← Book details African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals Local reading mode
READING PART 5 OF 35

Sashe 5

African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals · about 8 min read

"Da gaskiyarki,ban sanki ba,asalima yau na tab'a ganinki a inda bai cancanci ace kina nan ba. A matsayinki kuma na kilaki. So,as you said,bake zaki bani amsar kowacce tambayata ba. Ke kuma kiyi hankali da kazantacciyar rayuwar da kike ciki,na lura baki da damuwa ko kuma d'igon bakin cikin wannan rayuwa taki. Saidai fa..."

Ya dubeta,sai lokacin ya sakar mata murmushi wanda daga gani kasan na yak'e ne

"Akwai ranar k'in dillanci."

Daga haka ya sauka zuwa falon k'asa domin jiran aminin nashi.

Ta maido dubanta ga falon,ta lumshe ido tana murmushi

"He's very handsome,saidai ba wayewa."

Ta furta cikin zazzak'ar muryarta,bata ko damu da kalamansa ba ta maida earpiece dinta ta kunna wak'a abinta tana kurb'ar lemo,a gefe kuma zuk'ar taba.

*******

Taxi yana tsayawa,kb ya biyashi ya fito. Da azama Maigadinsa ya iso a guje yana kokarin karb'ar akwatin hannunsa. Kyakkyawan mari yayi mishi a kunci,kafin ya soma magana a fusace

"Don ubanka wace doka na sanya maka?!!! Bance maka idan bana gari ba,banda baby kada kabar kowa ya shigomin gida ba?!!"

Matashin maigadi wanda yaci suna Amadu,yana rike da fuskarsa ya russuna cike da girmamawa

"Kayi hakuri yallabai,wallahi ina fama da ciwon ciki shine na lek'a kemis bansan da zuwan Madam ba."

"Mts!"

Kb yaja tsaki yayi gaba,da azama Amadu ya ciccib'i akwatinsa jiki yana rawa yabi bayanshi bayan ya watsawa Ado maigadin makwaftansu kallon baka kyautamin ba.

'YAR BARIKI

©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)

(11)

"Babyna wannan motar kuma?"

Ta dubeshi

"Nufinka na sauka na baka abarka?"

Yayi azamar dakatar da ita

"No,bance ba. Saidai kinga Haris zai iya d'ago..."

Ta soma kiciniyar bud'e mota, yayi saurin dakatar da ita.

"Haba babyna,please ni bance ki sauka ba. Ga handbag dinki,daga baya zanzo gidan please. Kada kiyi fushi dani."

Sai lokacin ta sakar mishi murmushi na gefen kumatu

"Ko kaifa."

Daga haka ya matsa tayi ribas,tuni Amadu ya bud'e mata k'ofa ta fice.

Kb ya dawo da hankalinsa akan motar Baby,dabara ta fad'o mishi,ya sami k'usa ya sace taya d'aya kafin ya mike. Ido hudu sukayi da Haris wanda fitowarsa kenan,ya dubi motar kafin ya nufi tasa a fusace ya hau kokarin budewa. Kb ya isa da sauri ya riko hannunsa

"Don Allah kada kayimin gurguwar fahimta mana,tayar motarta d'aya ne ya sace shine dalilin daukar tawa da tayi. Amma idan an gyara zan aika mata sai a karb'omin tawa. Kada.."

"Ya isa Kabir,gyara kuma ya rage tsakaninka da Mahaliccinka. Shi yafi cancanta ka tsorata ba kowa ba. Kayi tunani da ka haihu,baka gudun ace yau diyarka ce cikin wannan..."

"Haris please! Banason wannan irin zantukan! Ya wuce,na fadamaka kaddara ce yasa nake kula wannan d'inma amma nayi maka alk'awarin daga yau ta k'are. Don Allah ka rufamin asiri."

Ya tabe baki gami da daga kafad'a

"Ka tsaya mana muyi sallah,nasan ko magrib bakayi ba. Gashi kafin ka kai gida nasan anyi isha'i."

