Sashe 22
African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals · about 8 min read
"Haka na tattara kayana na hada da muhimman takardun makarantana da kuma hotunanmu da duk dai abunda nasan zai amfaneni ciki kuwa harda Atmcard dina. Mai taxi na samu bayan munyi cinikin inda zai kaini na shiga. Abu na farko da na soma yi shine,rubuta wasika na damk'awa maigadin gidansu Rilwan,nace ya bawa mahaifinsa a karshe nayi mishi sallama na hau taxi,muna cikin tafiya ina kuka,naji maganar mai taxi yana fadin"Kinga Hajiya idan babu damuwa ga wata can da alama itama tashar ta nufa ko zamu dauketa?"
Bance kala ba duk da nasan shatarsa nayi ina da ikon cewa aa saidai tashin hankalin dake gabana yafi gaban na bata lokacina anan. Ya tsaya ko kallon matar banyi ba,illai kuwa itama tashar dikkon ta nufa. Tana zama wani kamshi ya dokarmin hancina,duk da haka dai ban kalleta ba saidai na share hawayena sai numfarfashi nakeyi.
"Sannu ko? Nagode fa."
Tace dani, na dan kalleta,tabbas da ganin shigarta kasan tana hutawa kuma tafi kama da irin masu kud'in nan. Sanye take da wata atamfa yar ubansu tasha kwalliya ko yatsunta ka kalla kaga jerun zobbuna biyu na gwal sun wadatar dakai ka gane ba karamar Hajiya bace. Ita dinma ni take kallo fuskarta dauke da murmushi,wannan yasa na maida mata martani da murmushin da baikai zuci ba kafin na maida dubana ga gefen titi. Ina jinta tana waya kamar dai mota akayi niyyar aikomata don naji tana surfa ashariya tana fadin ita tafi karfin wulakanci,yasan yana. Tsoron matar tasa ya kwana da ita a hotel? Anan na fahimci lallai ba macen arziki bace. Har muka isa waya takeyi tun suna hayaniya har dai akarshe ta hau tuntsira dariya tana fadin babu komai ma zatabi motar kasuwa.
Da isarmu na sauka,zan biya mai taxi ta dakatar dani tace ai nayi mata alfarma don haka kada na damu itama yimin zatayi,ina kallo ta biya. Nayi godiya,ina shirin kinkimar akwatina ta zagayo ta dubeni
"Ina zaki ne?" Ganin da nayi mata na wacce ta fini shekaru yasa na amsa ba don naso ba don ta soma bani haushi ta soma takuramin.
"Kano." Tayi dariya"Nima nan na nufa,tsaya a sama mana mota."
Nidai bance uffan ba,abunda na soma tunani bai wuce ma ina zan nufa ba a Kanon? Waye zai amsheni da cikin shege??
Banyi mamaki sosai ba ganin Hajiyar nan ta dauki shatar karamar mota mai zuwa Kano guda daya. Tace nazo muje,wallahi Haris banji ko d'arr wai na rashin yarda da ita ba. Na sadakar idan ma yar yankar kai ce toh ta kaini a yankani na huta da bakar rayuwar da nake ciki. Koma dai menene alokacin ji nayi muje kawai.
Motar mu ta d'aga daga ni sai Hajiyar nan da direba,lokacin wajejan uku na rana. Daidai lokacin da muka soma tafiya wayata ta dauki kara,shaf na mance ban kasheta ba. Na duba,sunan wanda na gani yasa a fusace na kashe wayar na fiddo sim din na cusa dukansu a jakata. Me kuma rilwan zai min? Ina waigowa karaf muka hada ido da Hajiyar nan.
"Namiji ko?"
Mamaki ya kamani,tayi murmushi tana kashe ido na yan duniya "Ai bakin cikin mace bai wuce akan d'a namiji baiwar Allah. Tun ganina dake a farko na fahimci kina cikin matsanancin damuwa,idanunki kadai zasu tabbatarwa mutum kinci kuka kin koshi. Idan bazaki damu ba,zaki amince dani ko zaki sanar dani matsalarki? Ni kuma zanyi maki taimako daidai gwagwadon iyawata."
