Sashe 19
African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals · about 8 min read
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(36)
Karasowa yayi ya durkusa a gabana,hannuna ya
riko na hagu kafin ya fashe da kuka. Hankalina ya
tashi ainun ganin kukan Yaya abdullah tamkar na
wani karamin yaro. Saidai ban iya cewa uffan ba
nima sai karfin kukana daya k'aru. Na ajiye
lemun b'awon dake hannuna. Ya dawo ya dubeni
cikin rawar murya yace
"Why Tasleem? Why?! Meyasa kika bari rayuwarki
ta lalace har haka? Wane irin halin rashi kike ciki
da har zaki bawa wani kanki? Meyasa Tasleem?
Akan wane dalili kika boyemin rashin Mamma a
gidan nan?"
Ya karashe cikin sheshahekar kuka. Na tsayar da
idanuna bana ko iya kiftasu a kansa, bakina a
bude na kasa cewa komai. Tsananin mamakin
yanda akayi yayana jinina ya yarda da wannan
kazafin da akayimin nakeyi. Ashe Yaya abdullah
shima zai amince da wannan zancen nasu?
Ya mike tsaye ya zauna gefen gadon,na cigaba da
bin fuskarsa da kallo yayinda ya dauke kansa
yana mai kara tamkemin fuska. Murmushin bakin
ciki nayi,tabbas an rabani da yayana kuma dan
uwana. Babu sauran wata magana,banga amfanin
sanar dashi komai dangane da lamarina ba. Babu
wani amfani a yin hakan. Zuciya irin tawa tasa
nak'i bayyanawa Yayana gaskiyar abunda na
sani. Maganarsa ta katseni
"Nayi bakin cikin jin rabuwar Abba da Mamma.
Kodayake naga alamar akwai wata a kasa tun
rayuwar da nayi a abroad. Wallahi Abba baida
masaniyar a yanda na kammala karatuna na
dawo. Duk a zatona Mamma tana tare da
Abbana,wannan yasa nayi kiranta na shaida mata
dukkan halin da nake ciki,bani da komai sannan
na tabbatar idan a wannan gab'ar nace zan ajiye
karatuna na dawo toh fa nan ma wata matsalarce
don bani da kudin jirgi. Mamma hankalinta ya
tashi tace kada na sake nayi kokarin tahowa na
bata nan da kwana uku. Haka na cigaba da zama
a gidan yayan abokina,Rilwan da muke makaranta
tare. Har saida ya zamana inajin nauyinsu,gani
nakeyi kamar ina matsa musu. Rilwan ya fahimci
halin da nake ciki domin ya lura har lokacin bani
da niyyar biyan kudin makaranta. Bansan ya
akayi ba sai ji nayi yace na shirya na rakashi
wani waje. Ban kawo komai ba nayi shirina tsaf
muka tafi. Nayi mamakin ganin Rilwan ya
biyamin kudaden nan,bawai ina mamakin ko a ina
ya samu kudaden nan bane,ko kadan saboda
nasan waye mahaifin Rilwan. Babban ma'aikaci
ne a 9ja garin Abuja. Mamakin da nakeyi har
wane matsayi Rilwan ya bani da sai biyamin
kudin shekara biyun daya ragemin. Na rasa
kalmar daya kamata na godemishi. Har hawayen
farin ciki nayi,ya nunamin babu komai domin shi
don Allah yake sona. A haka bayan kwana uku sai
gashi Mamma ta turomin kudi har dubu dari uku.
Nayi mamaki sosai,a karshe nayi kiranta na
shaida mata yanda akayi,kusan ta fini murna tace
na tattala wadannan zasuyimin amfani kada na
damu Abba ayyuka sukayimishi yawa shiyasa naji
shiru. Na bita a haka. Kinji yanda na kammala
karatuna,da taimakon Rilwan da Mamma sai
matar da nake niyyar aura, Hasinat kamar yanda
kika san tsakanina da ita. Ita kam dukkan wani
abu daya danganci sutura da kayan kamshi ita ke
siyamin batare dana sanyata ba. Tun bana shiga
harkarta har nazo ina shiga,iyayenta sun sani
hakanan mamanta na yawan waya da Mamma.
Itama hasinat tasan mamma sosai."
Yaya abdullah ya numfasa ya share hawayensa
yana dubana cikin mugun takaici
"Na kammala na dawo saina riski labari marar
dadin ji daga bakin Maman twins(Raliya),wai
Tasleem kin siyar da mutuncinki saboda abun
duniya?!! Wane irin kunci kika shiga?!! Abba ya
cucemu daya dauke mana mahaifiyarmu daga
gidansa!"
