← Book details African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals Local reading mode
READING PART 14 OF 35

Sashe 14

African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals · about 8 min read

Wataranar alhamis na dawo daga makaranta ina mai murnar kammala paper dina na jarabawar karshe da mukeyi. Karab mukayi ido hudu da Yaya Usman tsaye a bakin motarsa sanye da kananun kaya tana shirin fita. Naja tsaki ganin yanda yake sakar mini murmushi,a fili nayi magana

"An girma ba'asan an girma ba."

"Tasleem."

Sunana daya kira yasa na tsaya don kuwa bai taba ambaton sunana ba saidai yace "ke."

"Zo nan."

Na nufi inda yake cikin tsabar takaici domin a rayuwa na tsani 'ya'yan Raliya gaba dayansu musamman ma wadannan agololin da suke mana karfin hali a gidan uba. Na isa na tsaya kerere gami da hard'e hannuwana a kirji fuska ba walwala don a yanzu sam bana tsoron ta kwab'e mana dasu. Inajin zan iya karawa da duk shegen da zai hanani taka rawata da tsalle a gidan mahaifina.

"Gani."

Na dauka zanji babu dadi sai ga mamakina cikin maganarsa mai sauri yace

"Inye,au yanzu an daina ganin girmana ko? Ba laifinki bane,kin isa ne don a yanzu kin zama biggurl."

Furucinsa yasa na dubeshi,ya dagamin gira hakora a washe, na tsuke baki gabana yana faduwa nadai daure nace

"Ina sauri ne,nagaji."

"Kada ki damu,nima saurin nakeyi zan fita. Tambayar da zanyi maki daman meyasa bakya shiga sashena? Kodai baki daukeni yayanki ba? Kin daukeni bare?"

Na kauda kaina don a zahiri ban fiyeson kallo ba. Banayi banso kuma a tsawaita yimin,saidai yanda na kula Usman mayen kallo ne. Muddin waje da mata baya saurarawa,yan matan dake gidan Waziri nasha jinsu suna korafin yawan kallonsa da son kulasu da yakeyi acewarsu haushin zuwansa sukeji saidai kuma abokin yayansu ne,Bukhari ba yanda zasuyi.

"Daman ai ba wani zumuncin mukeyi a tsakaninmu ba ballantana har na dunga ziyartar gidajenku. Babu laifi idan mun hadu sai adunga gaisawa."

Yayi mamakin maganata,har yayi dariya. Nikam wani lokacin ma mamaki yake bani,mutum mai zuciya da ashariya shine yake bina har haka?

"Gaskiyane Tasleem,komai ya wuce. Ke dince akwai rashin kunya sadda kina da kuruciya,amma yanzu tunda kin nutsu ai shikenan."

Na d'an tabe baki kafin naja kafata nayi gaba

"Ban sallameki bafa."

Ko kallonsa ban k'arayi ba domin na tsani rainin hankali. Ya tsayar dani da surutan banza. Da sallama na shiga saidai babu kowa a falon,na karasa dakin Mamma,kafin nakai na tsaya cak saboda maganar Mamma da naji cikin kuka.

"Kulu don Allah ki rikemin sirrina,nayi iyakar kokarin ganin na gyara zamantakewata da Abban Abdullah,saidai tamkar tunzurashi nakeyi. Bansan takamaiman abunda nayi mishi ba ya tsaneni. Kada ki sanarwa Tasleem komai dangane da abunda na fadamaki. Ayau zan koma garinmu,na bar maki amanar yarana Kulu. Bada son raina ba na rabu dasu. Haka Allah Ya kaddaro zamana da Abbansu bazaije ko'ina ba. Bari na tafi domin banason Tasleem ta iskeni....."

Shigar da nayi ba a hayyaci bane yasa sukayi turus gaba daya. Mamma ce rike da akwatin kaya sai jakar hannu,sanye cikin hijabi fuskarta tayi jazur ga hawayen da take fitarwa daya yana bin wani. A durkushe kuma Kulu ce ke kuka sosai.

