zagin
mutane ba." Daga haka ta hau buguna kamar Allah Ya
aikota. Ihu nakeyi ina kuka kakkarfa saboda radadin
daya hademin biyu. Ta sakeni tayi wuf ta fita ina nan
zaune ina jan jikina zan shiga bandaki ta dawo rike da
bokiti,kafin na ankara ta gwalemin kafafuna ta
watsamin. Ai bansan sadda na saki razananniyar k'ara
ba saboda azabar ruwan zafin nan,daga haka na sume.
Ban farka ba sai a gadon asibiti. Nayi mamakin ganin
har da Abba cikin wadanda ke tsaye a kaina,sai Raliya
da kuma Gwaggon Meena. Na dubesu daya daya kafin
na maida dubana ga Abba cikin matsanancin tsanarsa.
Dukkansu babu masoyina ciki,makiyana ne. Bansan me
suka kawoni ayimin ba bayan sun rigaya sun gama da
rayuwata,inama ace sun barni na karasa rayuwata
anan. Na kauda kaina ina mai jin saukin radadin azabar
da nakeji a gabana bansani ba ashe wai har dinki
akayimin. "Munafuka,ke juya keyarki mana kin jawo
mana zagin mutanen gari. Haba Tasleem,me muka
rageki dashi da har sai kinje ga bibiyar yan iskan gari?
Har nawa suka baki kika basu kanki? Tir!" Cewar Raliya
tana matsar kwallar munafunci. Bance uffan ba,jira
nake naji abunda zai fito daga bakin Abba saidai baice
komai ba fuskarsa cike da bacin rai ya nufi hanyar
ficewa. "A'a Doctor ina zakaje kuma?" Cikin takaici ya
fice baiko k'ara kallonmu ba. Yana fita itama Gwaggon
Meena tace zata koma gida don ba aikin kula dani ya
kawota gidan ba. Bayan fitarta Raliya ta tuntsire da
dariya harda hawaye,idona na runtse inaji kamar na
mike na janyota na d'irka. Naji maganarta daf dani
"Usman ya biyani! Da ace tun farko nasan kudurin nan
yayi a kanki da tuni na bashi goyon baya hakanan da
banji bacin ran kulaki da ya dungayi ba. Ki godewa
Allah ma da abun ya tsaya a iya nan. Na tsaneki! Na
tsani uwarki da dukkan tsatsonta! Nafison ganina da ya
yana kadai a gidan ubanki.! Sai kiyi jinyar kanki!" Ta
kara tuntsirewa da dariya ta juya zata fita, wallahi
bansan lokacin dana fisgota ba na janyo almakashin
dake ajiye cikin tasa a gefen kaina. Saitin wuyanta na
sanya kafin na soma magana a fusace "Kina zaton kinci
galabar abunda kikayimin ko? Toh wallahi ki ajiye a
ranki saina dauki fansa akan Usman! Sai ya gane shayi
ma ruwa ne RALIYA! Don ina shanye dukkan wahalhalun
da kuke sanyani ba wai hakan yana nufin tsoronku
nakeji ba! Kawai dai biyayya nakeyi ga MAHAIFIYATA!
Wallahi ko ba dade ko ba jima sai na dauki FANSA.!" Na
wuncikalar da ita,na ajiye almakashin,a fusace tayo
kaina wanda hakan yayi daidai da shigowar nos. Ba don
taso ba ta bini da mugun kallo,na tabbata tayi mamakin
karfin hali irin nawa,da shekarunta da komai nayi mata
haka? Hum, bari dai akai mutum bango Haris, wani
abun da bai taba zaton zai aikata ba sai ya aikatashi.
Kwanana uku a asibitin Abba,wata nos me mutunci ke
kula da lafiyata bansani ba ko bisa umarnin Abban ne
kodai a'a. Ni nake lallabawa nayi wankana nasa sutura.
A rana ta hud'u ne ina zaune ina shan lemun b'awo naji
sallamar wanda banyi tsammanin ganinsa nan kusa ba.
YAYA ABDULLAH. Gaba daya ya chanja yayi
haske,saidai fa ya rame akan yanda naga hotonsa
kwanakin baya. Sanye yake da shirt da wandon jeans
bak'i ya dora brown jacket a samanta. Farin cikin
ganinsa ya koma ciki sakamakon yanayin dana gani a
fuskarsa. Kallon da yakeyimin ba karamin kad'amin 'yan
hanji sukayi ba. Salati na shigayi a zuci kafin na
russunar da kaina sai hawaye.......
Chapter 18 · 0% Book details