← Book details African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals Local reading mode
READING PART 33 OF 35

Sashe 33

African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals · about 8 min read

Washegari wajejan uku na rana,mutan gidan basunan sunje gaisuwa acan k'asa gidan wani almajirin Liman wanda ya rasu sakamakon hatsari. Tasleem ce zaune a tsakar gidan cike da tunanin kawayenta. Tunani takeyi ko Manal tayi aure? Toh Dalal da Hibba fa ya suke? Tunanin neman layin Hibba ya fadomata. Bata mantawa saboda saukin lambar wayar Hibba ta haddaceta a kwanyarta har akwai ranar data taba karantowa sukayita mamaki har hibbar domin ko ita bata da haddar lambarta aka. Da azama ta mike tayi daki,wayar dai data tsana ita ta dauko ta dawo ta zauna. Ta duba akwai kud'i har dubu daya a ciki. Baki ta tab'e wannan kam a wurinta karamin kudi ne bazai burgeta ba. Batason wulakanci a rayuwa. A nutse ta jera lambar ta kira. Akayi sa'a ta hau ringing.

Hibba alokacin tana zaune a gefan ruwan Tiga Dam ita fa sabon saurayinya,HAYAT. Tunda ta soma bariki bata taba tsintar kanta dumu dumu cikin soyayyar wani d'a namiji ba illah Hayat. Matashi mai ji da naira da hutu. Ganin unknown number yasa ta jan tsaki ta ajiye wayar. Hayat ya dafa cinyarta yana kasheta da kallon kauna

"Lafiya dai my beb."

"Wata number ce da bansan da zamanta ba."

Acan kuwa baby tsaki taja sai lokacin ta tuna ko ita akayi kira da unknown no.a wayarta bata fiye dauka ba. Ta yanke shawarar tura sak'o.

"Hibba,it's me Baby. Pick d call."

Tana shirin turawa yayi sallama ya sanyo kai. Ta amsa bayan tayi saurin ajiye wayar a gefe. Hankalinsa yayi kan wayar cike da zargi kafin ya basar ta hanyar fad'in

"Ina mutan gidan?"

Itama fuskarta ba yabo ba fallasa saidai kirjinta sai bugu yakeyi.

"Basunan sunje gidan gaisuwa."

Bata ankara ba taga yasa hannu ya dauki wayar yayi tsai yana karanta sak'on....

'YAR BARIKI

©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)

(62)

Fuskarta a tamke baisan sadda ya daga wayar ya bugata da bango ba kafin ya fisgo Tasleem wacce ta mike tsaye ganin yanda ya yiwa wayar. Murde hannunta tayi ya komar dashi ta bayanta,har suna shakar numfashin juna ita kam na tsoro ne. Tayi ta murza hannun saidai fa iyaka yatsunta ne don kuwa ba rikon wasa ta samu daga wajen maza ba.
Cikin kakkausar muryar da batasan Haris da ita ba yace

"Menene gaminki da ita a karo na biyu?! Me kike shirin yimin? Daga yau ki sani cewa banason mu'amalarki da kowace abokiyar shaidancinki ta baya! Wannan shine gargadina a gareki na karshe."

Daga haka ya saki hannunta,tayi saurin ja baya tana zubar hawaye. Ta dubeshi ido cikin ido kallon nan na alamar tambaya(Kaine kuwa?..lol). Ya kauda fuskarsa,har ya juya zai fita kuma ya dawo baya ya dauki wayar wacce tuni screenface dinta ya tsage,sim d'in ya fidda kafin ya cilla wayar jikinta daga haka yayi gaba cikin takunsa kamar wani basarake.

Ta dubi hannunta wanda har yatsun Haris sun bayyana jikinsa,kafin ta lumshe ido ta zauna d'abas akan sumintin tsakar gidan tana kuka. Karshe dai mikewa tayi ta dauki wayar tayi daki. Jimawa kadan taji sallamar Baharu,bata ko fito ba har ya shigo ya miko mata simcard sabo.

"Gashi inji angonki,yanzun nan suka wuce. Yace ki sanya a wayarki zai kiraki."

Bata ko kalleshi ba ballantana yasa ran zata karb'a,ganin shiru ya ajiye ya fita yana mai jin haushin yanda antin nan tasa ta kasa gano kaunar da Haris keyi mata.