Na dubeta sai naji na aminta da ita. Hakanan na zayyane mata komai dangane dani da rayuwata. Ta jajinta min,na kara da cewa
"Babu abunda na tsana a yanzu kamar cikin nan Hajiya! Ki taimakamin don Allah ki kaini inda kikasan za'a ciremin shi."
Tayi murmushi ta rungumo kafadata
"Kinzo wajen share hawayenki BABY."
*****
Baby ta dubi Haris "Wannan itace Hajiya Hannatu Bariki wato MOMY. Itace ta sanyamin suna Baby wanda har ila yau ya bini, don wasu da yawa basu sanni da Tasleem. A gidanta na soma sauka inda kuma washegari ta kaini aka zubarmin da cikin jikina. Itace ta gogar dani a harkar bariki. Ita ta kasance tana nunamin hanyar da acewarta shi kadai ne jin dadin rayuwa babu wanda zai takura maka babu mai matsa maka. Tun ina tsoro har dai na bada kai bori ya hau,abun nufi dai ta shiga hadani da manyan alhazai wadanda cikin sa'a kowannensu rububina yakeyi. Komai Momi ita ta koyamin,Momi itace shugabarmu,yan mata da yawa da zauwarawa sanadinta suka rike kansu suka zama tantiran 'YAN BARIKI. Sai ya zamana nabar yayin dukkan manyan kayana,koda dai ba sosai daman nake sakasu ba nafi mu'amala da kananun. Saidai fa a lokacin ya k'aru sosai,Momi haka ta bada oda aka kawomin su kala kala daga Dubai. Haka nan babu kudina da ake tabawa,haka kawai jininmu ya hadu sosai da Momi tana ji dani kwarai da gaske. Duk da wasu kayan maye da Momi ke sha da sauran yan kungiya,bana shan komai sai taba,shima sai idan ina cikin matsanancin damuwa ko nishadi ban fiya sha sosai ba gaskiya."
Baby ta murmusa adaidai nan,da alama kuma abunda zata fadi,fari ne fat a wajenta.
"Daidai wannan lokacin ne,na shirya daukar fansa a wajen Usman. Ga Rilwan kuwa,Abbansa na zayyanewa komai a wasikar nan kuma inada tabbacin Abbansa mutum ne nagari da yasan ya kamata,kamar dai yadda nasan Rilwan da fadar gaskiya komai dacinta. Nasan bazai musa cewar shine yayimin wannan aika aikar ba. A yanda kuwa akayi na dauki fansar da taimakon Momi shine......."
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(42)
Prince,dattijo ne mai kimanin shekaru arba'in,sunansa na gaskiya Alhaji Shitu Ibrahim. Shine na kusa kusa ga Momi,hakanan wani suka ne a gwamnati. Yana da yaransa ko kuma ince maka 'yan dabansa da yake sanyasu kashe dukkan wani rai dake kawomishi matsala a rayuwa. Daidai lokacin da muka sameshi da bukatarmu yayi dariya yace"Wannan abu ne mai sauki ai,yarana da suke kashe rai wannan karamin aiki ne a wajensu. Saidai kuma nima inaso a bani abunda na jima ina marari amma an tsaya yimin yanga." Ya karashe dadm dariyar 'yan duniya yana kallona. Murmushi nayi don a duniya ji nake alokacin ko me Prince ke so zan bashi saboda ya gama yimin komai da na bukata. Ba shiri na harhada kayana muka wuce dashi. Acan ya had'ani da babban yaronsa nayi mishi bayanin abunda nakeso ayi. Farko dai nayi mishi kwatancen inda babban shagon Usman yake domin alokacin yaci gaba har ma ya fito daga kwari ya bude babban shagon kaya wadanda yake sarowa daga Dubai. Nayi umarnin a k'onashi kafin nayi musu iznin nakastamin rayuwarshi ta hanyar yanke mishi dukkanin kafufuwansa."
