Sashe 29
African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals · about 8 min read
"Mahaifinki a yanzu idan kika ganshi,kikaga yanda yake fama da ciwon sugar da hawan jini,zaki tausaya mishi saboda ramar da yayi tayi yawa,aikinsa tuni ya ajiyeshi gefe. Zakiyi mamaki idan nace maki kullum cikin zubar hawaye yake duk a dalilin rashin sanin takamaiman inda kike. Ban boyemishi dukkan abunda ya faru ba ya nunamin kurena,yace idan shi ya koreki ba'a hayyacinsa na meyasa zanyi wannan ta'asar? A karshe yace laifin nashi ne. Da ace bai koreki ba babu yanda za'ayi ki shiga wata rayuwa ta daban."
"Yaya bani labari mana game da abunda ya kawo chanjin Abba."
"Tun bayan tafiyarki da watanni uku, mummunan iftila'i ya fad'awa Usman na konewar babban shagon da baiyi ko wata biyar da bud'ewa ba,hakanan wasu b'arayin sun tareshi a hanya sun mishi duka har suka nakastashi suka kwace wayoyi da kudadensa. Abun mamaki kuma sati ba'a rufa na itama marigayi raliya akayi hada mata jini da majina a karshe aka watsar da ita a kofar gida. Jinyar da tayi kamar bazata tashi ba,gashi kuma wata kaddarar komai na Abba ya soma ja da baya Tasleem. Kamar wanda aka sanyawa hannu fitar ma da yake zuwa asibitinsa ya gaza. Hakanan raliya ta matsa mishi akan sai an fidda d'anta waje anyi mishi aiki saboda tuni matarsa tace bazata iya zama da nakasashshe ba ta ajiye mishi 'yar sa ta tafi. Akan dole Abba ya kashe makudan kudade wajen aikin kafar Usman ta hanyar fitar dashi waje saidai aiki baiyi ba wai a niyyarsu a sanyamishi kafafun roba saidai garin haka mutuwa ta riskeshi acan. Nan raliya ta hau ihu da zage zage,abun ne ya zame mata wajen goma ba. A gefe ga d'iyarta ta tsunduma kanta a harkar bin maza itama. Can kuwa nura ne ya kara lalacewa da bin mata. Matarsa ma ta gujeshi,hamza kuwa ya zamo mijin tace a wajen matarsa. Ke rayuwa fa tayi mata zafi ga mutuwar Usman,haka ta dawo ta rungumi jikokinta da suke a wajenta. Bata isa ta sanya Hamida da Hamid aiki ba suyi,kamar wata sa'arsu haka zakiga sunayi mata tsawa. Duk cikinsu,hindatu kadai ta fita daban,babu ruwanta ke sai kice ma ba daga jikin raliya ta fito ba. Nazo jana'izar Usman sannan na tattara na koma Abuja ina mai cike da dumbin mamakin ramar da Abba yayi sannan gaba daya duk yayi sanyi kamar bashi ba.
Wata biyu rabona dashi saidai nakan kokarta kiranshi na gaisheshi,wataranar juma'a ina zaune na dawo daga masallaci na amsa kiransa inda ya nemi nazo na sameshi da sauri. Ba shiri washegari na tafi a mota. Kuka sosai na samu Abba yana yi,cike da fargaba nikam na karasa wajenshi don gani nakeyi kamar zai yimin magana cikin fada fada kamar yanda ya saba. Ga mamakina naga ya rungumeni yana neman gafarata,yace a baya yakan damu idan yayimana wani abun ashe ba'a son ransa yakeyi ba Tasleem. Yace min ya iske raliya tana waya da bokanta inda takeso tazo ayi mata aikin da za'a kasheshi suci ragowar kudinsa saboda ta fahimci ya soma talaucewa ita kam bata tab'a ganin jinin sarauta mai bak'in jini kamar Khalid ba. Kowa gudunsa yakeyi yan uwan duk sun juyamishi baya saboda ganin shi kadai ne ba uwa ba uba.(Ta manta itace ta janyomishi tsanar,don akwai randa yayansa waziri yana son ganinsa yace bai zuwa. Kusan sati shiru har da kanshi wazirin yazo gidan,ganin babban mutum yasa maigadin budemishi dakin bak'i,yayita zaman jira amma raliya ta rike abba ta hanashi fitowa a karshe waziri ya fusata yabar gidan da alkawarin bazai kara shiga harkar Khalid na tunda bashi da bukatarsu hakanan ya gargadi dukkam zuri'arsu kada wanda ya k'ara lek'awa gidansa. Wannan labarin nima baba Maigadi ke bani,hankalina ya tashi don har gidan waziri naje na bashi hakuri ya sakarmin fuska sosai ya nunamin ai mu d'in nasu ne. Yace kuma zai sanya ayi addu'a sosai gareshi don bai amince da yanayinsa ba. Shima ya d'agawa mahaifinmu kafa ne har zuwa wani lokacin.
