Sashe 12
African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals · about 8 min read
Tun ina da kankanin shekarun nan na soma tsanar Abba ganin yanda yake budewa Mamma wuta ba tare da tayi mishi wani kwakkwaran laifi ba.
Yasha cewa wai yaranta basu da tarbiyya ta k'ara gyara tarbiyyarmu tunda har a matsayina na babba bana tausayin kannena nakan kamasu na duka. Mamma taji ciwon furucin Abba saidai kawai ta bashi hakuri akan bazai kara faruwa ba.......!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(27)
Auren da Hamza yayi shine ya kawomin kwanciyar hankali kad'an a gidan. Domin duk sadda yazo idan har zamu had'u ban tsira ba.
A wannan lokacin ne Abba da Raliya suka tashi tafiya Saudiya domin aikin umrah aka shirya tafiya harda yaranta. A lokacin ne nayita kuka ina korafin Abba bai taba zuwa dani ba. Nan ta Mamma ta hau yimin fad'a na rufe bakina,domin ko yayana abdullah bai taba ketarawa zuwa Saudia ba ballantana kuma akai ga ni. Haka nayita fushi,a karshe naje batare da sanin Mamma ba na iske Abba a falonsa shi kadai. Rok'onsa na shiga yi akan a tafi dani saidai hakuri daya bani kan cewar nima zanje wataran. Duk da kankancin shekaruna nayi bakin ciki kan haka. Ga twins masu aikin yi mini gwalo. Babu yanda na iya haka suka fice akan idanunmu.
Saida sukayi sati biyu sannan sukayo waya zasu dawo. Mamma bata damu ba ta shirya abinci ta jera akan dinningtable na sashen Abba bayan an gyara komai na sashensa. Na kalli jerun kulolin da aka ajiye naja tsaki cike da bakin cikin wannan rashin damuwa da Mamma batayi akan irin cin kashin da kuma bambanci da ake nuna mata. Dabara ta fadomin,a guje na koma sashenmu,jakar Yaya abdullah na bude na fiddo office pins guda hud'u kafin na koma a guje sashen Abba. Mamma na kwalamin kira tana tambayar inda na nufa saidai ban ko saurareta ba. Haka nace na samu kujerun da Raliya da yaranta suka mayar kamar na gado, na caccaka kafin na kwashe da dariya. Ina hanyata ta fita dakin mukaci karo da Abdullah. Harara ya watsamin kafin ya tambayeni abunda nayi da officepins dinsa,a zatona bai ganni ba saidai fa yana daga falo alokacin,ganin na fito daga dakinsa yasa shi shiga kuma ya taras na zubda wasu a k'asa. Na nuna mishi banyi komai ba yace karya nakeyi,wannan yasa na fashe da kukan karya sanin da nayi baison ganin hawayena.
Nan fa ya hau rarrashina ya ja hannuna muka koma dakinsa ya bani alawa. A zuciyata banda Allah Allah da nakeyi na dawowarsu bana komai. Ai fa wajen magrib sai gasu sun shigo. Nan yan uwan Raliya da sukazo tararsu suka kacame da ihu da murna cikinsu kuwa harda hamza da matarsa Zakkiyya. Sai wajen bayan isha'i kowa ya watse. Yan biyu da kuma Hindu sun kara murjewa abinsu,da ace sun fini kyau dana sha haushi alokacin don har kalloni sukeyi suna gwalo. Na tabbatar sai sun dunga mamakin yanda nake murmushi ga wani ladabi dana soma yiwa Raliya. Ni ce harda zuwa sashenta na durkusa ina yi mata sannu da zuwa. Ita kanta tayi mamaki,saidai ta amsa tana dariyar mugunta. Nima ficewata nayi da dariyar ta mugunta.
Misalin tara na dare akayi zaman cin abinci,saida na tabbatar da kujerun da ban sanya alluran nan ba,ba nan mamma da abdullah suka zauna ba,haka nan Abba baya chanja wajen zama,waje daya ne kadai nashi. Nima naja na zauna don nafi kowa zumudin azo aci. Abba ya dubeni
"Tasleem tashi maza kije ki kirawo Maman.."
