Sashe 21
African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals · about 8 min read
Anyi auren Yaya Abdullah da anti hasina. Har alokacin sun cinye wata daya suna shan amarcinsu. Tsakanina da Yaya rilwan soyayya ce tsantsa,yana mutuwar kaunata hakanan nima ina sonshi so bana wasa ba. Ana cikin haka kuma na soma jarabawa ta 1st semester ?a daidai lokacin Yaya abdullah ya dauki hutu zaije Kazaure tare da anti hasina. Har kuka nayi wai dole sai na bisu,ya bani hakuri yace idan na kammala jarabawa sai naje yanzu kam bazasu iya zuwa dani ba. Hakanan na hakura ina ji ina gani sukayi tafiyarsu............"
Baby ta dubi Haris
"Alokacin kuma KADDARA ta biyu ta afku gareni Haris......!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(39)
"Koda dai bazance kaddara ba Haris, nafi jin kunyar nan gab'ar akan na baya domin kuwa a wannan sai ince a hayyacina nake kawai RUD'IN SHAIDAN ne ya jani."
Baby ta muskuta tana runtse ido sakamakon gajiyar da hannunta mai rauni yayi. Ta jingina kanta jikin kujera tana mai duban wata mai suyar kosai a gefen titi
"Rilwan masoyina ne,wanda ganin irin kusancinsa da Yaya abdullah yasa na saki jiki na hakikance bazai yaudareni ba. Soyayya ta zamani babu irin wacce baya gwadamin. Kayi hakuri da abunda nake fadi Haris, saidai bansan sha'awa ba sai akan Rilwan. Bansan wata soyayyar ba ma sam sai akan Rilwan. Wannan shine babban kuskure dana soma tafkawa a rayuwa. A inda har watarana misalin goma na dare muna hira da Rilwan anan falon gidan kamar yanda muka saba. Shaidan ya rudemu muka aikata b'arna a karo na farko dashi. Sai bayan da komai ya gama afkuwa sannan muka ankara, kuka na fashe dashi ina dukansa ina ihun kiran ya cuceni. A karshe na gudu zuwa daki na kulle,bugu yakemin yana kirana yana mai bani hakuri saidai ina na riga na fita hayyacina. Kukan da bazai dawomin da kima da darajata ba a karo na biyu nayi asara. Dakyar a daren na rarrashi kaina. Nayita istigfari,gaba daya na rame ko makaranta naje bana fahimtar komai na daga tambayoyin da akeyi mana a jarabawa saidai na rubuta abunda na tuna. Ana tashi kuwa a mota har nakai gida ina driving ina kuka. Mantawa nayi ban gayamaka ba,a rayuwar da muka shimfida da Rilwan har tuki ya koyamin motar kanta da nake hawa shine ya siyamin. Yan uwan rilwan suna kaunata,mutane ne marasa daukar kai wani abu. Ko sadda ya siyamin motar banso karb'a ba har ma yayana saida ya yi mishi magana ya nunawa yayanmu wallahi da gaske aurena yakeson yi,kada yayanmu ya damu."
Baby ta dubi Haris "Na amince da hakan kuma,saidai zan kira abunda ya faru tsakanina dashi RUDIN SHAIDAN,wannan na daya daga cikin illar kadaicewa tsakanin namiji da macen da ba muharramai ba.
Sati biyu da faruwar al'amarin,Yayana suka dawo. Nasha tambaya a wajensu na dalilin ramata saidai na rufesu da cewa rashin lafiya nayi. Suka aminta da hakan. Yayana yana dariya yayimin albishir da samun cikin anti hasina,ihun murna na sanya kafin na rungumeta muna dariya. Ya dakamin tsawa wai nayi a sannu kada na karyamishi mata. Na saketa muna dariya har lokacin. Nasha tsaraba daga Mamma,ciki kuwa harda hotunan graduation dina Yaya musty ya bada aka wanko ya aikomin da Camera dita. Nan na hadasu na adana da wadanda mukayi dasu Mamma ranar birthday dina na sanyasu a akwatina amatsayin tarihi.