Zuwa lokacin hawayena sun gaji da zuba sun
dauke,murmushi kawai nakeyi wanda yafi kuka
ciwo
"Kaddarata ce mai yiwuwa! Haka nawa..."
"Ba kaddara bace!!"
Ya katseni a tsawance har na firgita ina dubansa
yanda ya mike cikin fusata.
"Son zuciyarki kika bi tasleem! Kin manta
tarbiyyar da Mamma ta jima tana iyakar kokarinta
wajen baki? Meyasa zaki lalata rayuwarki har
haka? Nayi bakin ciki marar iyaka jin wannan
batu! Nayi danasanin tafiyata na barki,wallahi da
nasan Abba zai rabu da Mamma da ban amince
na ketara ko nan da can ba!"
Ya dakata yana mai hade kansa da bango kafin
yayi wuf ya fice, ina kiransa saidai ko waigowa
baiyiba.
Kaina na cusa cikin filo ina kuka mai karfi. Gaba
daya zaman asibitin ya isheni hakan yasa na
sauko na dauki hijabin da bansan ko na waye
ba,dashi dai nakeyin salla,ban iske takalmi ba
hakanan na fice.
Ban tsaya ko'ina ba sai kofar gidanmu,na nemi
rance wajen baba Maigadi don bawa mai
adaidaita,baba maigadi yace babu komai naje zai
sallameshi. Yayimin sannu banko tsaya amsawa
ba nayi ciki. Tsayawa nayi cak ina duban ko'ina
na gidan,ina ya dace na nufa? Wajen wa zanje?
Waye zai saurareni? Na kara taku daya biyu,na
daga da niyyar yin na uku mukayi ido hudu
dashi,cikin sanyin jiki na maida kafar baya na
dukar da kaina. Ya k'araso a fusace
"Me kika dawo kiyimin?!!!"
Na dago kaina murya na rawa na soma magana
"Abb..." Marin daya saukemin a fuskata ya
dakatar dani daga karasawa
"Fitarmin daga gida,yar iskar yarinya! Kin bata
wayonki! Bazaki zo ki b'atamin tarbiyyar yarana
ba! Shegiya! Kedai kam ina kwakwanto akanki!
Anya nine ubanki?!!!"
"Wannan shine furuci na biyu cikin ukun da bazan
taba daina tuna su ba,hakanan tunaninsu ya
sanyani yin mummunan hatsarin da har ka kaini
asibiti Haris." Cewar Baby tana duban
Haris,sannan ta cigaba.
Kalaman Abba yayi daidai da fitowar yayana
Abdullah a guje daga sashen Mamma.
Gwuiwoyinsa a k'asa ya shiga rokon Abba akan
yayimin afuwa ya barni na rayu koda a sashen
'yan aiki ne. Abba ya hankad'ashi
"Gidana ne! Ina ajiye wanda naso a ciki amma
banda yan iska! Kaima kuma idan bakayi wasa ba
yanzun nan zaka bita ku tafi."
Maganar da Abba keyi da karfi ce ta janyo
hankulan yan aiki. Zuciya ta kwasheni cikin kuka
da daga murya nace
"Naji gidanka ne! Zan fita na barshi,zan barshi
har abada!! Kai uba ne ga wasu amma ba ni ba!
Na amince idan har ka manta hakkina dake
kanka ka manta akwai hisabi a tsakaninmu! Toh
hakika zan bar gidanka yanzu ba anjima ba. Ko a
kiyama bana fatan Allah Ya kara hadani da
azzalumin uba..."
Mari Yaya abdullah ya daukeni dashi,
"Kina hayyacinki kuwa? Kin manta waye
agareki?!!"
Cikin kuka da daga murya nace
"Ban manta ba yaya abdullah! Amma shi ya
mance diya nake awajensa. Abba ina kake sadda
nake rayuwar garari acikin gidan ka?! Ina kake
sadda abincin yan aiki ma yafi nawa mutunci da
dadi a harshe? Ina kake sadda na kammala
karatu?!! Ka taba zaunar dani kaji damuwata?! Ka
taba yimin nasiha koda sau daya akan rike
addinina?! Ka taba damuwa da ni?! Wallahi na
tabbatar ko sunana bazaka iya tunawa ba saboda
baka sona! Ka tsaneni! Har gashi ayau kana
kokwanto ko kaine ubana!!! Shikenan gaka ga
gidan naka! Allah zai mana sakayya!!"