Bai karasa ba sai gasunan sun iso,Raliya sai shan kamshi takeyi ala dole an zama Hajiya. Abunda yafimin dadi lokacin bai wuce na itace ta soma zama ba,sai ta sanya k'ara ta mike tsaye tana sosa mazaunanta. Abba da Mamma suna cikin tambayarta ko lafiya,suma yan biyu suka zauna har da Hindu. Ai kuwa Hindu ta canyara ihun kuka,yan biyu ma haka. Raliya ta fusata ta hau duba kujerun,ai kuwa nan ta fiddo alluran,ta ajiyesu kan teburin. Dukkaninmu muka kalla,ciki harda ni,bansan ya akayi ba sai ji nayi na saki dariya. Abba ya buga tebur a fusace
"Waye da wannan aikin? Ke kuma yar iskar yarinya shine kike dariya?!"
Mamma a sanyaye tace
"Wallahi bansani ba doctor,Tasleem kodai kece?"
Ta jefomin tambaya,Yaya abdullah kawai hararata yakeyi,
"Bani bace nima.."
"Kinci kaza kazanki! Munafuncin da uwarki ta koyamaki kenan na ki raina matata ko? Toh yau zaki gane shayi ruwa ne! Amma kuwa Maryam kin bani mamaki,sai kace wata jahila har kike tiwa yaranki tarbiyya b'atacciya! Me kikeso ki koyarwa yarana ne?!"
Bansan lokacin dana mike ba
"Abba ba laifin Mamma bane! Ka daina yi mata fad'a."
Mari naji,nan kuma Raliya ta rufeni da duka,Abba cewa yakeyi
"Kinga irin tarbiyyar ko? Wallahi kedai Maryam kin cuceni."
Mamma mikewa tayi a fusace tabar falon na tabbata haushina taji,Yaya abdullah ma fita yayi. Raliya ta dauki allurar nan tayi ta tsikaramin ina ihun kuka. Saida ta gaji da jibgata sannan ta sakeni,Abba baice komai ba. Haka na fice ina kuka. Saidai kuwa ina shiga falon Mamma na tarar da ita zaune tana kuka wannan ne silar shanye nawa kukan. Na karasa na durkusa a gefe,
"Ya zanyi dake Tasleem? A shekarunki da ko tara baki cika ba kinsan kiyi wannan muguntar me zaki zama a yayinda girma ya tasa ki? Ashe haka zaki cigaba da janyomin magana da cin mutunci?"
Gaba daya hankalina ya tashi,mukayita bawa Mamma hakuri,anan ta gargadeni da kada na kuma. Saida mukayi yini cur Yaya Abdullah bayamin magana don tsabar bakin ciki,hakanan a karshe ya sauko.
Na sanya a raina sai nasa an jibgi twins a makaranta. Na fidda homeworks dinsu a jaka na cusa a nawa jakar dayake antinsu muguwa ce. Ai kuwa a ranar saida ta zanesu don har muka baro makaranta suna kuka da Allah Ya isa. Banda kyakyata dariya dana dunga yi a motar bance uffan ba. Saida mukazo gida na fiddo na basu abinsu. Ai kuwa kai tsaye wajen Mamma sukaje suka gayamata. Mamma bata taba dukana ba sai a ranar,Kulu ce ta kwaceni daga hannunta.
Bayan dana cika shekaru goma sha biyu a duniya.............
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(29)
Ina nan zaune tare da Gwaggo Hajara naji sallamar Yaya abdullah. Harara ya soma makomin kafin kuma ya kama kunnena ya murd'a. Tunda nake da yayana bai taba yimin abunda naji zafi ba sai yau. Ihu nakeyi,wanda hakan ya shigo da gwaggo Hajara dake dakinta. Ta dakamishi tsawa kafin ya hankad'ani nayi baya ina kuka.
"Menene haka Abdullah? Metayi maka?"
Yana huci yace
"Duk wata matsala da mamma ke shiga,Tasleem tana da kamasho a ciki. Yanzu kin janyo Malam yayi fushi yace ta zauna har sai ya nemi Abbanmu yaji abunda ke faruwa anyi zaman sulhu. Ga mamma na kuka,nikam ban taba ganin yarinya irinki ba. Duk da irin kwab'ar.."