Abba ya cigaba da labartamin,yace tun sadda yaji wannan zancen yaji kamar bashi ba,komai na rayuwarsa ya daidaita,kirjinsa yabar nauyi. A ranar kuwa ya yiwa raliya abunda bai tab'a yinsa ba sakamakon tsanarta da yaji,duka yayi mata sosai sannan ya saketa. Tace wallahi bazata bar gidan ba,saida ya hado da jami'an tsaro har jikokinta yace duk ta tattara ta tafi dasu shi kam baisan menene ya kwasheshi ya auro wannan kaddarar ba. Hakanan ya kori nura wanda har ya nemi ya zageshi. Hindatu kam tasha kuka,ta hau rokonsa ya barta a wajensa itama ta tsani uwarta. Haka dai ya hakura yabar yaransa. Washegarin faruwar al'amarin ne yayi kirana yake sanar dani. Nayi godiya ga Allah da baisa zan mutu kafin wannan rana ba. Nan Abba ya tambayeni game da mamma,na bashi labarin komai har zuwa gidana da kikayi da sauransu. Anan ne nadama tsantsa ya kamashi. Tun dai daga lokacin ya kamu da rashin lafiya,karshe yasa na kaishi wajen waziri. Muna shiga waziri yana zaune a fada,yana ganin Abba cikin yanayin zubar hawaye yana nufoshi,tsam ya mike har na tsoraci ko marinsa zaiyi kawai sai ya rungumeshi wanda hakan ya bawa abba kuka sosai a jikinsa. Ya jashi inda fadawan suka mike suna zuba kirari,sukayi ciki. Kinji yanda aka sasanta,Abba ya tsanantawa su Hamid ya hanasu fita ko'ina ya santa ido sosai a kansu,ganin batanci da rashin maida hankalin Hamid a karatu zaiyi yawa yasa shi turashi makarantar horo. Hamida kuwa kasancewar tana tsoron abba alokacin ganin irin korar da yayiwa mamanta sannan taje taga muhallin da raliya take babu wani kayan morewa rayuwa dolenta ta nutsu,Abba yace ya bata sari ta fiddo miji ko kuma ya aurar da ita ga wanda yaso. Har nan kazaure na rakoshi ya roki gafararsu kafin ya koma kuma rashin lafiya ta hau shi. Yayimin fadan dalilina na boyewa iyayen mamma inda kike karshe abba ya hau yawaita addua da tsayuwar dare da kuma zubar hawaye duk saboda rashinki da alhakin daya dauka namu. Raliya kuwa gobara sukayi a gidan babu wanda ya tsira daidai da nura,sakamakon jonin wuta direct da Nura yayo musu acewarsa bazai iya rayuwa ba wutar lantarki ba ya gama zage mahaifiyarsu tas akan bakin cikin data janyomusu suna cikin daula. Karshensu kenan. Yanzu haka hamida tayi aure ga wani alhaji mai mata biyu har ta haihu,duk da wulakancin da take sha hakanan take zaman hakuri. Hindatu kuwa tana nan tare dani a Abuja ta soma karatunta a jami'a, hakanan Abba da nake jinyarsa saidai yanzun jikinsa da sauki sosai. Waziri ma ya matsamin na maidoshi gabansa inajin hakan zaiyi tunda shima Abban yace ya gaji da zama gidana saboda kunyar hasina. Duk da dai yanzu gidane na kashin kaina."