Rilwan koyaushe cikin rarrashina yake amma sam na daukemishi wuta,kudin da yake turomin ta account har ba'a magana. Ganin abun zaiyi yawa naje na samu yayana da anti suna zaune a falo na fashe da kuka. Hankalinsu ya tashi suka hau tambayata ko lafiya,nan na sanar dashi bayanin kudaden da Rilwan ke aikomin ta account na kara da cewa yayi mishi magana banaso ya daina sannan ya fita hanyata. Sukayi sukayi suji dalilina amma ina saima na kara fashewa da sabon kuka domin lokacin ma shekaruna ashirin da daya(21). Ganin haka yayana yace shikenan zai mishi magana. Bansan yanda sukayi ba saidai kam hankalina ya kwanta sakamakon daina shiga harkata da Rilwan yayi. Ko gidan yazo baya matsawa sai an kirani,amma da zarar ya hangeni ya shiga satar kallona kenan saidai na ja tsaki na harareshi.
Hum,yawan samarin da suke biyoni har gida hakanan a makaranta su matsamin yasa yayana kirana yaji ta bakina ko aure nake ra'ayin yi. Nayi azamar cewa a'a yace toh dai na kula domin baison tara samari da nakeyi. Allah Sarki baisan ma basu gabana ba,don har lokacin akwai burbushin son Rilwan a zuciyata duk da tsanar da nakeji nasa a wani gefe na sashen zuciyata.
Hum! Bayan watanni uku,mummunan labari ya fito wanda yayi silar rabuwata da yayana da duk wani na jikina.........
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(40)
"Ba don Allah Ya kiyaye ba da auren hasina da yayana sai ya mutu. Mummunan labarin kuwa,fitowar ciki a jikina a karo na biyu."
Baby ta karashe tana mai jin takaici da tsanar kanta,Haris kansa ya girgiza hakanan yaga bak'in baby anan da har ta kara mikawa wani gangar jikinta duk da dai ta kirayi hakan RUDIN SHAIDAN. Maganarta ta katseshi
"Kasalar jiki,yawan bacci da kuma amai da nakeyi ya janyo anti hasina soma tsorata da abunda ta hango a jikina matsayinta na kwararriyar likitar mata kasancewar fannin data karanta kenan. Har take shirin soma aiki a asibitin da Abbanta ke ginawa a garin Abuja. Ta sameni kwance a gadona amai har ya galabaitar dani. Fuskarta a daure cike da tashin hankali ta kirayi sunana. Na dago idanuna na dubeta. "Yaushe rabonki da ganin al'adarki?" Gabana ya bada dam,lallai sai lokacin na ankara da abunda ke shirin faruwa dani.
"Innalillahi wa inna ilaihir raaji'un! Haris bana fatan na kara ganin wannan ranar,ranar da dan uwan da muka fito ciki daya yayimin dukar kawo wuka kafin ya umarceni da na fice na bar mishi gida." Baby ta fada hawayenta babu ko digon hawaye,muryarta har ta dashe tsabar kukan data sha.
"Rabona da period kuwa,tun a watan da Rilwan ya sadu dani. Hum! Ina gayawa anti hasina nakai wata uku rabona da period, sai ta buga salati tana kwalawa yayana kira "My dil! My dil!!" Da gudu Yayana ya shigo,kana ganinsa kasan a firgice yake. "Lafiya?" Ya watso mata tambaya,ni kuwa kuka na sanya don nasan abunda anti hasinat ta gano. Jikina banda kakkarwa ba abunda yake, kafin na ankara tuni ta sanarwa Yaya Abdullah ciki ne dani. Wallahi nan da nan tsikar jikinsa ta tashi,kukan kura yayi ya jawoni ya zare belt din jikinsa yayi ta buguna. Ihu nakeyi ina kuka saidai bai fasa ba. Na tabbata ni ce da laifi. Duk wani zargin da sukayimin a baya cewar karuwanci nakeyi ya fito a bayyane yanzu kam bani da wata mafita. Anan ne yaya abdullah yayi sub'ul da baka da cewa "Shi ne kika kara daukar ciki Tasleem! Kika kara bawa wani kanki?!!! Kin cucemu!"