"Kai dakata,menene ya faru da Adda Maryam din?"
Gwaggo Hajara tayi tambayar da batasani ba. Abdullah baice komai ba ya fice. Sai ni na labarta mata komai ina kuka. Na kara da cewa indai Mamma bazata koma ba toh nima babu inda zanje anan wajenta zan cigaba da rayuwata
Gwaggo Hajara dai batace mini komai ba sai jinjina halin zurfin ciki irin na Mamma takeyi. Ba don ma dai so GAMON JINI bane,manyan mutane nawa ne a kauyen nan da suka nemi auren Maryama basu samu ba,Allah Yayi sai tayi zaman birnin Kano.
Muna ganin abun da wasa sai gashi kuwa hutunmu yana k'arewa na sati daya da zamuyi a Kazaure. Direbanmu yazo,nan Malam yace babu inda Mamma zataje sai Abba ya tako yazo anyi magana. Ko a jikina,don da a sona ne nima bazan koma va saida Mamma ta budemin wuta daman cike take da haushin na tona sirrinta da take rike dashi. "
Baby ta numfasa ta dubi kwayar idanun Haris
"Ban taba ganin mace mai matukar son mijinta ba kamar Mamma. Duk da wannan wahalar da take sha wajen Abba bai sanya ta tsaneshi ba. Kullum cikin fatan su dawo daidai takeyi."
"Haka muka koma muka barta,Abba kuwa har mukayi kwana uku baisan ba tare da Mamma muka dawo ba. Kwananmu uku da dawowa kuma yabar garin zuwa Minna don yin wani aiki daya shafi likitanci. Wannan abu ya konamana rai. Kullum sai munyi waya da Mamma. Har na soma damuwa,nayi danasanin zamanta a gida. Kulu ita zatayi ta rarrashina da ban baki. Ita ta zame mana madadin Mamma. Ita ke mana girki da komai na gyare gyare. Dattijuwa ce sosai da zatakai shekaru arba'in. Yaya abdullah yafini kewar Mamma,saboda tsananin shakuwar da yayi da ita. Don kuwa Mamma alokacin data haifi Abdullah ta dauki son duniya ta doramishi musamman ma da taga ta shafe shekaru uku bata haihu ba saita dauka shi kadai ne rabonta. Sau da yawa sai su kashe su binne ina can ina harkata bansan sunayi ba. Wataran ma saidai ina gefe ina assignment na jiyo dariyarsu.
Ranar wata asabar ina zaune cikin garden dinmu ina game da wayata da Mamma ta siyamin. Allah Ya yini mace mai son game a rayuwa hakanan ban fiyeson kaya masu nauyi ba gaskiya. Lokacinma sanye nake da riga da wando marasa nauyi 'yan kanti. Shekaruna sha uku alokacin,kaga kenan ban zama wata cikakkiyar budurwa ta azo a gani ba. Hankalina gaba daya ya raja'a akan wayata,banyi zato ba naji hannu yana shafani. A firgice na wurgar da wayar ina mikewa zaune daga kwanciyar da nayi akan lilon. Tsananin tsoro da mamaki da kuma rawar jikin da nakeyi yasa na kasa cewa komai. Ba kowa bane illa Usman. Kallo daya ya tabbatarmin a bugensa yake. Yana dariya irin ta maye yace
"Hey you girl,mene kike ja da baya? Ke kanwa kike gareni menene ciki?"
Ya fada yana k'ara nufoni,na suri wayata na arce a guje. Ina zuwa falo nayi arba da yaya abdullah wanda ke shirin fita hannunsa rike da ruwan swan. Na rukunkumeshi ina rawar jiki.
Ya dagoni a tsorace yana fiddo ido
"Ke! Menene haka?"
Na hadiyi miyau ban iya cewa komai ba. Ya dakamin tsawa
"Bakyajina?! Me akayi maki?"
Na tsorata da yanayinsa duk da kankantar shekarun yaya abdullah,wato sha shida. Babba ne a kaina. Ga mamakina sai na kasa fada mishi na girgiza kai
"Kadangare ya biyoni."
