Sashe 7
African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals · about 8 min read
"Look Haris, nasan na aikata ba daidai ba. Nasan zuwa yanzu ka dauki zafi dani baka kaunar sanyani a idanuwanka ma,amma don Allah kayimin uzuri wallahi kaji na rantse maka babu macen da nake mu'amala da ita a waje idan ba Baby Tasleem ba."
"Baby Tasleem."
Haris ya nanata sunan a ransa,sai yau ma yasan sunanta. Kb ya cigaba da magana
"Nasan ban kyautawa Yasmeen ba kamar yanda ban kyautawa kaina ba. Gaskiyar magana rabuwa da Tasleem abune mai matukar wuya agareni,shiyasa na yanke shawarar zan aureta a matsayin matata ta sunna."
Wani mugun kallo da Haris ya watsa mishi ya sanyashi kauda kansa cikin jin nauyi,ya numfasa kafin ya cigaba
"Yes Haris, kabar yimin irin wannan duban,raya sunnah nakeson yi ba wai zina ba. Duk da dai zuwa yanzu Baby tak'i bani had'in kai,ta nunamin babu abunda ta tsana kamar aure,wannan shine hakikanin damuwata. A matsayinka na amini kuma d'an uwana don Allah ka taimakamin da shawara."
Ba tare da ya jira cewar Haris ba ya mike tsam ya nufi hanyar fita cikin jin nauyin amininsa. Saida yakai k'ofa sannan ya dakata ba tare da ya juyo ba
"Ba hakan dana fada yana nufin na rabu da soyayyar matata ba,a'a. Inason Yasmeen matuka saidai inason raya sunna. Idan har ka amince da bukatana,ka taimakeni kayi jihadi wajen shawomin kan Tasleem domin cetomu daga wannan rayuwa please Haris. Goodbye."
Ya fice cikin sauri ba tare da ya juyo ba ballantana ya lura da irin firgicin dake akan fuskar amininsa.
Rike kai yayi yana mai runtse ido,gabansa na duka da sauri da sauri. Aure?!! Tsakanin Kb da baby tasleem?!!
Ya nanata a zuciyarsa,kafin ya kwantar da kansa akan kujerar ya runtse ido. Toh menene matsalarsa? Me zaisa zancen nan ya dameshi? Amma kuma dole zai dameshi ai,ko babu komai,kanwarsa ce fa Kb ke shirin yiwa kishiya da karuwa! Dole yaji tsanar auren,dole ne ya taya 'yar uwarsa kishi. Kishi mai tsanani.
Ya bud'e ido,kafin ya hasko halittar Baby da wayewarta sannan ya dawo ga kanwarsa wacce baby bazata nunawa kyau ba saidai ta fita a halittar jiki da kuma barikanci. Ita d'in ta kasance saliha,domin ko a gida bata fiye magana mai tsawo ba,sam, bata da hayaniya tamkar Haris d'in take. Wannan yasa duk cikin kannensa yafi tausayinta yafi sonta tasu tafi zuwa d'aya. Anya kanwarsa zata iya kishi da gogaggiyar mace irin Tasleem?
"Idan har ka amince da bukatana,ka taimakeni kayi jihadi wajen shawomin kan Tasleem domin cetomu daga wannan rayuwa please Haris."
Ya tuno zancen Kb,wannan ya nuna kenan yayi kokarin shawo kan Tasleem domin ta amince da bukatarsa na suyi aure amma sam,tak'i aminta.
Haris ya girgiza kai cikin takaici da bacin rai
"Tabbas Kabir bashi da kunya."
Ya fad'a a fili. K'arar wayarsa ta katseshi,ya duba yaga sunan Daddy. Da sauri ya d'auka. Bayan sallama da gaisuwa ne Daddy ya sanar dashi ya shigo yazo ofishinsa yana nemansa. Ya amsa kafin ya tashi a hanzarce ya nufi ofishin director kuma uba a gareshi,Alhaji Idris.
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(17)
Ya shiga da sallama. Daddy zaune akan kujerarsa sanye yake da riga 'yar ciki da wando ya rataye babbar rigar jikin (hanger). Idanunsa boye cikin farin gilashi. Ya bar danna laptop dinsa ya dago yana mai amsa sallamar d'ansa. Cike da girmamawa ya russuna ya gaida Daddy. Daddy ya amsa fuska a sake kafin yace
"Gaisuwarka bata k'arewa Harisu,ayi ta gida ayi ta ofis ko?"