Tasleem tayi shiru,tabbas rayuwa abar tsoro ce. A sanyaye ta kara tambayarsa
"Ina labarin Ridwan kuma?"
Murmushi Abdullah yayi
"Allah Sarki,abbansa fa ya jima yana fushi dashi har korarsa yaso yi na hana. Amma yanzu yayi aure yana zaune acan London wajen uncle dinsa da matarsa Jidda. Yaransu biyu ma,daya taci sunanki dayar kuwa sunan mamansa."
Tayi murmushi kawai.
*****
Washegari yaya abdullah yana tafiya,itama ta shirya koda ta yiwa mamma sallamar komawa wajensu inna bata ko kalleta ba. Haka nan ta wuce a sanyaye.
Da la'asar Liman ya tura ayi kiranta.....!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar
(55)
Bata kawo komai ba ta mike ta yafa mayafinta ta nufi dakin Liman jikinta akwai yanayin sanyi wanda tun dawowarta daga gidan mamma take cikinsa. Koda inna ta tambayeta ta amsa da babu komai.
Yana zaune yana duba wani littafi na hadisai yaji sallamarta wanda hakan yasa shi ajiye littafin a gefe yana mai amsawa fuska a sake. Ta shigo tana yamutsa fuska kadan kafin ta soma kokarin zama tana fad'in
"Nidai wannan tsohon kana neman matsamin fa,yanzu kuma menayi aka d'agoni bama a tarbeni da 'yar shila ba."
Yayi dariya
"Shak'iyiya,wanda kika ci bai isheki bane a k'aro maki gobe? Nutsu don magana zamuyi."
Ya soma da yi mata doguwar nasiha akan muhimmancin aure wanda tun daga haka tasha jinin jikinta,kirjinta kuma bai bar bugu da sauri da sauri ba. Saida ya kammala sannan ya bijiro mata da bukatarsa na neman amincewarta kan batun aurenta da Haris.
Cikin tsananin mamaki da fargaba ta dubeshi
"Shi Haris dinne yace yana sona baffa?"
Jin dadi game da amsar da zai bata yasa Liman yin wata 'yar dariya
"Shakka babu,harisu ne yazo da batun kamar yasan fatanmu kenan ni da aminina. Kuma munyi na'am da batunsa nasan bazaki watsa mana k'asa a ido ba kasancewarki yarinya mai biyayya."
Tayi k'asa da kanta,nan da nan abokan hirarta suka ziyarci fuskarta(hawaye). Ina ita ina Haris wai? Haris yasan abunda yake kuwa? Me zaiyi da sauran maza? Sam bazata bari ta cuci mai niyyar taimakonta ba,kai ta kasa gaskata da gasken shine yayi tayin auren nata.
"Kuyi hakuri bafamfa,bazan iya aurensa ba!"
Nan take annurin dake saman fuskarsa ya dauke,tamkar bai taba dariya ba ya koma Abdulmaleek Hussein dinsa sak!
"Nufinki zaki bani kunya ne Tasleem? Toh bari na fadamaki wallahi tunda nake da Aminina tun zamanin kuruciyarmu dayanmu bai taba zuwar wa dayanmu da bukata ba munyi watsi da ita. Baki isa ba Tasleem! Ko uwarki k'arya takeyi na nemi bukata awajenta tak'iyi,na takaice maki ma aminina shine ya wuce gaba wajen aurenta da Ubanki tun a farko domin a baya banso tayi nesa har haka ba. Ki tashi ki barmin d'akina,aure kuwa keda Harisu saidai idan anyishi ki mutu."
Daga haka ya maida fuskarsa gefe babu wata walwala a samanta.
A sanyaye tasleem ta mike tana k'ara mannewa da abokin hirarta harda sheshshek'a.
Kallo daya tayi mata kafin tabar murza robb a hancinta
"Lafiya kuwa?"