Anan anti hasina tasan cewar cikina na farko ma shege ne. Har tayita hayaniya da fadin ita kam saidai ya maidani gidanmu idan kuwa ba haka ba ita ta fita ta bar mishi gidan. Yaya abdullah ya rasa ya zai ce mata,tuni ta fice ta koma dakinta ya bita ya a bugu amma tak'i bud'ewa. Nikam dakyar na iya mikewa tsaye duk fatata tayi rud'u rud'u tayi jazur. Ina zaune bakin gadona ina kuka da bakin cikin tsanar kaina Yaya abdullah ya k'ara fad'owa d'akin a fusace,jikinsa har rawa yakeyi ya tsaya a kaina.
"Kin bani mamaki kanwata,kin bata wayonki. Har da kanki ki dunga kai kanki dakin namiji?!! Tirr da wannan d'abi'a taki. Toh wallahi ki barmin gidana,kuma kika kuskura kikaje ga mahaifiyarmu kika kashe aurenta,wallahi saikin raina kanki! Kije duniya ce! Daidai take da kowa!"
****
Baby ta tsagaita anan gami da dafe kanta tayi jim,a karshe kuma kukan ya taho mata ta fashe da kukan sosai,cikin kukan tace
"Tell me Haris, ya akeso nayi da rayuwata ne? Ina akeson naje? Mahaifina wanda yayi silar zuwana duniya,wanda shi kadai ne waliyin aurena,shine abun alfaharina,ya koreni daga gidansa yace na fice mishi. A gefe ga yayana wanda muka fito ciki d'aya dashi,komai nawa na damuwa a ganina da hangena ya shafeshi,saidai ashe ba haka bane. Sai gashi da kansa yake yimin korar kare daga gidansa,bayan yayimin kashedin kada naje da mahaifiyarmu! Ina akeso na shiga? Ina akeso naje naji sanyi a duniyar nan? Shakikaina sun gujeni,sun koreni daga wajensu,ya akeso nayi? Waye kuma zai so zama tare dani?"
Haris baisan sadda ya janyo hannunta ba ya sanya cikin nashi,alokacin hawayensa sun kasa tsayawa sai zuba sukeyi. Yana son cewa wani abu sai kuma ya fasa gami da sakin hannunta ya janyo handkerchief data ajiye ya mika mata
"Kiyi hakuri." Ya fada murya a dusashe.
Ta dago kwayar idanunta tana dubansa,yayi amfani da wannan damar ganin bata da niyyar karb'ar handkerchief din ya kai hannu zai share mata fuska,ta rike hannun tana girgiza masa kai kafin ta mayar mishi da hannun kasa. Dariyar bakin ciki ta saki tana mai kauda kanta
"Kada ka wahalar da kanka ga fidda hawayen da bazasu taba daina zuba ba a rayuwata Haris. Banajin zan daina zubar hawaye. Banajin ina da sauran dama na jin dadi a rayuwata. Don haka kabar sharemin abokan rayuwata,na tabbata su kadai sukafi kusanci dani, banason suma a rabani dasu."
Baby ta fadi cikin sheshek'a,ya sunkuyo yana duban fuskarta
"Nayi maki alkawarin idan har ina raye BAZAN BARKI BA tasleem. Daga yau inaso ki bani damar kasancewa mai share maki su, idan ina raye Tasleem bazan k'ara barinki kiyi rayu...."
Meke damunsa ne?! Ya tambayi kansa, me yake shirin cewa? Ya dauke kansa ganin yanda baby ta saki baki tana kallonsa. Ya Salam,ya fada yana mai juya kansa. Murmushi kawai tayi
"Kanason jin karashen labarina? Ban matsa maka.."