Haris yayi murmushi mai bayyana hak'ora,baice komai ba ya zauna saman kujera bayan yayi kokarin d'an rage tsawo duk da hakan. Daddy yayi gyaran murya ya soma magana
"Haris,kwanaki sun shude sun zama watanni,ga watannin sun koma shekaru. Dan uwanka gashinan zaune da iyalinsa,a dukkan tsawon watannin nan mun barka ne akan ka nemi zab'inka gudun shiga rayuwarka. Saidai har kawo yanzu,shiru Harisu."
Daddy ya k'arashe cikin rarrauniyar murya mai russunar da zuciyar wanda ake yiwa. Haris baice komai ba yayi shiru yana sauraron Daddy
"Ga iyayenka nan girma yana k'ara hawan kanmu,wannan ya sanya naga tunda abun ya zama haka na baka zab'in zuwa can Kazaure,ka duba cikin 'yan uwanka dake can ko Allah zaisa ka sami wata cikinsu da zakaji nutsuwar zuciya akanta. Nidai fatana Allah Ya baka mace ta gari."
Haris yayi murmushi kad'an jin wannan batu da Daddy,a gefe kuma ya gama gaskata cewa ba k'aramin so Daddy da Hajiya sukeyi mishi ba,tamkar daga cikinsu ya fito. Ya tabbata gudun abunda zai b'ata ransa ne yasa Daddy b'ullowa ta wannan hanyar.
"Tashi ka koma ga aikinka Harisu,zan jiraka daga nan zuwa gobe duk abunda ka yanke toh,idan ma akwai wacce ka gani kake so toh Alhamdulillah. Wannan ma shi muka fi muradi. Allah Yayi jagora. Tashi ka tafi, ka turomin sakatare."
Cike da jin nauyi Haris ya mike yana mai amsawa da toh,ya fice jiki a sanyaye. Ya isar ga sak'on Daddy ga sakatare kafin ya koma ofis.
Kasa nutsuwa yayi,zancen Daddy yake ta juyawa. Toh wai ko zai koma ya sanar dashi cewar ya bashi zab'ine? Su zab'a mishi kawai mace tagari? Idan ba hakan ba ya zaiyi toh? Shi kam bai taba budurwa ba,a takaice ma basa gabansa. Allah Ya yishi mutum ba mai son magana sosai ba,baisan ta inda zai soma zuwa ga mace da zummar soyayya ba. Toh yace mata me? Ai shi kam matan ma bakin jini yake a gurinsu,bai mantawa dai da wata abokiyar karatunsa a Malaysia,Rahima. Babu irin bibiyar da batayi ba akan ya amince da soyayyarta amma sam bata samu fuska ba.
Bai mance ranar da Kb ya tursasashi akan sai ya saurareta ba. Suka shirya suka fita wajen shak'atawa inda tuni Kb ya yiwa Rahima maganar ta isa wajen zasu zo. Koda sukaje,nan suka hangeta zaune a kujera bakin swimmingpool na wajen. Kb ya daki kafadarsa yana dariyar mugunta
"Oya jeka,sannan don Allah kada ka bani kunya. Nasan wannan ne farkon tsayuwarka gaban mace a matsayin saurayinta,be a man!"
Harararsa yayi kafin yayi gaba cikin takunsa na nutsuwa,tana ganinshi ta mike tsaye domin girmamawa gareshi tana dariyar farin ciki.
"Sannu da zuwa Haris na."
Yayi dan murmushi kafin ya amsa ya zauna,hakan ya sanyata zama itama. Shiru ya ratso,ya zamana hirar ita keyi yayinda shi ya zama macen. Daga um,sai um um,ga murmushi da yakeyi baya ko dariya. Tun yana burge Rahima,har ya daina cikin yanayin damuwa tace
"Haris na yadai? Ko ka gaji da ganina ne? Na dameka?"
Ya duba agogo kafin ya kalleta yana murmushi
"No,ba haka bane saidai akwai wani uzuri dake gabana yanzu. Kiyi hakuri dai sai mun hadu a makaranta."
Daga haka ya mike da niyyar tafiya,tayi azamar dakatar dashi ta hanyar cewa
"Ya makomar soyayyarmu? Ka amince dani ne ko kuwa..."