Cikin kukan dai ta labarta mata yanda sukayi da Liman,inna taja tsaki gami da fadin
"Allah Ya kyauta,ina goyon bayan Liman,wannan hukuncin yayi. Domin kuwa samun yaron mutunci irin Harisu a zamanin nan akwai wuya. Nikam dari bisa dari na amince kuma banga aibu da aurenku ba. Budurwa sharab dake,ai wallahi sai yanda kikayi dashi ta hanyar biyayya da kissar d'iya mace."
"Yaya bani labari mana game da abunda ya kawo chanjin Abba."
"Tun bayan tafiyarki da watanni uku, mummunan iftila'i ya fad'awa Usman na konewar babban shagon da baiyi ko wata biyar da bud'ewa ba,hakanan wasu b'arayin sun tareshi a hanya sun mishi duka har suka nakastashi suka kwace wayoyi da kudadensa. Abun mamaki kuma sati ba'a rufa na itama marigayi raliya akayi hada mata jini da majina a karshe aka watsar da ita a kofar gida. Jinyar da tayi kamar bazata tashi ba,gashi kuma wata kaddarar komai na Abba ya soma ja da baya Tasleem. Kamar wanda aka sanyawa hannu fitar ma da yake zuwa asibitinsa ya gaza. Hakanan raliya ta matsa mishi akan sai an fidda d'anta waje anyi mishi aiki saboda tuni matarsa tace bazata iya zama da nakasashshe ba ta ajiye mishi 'yar sa ta tafi. Akan dole Abba ya kashe makudan kudade wajen aikin kafar Usman ta hanyar fitar dashi waje saidai aiki baiyi ba wai a niyyarsu a sanyamishi kafafun roba saidai garin haka mutuwa ta riskeshi acan. Nan raliya ta hau ihu da zage zage,abun ne ya zame mata wajen goma ba. A gefe ga d'iyarta ta tsunduma kanta a harkar bin maza itama. Can kuwa nura ne ya kara lalacewa da bin mata. Matarsa ma ta gujeshi,hamza kuwa ya zamo mijin tace a wajen matarsa. Ke rayuwa fa tayi mata zafi ga mutuwar Usman,haka ta dawo ta rungumi jikokinta da suke a wajenta. Bata isa ta sanya Hamida da Hamid aiki ba suyi,kamar wata sa'arsu haka zakiga sunayi mata tsawa. Duk cikinsu,hindatu kadai ta fita daban,babu ruwanta ke sai kice ma ba daga jikin raliya ta fito ba. Nazo jana'izar Usman sannan na tattara na koma Abuja ina mai cike da dumbin mamakin ramar da Abba yayi sannan gaba daya duk yayi sanyi kamar bashi ba.
Wata biyu rabona dashi saidai nakan kokarta kiranshi na gaisheshi,wataranar juma'a ina zaune na dawo daga masallaci na amsa kiransa inda ya nemi nazo na sameshi da sauri. Ba shiri washegari na tafi a mota. Kuka sosai na samu Abba yana yi,cike da fargaba nikam na karasa wajenshi don gani nakeyi kamar zai yimin magana cikin fada fada kamar yanda ya saba. Ga mamakina naga ya rungumeni yana neman gafarata,yace a baya yakan damu idan yayimana wani abun ashe ba'a son ransa yakeyi ba Tasleem. Yace min ya iske raliya tana waya da bokanta inda takeso tazo ayi mata aikin da za'a kasheshi suci ragowar kudinsa saboda ta fahimci ya soma talaucewa ita kam bata tab'a ganin jinin sarauta mai bak'in jini kamar Khalid ba. Kowa gudunsa yakeyi yan uwan duk sun juyamishi baya saboda ganin shi kadai ne ba uwa ba uba.(Ta manta itace ta janyomishi tsanar,don akwai randa yayansa waziri yana son ganinsa yace bai zuwa. Kusan sati shiru har da kanshi wazirin yazo gidan,ganin babban mutum yasa maigadin budemishi dakin bak'i,yayita zaman jira amma raliya ta rike abba ta hanashi fitowa a karshe waziri ya fusata yabar gidan da alkawarin bazai kara shiga harkar Khalid na tunda bashi da bukatarsu hakanan ya gargadi dukkam zuri'arsu kada wanda ya k'ara lek'awa gidansa. Wannan labarin nima baba Maigadi ke bani,hankalina ya tashi don har gidan waziri naje na bashi hakuri ya sakarmin fuska sosai ya nunamin ai mu d'in nasu ne. Yace kuma zai sanya ayi addu'a sosai gareshi don bai amince da yanayinsa ba. Shima ya d'agawa mahaifinmu kafa ne har zuwa wani lokacin.