Daga haka nayi waje a guje,Yaya abdullah yana
kirana amma ko juyowa banyiba. Nayi nisa sosai
da gidanmu kafin na samu kasan bishiya na zube
ina kuka da numfarfashi. Kaicona!!!!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(37)
Taku naji da sauri sauri kafin aci burki a gabana. Na dago kaina,Yaya abdullah ne. Kaina na cusa cikin cinyoyina,dagomin kai yayi kafin ya rungumeni shi kansa hawayen yake. Ganin mutane sun soma taruwa ne yasa ya mikar dani tsaye yaja hannuna. Na turje na tsaya cak, ya dubeni na girgiza kaina
"Kayi hakuri yaya,bazan koma gidan nan ba."
Ya dan dubi mutanen da suka taru kafin ya sassauta muryarsa
"Nima ba nan zan kaiki ba,biyoni kawai."
Adaidaita sahu ya tarar mana muka shiga. Har lokacin jikina kakkarwa yakeyi ga hawaye wani yana bin wani.
"Duk da laifin da kika aikata Tasleem,I can't change the fact that you are my blood sister. Bazan iya bari rayuwarki ta tagayyara ba Tasleem. Abba mahaifinmu ne,a yanda Mamma ta koyamin tace duk runtsi da tsanani kada na gujeshi wataran sai labari. Zan kaiki inda nasan zaki zauna cikin aminci har zuwa lokacin da Abba zai sakko ya yafemaki. Amma bayan da na samu labarin Mamma tayi aure bazan amince da zuwanki Kazaure ba har ki dagamata hankali."
Tunda ya soma maganganun hankalina yana ga waje, sai alokacin na waigo na dubeshi. Kallonshi nakeyi kamar wata tab'abb'iya ina mamakin yanda Yaya abdullah ya hakikance cewar na aikata zina da gangan. Murmushi nayi alokacin da ruwan hawaye ya malalo kan hancina. Na yarda sharrin mace yafi na shaidan. Usman!! Shine wanda ya fadomin a raina,kwarai ya tafka babban kuskure a rayuwa tunda yayi gangancin yimin wannan ta'asar,nasha alwashin daukar FANSA.
Unguwar tarauni,anan muka yada zango,yaya abdullah yayita yiwa mai adaidaitan nuni,har a karshe muka tsaya a wani gida karami na sumunti saidai babu ko fenti. Muka fito ina ta kallon gidan kallon rashin sani.
"Muje." Ya katsemin tunani bayan yace mai adaidaitan yayi tsumayinshi. Yace na soma shiga. Na shiga da sallama,matar dake zaune ta juya baya tana alwala ta waigo tana amsawa. Ganin Kulu yasa naje a guje itama ta mike da azama na rungumeta na fashe da kuka sosai. Tun tana farin cikin ganina har dai jikinta yayi sanyi,sallamar Yaya abdullah ta katseta daga tambayar da take shirin jefomin. Ta sakeni tana "Lale marhabin da d'ana. Saukar yaushe?" Yayi murmushi yana kokarin mayarda kwallarsa,ta dubeni ta dubeshi a sanyaye tace"Lafiya kuwa d'ana? Menene ya faru?"
Kafin muce wani abu tayi daki tana fadin"Ina zuwa."
Ta fito dauke da tabarma ta shimfida. Bayan mun zauna yaya abdullah ya dubeta
"Nayi bakin cikin dawowa naga bakya gidan Kulu,kamar yanda mutuwar auren Mamma ya tayarmin da hankali. Saidai tunda a yanzu tayi aure mun dauki hakan matsayin KADDARA."
Kulu wacce tun soma maganarsa taji babu dadi saidai furucinsa na karshe ya dan sanya ta saki fuska"Kai Hajiya tayi aure? Toh ai Alhamdulillah. Kada ka damu dana karatun da kakeyi ne yasa ba'a bari labarin ya riskeka ba amma komai na Allah ai mai kyau ne."
Ya gyada kai"Hakane." Ya danyi shiru kafin yace"Kulu nazo neman karamar alfarma a..." "Fadi ko menene D'ana,babu abunda banajin zaka nema da nayi maka na kasa yinsa."
Ya numfasa yana murmushi"So nakeyi ki rikemin amanar Tasleem zuwa nan da wani lokaci......"
