← Book details African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals Local reading mode
READING PART 16 OF 35

Sashe 16

African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals · about 8 min read

A ranar kuwa nasha zagi wajen Raliya dana koma,saidai batayi gigin taba lafiyata ba. Aikin da acewarta na gudarwa,dole na yishi. A banza kam tunda na samu ranar nan ta tafimin cikin matsanancin farin ciki. Ban kwanta ba sai wajen goman dare. Anan ma banyi baccin ba don hira nayi tayi da hindatu akan makarantarmu kafin bacci ya suremu........!
Tun daga wannan ranar kuma sai na soma
sakewa Usman kadan kadan,nakan gaisheshi
hakanan nakan je dukkan wani aiken da zaiyimin
zuwa gidansa ko kicin din Raliya da sauransu.
Ban dai sakarmishi sosai ba,amma babu wannan
rainin sosai. Har kuwa zuwa lokacin bai rabu da
fita yawon dare ba. Nasha ganin Meena tazo
wajen Raliya tana bala'i akan ita ta soma gajiya
da bin mata irin na Usman,mutum tamkar wanda
aka yiwa asiri. Raliya saidai ta bata hakuri don
babu laifi iyayen meena akwai naira hakanan
takan lasawa Raliya sosai domin ita din macece
wacce bata godiya ga Allah. Duk da irin arzikin da
ta hau kai tayi zaune na Abba,ga kuma business
da takeyi,hakan bai hanata hangen na wasu ba.
Bayan watanni uku,lokacin Mamma ta kusa
shekara a gidansu,kawai na tsinci wayar Yaya
musty yana yimin albishir cewar an daurawa
Mammana aure da wani almajirin Malam. Har
tsalle nayi don murna. Yara da yawa sukanyi
bakin ciki idan uwarsu zatayi wani auren alhalin
ubansu na raye, kai koda ace baya raye akwai
yaran dake taya ubansu kishi amma nikam
baruwana ko a jikina. Daga dariya kuma sai na
fashe da kuka. Ina cewa shine ko a gayamin nazo
da wuri? Dariya yayi yace kada na damu anan
Kazaure Mamma zata zauna duk sanda naga
dama na tambayi Abba ya barni toh nazo na
ganta. Naji dadi kwarai ya kara tambayata game
da Yaya abdullah nace mishi sauran mishi
watanni uku kawai ya dawo. Daga haka mukayi
sallama tare da alkawarin idan yaje gidan zai
kirani mu gaisa da Mamma.
Ai kuwa ko awa biyu ba'ayi ba yayi kirana,na hau
bud'a karshe na saki dariya. Nayi mamaki dana ji
muryar Mamma a sanyaye har na tambayeta ko
bata farinciki da auren nan? Bata bani amsa ba
ta share da tambayar lafiyata. Nace
alhamdulillah,tace zan cigaba da karatune? Na
tabe baki "Bansani ba Mamma." "Kamar ya baki
sani ba Tasleem? Keda mahaifinki? Kije kiyi mishi
magana tun lokaci bai kure maki ba."
Na amsa da toh saidai kuma abunda Mamma
batasani ba shine,idan har sai naje ga Abba na
gwammace nayita zama haka a gidan. Haka
mukayi sallama da ita.
Bayan kwana biyu,Meena matar Yaya Usman ta
haife tsohon cikinta ta samu d'iya mace. Murna a
wajen yan gidan ba'a magana. Nikam ko ajikina
daman ba wani mutuncinsu nake gani ba.
*******
Bayan kwana uku da haihuwar meena,misalin
biyar na yamma,ina zaune a bakin firij na Raliya
ina gogewa,ita kuwa da yaranta suna falon suna
kallon wasan Hausa saidai ko inda suke bana
kalla ballantana film din da suke kallo ya dauki
hankalina don tun fil'azal fina finan hausa ba
burgeni sukeyi ba barni da da kallon Indian series
da Korea anan kam ko makiyina ke kallo zan saci
kallo. Sallamar Usman ta katsesu,Hamid bai
amsa ba saima ya mike ya fice saboda a yanzu
haushinsa yakeji akaina. Bayan su hamida sun
gaisheshi ya dubi Raliya.