Abba ya cigaba da labartamin,yace tun sadda yaji wannan zancen yaji kamar bashi ba,komai na rayuwarsa ya daidaita,kirjinsa yabar nauyi. A ranar kuwa ya yiwa raliya abunda bai tab'a yinsa ba sakamakon tsanarta da yaji,duka yayi mata sosai sannan ya saketa. Tace wallahi bazata bar gidan ba,saida ya hado da jami'an tsaro har jikokinta yace duk ta tattara ta tafi dasu shi kam baisan menene ya kwasheshi ya auro wannan kaddarar ba. Hakanan ya kori nura wanda har ya nemi ya zageshi. Hindatu kam tasha kuka,ta hau rokonsa ya barta a wajensa itama ta tsani uwarta. Haka dai ya hakura yabar yaransa. Washegarin faruwar al'amarin ne yayi kirana yake sanar dani. Nayi godiya ga Allah da baisa zan mutu kafin wannan rana ba. Nan Abba ya tambayeni game da mamma,na bashi labarin komai har zuwa gidana da kikayi da sauransu. Anan ne nadama tsantsa ya kamashi. Tun dai daga lokacin ya kamu da rashin lafiya,karshe yasa na kaishi wajen waziri. Muna shiga waziri yana zaune a fada,yana ganin Abba cikin yanayin zubar hawaye yana nufoshi,tsam ya mike har na tsoraci ko marinsa zaiyi kawai sai ya rungumeshi wanda hakan ya bawa abba kuka sosai a jikinsa. Ya jashi inda fadawan suka mike suna zuba kirari,sukayi ciki. Kinji yanda aka sasanta,Abba ya tsanantawa su Hamid ya hanasu fita ko'ina ya santa ido sosai a kansu,ganin batanci da rashin maida hankalin Hamid a karatu zaiyi yawa yasa shi turashi makarantar horo. Hamida kuwa kasancewar tana tsoron abba alokacin ganin irin korar da yayiwa mamanta sannan taje taga muhallin da raliya take babu wani kayan morewa rayuwa dolenta ta nutsu,Abba yace ya bata sari ta fiddo miji ko kuma ya aurar da ita ga wanda yaso. Har nan kazaure na rakoshi ya roki gafararsu kafin ya koma kuma rashin lafiya ta hau shi. Yayimin fadan dalilina na boyewa iyayen mamma inda kike karshe abba ya hau yawaita addua da tsayuwar dare da kuma zubar hawaye duk saboda rashinki da alhakin daya dauka namu. Raliya kuwa gobara sukayi a gidan babu wanda ya tsira daidai da nura,sakamakon jonin wuta direct da Nura yayo musu acewarsa bazai iya rayuwa ba wutar lantarki ba ya gama zage mahaifiyarsu tas akan bakin cikin data janyomusu suna cikin daula. Karshensu kenan. Yanzu haka hamida tayi aure ga wani alhaji mai mata biyu har ta haihu,duk da wulakancin da take sha hakanan take zaman hakuri. Hindatu kuwa tana nan tare dani a Abuja ta soma karatunta a jami'a, hakanan Abba da nake jinyarsa saidai yanzun jikinsa da sauki sosai. Waziri ma ya matsamin na maidoshi gabansa inajin hakan zaiyi tunda shima Abban yace ya gaji da zama gidana saboda kunyar hasina. Duk da dai yanzu gidane na kashin kaina."
Tasleem tayi shiru,tabbas rayuwa abar tsoro ce. A sanyaye ta kara tambayarsa
"Ina labarin Ridwan kuma?"