Tsaki yaja kafin ya tureni yana fadin
Yasha cewa wai yaranta basu da tarbiyya ta k'ara gyara tarbiyyarmu tunda har a matsayina na babba bana tausayin kannena nakan kamasu na duka. Mamma taji ciwon furucin Abba saidai kawai ta bashi hakuri akan bazai kara faruwa ba.......!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(27)
Auren da Hamza yayi shine ya kawomin kwanciyar hankali kad'an a gidan. Domin duk sadda yazo idan har zamu had'u ban tsira ba.
A wannan lokacin ne Abba da Raliya suka tashi tafiya Saudiya domin aikin umrah aka shirya tafiya harda yaranta. A lokacin ne nayita kuka ina korafin Abba bai taba zuwa dani ba. Nan ta Mamma ta hau yimin fad'a na rufe bakina,domin ko yayana abdullah bai taba ketarawa zuwa Saudia ba ballantana kuma akai ga ni. Haka nayita fushi,a karshe naje batare da sanin Mamma ba na iske Abba a falonsa shi kadai. Rok'onsa na shiga yi akan a tafi dani saidai hakuri daya bani kan cewar nima zanje wataran. Duk da kankancin shekaruna nayi bakin ciki kan haka. Ga twins masu aikin yi mini gwalo. Babu yanda na iya haka suka fice akan idanunmu.
Saida sukayi sati biyu sannan sukayo waya zasu dawo. Mamma bata damu ba ta shirya abinci ta jera akan dinningtable na sashen Abba bayan an gyara komai na sashensa. Na kalli jerun kulolin da aka ajiye naja tsaki cike da bakin cikin wannan rashin damuwa da Mamma batayi akan irin cin kashin da kuma bambanci da ake nuna mata. Dabara ta fadomin,a guje na koma sashenmu,jakar Yaya abdullah na bude na fiddo office pins guda hud'u kafin na koma a guje sashen Abba. Mamma na kwalamin kira tana tambayar inda na nufa saidai ban ko saurareta ba. Haka nace na samu kujerun da Raliya da yaranta suka mayar kamar na gado, na caccaka kafin na kwashe da dariya. Ina hanyata ta fita dakin mukaci karo da Abdullah. Harara ya watsamin kafin ya tambayeni abunda nayi da officepins dinsa,a zatona bai ganni ba saidai fa yana daga falo alokacin,ganin na fito daga dakinsa yasa shi shiga kuma ya taras na zubda wasu a k'asa. Na nuna mishi banyi komai ba yace karya nakeyi,wannan yasa na fashe da kukan karya sanin da nayi baison ganin hawayena.
Nan fa ya hau rarrashina ya ja hannuna muka koma dakinsa ya bani alawa. A zuciyata banda Allah Allah da nakeyi na dawowarsu bana komai. Ai fa wajen magrib sai gasu sun shigo. Nan yan uwan Raliya da sukazo tararsu suka kacame da ihu da murna cikinsu kuwa harda hamza da matarsa Zakkiyya. Sai wajen bayan isha'i kowa ya watse. Yan biyu da kuma Hindu sun kara murjewa abinsu,da ace sun fini kyau dana sha haushi alokacin don har kalloni sukeyi suna gwalo. Na tabbatar sai sun dunga mamakin yanda nake murmushi ga wani ladabi dana soma yiwa Raliya. Ni ce harda zuwa sashenta na durkusa ina yi mata sannu da zuwa. Ita kanta tayi mamaki,saidai ta amsa tana dariyar mugunta. Nima ficewata nayi da dariyar ta mugunta.
Misalin tara na dare akayi zaman cin abinci,saida na tabbatar da kujerun da ban sanya alluran nan ba,ba nan mamma da abdullah suka zauna ba,haka nan Abba baya chanja wajen zama,waje daya ne kadai nashi. Nima naja na zauna don nafi kowa zumudin azo aci. Abba ya dubeni
"Tasleem tashi maza kije ki kirawo Maman.."