"Wa kike ganin ya dace ta zauna wajen Meena
ne?"
Yayi maganar tamkar da sa'arsa,Raliya bata ko
damu ba ta kyabe baki
"A'a toh,ko Dijangala ai sai ta zauna. Idan kuwa
batason aikinta ga waccan tsiyar saiku kwasa."
Sai lokacin na dubeta kafin na watsawa Usman
mugun kallo wanda na jima banyi mishi irinsa ba.
Murmushi yayi ya dubi Raliya
"A'a dijangala shiririta ne da ita,tunda dai ga
gwaggon meena zata dunga yi musu wanka sai
Tasleem ta dunga gyare gyarem gidan."
Raliya bata musa ba domin duk yanda zan
kuntata a rayuwa shi tafi kauna. Tace
"Hakan ma yayi,ke! Idan kin kammala ki tattaro
kayanki ki koma gidan Usman har sai matarsa ta
gama wanka sannan zaki dawo."
Bance uffan ba don bakin ciki,a matukar fusata ta
kammala aikin na mike na shiga daki. Haka na
tattaro kayan na fito. Hamida mukayi arba da ita
ta tuntsire da dariya gami da yimin gwalo"Haka
zaki k'are." Kamar nace mata wani abu saidai na
fasa nayi gaba,Raliya har lokacin tana falon
banko kalleta ba nayi gaba abina a fusace.
Saida nazo daidai garden na zube anan na fashe
da kuka,wai haka rayuwata zata k'are? Wane irin
uba gareni da bai daukeni komai ba? Ya manta
da ya haifeni ne har ya banzatar dani a gidansa
ya maidani wofi? Ace yan aiki ma sun fini daraja
da kima a gidannan? Na daga kaina nakai duba
da d'an lilon da muka saba wasa da Yayana.
Haka zaiyita cillani yana goyani muna zagaye
garden dinnan muna dariya. Ba zato naji an
dafani ta baya,nayi azamar juyowa ganin Usman
bansan lokacin da naja tsaki ba nayi kokarin
mikewa yayi saurin dawowa ta gabana.
"Haba Tasleem,ashe tsanar da kika yimin har
takai ace kije ki taimakawa matata ki zauna kina
kuka? Duk cikinmu waye mai tausayinki bayan
ni? Haba Tasleem,banji dadi ba wallahi."
Ganin yanayin fuskarsa sai naga kamar ban
kyauta ba,nace
"Ni ba gidanka ko matarka na tsana ba ai,irin
wannan rainin hankalin da akeyimin a gidan
ubana ne na kasa gane dalilinsa. Bansan kuma
me na tsarewa mutane ba."
Na karashe cikin tsiwa,yayi dariya ya kawo hannu
zai dora kan lebbana nayi azamar ja da baya,cikin
tsoron yanayin kallon da yakemin
"Tasleem komai naki abun sha'awa ne wallahi. Ni
bana k'inki,inason ganin kanwata a kusa dani
shine ma dalilin da yasa na nemi alfarmar
zuwanki. Kiyi hakuri inajin dadin yanda kika kware
a gyara muhalli. Meena KAZAMAR GIDA ce,
banason ganin gidan nan da kazanta. Don Allah
kanwata wallahi tana yin arba'in I promise you
zaki komo gida."
Bance komai ba na mike na dauki jakata nayi
gaba yana magana ko juyowa banyi,menene
saukin da nan da can din?
****
Baby ta numfasa,hawayenta ya karu wani yana
bin wani. Haris ya miko mata (handkerchief)
dinsa,tasa hannu ta karb'a saidai bata da niyyar
share hawayen. Ta dubi Haris wanda shima ya
gaji da waigenta ya karkato gaba daya yana
duban fuskarta don jin dadin hirar.
"Haris a wannan zuwan nawa ne gidan Usman
komai na rayuwata ya soma tabarbarewa. Yanda
akayi kuwa shine......."