Baby ta dakata a yayin data tuntsire da dariya cike da jin wani irin nishad'i,Haris kuwa mamaki kwarai yakeyi ashe daman zata iya aikata mugunta har haka? Tunaninsa ya tsaya cak sa'ilin da dariyar dake kan fuskarta ta dauke ta koma zubar hawaye. Kanta ta girgiza cike da takaici
"Saidai Haris, nasan ban dauki fansa ba. Domin babu yanda za'ayi na dawo da budurcina kuma mutuncina. Ya rigaya ya cuceni ya cuci rayuwata tun farko."
Baby ta fada kafin ta kara duban Haris
"Yanda kuwa na lissafa musu babu ko tangard'a hakan suka aikatamin. Ita kuwa Raliya itama saida suka tabbatar da fitowarta ita d'aya tana driving wataran suka tareta suka daure baki da idanunta. Ba wani abu sukayi mata mai yawa ba illah dai jibgarta dana sanya sukayi,yayinda a karshe dayansu ya kusanceta. Kafin su yi mota biyu da daddare daya yana jan nata,sauran kuma duk suna motar baya, wajejan sha biyun dare kenan. Daidai kofar gidan ya dire ta kafin ya koma motarsu suyi gaba ban kara bi takansu ba. Koda suka sanarmin sun cikamin aikina sai naji kuma na fashe da kuka kafin na saki dariya. Momy taso shima Abba a dan tab'ashi saidai naji bazan iya ba."
Baby ta dubi haris cikin hawaye tace
"Ban dauki fansa ba Haris,ban dauka ba. Saidai bana nadama ko kadan akan abunda nasa aka aikata musu a rayuwa. Haris tafiyata taci gaba kafin na samu na sayi gida wanda anan nake da zama yanzu. A hanya ne kuma na tab'a buge Manal da kullin kayanta,bayan na kaita asibiti naji likitan yana sanarmin wai tayi b'arin juna biyu. Koda ta farfado take bani labarin cewa marainiya ce,marikinta yayi mata ciki. Kaji silar haduwarmu da Manal. Dalal da Hibba a club muka hadu dasu, anan kuma kawancennu ya d'ore kafin daga baya nace subar gidan hayar da suke zaune su dawo nawa. Ni na hadasu da Momy,kaji yanda alakarmu tayi tafiya. Wannan shine labarina Haris."
Haris ya numfasa kafin yace
"Kin tafka kura kurai da yawa a rayuwarki Tasleem,ciki kuwa babban shine fitowa da kikayi kika fada harkar bariki maimakon ki kame kanki da mutuncinki,a'a saima zuciya data kwasheki kika maida kanki karuwar gaske. Kinyi ganganci kin manta da dokokin addininki daya hanemu aikata zina. Kuskurenki na gaba kuma,daukar fansa da kikayi akan wadannan bayin Allah inda kika manta cewar Allah baya kyale wadanda suka zalunci bawanSa,kika manta da kalmar hakuri har kika ji a zuciyarki cewar lallai ke da kanki kin isa sakawa kanki batare da kinyi hakurin ganin Sakayyar Ubangijinki ba. Rayuwar da kikeyi Tasleem,rayuwa ce ta wofi wanda karshensa nadama. Na hakikance ba kwadayin abun duniya ne ya kawoki bariki ba illah kawai kuncin rayuwa. Haba Tasleem,a rayuwa akwai wadanda suka fiki shiga kunci da wahalar rayuwa. Ki godewa Allah ma a gefe kina da iyayenki da yan uwa, wasu fa basu da ko daya,wasu rayuwarsu har su mutu cikin kunci da bakin ciki sukayita amma basu fada karuwanci ba,basu nemi daukar fansa ba illah dai sun kasance masu tawakkali da mik'a zuciyoyinsu ga Allah."