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(36)
Karasowa yayi ya durkusa a gabana,hannuna ya
riko na hagu kafin ya fashe da kuka. Hankalina ya
tashi ainun ganin kukan Yaya abdullah tamkar na
wani karamin yaro. Saidai ban iya cewa uffan ba
nima sai karfin kukana daya k'aru. Na ajiye
lemun b'awon dake hannuna. Ya dawo ya dubeni
cikin rawar murya yace
"Why Tasleem? Why?! Meyasa kika bari rayuwarki
ta lalace har haka? Wane irin halin rashi kike ciki
da har zaki bawa wani kanki? Meyasa Tasleem?
Akan wane dalili kika boyemin rashin Mamma a
gidan nan?"
Ya karashe cikin sheshahekar kuka. Na tsayar da
idanuna bana ko iya kiftasu a kansa, bakina a
bude na kasa cewa komai. Tsananin mamakin
yanda akayi yayana jinina ya yarda da wannan
kazafin da akayimin nakeyi. Ashe Yaya abdullah
shima zai amince da wannan zancen nasu?
Ya mike tsaye ya zauna gefen gadon,na cigaba da
bin fuskarsa da kallo yayinda ya dauke kansa
yana mai kara tamkemin fuska. Murmushin bakin
ciki nayi,tabbas an rabani da yayana kuma dan
uwana. Babu sauran wata magana,banga amfanin
sanar dashi komai dangane da lamarina ba. Babu
wani amfani a yin hakan. Zuciya irin tawa tasa
nak'i bayyanawa Yayana gaskiyar abunda na
sani. Maganarsa ta katseni
"Nayi bakin cikin jin rabuwar Abba da Mamma.
Kodayake naga alamar akwai wata a kasa tun
rayuwar da nayi a abroad. Wallahi Abba baida
masaniyar a yanda na kammala karatuna na
dawo. Duk a zatona Mamma tana tare da
Abbana,wannan yasa nayi kiranta na shaida mata
dukkan halin da nake ciki,bani da komai sannan
na tabbatar idan a wannan gab'ar nace zan ajiye
karatuna na dawo toh fa nan ma wata matsalarce
don bani da kudin jirgi. Mamma hankalinta ya
tashi tace kada na sake nayi kokarin tahowa na
bata nan da kwana uku. Haka na cigaba da zama
a gidan yayan abokina,Rilwan da muke makaranta
tare. Har saida ya zamana inajin nauyinsu,gani
nakeyi kamar ina matsa musu. Rilwan ya fahimci
halin da nake ciki domin ya lura har lokacin bani
da niyyar biyan kudin makaranta. Bansan ya
akayi ba sai ji nayi yace na shirya na rakashi
wani waje. Ban kawo komai ba nayi shirina tsaf
muka tafi. Nayi mamakin ganin Rilwan ya
biyamin kudaden nan,bawai ina mamakin ko a ina
ya samu kudaden nan bane,ko kadan saboda
nasan waye mahaifin Rilwan. Babban ma'aikaci
ne a 9ja garin Abuja. Mamakin da nakeyi har
wane matsayi Rilwan ya bani da sai biyamin
kudin shekara biyun daya ragemin. Na rasa
kalmar daya kamata na godemishi. Har hawayen
farin ciki nayi,ya nunamin babu komai domin shi
don Allah yake sona. A haka bayan kwana uku sai
gashi Mamma ta turomin kudi har dubu dari uku.
Nayi mamaki sosai,a karshe nayi kiranta na
shaida mata yanda akayi,kusan ta fini murna tace
na tattala wadannan zasuyimin amfani kada na
damu Abba ayyuka sukayimishi yawa shiyasa naji
shiru. Na bita a haka. Kinji yanda na kammala
karatuna,da taimakon Rilwan da Mamma sai
matar da nake niyyar aura, Hasinat kamar yanda
kika san tsakanina da ita. Ita kam dukkan wani
abu daya danganci sutura da kayan kamshi ita ke
siyamin batare dana sanyata ba. Tun bana shiga
harkarta har nazo ina shiga,iyayenta sun sani
hakanan mamanta na yawan waya da Mamma.
Itama hasinat tasan mamma sosai."
Yaya abdullah ya numfasa ya share hawayensa
yana dubana cikin mugun takaici
"Na kammala na dawo saina riski labari marar
dadin ji daga bakin Maman twins(Raliya),wai
Tasleem kin siyar da mutuncinki saboda abun
duniya?!! Wane irin kunci kika shiga?!! Abba ya
cucemu daya dauke mana mahaifiyarmu daga
gidansa!"