Murmushi Abdullah yayi
"Allah Sarki,abbansa fa ya jima yana fushi dashi har korarsa yaso yi na hana. Amma yanzu yayi aure yana zaune acan London wajen uncle dinsa da matarsa Jidda. Yaransu biyu ma,daya taci sunanki dayar kuwa sunan mamansa."
Tayi murmushi kawai.
*****
Washegari yaya abdullah yana tafiya,itama ta shirya koda ta yiwa mamma sallamar komawa wajensu inna bata ko kalleta ba. Haka nan ta wuce a sanyaye.
Da la'asar Liman ya tura ayi kiranta.....!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar
(55)
Bata kawo komai ba ta mike ta yafa mayafinta ta nufi dakin Liman jikinta akwai yanayin sanyi wanda tun dawowarta daga gidan mamma take cikinsa. Koda inna ta tambayeta ta amsa da babu komai.
Yana zaune yana duba wani littafi na hadisai yaji sallamarta wanda hakan yasa shi ajiye littafin a gefe yana mai amsawa fuska a sake. Ta shigo tana yamutsa fuska kadan kafin ta soma kokarin zama tana fad'in
"Nidai wannan tsohon kana neman matsamin fa,yanzu kuma menayi aka d'agoni bama a tarbeni da 'yar shila ba."
Yayi dariya
"Shak'iyiya,wanda kika ci bai isheki bane a k'aro maki gobe? Nutsu don magana zamuyi."
Ya soma da yi mata doguwar nasiha akan muhimmancin aure wanda tun daga haka tasha jinin jikinta,kirjinta kuma bai bar bugu da sauri da sauri ba. Saida ya kammala sannan ya bijiro mata da bukatarsa na neman amincewarta kan batun aurenta da Haris.
Cikin tsananin mamaki da fargaba ta dubeshi
"Shi Haris dinne yace yana sona baffa?"
Jin dadi game da amsar da zai bata yasa Liman yin wata 'yar dariya
"Shakka babu,harisu ne yazo da batun kamar yasan fatanmu kenan ni da aminina. Kuma munyi na'am da batunsa nasan bazaki watsa mana k'asa a ido ba kasancewarki yarinya mai biyayya."
Tayi k'asa da kanta,nan da nan abokan hirarta suka ziyarci fuskarta(hawaye). Ina ita ina Haris wai? Haris yasan abunda yake kuwa? Me zaiyi da sauran maza? Sam bazata bari ta cuci mai niyyar taimakonta ba,kai ta kasa gaskata da gasken shine yayi tayin auren nata.
"Kuyi hakuri bafamfa,bazan iya aurensa ba!"
Nan take annurin dake saman fuskarsa ya dauke,tamkar bai taba dariya ba ya koma Abdulmaleek Hussein dinsa sak!
"Nufinki zaki bani kunya ne Tasleem? Toh bari na fadamaki wallahi tunda nake da Aminina tun zamanin kuruciyarmu dayanmu bai taba zuwar wa dayanmu da bukata ba munyi watsi da ita. Baki isa ba Tasleem! Ko uwarki k'arya takeyi na nemi bukata awajenta tak'iyi,na takaice maki ma aminina shine ya wuce gaba wajen aurenta da Ubanki tun a farko domin a baya banso tayi nesa har haka ba. Ki tashi ki barmin d'akina,aure kuwa keda Harisu saidai idan anyishi ki mutu."
Daga haka ya maida fuskarsa gefe babu wata walwala a samanta.
A sanyaye tasleem ta mike tana k'ara mannewa da abokin hirarta harda sheshshek'a.
Kallo daya tayi mata kafin tabar murza robb a hancinta
"Lafiya kuwa?"
Cikin kukan dai ta labarta mata yanda sukayi da Liman,inna taja tsaki gami da fadin
"Allah Ya kyauta,ina goyon bayan Liman,wannan hukuncin yayi. Domin kuwa samun yaron mutunci irin Harisu a zamanin nan akwai wuya. Nikam dari bisa dari na amince kuma banga aibu da aurenku ba. Budurwa sharab dake,ai wallahi sai yanda kikayi dashi ta hanyar biyayya da kissar d'iya mace."