Baby babu alamar jin haushin Haris a fuskarta saima kallo da take binsa dashi tana murmushi kafin daga bisani hawayenta su zubo. Ganin hawayen ya sanyashi tsayawa da maganarsa
"Ina fatan ban b'ata ranki ba Tasleem?"
Ta girgiza kai tana 'yar dariya
Bance kala ba duk da nasan shatarsa nayi ina da ikon cewa aa saidai tashin hankalin dake gabana yafi gaban na bata lokacina anan. Ya tsaya ko kallon matar banyi ba,illai kuwa itama tashar dikkon ta nufa. Tana zama wani kamshi ya dokarmin hancina,duk da haka dai ban kalleta ba saidai na share hawayena sai numfarfashi nakeyi.
"Sannu ko? Nagode fa."
Tace dani, na dan kalleta,tabbas da ganin shigarta kasan tana hutawa kuma tafi kama da irin masu kud'in nan. Sanye take da wata atamfa yar ubansu tasha kwalliya ko yatsunta ka kalla kaga jerun zobbuna biyu na gwal sun wadatar dakai ka gane ba karamar Hajiya bace. Ita dinma ni take kallo fuskarta dauke da murmushi,wannan yasa na maida mata martani da murmushin da baikai zuci ba kafin na maida dubana ga gefen titi. Ina jinta tana waya kamar dai mota akayi niyyar aikomata don naji tana surfa ashariya tana fadin ita tafi karfin wulakanci,yasan yana. Tsoron matar tasa ya kwana da ita a hotel? Anan na fahimci lallai ba macen arziki bace. Har muka isa waya takeyi tun suna hayaniya har dai akarshe ta hau tuntsira dariya tana fadin babu komai ma zatabi motar kasuwa.
Da isarmu na sauka,zan biya mai taxi ta dakatar dani tace ai nayi mata alfarma don haka kada na damu itama yimin zatayi,ina kallo ta biya. Nayi godiya,ina shirin kinkimar akwatina ta zagayo ta dubeni
"Ina zaki ne?" Ganin da nayi mata na wacce ta fini shekaru yasa na amsa ba don naso ba don ta soma bani haushi ta soma takuramin.
"Kano." Tayi dariya"Nima nan na nufa,tsaya a sama mana mota."
Nidai bance uffan ba,abunda na soma tunani bai wuce ma ina zan nufa ba a Kanon? Waye zai amsheni da cikin shege??
Banyi mamaki sosai ba ganin Hajiyar nan ta dauki shatar karamar mota mai zuwa Kano guda daya. Tace nazo muje,wallahi Haris banji ko d'arr wai na rashin yarda da ita ba. Na sadakar idan ma yar yankar kai ce toh ta kaini a yankani na huta da bakar rayuwar da nake ciki. Koma dai menene alokacin ji nayi muje kawai.
Motar mu ta d'aga daga ni sai Hajiyar nan da direba,lokacin wajejan uku na rana. Daidai lokacin da muka soma tafiya wayata ta dauki kara,shaf na mance ban kasheta ba. Na duba,sunan wanda na gani yasa a fusace na kashe wayar na fiddo sim din na cusa dukansu a jakata. Me kuma rilwan zai min? Ina waigowa karaf muka hada ido da Hajiyar nan.
"Namiji ko?"
Mamaki ya kamani,tayi murmushi tana kashe ido na yan duniya "Ai bakin cikin mace bai wuce akan d'a namiji baiwar Allah. Tun ganina dake a farko na fahimci kina cikin matsanancin damuwa,idanunki kadai zasu tabbatarwa mutum kinci kuka kin koshi. Idan bazaki damu ba,zaki amince dani ko zaki sanar dani matsalarki? Ni kuma zanyi maki taimako daidai gwagwadon iyawata."