Tsananin tashin hankali yasa naji kafafuwana sun kasa rikeni,kawai sai na zube a k'asa kafin nasa tafukan hannuwana na rufe idanuna ina kuka sosai. Mamma ta karaso ta ja hannuna na fisge naja baya ina kuka

"Ki rabu dani nace! Ba kin riga kin shirya guduwa ki barmu a wannan bak'in gidan ba? Kin shirya barinmu wajen azzalumin uban.."

Ta toshemin bakina da sauri

"Kina da hankali kuwa? Kada ki k'ara zaginsa,kada ki kara zagarmin...."

Na fisge hannunta

"Wa?! Waye naki? Mamma ki farka ya rigaya ya sakeki! Baya kaunarmu tunda bayason mahaifiyarmu. Shekaru nawa yana nunamana kiyayya? Babu wata shakuwa tsakaninmu dashi a matsayinsa na ubanmu,tunda nake da wayona ban taba ganin Abba ya tako zuwa sashenki domin duba lafiyarki daga kowace irin cuta data sameki ba! Mamma wallahi bazaki tafi ki barni ba! Nima bana sonsa bana kaunarsa! I hate me so..."

Marin data sakarmin ya dakatar dani, saidai ban fasa fad'i ba na mike naja baya ina kuka da karfin murya nace

"Saidai ki kasheni Mamma! Amma na tsani Abba! Na tsani Raliya! Har abada bazan taba son makiyin uwata ba kowanene!"

Na fice a guje,kayana na soma hadawa a akwati,kulu ta shigo ta sameni. Duk yanda taso ta hanani amma nak'i hanuwa. Na fito saidai Mamma tuni ta fice. Banyi wata wata ba nima na mara mata baya. Kulu na bina tana kwalamin kira saidai ko waigowa banyi ba.

*****
Ga wanda baisani ba,sai yace tare muka isa Kazaure da Mamma domin shigarta da mintuna nima na shigo. Malam na soma cin karo dashi yayi niyyar tafiya masallaci gabatar da sallar la'asar.

"A'a,matata daman tare kuke?"

Kawai saina sanya kuka,wannan ya fiddo mutan gidan. Ba karamin mamaki nagani akan fuskar Mamma ba,saidai batace komai ba ta juya ta koma ciki. Malam ya rikeni
"Lafiya kuwa? Meke faruwa ne?"

Cikin kuka na sanar dashi sakin da Abba ya yiwa Mamma. Matan suka hau salallami,Malam banda innalillahi wa inna ilaihir raaji'un babu abunda yake maimaitawa. Kafin ya numfasa yace

"Shiga kiyi sallah Tasleem,bari har na dawo daga masallaci."

Daga haka naja akwatina,ban yarda na shiga dakinsu Mamma ba,sai nayi zamana dakin Gwaggo Fatsima,matar kanin Malam, Yunus. A zatona Mamma zata shigo ta rufeni da duka,wanda na riga na kudurta a raina ko kasheni zatayi bazan koma ba saidai ko alamunta banji ba.

Malam sai bayan isha'i ya nemi Mamma. Sun jima suna magana kafin yayi kirana. Nan ya lallabani akan nayi hakuri na koma ga mahaifina na tubure mishi karshe na sanya kuka ina fadin sun tsaneni suma. Jin haka Malam yace Mamma ta barni na zauna. Mamma zatayi magana ya hanata yace na tashi na tafi. Bansan me suka tattauna ba,nidai burina ya cika tunda Mamma bata kara matsamin ba akan batun kome na daga ranar.....
'YAR BARIKI

©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)

(31)

Kwana uku da zuwana Kazaure,Mamma ta sakarmini sosai. Inajin dadin kauyen nan domin duk sadda naje kowa haba haba yakeyi dani. Sau da yawa Malam ya kanyi murmushi idan yaga nayi wani abun musamman yanayin maganata da yasha fadamin yana bashi mamaki,yakan ce ni nayi gadon waziri kakana bawai Abbana ba. Bashi kadai bama,hatta kawayena da wasu cikin yan uwana sunsha gayamin na fiye jin kaina da kasaita,wanda ya jima tare dani ne zai gane nature na ne haka bawai girman kai ko wulakanci bane kamar yanda wasu ke dauka suke kuma jin haushina.