Bai karasa ba sai gasunan sun iso,Raliya sai shan kamshi takeyi ala dole an zama Hajiya. Abunda yafimin dadi lokacin bai wuce na itace ta soma zama ba,sai ta sanya k'ara ta mike tsaye tana sosa mazaunanta. Abba da Mamma suna cikin tambayarta ko lafiya,suma yan biyu suka zauna har da Hindu. Ai kuwa Hindu ta canyara ihun kuka,yan biyu ma haka. Raliya ta fusata ta hau duba kujerun,ai kuwa nan ta fiddo alluran,ta ajiyesu kan teburin. Dukkaninmu muka kalla,ciki harda ni,bansan ya akayi ba sai ji nayi na saki dariya. Abba ya buga tebur a fusace
"Waye da wannan aikin? Ke kuma yar iskar yarinya shine kike dariya?!"
Mamma a sanyaye tace
"Wallahi bansani ba doctor,Tasleem kodai kece?"
Ta jefomin tambaya,Yaya abdullah kawai hararata yakeyi,
"Bani bace nima.."
"Kinci kaza kazanki! Munafuncin da uwarki ta koyamaki kenan na ki raina matata ko? Toh yau zaki gane shayi ruwa ne! Amma kuwa Maryam kin bani mamaki,sai kace wata jahila har kike tiwa yaranki tarbiyya b'atacciya! Me kikeso ki koyarwa yarana ne?!"
Bansan lokacin dana mike ba
"Abba ba laifin Mamma bane! Ka daina yi mata fad'a."
Mari naji,nan kuma Raliya ta rufeni da duka,Abba cewa yakeyi
"Kinga irin tarbiyyar ko? Wallahi kedai Maryam kin cuceni."
Mamma mikewa tayi a fusace tabar falon na tabbata haushina taji,Yaya abdullah ma fita yayi. Raliya ta dauki allurar nan tayi ta tsikaramin ina ihun kuka. Saida ta gaji da jibgata sannan ta sakeni,Abba baice komai ba. Haka na fice ina kuka. Saidai kuwa ina shiga falon Mamma na tarar da ita zaune tana kuka wannan ne silar shanye nawa kukan. Na karasa na durkusa a gefe,
"Ya zanyi dake Tasleem? A shekarunki da ko tara baki cika ba kinsan kiyi wannan muguntar me zaki zama a yayinda girma ya tasa ki? Ashe haka zaki cigaba da janyomin magana da cin mutunci?"
Gaba daya hankalina ya tashi,mukayita bawa Mamma hakuri,anan ta gargadeni da kada na kuma. Saida mukayi yini cur Yaya Abdullah bayamin magana don tsabar bakin ciki,hakanan a karshe ya sauko.
Na sanya a raina sai nasa an jibgi twins a makaranta. Na fidda homeworks dinsu a jaka na cusa a nawa jakar dayake antinsu muguwa ce. Ai kuwa a ranar saida ta zanesu don har muka baro makaranta suna kuka da Allah Ya isa. Banda kyakyata dariya dana dunga yi a motar bance uffan ba. Saida mukazo gida na fiddo na basu abinsu. Ai kuwa kai tsaye wajen Mamma sukaje suka gayamata. Mamma bata taba dukana ba sai a ranar,Kulu ce ta kwaceni daga hannunta.
Bayan dana cika shekaru goma sha biyu a duniya.............
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(29)
Ina nan zaune tare da Gwaggo Hajara naji sallamar Yaya abdullah. Harara ya soma makomin kafin kuma ya kama kunnena ya murd'a. Tunda nake da yayana bai taba yimin abunda naji zafi ba sai yau. Ihu nakeyi,wanda hakan ya shigo da gwaggo Hajara dake dakinta. Ta dakamishi tsawa kafin ya hankad'ani nayi baya ina kuka.
"Menene haka Abdullah? Metayi maka?"
Yana huci yace
"Duk wata matsala da mamma ke shiga,Tasleem tana da kamasho a ciki. Yanzu kin janyo Malam yayi fushi yace ta zauna har sai ya nemi Abbanmu yaji abunda ke faruwa anyi zaman sulhu. Ga mamma na kuka,nikam ban taba ganin yarinya irinki ba. Duk da irin kwab'ar.."