"Yanzu kam karatu ne a gabana ba soyayya ba. Kiyi hakuri "
Yayi gaba,yayin da ya barta cike da bakin ciki da dana sanin zuwanta. Yana haduwa da kb wanda yake dubansu. Ya shiga dariyar mugunta har yana kwarewa. Daman yasan amininsa ba iya zancen yayi ba,saidai ta duri haushi. Abun ma bai bashi dariya ba saida Haris ya labarta mishi yanda sukayi shima yana dariyar. Kb ya bugi sitiyari
"Amma kai kam anyi d'an iska,wato baka soyayya sai karatu. Kalaman yayi yanayi dana mace."
Tun daga wannan ranar Rahima bata k'ara neman shiga harkarsa ba. Hakan ma sai yayi mishi dadi domin sam ba sonta yakeyi ba.
****
Haris yana kaiwa nan a tunaninsa yayi murmushi kafin ya watsar da komai ya cigaba da aikinsa.
****
Dalal,Manal da kuma Hibba,sai Baby. Zaune a falon.
Baby sanye da wando three quarter sai 'yar shimi,kwance take akan two sitter ta d'ora k'afa d'aya kan d'aya tana (game) da iPad dinta,tana yi tana taunar cingam. Hankalinta kwance,jifa jifa take sanya baki a hirarsu na duniya. Manal ta dubesu tana murmushi
"Albishirinku."
Suka amsa da goro banda Baby dake sha'aninta saidai kuma hankalinta yana ga sauraron abunda zai fito daga bakin Manal.
"Zanje zaman wata uku gidan Alhaji Ubale Kwangila."
Cikin rashin fahimta Dalal da Hibba suka yamutse fuska
"Bamu fahimceki ba."
Kafin ta basu amsa,Baby tayi dariya ba tare data dubesu ba
"Kudai kam baku saurin fahimtar mutum,kasuwanci na wata uku zataje yi gidan Alhaji Ubale. Don wannan baikai kimar da za'a kirashi da aure ba."
Dalal da Hibba suka buga shewa,Manal tana dariya tace
"Dad'ina dake saurin fahimta Baby,toh kun fahimta inace?"
Hibba tace
"Kwarai kuwa,amma fa yana da mata ko?"
Ta rausaya idanu
"Taci kaza kazanta(ashar),ke aure ne fa tun ana fama da shan miyar kuka a kauye. Babu abunda zata hanani,wai kin manta nafi kunama radadi?"
Ta buga hannuwanta
"Wata uku kacal,nayi na gama dashi na fito. Batun da nakeyi maku wahalallen ya kammala yimin gyaran gidansa na Abuja. Can zan lula mubar shegiyar a Kaduna. Magana ma ta isa kunnen Momi,aure nan da wata d'aya sai a soma shiri."
Sukayi dariya gaba daya har Baby,domin yanayin da Manal tayi furucin duka ya basu dariya.
"Kidai shiga da shirinki,kada a samu matsala ya gark'ameki. Me akeyi da aure?" Cewar Hibba.
Dalal tayi dariya
"Shegiya,kada ki manta shine ya haifeki,ko kin mance gyatumarki Sarai mai kosai na tuna maki?"
Dam! Kirjin Baby ya buga,jin furucin daya fito daga bakin Dalal......!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(18)
Shewarsu ta katse mata tunani,hibba tace
"Allah Sarki uwata,hauka nakeyi zan mance da ita? Karki ganni anan, duk wata saina tura mata kud'i ta account kawata Balaraba. Ba don wannan mugun uban nawa ba ai da wataran saidai ta ganni naje ziyara. Kunsan dai duk iskancina bana manta MAHAIFIYA."
Baby tayi shiru,jikinta a sanyaye. Ita kam yaushe rabonta da tata uwar? Shekaru biyu kenan,gwara ma mahaifinta,tana da masaniya akansa,ta tsaneshi shima ya tsaneta,wannan dalilin ne yasa babu wanda ya taba yunkurin neman wani a cikinsu. Amma mahaifiyarta fa?
Dalal tace "Ai gwara a dungayi ana tuna asali,nikam saidai nace Allah Ya jik'an nawa iyayen. Ita kuwa Gwaggona da ita muke ci da sha. Ina yawan zuwa gidanta a Kano,kuma kun sani."