Saida na cika sati daya cif a kazaure sannan saiga direbanmu. Nayi mamakin zuwansa,yayi sallama da Malam ya gayamishi cewar Abba ne yace yazo ya tafi dani. Malam ransa bai baci ba domin zuwa yanzu ya dawo daga rakiyar Abba. Ya lura abun nashi sai addu'a. Ya shigo yace na shirya na tafi. Ai kuwa na fasa ihun kuka,yayita ban baki shi da inna,kafin Mamma ta hadamin jakata ta jawoni daki tana rarrashi.

"Na sanki,yarinya kike mai basira da kula dakai. Kada ki sake ki bari shaidan yayi maki hud'uba Tasleem. Kibi matar ubanki sau da k'afa,kiyi biyayya ga mahaifinki kada ki sanya damuwar komai a ranki. Allah Yana tare dake."

Wadannan shine kalaman karshe da Mamma ta gayamin,wanda bani taba mancewa. Haka na share hawayena mukayi sallama da kowa nabi direbanmu muka tafi raina cike da bakin cikin komawa gidan mutumin dana fi tsana a rayuwata.

Babban tashin hankali dana tarar bai wuce ganin babu komai na Mamma a sashenta ba. Toh wai yaushe akayi kwasar kayanta ina Kazauren amma bansamu labari ba. Hankalina ya tashi,babu komai sai ragowar kayana dana Yaya abdullah a kwabobinmu. Na hau kwalawa kulu kira saidai tsit,na fito na tambayi Direba ina kulu. Kafin ya bani amsa sai ga Abba.

"Ta koma kauyensu ai."

Cewar direba,nikuwa kallon Abba nakeyi cike da tsanarsa. Ya kalleni fuskarsa a daure,kafin yace

"Ki sameni a falona."

Daga haka ya wuce,kamar bazanje ba sai kuma na nufi falon saboda tunano nasihar da Mamma tayimin. Yana zaune,daga shi sai matarsa dake b'antalar tuffa a nishadance tana ci. Na durkusa gefe bance uffan ba.

"Ke." (Sai ince da wayona shine sunan da Abba ke kirana kamar bai yankamin rago da Tasleem ba.)

Banko dubeshi ba saboda gudun kada kallon da zan mishi ya zamana na samun zunubi don kallone na tsana.

"Ki tattaro kayanki ki dawo sashen maminki da zama. Bazai yiwu abarki ke d'aya ba kuma kina mace a wancan bangaren. Don haka kizo ku hadu da yanuwanki don bana shakka akan kyakkyawar tarbiyya irinta Hajiya Raliya. Na tabbatar bazanyi kaico ba."

Raliya tasa dariya,wallahi Haris bansan sadda na jefeta da mugun kallo ba,banyi aune ba ta jefomin ragowar tuffan da take ci tana zaromin idonta masu razana matsoraci.

"Yar iskar yarinya ni sa'ar kice da kikeyimin wannan kallon?"

Abba ya dubeta da mamaki,sai naga ta bagarar tana murmushi

"Bakaga hararar da tayimin bane? Lallai sai nayi da gaske wajen gyarawa Tasleem tarbiyya domin na kula tayi nisan da batajin kira a gurbataccen tarbiyyar da uwarta ta bata."

Zuciya ta kaini bango,me suke nufi? Kenan suna tantamar tarbiyyar da Mamma tayimin? Muryar Abba ta katseni

"Tashi kije kiyi abunda nace. Hajiya Raliya bana shakkarki,na gaskata cewar zaki rike amanar dana damk'a maki. Zaki kula da.."

"Wai Doctor ya kake wasu maganganu ne? Yarinyar nan fa ba 'yar gwal bace. Haihuwata nawa,yara nawa kuma na raina? Yanzu ya kake zargin bazan iya kula da 'yar tsakon 'diyarka ba?"

Abba yayi murmushi,kafin naji me zaice nayi wuf na mike na fita saboda nagaji da ganinsu. Ji nakeyi da ace kisa halal ne ni zan zama ajalinsu."

Haris ya katseta cike da mamaki

"Wace irin tsana kika yiwa mahaifinki haka ke kuwa?"

Baby tayi murmushin takaici

"Bazai misaltu ba Haris."

"Bazai misaltu ba?!"

Ya nanata a ransa,baby ta share zancen ta cigaba
Chapter 14 · 0% Book details