Zuwa lokacin hawayena sun gaji da zuba sun
dauke,murmushi kawai nakeyi wanda yafi kuka
ciwo
"Kaddarata ce mai yiwuwa! Haka nawa..."
"Ba kaddara bace!!"
Ya katseni a tsawance har na firgita ina dubansa
yanda ya mike cikin fusata.
"Son zuciyarki kika bi tasleem! Kin manta
tarbiyyar da Mamma ta jima tana iyakar kokarinta
wajen baki? Meyasa zaki lalata rayuwarki har
haka? Nayi bakin ciki marar iyaka jin wannan
batu! Nayi danasanin tafiyata na barki,wallahi da
nasan Abba zai rabu da Mamma da ban amince
na ketara ko nan da can ba!"
Ya dakata yana mai hade kansa da bango kafin
yayi wuf ya fice, ina kiransa saidai ko waigowa
baiyiba.
Kaina na cusa cikin filo ina kuka mai karfi. Gaba
daya zaman asibitin ya isheni hakan yasa na
sauko na dauki hijabin da bansan ko na waye
ba,dashi dai nakeyin salla,ban iske takalmi ba
hakanan na fice.
Ban tsaya ko'ina ba sai kofar gidanmu,na nemi
rance wajen baba Maigadi don bawa mai
adaidaita,baba maigadi yace babu komai naje zai
sallameshi. Yayimin sannu banko tsaya amsawa
ba nayi ciki. Tsayawa nayi cak ina duban ko'ina
na gidan,ina ya dace na nufa? Wajen wa zanje?
Waye zai saurareni? Na kara taku daya biyu,na
daga da niyyar yin na uku mukayi ido hudu
dashi,cikin sanyin jiki na maida kafar baya na
dukar da kaina. Ya k'araso a fusace
"Me kika dawo kiyimin?!!!"
Na dago kaina murya na rawa na soma magana
"Abb..." Marin daya saukemin a fuskata ya
dakatar dani daga karasawa
"Fitarmin daga gida,yar iskar yarinya! Kin bata
wayonki! Bazaki zo ki b'atamin tarbiyyar yarana
ba! Shegiya! Kedai kam ina kwakwanto akanki!
Anya nine ubanki?!!!"
"Wannan shine furuci na biyu cikin ukun da bazan
taba daina tuna su ba,hakanan tunaninsu ya
sanyani yin mummunan hatsarin da har ka kaini
asibiti Haris." Cewar Baby tana duban
Haris,sannan ta cigaba.
Kalaman Abba yayi daidai da fitowar yayana
Abdullah a guje daga sashen Mamma.
Gwuiwoyinsa a k'asa ya shiga rokon Abba akan
yayimin afuwa ya barni na rayu koda a sashen
'yan aiki ne. Abba ya hankad'ashi
"Gidana ne! Ina ajiye wanda naso a ciki amma
banda yan iska! Kaima kuma idan bakayi wasa ba
yanzun nan zaka bita ku tafi."
Maganar da Abba keyi da karfi ce ta janyo
hankulan yan aiki. Zuciya ta kwasheni cikin kuka
da daga murya nace
"Naji gidanka ne! Zan fita na barshi,zan barshi
har abada!! Kai uba ne ga wasu amma ba ni ba!
Na amince idan har ka manta hakkina dake
kanka ka manta akwai hisabi a tsakaninmu! Toh
hakika zan bar gidanka yanzu ba anjima ba. Ko a
kiyama bana fatan Allah Ya kara hadani da
azzalumin uba..."
Mari Yaya abdullah ya daukeni dashi,
"Kina hayyacinki kuwa? Kin manta waye
agareki?!!"
Cikin kuka da daga murya nace
"Ban manta ba yaya abdullah! Amma shi ya
mance diya nake awajensa. Abba ina kake sadda
nake rayuwar garari acikin gidan ka?! Ina kake
sadda abincin yan aiki ma yafi nawa mutunci da
dadi a harshe? Ina kake sadda na kammala
karatu?!! Ka taba zaunar dani kaji damuwata?! Ka
taba yimin nasiha koda sau daya akan rike
addinina?! Ka taba damuwa da ni?! Wallahi na
tabbatar ko sunana bazaka iya tunawa ba saboda
baka sona! Ka tsaneni! Har gashi ayau kana
kokwanto ko kaine ubana!!! Shikenan gaka ga
gidan naka! Allah zai mana sakayya!!"
