← Book details African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals Local reading mode
READING PART 34 OF 35

Sashe 34

African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals · about 5 min read

Haris dake kwance akan gado kawai yana hutawa domin ya jima da tashi daga bacci,darem jiya sun sha waya da Zahra wacce babu laifi ta samu gurbi sosai a zuciyarsa duk da dai karfin hirar itace shi kam yakan rasa abun cewa saidai ta jefo mishi tambaya.

"Kiyi hakuri small,ban manta dake ba. Ai babu matar da zata mantar dani ke. Ya kuke? Ya dotana?"

Yasmeen tayi dariya

"Gatanan tana tsalle tsallenta,babanta ma yanzu ya tafi Airport zai wuce Kazaure idan ya sauka anan Kano. Wallahi naso ya taho dani naga amare amma yak'i."

Tunda Haris yaji wai KB ya taho Kano zaije Kazaure yaji bacin rai matuka ya dirar masa. Bazai fa amince da wannan sakarcin ba,ya dace tun yanzu ya sanyawa lamarin burki.

"Hello." Cewar Yasmeen jin yayi shiru.

"Small,bani mintuna." Ya katse kiran ya mike zaune yana mai zuro kafafunsa k'asa. Dabara ce ta fadomishi na kiran Mamma. Matar da tunda ta ganshi ta nuna mishi kauna hakanan sun jima a falonta su biyu suna tattaunawa game da Tasleem sannan ya nuna mata komai dangane da lamarinta ya sani. Har kwallah tayi don farin cikin jin cewar yaji ya gani yana son diyarta zai iya aura. Bayan sun gaisa yace yanason Nura yaje ya dauko Tasleem a mota harda kayanta ta zauna a wajenta. Mamma ta tambaya ko lafiya. Bai sanar mata ba saidai yace akwai 'yar matsala ne. Tace bakomai zatayi hakan.

Tasleem tayi mamakin ganin Nura yazo wai Mamma da kanta ta nemi komawarta gidanta. Har inna tana fada wai Mamma babu ko kara,bata tambayi ko da iznin Haris ba ko Aa saboda taji Nura yace shine yayi kira. Hakanan ta hau mota,Nura yaja suka nufi gidan Mamma sai tambaya takeyi Mamma da fara'a tayi maganar zuwanta ko a'a shidai Nura tun yana amsawa har tambayoyin sukayita bashi dariya ma.

******

KB yana dira a Kano,direbansa ya kaishi gida. A gaggauce yaci abinci yayi wanka sannan ya saka kananun kaya. Jakar kayansa ya dauka ya saka a mota. Jeep dinsa ya dauki yayi hon Maigadi ya bude.. Sai Kazaure......!

'YAR BARIKI

©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)

(64)

Hankalin Haris bai kwanta ba har saidai ya lalubi layin baby saidai baiyi mamakin jinsa a kashe ba yasan tayi fushi tak'i sanyawa ne. Wannan yasa ya k'ara nemanta ta hanyar layin Mamma. Ya sanarwa Mamma yanason magana da baby. Ta mik'awa Tasleem lokacin tana zaune anan gefen Mamma suna 'yar hira don babu laifi ta sakarmata.

"Sai ki tashi ki shiga daga ciki mijinki ne."

Ta mike ba don taso ba wayar na hannunta. Saida ta zauna gefen gado sannan tayi mishi sallama. Ya amsa ciki ciki

"Kina jina ko? Kb yana hanyarsa ta Kazaure."

Tabe baki tayi,ai daman tasan ko ba dade ko ba jima sai KB ya samu labarin inda take tunda har yasha alwashin nemanta ruwa a jallo.

"Ya akayi yasan da zamanki a Kazaure?"

(Ya fadi hakan da niyyar bugar cikinta duk da bashi da tabbacin saboda ita Kb zaije Kzu.)

Cikin rashin fahimta tace

"Kana zargina ne da gayawa KB inda nake Haris? Ko ka mance garinsu ne?"

Ya lumshe ido ya kara gyara zaman towel din dake daure a kugunsa,fitowarsa kenan daga wanka. Zak'in muryarta daban ce,hakika zai iya rantsewa bai taba sauraron muryar mace a fili ko waya ba, da yayi mishi dadi irin na Tasleem.

"Nidai ina mai gargadinki,stay away from him. Kada koda wasa na samu labarin kun hadu har maganar fatar baki ta shiga tsakaninku. OK?"

Ta rausayar da ido tana tsuke baki cikin jin haushin Haris. Banda abunsa ma,kare ne ya cijeta da zata k'ara waiwayar BARIKI. Don KB barikin ne ma gaba daya a rayuwarta.

"Kin rasa baki ne?"

"Naji zan kiyaye."

"Good,had'ani da Mammana."

"Ko a ina ta zama taka?" Ta fadi a zuci,a fili kuwa da toh ta amsa kafin ta mike ta fita zuwa falon.

Mamma ta karbi wayar,sunyi magana wacce Tasleem batasan abunda yace mata ba saidai ta lura da hararar da Mamma ta dafko mata kafin ta amsawa Haris da cewa

"Kada ka damu d'ana,baza'a samu wata matsala ba."

Daga haka ta kashe wayar ta mike tayi dakinta a fusace. Wannan ya sanyayarwa da Taslewm da jiki ta mike ta rufa mata baya. Kuka sosai ta tarar Mamma nayi. Ganin ta shigo ta zauna Mamma ta ja majina

"Kin cuceni Tasleem. Idan na tuno kinyi karuwanci raina baci yakeyi naji ke kanki ina jin haushinki. Wallahi koda wasa naji kin sab'awa mijinki babu ni babu ke. Ba don Liman ne da kansa yazomin da batun aurenki da yaron mutuncin nan ba wallahi ban yarda a cuci rayuwarsa a aura mishi ke."

Jin haka itama Baby ta fashe da kuka sosai ta durkusa gaban Mamma

"Wannan ya nuna har wannan lokacin baki yafemin ba Mamma. Ya kikeso nayi,Mamma idan bada sanya albarkarki gareni ba komai na rayuwata bazata tafi a daidai ba. Please Mamma kada kiyimin bakin da zan kasa zaman aure."

Jin wannan furucin ne ya tashi hankalin Mamma,ta rungumo diyarta tana fadin

"Na yafemaki Tasleem,bazaki fi haka lalacewa ba. Har abada in sha Allah kin shiryu kenan,bana fiddaki a addu'ata."

Farin ciki yasa Tasleem dariya. Mamma ta kara dubanta bayan ta saketa

"Kabiru da Harisu sun taba ganinki cikin waccan rayuwar,hakan yasa Harisu rokona akan kada na bari ki hadu dashi."

Ranta idan yayi dubu ya baci,Haris yafison kare sirrin abokinsa akan nata??
Chapter 34 · 0% Book details