Ga mamaki sai sukaga Manal na hawaye tace
"Gwara ku, kuna da iyayen. Nikam idan baku manta ba tsintata akayi a bola,sai ya zamana wanda ya daukeni ya rikeni har girmana,shine mutumin farko daya soma aikata masha'a dani."
"Baby Tasleem."
Haris ya nanata sunan a ransa,sai yau ma yasan sunanta. Kb ya cigaba da magana
"Nasan ban kyautawa Yasmeen ba kamar yanda ban kyautawa kaina ba. Gaskiyar magana rabuwa da Tasleem abune mai matukar wuya agareni,shiyasa na yanke shawarar zan aureta a matsayin matata ta sunna."
Wani mugun kallo da Haris ya watsa mishi ya sanyashi kauda kansa cikin jin nauyi,ya numfasa kafin ya cigaba
"Yes Haris, kabar yimin irin wannan duban,raya sunnah nakeson yi ba wai zina ba. Duk da dai zuwa yanzu Baby tak'i bani had'in kai,ta nunamin babu abunda ta tsana kamar aure,wannan shine hakikanin damuwata. A matsayinka na amini kuma d'an uwana don Allah ka taimakamin da shawara."
Ba tare da ya jira cewar Haris ba ya mike tsam ya nufi hanyar fita cikin jin nauyin amininsa. Saida yakai k'ofa sannan ya dakata ba tare da ya juyo ba
"Ba hakan dana fada yana nufin na rabu da soyayyar matata ba,a'a. Inason Yasmeen matuka saidai inason raya sunna. Idan har ka amince da bukatana,ka taimakeni kayi jihadi wajen shawomin kan Tasleem domin cetomu daga wannan rayuwa please Haris. Goodbye."
Ya fice cikin sauri ba tare da ya juyo ba ballantana ya lura da irin firgicin dake akan fuskar amininsa.
Rike kai yayi yana mai runtse ido,gabansa na duka da sauri da sauri. Aure?!! Tsakanin Kb da baby tasleem?!!
Ya nanata a zuciyarsa,kafin ya kwantar da kansa akan kujerar ya runtse ido. Toh menene matsalarsa? Me zaisa zancen nan ya dameshi? Amma kuma dole zai dameshi ai,ko babu komai,kanwarsa ce fa Kb ke shirin yiwa kishiya da karuwa! Dole yaji tsanar auren,dole ne ya taya 'yar uwarsa kishi. Kishi mai tsanani.
Ya bud'e ido,kafin ya hasko halittar Baby da wayewarta sannan ya dawo ga kanwarsa wacce baby bazata nunawa kyau ba saidai ta fita a halittar jiki da kuma barikanci. Ita d'in ta kasance saliha,domin ko a gida bata fiye magana mai tsawo ba,sam, bata da hayaniya tamkar Haris d'in take. Wannan yasa duk cikin kannensa yafi tausayinta yafi sonta tasu tafi zuwa d'aya. Anya kanwarsa zata iya kishi da gogaggiyar mace irin Tasleem?
"Idan har ka amince da bukatana,ka taimakeni kayi jihadi wajen shawomin kan Tasleem domin cetomu daga wannan rayuwa please Haris."
Ya tuno zancen Kb,wannan ya nuna kenan yayi kokarin shawo kan Tasleem domin ta amince da bukatarsa na suyi aure amma sam,tak'i aminta.
Haris ya girgiza kai cikin takaici da bacin rai
"Tabbas Kabir bashi da kunya."
Ya fad'a a fili. K'arar wayarsa ta katseshi,ya duba yaga sunan Daddy. Da sauri ya d'auka. Bayan sallama da gaisuwa ne Daddy ya sanar dashi ya shigo yazo ofishinsa yana nemansa. Ya amsa kafin ya tashi a hanzarce ya nufi ofishin director kuma uba a gareshi,Alhaji Idris.
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(17)
Ya shiga da sallama. Daddy zaune akan kujerarsa sanye yake da riga 'yar ciki da wando ya rataye babbar rigar jikin (hanger). Idanunsa boye cikin farin gilashi. Ya bar danna laptop dinsa ya dago yana mai amsa sallamar d'ansa. Cike da girmamawa ya russuna ya gaida Daddy. Daddy ya amsa fuska a sake kafin yace
"Gaisuwarka bata k'arewa Harisu,ayi ta gida ayi ta ofis ko?"