Na dubeta sai naji na aminta da ita. Hakanan na zayyane mata komai dangane dani da rayuwata. Ta jajinta min,na kara da cewa
"Babu abunda na tsana a yanzu kamar cikin nan Hajiya! Ki taimakamin don Allah ki kaini inda kikasan za'a ciremin shi."
Tayi murmushi ta rungumo kafadata
"Kinzo wajen share hawayenki BABY."
*****
Baby ta dubi Haris "Wannan itace Hajiya Hannatu Bariki wato MOMY. Itace ta sanyamin suna Baby wanda har ila yau ya bini, don wasu da yawa basu sanni da Tasleem. A gidanta na soma sauka inda kuma washegari ta kaini aka zubarmin da cikin jikina. Itace ta gogar dani a harkar bariki. Ita ta kasance tana nunamin hanyar da acewarta shi kadai ne jin dadin rayuwa babu wanda zai takura maka babu mai matsa maka. Tun ina tsoro har dai na bada kai bori ya hau,abun nufi dai ta shiga hadani da manyan alhazai wadanda cikin sa'a kowannensu rububina yakeyi. Komai Momi ita ta koyamin,Momi itace shugabarmu,yan mata da yawa da zauwarawa sanadinta suka rike kansu suka zama tantiran 'YAN BARIKI. Sai ya zamana nabar yayin dukkan manyan kayana,koda dai ba sosai daman nake sakasu ba nafi mu'amala da kananun. Saidai fa a lokacin ya k'aru sosai,Momi haka ta bada oda aka kawomin su kala kala daga Dubai. Haka nan babu kudina da ake tabawa,haka kawai jininmu ya hadu sosai da Momi tana ji dani kwarai da gaske. Duk da wasu kayan maye da Momi ke sha da sauran yan kungiya,bana shan komai sai taba,shima sai idan ina cikin matsanancin damuwa ko nishadi ban fiya sha sosai ba gaskiya."
Baby ta murmusa adaidai nan,da alama kuma abunda zata fadi,fari ne fat a wajenta.
"Daidai wannan lokacin ne,na shirya daukar fansa a wajen Usman. Ga Rilwan kuwa,Abbansa na zayyanewa komai a wasikar nan kuma inada tabbacin Abbansa mutum ne nagari da yasan ya kamata,kamar dai yadda nasan Rilwan da fadar gaskiya komai dacinta. Nasan bazai musa cewar shine yayimin wannan aika aikar ba. A yanda kuwa akayi na dauki fansar da taimakon Momi shine......."
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(42)
Prince,dattijo ne mai kimanin shekaru arba'in,sunansa na gaskiya Alhaji Shitu Ibrahim. Shine na kusa kusa ga Momi,hakanan wani suka ne a gwamnati. Yana da yaransa ko kuma ince maka 'yan dabansa da yake sanyasu kashe dukkan wani rai dake kawomishi matsala a rayuwa. Daidai lokacin da muka sameshi da bukatarmu yayi dariya yace"Wannan abu ne mai sauki ai,yarana da suke kashe rai wannan karamin aiki ne a wajensu. Saidai kuma nima inaso a bani abunda na jima ina marari amma an tsaya yimin yanga." Ya karashe dadm dariyar 'yan duniya yana kallona. Murmushi nayi don a duniya ji nake alokacin ko me Prince ke so zan bashi saboda ya gama yimin komai da na bukata. Ba shiri na harhada kayana muka wuce dashi. Acan ya had'ani da babban yaronsa nayi mishi bayanin abunda nakeso ayi. Farko dai nayi mishi kwatancen inda babban shagon Usman yake domin alokacin yaci gaba har ma ya fito daga kwari ya bude babban shagon kaya wadanda yake sarowa daga Dubai. Nayi umarnin a k'onashi kafin nayi musu iznin nakastamin rayuwarshi ta hanyar yanke mishi dukkanin kafufuwansa."