*****
Tsaye yake a farfajiyar hotel din na Nicon dake birnin tarayyar Abuja yayinda yake cike da farin ciki da walwala na ganin wacce bai taba tsammatar ganinta ba a wannan lokacin. Ta karaso bayan ta cewa wacce suke tare tayi jiranta minti biyu. Ta wulka ido irin na kwararrun 'YAR BARIKI kafin ta sakar mishi murmushi wanda ya kara fiddo zahirin kyawunta na asalinta na buzuwa.

"KB manya daman ana ganinku?"

Kb yayi yar dariya

"Gaisheki DALAL,kun b'ata b'at a garin ta dabo. Ashe kina nan kina holewarki."

Dalal tayi dariya

"Kai haba,mu a suwa? Kaine dai gakanan sai fresh kakeyi,nikam tunda mun hadu yau bazan bari ka gudu ba saika kaini na gaisa da k'awarmu. Wallahi just one week kenan da bamu ganta ba amma kewarta ta cikamu."

Cikin rashin fahimta yace

"Wai Dalal kuna zaton Baby tana tare dani ne?"

Tayi k'as k'as da cingam tana kallonsa shek'ek'e

"Bangane manufarka ba KB? Wai bakwa tare da Baby? Toh ina take?"

Yayi wani d'an malalacin murmushi kafin ya zura hannu aljihun wandon jeans nasa. 'Yan dubu dubu ne da baisan ko nawa bane ya zaro da d'an kaurinsu ya mik'a mata

"Idan basu isheki ba kiyi magana na k'ara maki Dalal,fatana da burina bai wuce ki taimaka wajen lalubomin inda kawarku take ba. Ko kuma idan kinsan wani labari game da rayuwarta please ki sanarmin sauran binciken zanyi da kaina."

Ta shinshina kud'in,ita kam ai kud'i koyaushe basu tsufa awajenta sabbi ne. Ta tura a jakarta bayan ta tuno da Manal data tab'a tabbatar mata cewar ita kadai tasan wacece baby da kuma garinsu saidai bisa amana ta gayamata ita kam bazata fadawa kowa ba.

"Aikinka zai cika muddin zaka saki kud'i Hajy KB."

Shima kallo yakeyi mata na kwararren 'Dan Bariki,kafin ya shafi sumarsa yana dariya

"Ba abune mai wuya ba,kina iya bani acc.no dinki hade da phone.no."

Ya amsa kafin suyi sallama ya shige don gabatar da abunda ya kawoshi cike da matsanancin farin ciki....!

'YAR BARIKI

©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)

(63)

A gajiye ta k'arasa kujerar tangameman falon wanda yaji kayan alatu ta zauna tana fadin wash! Manal ta zube gefanta suna dariya

"Shegiya Dalal,kina cin karenki babu babbaka nikam ina nan kamar kullin kayan wanki. Ke a yanda na lura anya kuwa Alhaji Ubalen nan idan munyi aure zai barni na fita wani wajen? Mahaukacin kishi gareshi,ji fa dai daga maganar aure har ya killaceni gidansa,babu wata harka wai yana bukatar nayi istibra'i,mts."

Dalal ta mike zaune tana dubanta bayan ta kyalkyale da dariya

"Kefa baki fahimci wannan d'an fulanin naki ba,toh wallahi dagaske yakeyi sonki yakeyi da gasken gaske."

Ta tabe baki

"Barshi dai yayita haukansa,wani sa'in ni kaina ina jin kauna da tausayinsa wallahi ya iya lallab'a mace ne. Ke nasa fa an bincikamin asalin aurensa da matarsa,ashe dole yabi umarnin mahaifinsa ya aureta har yanzu da suke da yara biyar bai taba sonta ba. Kinsan fa ba wani shekaru ne dashi ba,arba'in da wani abu yake."

"Yara biyar? Kuma ace ba soyayya? A ruwa tasha?"

Manal ta harareta da alama maganar ta bata ranta,Dalal kam murmushi tayi gami da jin tsoron auren wata uku ya koma na har abada....

"Wai kuwa kina samun Baby a waya? Nasha nemanta naji switched off."

Jin an ambaci Baby ya tunasar da Dalal abunda ya kawota. Ta zabura ta matso kusa da Manal har tana firgitata.