"Baki matsamin ba,cigaba don Allah."
Ta watsa mishi kallo mai tarin ma'anoni wanda yaji shi har tsakar kansa kafin ta gyara zama ta d'ora a inda ta tsaya............
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(41)
Baby ta dubi Haris
"Alokacin kuma KADDARA ta biyu ta afku gareni Haris......!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(39)
"Koda dai bazance kaddara ba Haris, nafi jin kunyar nan gab'ar akan na baya domin kuwa a wannan sai ince a hayyacina nake kawai RUD'IN SHAIDAN ne ya jani."
Baby ta muskuta tana runtse ido sakamakon gajiyar da hannunta mai rauni yayi. Ta jingina kanta jikin kujera tana mai duban wata mai suyar kosai a gefen titi
"Rilwan masoyina ne,wanda ganin irin kusancinsa da Yaya abdullah yasa na saki jiki na hakikance bazai yaudareni ba. Soyayya ta zamani babu irin wacce baya gwadamin. Kayi hakuri da abunda nake fadi Haris, saidai bansan sha'awa ba sai akan Rilwan. Bansan wata soyayyar ba ma sam sai akan Rilwan. Wannan shine babban kuskure dana soma tafkawa a rayuwa. A inda har watarana misalin goma na dare muna hira da Rilwan anan falon gidan kamar yanda muka saba. Shaidan ya rudemu muka aikata b'arna a karo na farko dashi. Sai bayan da komai ya gama afkuwa sannan muka ankara, kuka na fashe dashi ina dukansa ina ihun kiran ya cuceni. A karshe na gudu zuwa daki na kulle,bugu yakemin yana kirana yana mai bani hakuri saidai ina na riga na fita hayyacina. Kukan da bazai dawomin da kima da darajata ba a karo na biyu nayi asara. Dakyar a daren na rarrashi kaina. Nayita istigfari,gaba daya na rame ko makaranta naje bana fahimtar komai na daga tambayoyin da akeyi mana a jarabawa saidai na rubuta abunda na tuna. Ana tashi kuwa a mota har nakai gida ina driving ina kuka. Mantawa nayi ban gayamaka ba,a rayuwar da muka shimfida da Rilwan har tuki ya koyamin motar kanta da nake hawa shine ya siyamin. Yan uwan rilwan suna kaunata,mutane ne marasa daukar kai wani abu. Ko sadda ya siyamin motar banso karb'a ba har ma yayana saida ya yi mishi magana ya nunawa yayanmu wallahi da gaske aurena yakeson yi,kada yayanmu ya damu."
Baby ta dubi Haris "Na amince da hakan kuma,saidai zan kira abunda ya faru tsakanina dashi RUDIN SHAIDAN,wannan na daya daga cikin illar kadaicewa tsakanin namiji da macen da ba muharramai ba.
Sati biyu da faruwar al'amarin,Yayana suka dawo. Nasha tambaya a wajensu na dalilin ramata saidai na rufesu da cewa rashin lafiya nayi. Suka aminta da hakan. Yayana yana dariya yayimin albishir da samun cikin anti hasina,ihun murna na sanya kafin na rungumeta muna dariya. Ya dakamin tsawa wai nayi a sannu kada na karyamishi mata. Na saketa muna dariya har lokacin. Nasha tsaraba daga Mamma,ciki kuwa harda hotunan graduation dina Yaya musty ya bada aka wanko ya aikomin da Camera dita. Nan na hadasu na adana da wadanda mukayi dasu Mamma ranar birthday dina na sanyasu a akwatina amatsayin tarihi.