Baby ta dakata a yayin data tuntsire da dariya cike da jin wani irin nishad'i,Haris kuwa mamaki kwarai yakeyi ashe daman zata iya aikata mugunta har haka? Tunaninsa ya tsaya cak sa'ilin da dariyar dake kan fuskarta ta dauke ta koma zubar hawaye. Kanta ta girgiza cike da takaici
"Saidai Haris, nasan ban dauki fansa ba. Domin babu yanda za'ayi na dawo da budurcina kuma mutuncina. Ya rigaya ya cuceni ya cuci rayuwata tun farko."
Baby ta fada kafin ta kara duban Haris
"Yanda kuwa na lissafa musu babu ko tangard'a hakan suka aikatamin. Ita kuwa Raliya itama saida suka tabbatar da fitowarta ita d'aya tana driving wataran suka tareta suka daure baki da idanunta. Ba wani abu sukayi mata mai yawa ba illah dai jibgarta dana sanya sukayi,yayinda a karshe dayansu ya kusanceta. Kafin su yi mota biyu da daddare daya yana jan nata,sauran kuma duk suna motar baya, wajejan sha biyun dare kenan. Daidai kofar gidan ya dire ta kafin ya koma motarsu suyi gaba ban kara bi takansu ba. Koda suka sanarmin sun cikamin aikina sai naji kuma na fashe da kuka kafin na saki dariya. Momy taso shima Abba a dan tab'ashi saidai naji bazan iya ba."
Baby ta dubi haris cikin hawaye tace
"Ban dauki fansa ba Haris,ban dauka ba. Saidai bana nadama ko kadan akan abunda nasa aka aikata musu a rayuwa. Haris tafiyata taci gaba kafin na samu na sayi gida wanda anan nake da zama yanzu. A hanya ne kuma na tab'a buge Manal da kullin kayanta,bayan na kaita asibiti naji likitan yana sanarmin wai tayi b'arin juna biyu. Koda ta farfado take bani labarin cewa marainiya ce,marikinta yayi mata ciki. Kaji silar haduwarmu da Manal. Dalal da Hibba a club muka hadu dasu, anan kuma kawancennu ya d'ore kafin daga baya nace subar gidan hayar da suke zaune su dawo nawa. Ni na hadasu da Momy,kaji yanda alakarmu tayi tafiya. Wannan shine labarina Haris."
Haris ya numfasa kafin yace
"Kin tafka kura kurai da yawa a rayuwarki Tasleem,ciki kuwa babban shine fitowa da kikayi kika fada harkar bariki maimakon ki kame kanki da mutuncinki,a'a saima zuciya data kwasheki kika maida kanki karuwar gaske. Kinyi ganganci kin manta da dokokin addininki daya hanemu aikata zina. Kuskurenki na gaba kuma,daukar fansa da kikayi akan wadannan bayin Allah inda kika manta cewar Allah baya kyale wadanda suka zalunci bawanSa,kika manta da kalmar hakuri har kika ji a zuciyarki cewar lallai ke da kanki kin isa sakawa kanki batare da kinyi hakurin ganin Sakayyar Ubangijinki ba. Rayuwar da kikeyi Tasleem,rayuwa ce ta wofi wanda karshensa nadama. Na hakikance ba kwadayin abun duniya ne ya kawoki bariki ba illah kawai kuncin rayuwa. Haba Tasleem,a rayuwa akwai wadanda suka fiki shiga kunci da wahalar rayuwa. Ki godewa Allah ma a gefe kina da iyayenki da yan uwa, wasu fa basu da ko daya,wasu rayuwarsu har su mutu cikin kunci da bakin ciki sukayita amma basu fada karuwanci ba,basu nemi daukar fansa ba illah dai sun kasance masu tawakkali da mik'a zuciyoyinsu ga Allah."
Baby babu alamar jin haushin Haris a fuskarta saima kallo da take binsa dashi tana murmushi kafin daga bisani hawayenta su zubo. Ganin hawayen ya sanyashi tsayawa da maganarsa
"Ina fatan ban b'ata ranki ba Tasleem?"
Ta girgiza kai tana 'yar dariya