Haris yayi murmushi mai bayyana hak'ora,baice komai ba ya zauna saman kujera bayan yayi kokarin d'an rage tsawo duk da hakan. Daddy yayi gyaran murya ya soma magana
"Haris,kwanaki sun shude sun zama watanni,ga watannin sun koma shekaru. Dan uwanka gashinan zaune da iyalinsa,a dukkan tsawon watannin nan mun barka ne akan ka nemi zab'inka gudun shiga rayuwarka. Saidai har kawo yanzu,shiru Harisu."
Daddy ya k'arashe cikin rarrauniyar murya mai russunar da zuciyar wanda ake yiwa. Haris baice komai ba yayi shiru yana sauraron Daddy
"Ga iyayenka nan girma yana k'ara hawan kanmu,wannan ya sanya naga tunda abun ya zama haka na baka zab'in zuwa can Kazaure,ka duba cikin 'yan uwanka dake can ko Allah zaisa ka sami wata cikinsu da zakaji nutsuwar zuciya akanta. Nidai fatana Allah Ya baka mace ta gari."
Haris yayi murmushi kad'an jin wannan batu da Daddy,a gefe kuma ya gama gaskata cewa ba k'aramin so Daddy da Hajiya sukeyi mishi ba,tamkar daga cikinsu ya fito. Ya tabbata gudun abunda zai b'ata ransa ne yasa Daddy b'ullowa ta wannan hanyar.
"Tashi ka koma ga aikinka Harisu,zan jiraka daga nan zuwa gobe duk abunda ka yanke toh,idan ma akwai wacce ka gani kake so toh Alhamdulillah. Wannan ma shi muka fi muradi. Allah Yayi jagora. Tashi ka tafi, ka turomin sakatare."
Cike da jin nauyi Haris ya mike yana mai amsawa da toh,ya fice jiki a sanyaye. Ya isar ga sak'on Daddy ga sakatare kafin ya koma ofis.
Kasa nutsuwa yayi,zancen Daddy yake ta juyawa. Toh wai ko zai koma ya sanar dashi cewar ya bashi zab'ine? Su zab'a mishi kawai mace tagari? Idan ba hakan ba ya zaiyi toh? Shi kam bai taba budurwa ba,a takaice ma basa gabansa. Allah Ya yishi mutum ba mai son magana sosai ba,baisan ta inda zai soma zuwa ga mace da zummar soyayya ba. Toh yace mata me? Ai shi kam matan ma bakin jini yake a gurinsu,bai mantawa dai da wata abokiyar karatunsa a Malaysia,Rahima. Babu irin bibiyar da batayi ba akan ya amince da soyayyarta amma sam bata samu fuska ba.
Bai mance ranar da Kb ya tursasashi akan sai ya saurareta ba. Suka shirya suka fita wajen shak'atawa inda tuni Kb ya yiwa Rahima maganar ta isa wajen zasu zo. Koda sukaje,nan suka hangeta zaune a kujera bakin swimmingpool na wajen. Kb ya daki kafadarsa yana dariyar mugunta
"Oya jeka,sannan don Allah kada ka bani kunya. Nasan wannan ne farkon tsayuwarka gaban mace a matsayin saurayinta,be a man!"
Harararsa yayi kafin yayi gaba cikin takunsa na nutsuwa,tana ganinshi ta mike tsaye domin girmamawa gareshi tana dariyar farin ciki.
"Sannu da zuwa Haris na."
Yayi dan murmushi kafin ya amsa ya zauna,hakan ya sanyata zama itama. Shiru ya ratso,ya zamana hirar ita keyi yayinda shi ya zama macen. Daga um,sai um um,ga murmushi da yakeyi baya ko dariya. Tun yana burge Rahima,har ya daina cikin yanayin damuwa tace
"Haris na yadai? Ko ka gaji da ganina ne? Na dameka?"
Ya duba agogo kafin ya kalleta yana murmushi
"No,ba haka bane saidai akwai wani uzuri dake gabana yanzu. Kiyi hakuri dai sai mun hadu a makaranta."
Daga haka ya mike da niyyar tafiya,tayi azamar dakatar dashi ta hanyar cewa
"Ya makomar soyayyarmu? Ka amince dani ne ko kuwa..."