'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(33)
Kwana uku da yin candy dinmu,Abba ya dawo
daga tafiya hakanan Hamid shima ya dawo
daga makaranta anyi musu hutu. Zuciya irin
tawa ta hanani tunkarar Abba da zancen zuwa
Kazaure. Sai ince rabona da sanya Abba a ido
tun sadda yayi kirana yayimin batun komawa
sashen Raliya da zama.
Wataranar asabar ina gugar falon Raliya,ina yi
ina wake wakena wanda yana daya daga cikin
abunda ke konawa Raliya rai ganin bana nuna
damuwa a dukkan ayyukan da take sanyani.
Saidai batasan cewar kawai dannewa nakeyi
amma ji nakeyi kamar na shak'ota don bakin
ciki. Hamid ne ya shigo da takalmi ya bi ta inda
na taka zuwa bakin firij,na kalli yanda wajen ya
b'aci da k'asa bance komai ba na k'ara
gogewa,yazo ya kara wuce hannunsa rike da
lemon b'awo yana sha yana yarda kwallayen
nan ma bance uffan ba don na lura tsokanar
fad'a yakeyi. Saida nazo daf da kammalawa ya
kara tahowa zai shige. Ai kuwa na sanya mop
din na hankad'e kafafuwansa tuni ya zube a
wajen,banyi sanya ba na kara dauka na kwala
mishi a goshi. Ihun daya fasa yayi daidai da
shigowar Hamza da Usman da Nura. Tsayawa
nayi ina huci da fada"Wallahi gobe ma ka k'ara
gigin b'atamin aikina sai nayi maka abunda
yafi wannan haka kawai..."
Hannu Hamza ya daga da niyyar kwad'eni ga
mamakina Usman ya rikeshi,bani kadai ba
dukkansu suma sunyi mamaki hatta da Raliya
dasu Hamida da suka fito.
"Kana da hankali kuwa? Sakarmin hannu!"
Usman shima yace"Meyasa kake da son kaine
Hamza?(Kasancewar raini ya shiga tsakaninsu
bama kadan ba) Baka ganin laifin na dan
banzan yaron nan ne da har zakayi gigin marin
Tasleem? Wannan ma ai son kaine."
Ya saki hannunsa,ya dubeni
"Ke wuce ki tafi."
Na dauki mop da robar zan fita,Nura ya
dakamin tsawar data firgitani,ya iso ya janyo
rigata wannan yasa na fadi na zubda ruwan,ba
karamin buguwa k'uguna yayi ba. Kukana ya
tsaya sa'ilin da Usman ya daga hannu ya mari
Nura. Dakin yayi dif,ya cakumi wuyansa
"Wallahi ka kara gangancin taba lafiyarta saika
raina kanka! Metayi maka?!"
Nura ya fisge hannun Usman daga wuyansa
"Nika mara akan wannan yar iskar?"
"An mareka!!"
Nura yayi kwafa ya fice a fusace.
"Hamza bimin bayansa kada ka bari ya dawo
nan." Cewar Raliya sanin halin dabancin Nura
don ba karamin aikinsa bane ya dawo da wuka
ko wani makamin. Hamza ba musu ya fice.
Raliya ta dawo gaban Usman
"Meke yawo a kwakwalwarka?! Akan wannan
yar iskar ka daki kaninka abunda baka tabayi
ba shekara da shekaru sai yanzu da girmanku
da komai?! Me ta baka kaci?!"
Bai saurareta ba ya dawo gabana ya dagani
"Sannu Tasleem,tafi zansa a goge."
"Uban wa zakasa aikin? Wallahi kaji na rantse
maka idan baka fita harkar shegiyar nan ba
ranka zai mummunan baci. Dawo ki gogemin
waje!"
Ta dakamin tsawa,ina hawaye na sunkuya
dakyar zan dauki robar saboda zafin buguwar
da nayi saidai Usman ya rigani ya dauka ya
mikomin.
"Kiyi a hankali."
Raliya ta sanyashi ficewa na lura baiso hakan
ba,haka nayi aikin nan ina mamakin abunda ya
faru.
Chapter 16 · 0% Book details