Rilwan koyaushe cikin rarrashina yake amma sam na daukemishi wuta,kudin da yake turomin ta account har ba'a magana. Ganin abun zaiyi yawa naje na samu yayana da anti suna zaune a falo na fashe da kuka. Hankalinsu ya tashi suka hau tambayata ko lafiya,nan na sanar dashi bayanin kudaden da Rilwan ke aikomin ta account na kara da cewa yayi mishi magana banaso ya daina sannan ya fita hanyata. Sukayi sukayi suji dalilina amma ina saima na kara fashewa da sabon kuka domin lokacin ma shekaruna ashirin da daya(21). Ganin haka yayana yace shikenan zai mishi magana. Bansan yanda sukayi ba saidai kam hankalina ya kwanta sakamakon daina shiga harkata da Rilwan yayi. Ko gidan yazo baya matsawa sai an kirani,amma da zarar ya hangeni ya shiga satar kallona kenan saidai na ja tsaki na harareshi.
Hum,yawan samarin da suke biyoni har gida hakanan a makaranta su matsamin yasa yayana kirana yaji ta bakina ko aure nake ra'ayin yi. Nayi azamar cewa a'a yace toh dai na kula domin baison tara samari da nakeyi. Allah Sarki baisan ma basu gabana ba,don har lokacin akwai burbushin son Rilwan a zuciyata duk da tsanar da nakeji nasa a wani gefe na sashen zuciyata.
Hum! Bayan watanni uku,mummunan labari ya fito wanda yayi silar rabuwata da yayana da duk wani na jikina.........
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(40)
"Ba don Allah Ya kiyaye ba da auren hasina da yayana sai ya mutu. Mummunan labarin kuwa,fitowar ciki a jikina a karo na biyu."
Baby ta karashe tana mai jin takaici da tsanar kanta,Haris kansa ya girgiza hakanan yaga bak'in baby anan da har ta kara mikawa wani gangar jikinta duk da dai ta kirayi hakan RUDIN SHAIDAN. Maganarta ta katseshi
"Kasalar jiki,yawan bacci da kuma amai da nakeyi ya janyo anti hasina soma tsorata da abunda ta hango a jikina matsayinta na kwararriyar likitar mata kasancewar fannin data karanta kenan. Har take shirin soma aiki a asibitin da Abbanta ke ginawa a garin Abuja. Ta sameni kwance a gadona amai har ya galabaitar dani. Fuskarta a daure cike da tashin hankali ta kirayi sunana. Na dago idanuna na dubeta. "Yaushe rabonki da ganin al'adarki?" Gabana ya bada dam,lallai sai lokacin na ankara da abunda ke shirin faruwa dani.
"Innalillahi wa inna ilaihir raaji'un! Haris bana fatan na kara ganin wannan ranar,ranar da dan uwan da muka fito ciki daya yayimin dukar kawo wuka kafin ya umarceni da na fice na bar mishi gida." Baby ta fada hawayenta babu ko digon hawaye,muryarta har ta dashe tsabar kukan data sha.
"Rabona da period kuwa,tun a watan da Rilwan ya sadu dani. Hum! Ina gayawa anti hasina nakai wata uku rabona da period, sai ta buga salati tana kwalawa yayana kira "My dil! My dil!!" Da gudu Yayana ya shigo,kana ganinsa kasan a firgice yake. "Lafiya?" Ya watso mata tambaya,ni kuwa kuka na sanya don nasan abunda anti hasinat ta gano. Jikina banda kakkarwa ba abunda yake, kafin na ankara tuni ta sanarwa Yaya Abdullah ciki ne dani. Wallahi nan da nan tsikar jikinsa ta tashi,kukan kura yayi ya jawoni ya zare belt din jikinsa yayi ta buguna. Ihu nakeyi ina kuka saidai bai fasa ba. Na tabbata ni ce da laifi. Duk wani zargin da sukayimin a baya cewar karuwanci nakeyi ya fito a bayyane yanzu kam bani da wata mafita. Anan ne yaya abdullah yayi sub'ul da baka da cewa "Shi ne kika kara daukar ciki Tasleem! Kika kara bawa wani kanki?!!! Kin cucemu!"