"Kai dakata,menene ya faru da Adda Maryam din?"
Gwaggo Hajara tayi tambayar da batasani ba. Abdullah baice komai ba ya fice. Sai ni na labarta mata komai ina kuka. Na kara da cewa indai Mamma bazata koma ba toh nima babu inda zanje anan wajenta zan cigaba da rayuwata
Gwaggo Hajara dai batace mini komai ba sai jinjina halin zurfin ciki irin na Mamma takeyi. Ba don ma dai so GAMON JINI bane,manyan mutane nawa ne a kauyen nan da suka nemi auren Maryama basu samu ba,Allah Yayi sai tayi zaman birnin Kano.
Muna ganin abun da wasa sai gashi kuwa hutunmu yana k'arewa na sati daya da zamuyi a Kazaure. Direbanmu yazo,nan Malam yace babu inda Mamma zataje sai Abba ya tako yazo anyi magana. Ko a jikina,don da a sona ne nima bazan koma va saida Mamma ta budemin wuta daman cike take da haushin na tona sirrinta da take rike dashi. "
Baby ta numfasa ta dubi kwayar idanun Haris
"Ban taba ganin mace mai matukar son mijinta ba kamar Mamma. Duk da wannan wahalar da take sha wajen Abba bai sanya ta tsaneshi ba. Kullum cikin fatan su dawo daidai takeyi."
"Haka muka koma muka barta,Abba kuwa har mukayi kwana uku baisan ba tare da Mamma muka dawo ba. Kwananmu uku da dawowa kuma yabar garin zuwa Minna don yin wani aiki daya shafi likitanci. Wannan abu ya konamana rai. Kullum sai munyi waya da Mamma. Har na soma damuwa,nayi danasanin zamanta a gida. Kulu ita zatayi ta rarrashina da ban baki. Ita ta zame mana madadin Mamma. Ita ke mana girki da komai na gyare gyare. Dattijuwa ce sosai da zatakai shekaru arba'in. Yaya abdullah yafini kewar Mamma,saboda tsananin shakuwar da yayi da ita. Don kuwa Mamma alokacin data haifi Abdullah ta dauki son duniya ta doramishi musamman ma da taga ta shafe shekaru uku bata haihu ba saita dauka shi kadai ne rabonta. Sau da yawa sai su kashe su binne ina can ina harkata bansan sunayi ba. Wataran ma saidai ina gefe ina assignment na jiyo dariyarsu.
Ranar wata asabar ina zaune cikin garden dinmu ina game da wayata da Mamma ta siyamin. Allah Ya yini mace mai son game a rayuwa hakanan ban fiyeson kaya masu nauyi ba gaskiya. Lokacinma sanye nake da riga da wando marasa nauyi 'yan kanti. Shekaruna sha uku alokacin,kaga kenan ban zama wata cikakkiyar budurwa ta azo a gani ba. Hankalina gaba daya ya raja'a akan wayata,banyi zato ba naji hannu yana shafani. A firgice na wurgar da wayar ina mikewa zaune daga kwanciyar da nayi akan lilon. Tsananin tsoro da mamaki da kuma rawar jikin da nakeyi yasa na kasa cewa komai. Ba kowa bane illa Usman. Kallo daya ya tabbatarmin a bugensa yake. Yana dariya irin ta maye yace
"Hey you girl,mene kike ja da baya? Ke kanwa kike gareni menene ciki?"
Ya fada yana k'ara nufoni,na suri wayata na arce a guje. Ina zuwa falo nayi arba da yaya abdullah wanda ke shirin fita hannunsa rike da ruwan swan. Na rukunkumeshi ina rawar jiki.
Ya dagoni a tsorace yana fiddo ido
"Ke! Menene haka?"
Na hadiyi miyau ban iya cewa komai ba. Ya dakamin tsawa
"Bakyajina?! Me akayi maki?"
Na tsorata da yanayinsa duk da kankantar shekarun yaya abdullah,wato sha shida. Babba ne a kaina. Ga mamakina sai na kasa fada mishi na girgiza kai
"Kadangare ya biyoni."
Tsaki yaja kafin ya tureni yana fadin