Daga haka nayi waje a guje,Yaya abdullah yana
kirana amma ko juyowa banyiba. Nayi nisa sosai
da gidanmu kafin na samu kasan bishiya na zube
ina kuka da numfarfashi. Kaicona!!!!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(37)
Taku naji da sauri sauri kafin aci burki a gabana. Na dago kaina,Yaya abdullah ne. Kaina na cusa cikin cinyoyina,dagomin kai yayi kafin ya rungumeni shi kansa hawayen yake. Ganin mutane sun soma taruwa ne yasa ya mikar dani tsaye yaja hannuna. Na turje na tsaya cak, ya dubeni na girgiza kaina
"Kayi hakuri yaya,bazan koma gidan nan ba."
Ya dan dubi mutanen da suka taru kafin ya sassauta muryarsa
"Nima ba nan zan kaiki ba,biyoni kawai."
Adaidaita sahu ya tarar mana muka shiga. Har lokacin jikina kakkarwa yakeyi ga hawaye wani yana bin wani.
"Duk da laifin da kika aikata Tasleem,I can't change the fact that you are my blood sister. Bazan iya bari rayuwarki ta tagayyara ba Tasleem. Abba mahaifinmu ne,a yanda Mamma ta koyamin tace duk runtsi da tsanani kada na gujeshi wataran sai labari. Zan kaiki inda nasan zaki zauna cikin aminci har zuwa lokacin da Abba zai sakko ya yafemaki. Amma bayan da na samu labarin Mamma tayi aure bazan amince da zuwanki Kazaure ba har ki dagamata hankali."
Tunda ya soma maganganun hankalina yana ga waje, sai alokacin na waigo na dubeshi. Kallonshi nakeyi kamar wata tab'abb'iya ina mamakin yanda Yaya abdullah ya hakikance cewar na aikata zina da gangan. Murmushi nayi alokacin da ruwan hawaye ya malalo kan hancina. Na yarda sharrin mace yafi na shaidan. Usman!! Shine wanda ya fadomin a raina,kwarai ya tafka babban kuskure a rayuwa tunda yayi gangancin yimin wannan ta'asar,nasha alwashin daukar FANSA.
Unguwar tarauni,anan muka yada zango,yaya abdullah yayita yiwa mai adaidaitan nuni,har a karshe muka tsaya a wani gida karami na sumunti saidai babu ko fenti. Muka fito ina ta kallon gidan kallon rashin sani.
"Muje." Ya katsemin tunani bayan yace mai adaidaitan yayi tsumayinshi. Yace na soma shiga. Na shiga da sallama,matar dake zaune ta juya baya tana alwala ta waigo tana amsawa. Ganin Kulu yasa naje a guje itama ta mike da azama na rungumeta na fashe da kuka sosai. Tun tana farin cikin ganina har dai jikinta yayi sanyi,sallamar Yaya abdullah ta katseta daga tambayar da take shirin jefomin. Ta sakeni tana "Lale marhabin da d'ana. Saukar yaushe?" Yayi murmushi yana kokarin mayarda kwallarsa,ta dubeni ta dubeshi a sanyaye tace"Lafiya kuwa d'ana? Menene ya faru?"
Kafin muce wani abu tayi daki tana fadin"Ina zuwa."
Ta fito dauke da tabarma ta shimfida. Bayan mun zauna yaya abdullah ya dubeta
"Nayi bakin cikin dawowa naga bakya gidan Kulu,kamar yanda mutuwar auren Mamma ya tayarmin da hankali. Saidai tunda a yanzu tayi aure mun dauki hakan matsayin KADDARA."
Kulu wacce tun soma maganarsa taji babu dadi saidai furucinsa na karshe ya dan sanya ta saki fuska"Kai Hajiya tayi aure? Toh ai Alhamdulillah. Kada ka damu dana karatun da kakeyi ne yasa ba'a bari labarin ya riskeka ba amma komai na Allah ai mai kyau ne."
Ya gyada kai"Hakane." Ya danyi shiru kafin yace"Kulu nazo neman karamar alfarma a..." "Fadi ko menene D'ana,babu abunda banajin zaka nema da nayi maka na kasa yinsa."
Ya numfasa yana murmushi"So nakeyi ki rikemin amanar Tasleem zuwa nan da wani lokaci......"