"Yanzu kam karatu ne a gabana ba soyayya ba. Kiyi hakuri "
Yayi gaba,yayin da ya barta cike da bakin ciki da dana sanin zuwanta. Yana haduwa da kb wanda yake dubansu. Ya shiga dariyar mugunta har yana kwarewa. Daman yasan amininsa ba iya zancen yayi ba,saidai ta duri haushi. Abun ma bai bashi dariya ba saida Haris ya labarta mishi yanda sukayi shima yana dariyar. Kb ya bugi sitiyari
"Amma kai kam anyi d'an iska,wato baka soyayya sai karatu. Kalaman yayi yanayi dana mace."
Tun daga wannan ranar Rahima bata k'ara neman shiga harkarsa ba. Hakan ma sai yayi mishi dadi domin sam ba sonta yakeyi ba.
****
Haris yana kaiwa nan a tunaninsa yayi murmushi kafin ya watsar da komai ya cigaba da aikinsa.
****
Dalal,Manal da kuma Hibba,sai Baby. Zaune a falon.
Baby sanye da wando three quarter sai 'yar shimi,kwance take akan two sitter ta d'ora k'afa d'aya kan d'aya tana (game) da iPad dinta,tana yi tana taunar cingam. Hankalinta kwance,jifa jifa take sanya baki a hirarsu na duniya. Manal ta dubesu tana murmushi
"Albishirinku."
Suka amsa da goro banda Baby dake sha'aninta saidai kuma hankalinta yana ga sauraron abunda zai fito daga bakin Manal.
"Zanje zaman wata uku gidan Alhaji Ubale Kwangila."
Cikin rashin fahimta Dalal da Hibba suka yamutse fuska
"Bamu fahimceki ba."
Kafin ta basu amsa,Baby tayi dariya ba tare data dubesu ba
"Kudai kam baku saurin fahimtar mutum,kasuwanci na wata uku zataje yi gidan Alhaji Ubale. Don wannan baikai kimar da za'a kirashi da aure ba."
Dalal da Hibba suka buga shewa,Manal tana dariya tace
"Dad'ina dake saurin fahimta Baby,toh kun fahimta inace?"
Hibba tace
"Kwarai kuwa,amma fa yana da mata ko?"
Ta rausaya idanu
"Taci kaza kazanta(ashar),ke aure ne fa tun ana fama da shan miyar kuka a kauye. Babu abunda zata hanani,wai kin manta nafi kunama radadi?"
Ta buga hannuwanta
"Wata uku kacal,nayi na gama dashi na fito. Batun da nakeyi maku wahalallen ya kammala yimin gyaran gidansa na Abuja. Can zan lula mubar shegiyar a Kaduna. Magana ma ta isa kunnen Momi,aure nan da wata d'aya sai a soma shiri."
Sukayi dariya gaba daya har Baby,domin yanayin da Manal tayi furucin duka ya basu dariya.
"Kidai shiga da shirinki,kada a samu matsala ya gark'ameki. Me akeyi da aure?" Cewar Hibba.
Dalal tayi dariya
"Shegiya,kada ki manta shine ya haifeki,ko kin mance gyatumarki Sarai mai kosai na tuna maki?"
Dam! Kirjin Baby ya buga,jin furucin daya fito daga bakin Dalal......!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(18)
Shewarsu ta katse mata tunani,hibba tace
"Allah Sarki uwata,hauka nakeyi zan mance da ita? Karki ganni anan, duk wata saina tura mata kud'i ta account kawata Balaraba. Ba don wannan mugun uban nawa ba ai da wataran saidai ta ganni naje ziyara. Kunsan dai duk iskancina bana manta MAHAIFIYA."
Baby tayi shiru,jikinta a sanyaye. Ita kam yaushe rabonta da tata uwar? Shekaru biyu kenan,gwara ma mahaifinta,tana da masaniya akansa,ta tsaneshi shima ya tsaneta,wannan dalilin ne yasa babu wanda ya taba yunkurin neman wani a cikinsu. Amma mahaifiyarta fa?
Dalal tace "Ai gwara a dungayi ana tuna asali,nikam saidai nace Allah Ya jik'an nawa iyayen. Ita kuwa Gwaggona da ita muke ci da sha. Ina yawan zuwa gidanta a Kano,kuma kun sani."
Ga mamaki sai sukaga Manal na hawaye tace
"Gwara ku, kuna da iyayen. Nikam idan baku manta ba tsintata akayi a bola,sai ya zamana wanda ya daukeni ya rikeni har girmana,shine mutumin farko daya soma aikata masha'a dani."