"Ke nima bansan inda ta lulluk'a ba,anya ba garinsu ta koma ba?"

Manal tayi shiru tana tunani,daman tun sadda baby ta fito da shigar hausawa jikinta ya bata cewar Kazaure zataje.

"Gayamin sunan garinsu mana,kinga sai na gano mana ko lafiya?"

Cewar Dalal,Manal ta numfasa

"Banason karya alk'awarin dana daukarwa baby na cewar bazan sanarwa kowa ba game da garinta ko asalinta,wannan shine..."

"Haba Manal, bamusan halin da take ciki ba,idan ance ma tana bukatar taimako babu k'arya a ciki. Idan kin fadamin wa zan gayawa,just give me full address ni kuma zan binciko mana lafiyarta koda a b'oye ne. Kinga idan bata garin sai mu sanya cigiyarta ko kuma mu bi abokan harkarta gaba daya tunda ba wani yawa garesu ba muji ko suna tare."

Manal tace "KB fa?"

"Basu tare da KB,domin kuwa Momy tace min yazo nemanta wajenta amma bai sameta ba."

Dalal tayita siyasance Manal har saida ta samu ta shawo kanta tayi na'am da hakan batare data bata ko sisin naira biyar ba. Duk da dai Manal bata da tabbacin baby can tayi amma bata zaton zata je gidan yayanta da mahaifinta domin a yanda ta nunawa Manal ba karamin tsana tayi musu ba,mammanta ce ma take son sanyata ido wataran.
Ta gayamata ta rubuta.

"Idan kinje Kazaure ki nemi gidan babban limamin garin, nan ne gidan da nasan watakila ki samu labarin Baby."

Bayan ta gama rubutawa,Dalal ta tuntsire da dariya

"Amma Baby anyi shegiyar yarinya. Don ubanta ita daman d'iyar Liman ce take bura uba haka?"

Manal ma dariyar tayi,saidai tsoron kada Baby ta kamata da cin amanarta yasa bata gayawa Dalal cewar gidan kakannin baby ne ba ta wajen mahaifiyarta. Da zataji waye uban baby,zata fahimci cewar lallai Baby ta ketaresu kota ina tunda ba kudi ne ya fiddota bariki ba.

******

Kishingide yake a kujera mai zaman mutum uku,Yasmeen tana gefe tana mammatsa mishi kafafuwa yayinda ya maida hankalinsa ga kallon Ball. Wayarsa tayi k'arar shigowar sak'o

"Mikomin wayata."

Ya fada ba tare daya dauke idanunsa daga kallon ba. Ta dauki wayar ta mik'a masa. Ganin sak'on daga Dalal ne,ya sanyashi mikewa zaune.

"Kazaure gidan babban Liman,duk wanda ka tambaya za'a kaika. Idan kaje babu nasara zan k'ara bincika mana."

"Wuuu!"

Shine ihun murnar da KB ya saki. Yasmeen ta iso gareshi

"Lafiya prince?"

Ya mike ya dagata sama yana juyi da ita suna dariya. Babu kamar Yasmeen wacce take jin mamakinsa da kuma farin ciki. Yaushr rabon daya kula da lamarinta haka? Kai a ranar dai ya faranta mata fiye da tsammaninta. Shi kuwa Allah Allah yakeyi weekend yayi yaje ga Baby shi koda bai ganta bama ya samu shiga wajen liman. Domin kuwa yasan kwarai wanene Liman saidai bai taba kawowa shine uban tasleem ba. Har ya soma mamakin abunda zaisa Tasleem wacce ta fito gidan manya haka ta b'ata rayuwarta da barikanci. Meyayi zafi haka toh?

******
Karshen sati nayi,ya yiwa matarsa sallama da sunan zaije Kazaure gaida kakanninsu. Taso ya tafi da ita saidai koda ta matsa da magiya ya bata rai a dolenta ta hakura tana ji tana gani yayi mata sallama ya wuce airport domin hawa jirgin zuwa Kano.

Tunawa da tayi cewar tun angoncewar yayanta bai nemeta a waya ba yasa tayi kiransa. Yana dauka ta soma shagwaba murya

"Haba yayana ashe daman akwai sadda zaka share lamurana? Nikam har na soma fushi da yayyuna nasan waya dasu ya janyo ka shareni."
Chapter 33 · 0% Book details