Anan anti hasina tasan cewar cikina na farko ma shege ne. Har tayita hayaniya da fadin ita kam saidai ya maidani gidanmu idan kuwa ba haka ba ita ta fita ta bar mishi gidan. Yaya abdullah ya rasa ya zai ce mata,tuni ta fice ta koma dakinta ya bita ya a bugu amma tak'i bud'ewa. Nikam dakyar na iya mikewa tsaye duk fatata tayi rud'u rud'u tayi jazur. Ina zaune bakin gadona ina kuka da bakin cikin tsanar kaina Yaya abdullah ya k'ara fad'owa d'akin a fusace,jikinsa har rawa yakeyi ya tsaya a kaina.
"Kin bani mamaki kanwata,kin bata wayonki. Har da kanki ki dunga kai kanki dakin namiji?!! Tirr da wannan d'abi'a taki. Toh wallahi ki barmin gidana,kuma kika kuskura kikaje ga mahaifiyarmu kika kashe aurenta,wallahi saikin raina kanki! Kije duniya ce! Daidai take da kowa!"
****
Baby ta tsagaita anan gami da dafe kanta tayi jim,a karshe kuma kukan ya taho mata ta fashe da kukan sosai,cikin kukan tace
"Tell me Haris, ya akeso nayi da rayuwata ne? Ina akeson naje? Mahaifina wanda yayi silar zuwana duniya,wanda shi kadai ne waliyin aurena,shine abun alfaharina,ya koreni daga gidansa yace na fice mishi. A gefe ga yayana wanda muka fito ciki d'aya dashi,komai nawa na damuwa a ganina da hangena ya shafeshi,saidai ashe ba haka bane. Sai gashi da kansa yake yimin korar kare daga gidansa,bayan yayimin kashedin kada naje da mahaifiyarmu! Ina akeso na shiga? Ina akeso naje naji sanyi a duniyar nan? Shakikaina sun gujeni,sun koreni daga wajensu,ya akeso nayi? Waye kuma zai so zama tare dani?"
Haris baisan sadda ya janyo hannunta ba ya sanya cikin nashi,alokacin hawayensa sun kasa tsayawa sai zuba sukeyi. Yana son cewa wani abu sai kuma ya fasa gami da sakin hannunta ya janyo handkerchief data ajiye ya mika mata
"Kiyi hakuri." Ya fada murya a dusashe.
Ta dago kwayar idanunta tana dubansa,yayi amfani da wannan damar ganin bata da niyyar karb'ar handkerchief din ya kai hannu zai share mata fuska,ta rike hannun tana girgiza masa kai kafin ta mayar mishi da hannun kasa. Dariyar bakin ciki ta saki tana mai kauda kanta
"Kada ka wahalar da kanka ga fidda hawayen da bazasu taba daina zuba ba a rayuwata Haris. Banajin zan daina zubar hawaye. Banajin ina da sauran dama na jin dadi a rayuwata. Don haka kabar sharemin abokan rayuwata,na tabbata su kadai sukafi kusanci dani, banason suma a rabani dasu."
Baby ta fadi cikin sheshek'a,ya sunkuyo yana duban fuskarta
"Nayi maki alkawarin idan har ina raye BAZAN BARKI BA tasleem. Daga yau inaso ki bani damar kasancewa mai share maki su, idan ina raye Tasleem bazan k'ara barinki kiyi rayu...."
Meke damunsa ne?! Ya tambayi kansa, me yake shirin cewa? Ya dauke kansa ganin yanda baby ta saki baki tana kallonsa. Ya Salam,ya fada yana mai juya kansa. Murmushi kawai tayi
"Kanason jin karashen labarina? Ban matsa maka.."
"Baki matsamin ba,cigaba don Allah."
Ta watsa mishi kallo mai tarin ma'anoni wanda yaji shi har tsakar kansa kafin ta gyara zama ta d'ora a inda ta tsaya............
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(41)