Sanin da yayi haka dinne,ya sanyashi dakatawa. Sukayi sallah,sannan ya wuce.

******

Tun komawarsa gidansa,tunani da matsanancin tausayin kanwarsa Yasmeen sun hanashi sakat. Har lokacin surar yarinyar ya kasa b'aceqa daga idanuwansa,ba don komai ba saboda tsanarta da yakeji tare da mamakin karfin hali irin na karuwan mata masu maida gidan wani nasu. Kodayake dai babban laifin yana ga Kb wanda har ya iya bata wannan fuskar. Zina fa!! Wai ma menene abun dadi da tunkaho a cikinta?!! Me Kb yakeji idan ya tafka irin wannan sab'on? A gefe d'aya ga Yasmeen,a yanda yasan kanwarsa,yarinya ce mai hakuri da halayen mijinta. Tabbas bata boyemishi dukkan sirrukanta tun tana budurwa ma. Dukkan abunda hankali zai dauka na neman shawara,daidai da wanda ya dace ya sani takan sanarmishi ta waya. Ko kuma idan yaje su kwashi fin awa suna hira. Duk da ba gida d'aya suka taso da Yasmeen ba,sun shaku sosai dashi.
Idanunsa suka kad'a sukayi jazur,hakikanin gaskiya,ko kusa kanwarsa batayi sa'ar miji ba. Manemin mata wanda har yake zargin yana shaye shaye. Duk da har zuwa yanzu bai taba kamashi dumu dumu cikin mayen ba saidai ganin yanda neman matan nasa yayi yawa yasa ya soma gaskata komai akace kb yayi zai aminta da haka.

K'arar wayarsa ce ta katse mishi tunani,dakyar ya lalubota ya duba mai kiran. Yasmeen dince. Murmushi ya saki wanda yafi kuka ciwo,kafin ya daga. Tun kan yace wani abu,ta soma magana cikin farin ciki

"Yayana kasan wani abun mamaki kuwa? Au,Assalamu alaikum,yayana barka da dare."

Nan da nan ransa ya danyi sanyi jin cewar kanwarsa tana cikin farin ciki. Cikin tattausar muryarsa ya amsa sallamar ya d'ora da fad'in

"Fadamin da sauri little,bazan iya jira na wani lokaci ba."

Tayi dariya mai nuni da tana cikin farin ciki

"Wallahi yayana wannan zuwan naga chanji sosai a wajen Prince..."

"Me yayi maki?!! Gayamin ko menene?!!!"

Ta danyi shiru kad'an jin ya fusato,a sanyaye tace

"Cool down yayana,bafa wani abu yayimin na bacin rai ba. Kawai dai umm...mun dawo tamkar new couples."

Ta karashe tana dariya kasa kasa,ya lumshe ido yana mai sauke ajiyar zuciya.

"Alhamdulillah little, burina na ganki cikin kwanciyar hankali. Ina diyata?"

"Allah Sarki yayana,nima farin cikinka shine nawa. Ai bansan ya zanyi ba idan aurenka yazo don murna."

Murmushi yayi wanda bai shirya mishi ba,ita kam Yasmeen bata gajiya da tunasar dashi batun aure sai kace wani karamin yaro. Ya shafi sumar fuskarsa

"Zanyi,lokaci ne baiyi ba little. Ki tayani addu'a. Baki amsamin tambayata ba."

"Oh,nasreen tayi bacci. Ai yanzu muka gama waya da babanta yace min ma Monday zai juyo da safe."

"Kabir kenan."

Ya fad'a a zuci,don ya fahimci ba karamin razana yayi ba yau.
A fili kuwa ya amsa da ok.

"Bari na kyaleka kaji da gajiyar ofis. Bye."

Sukayi sallama ya ajiye wayar. Tausayin kanwarsa ya k'aru a zuciyarsa,tabbas har yanzu batasan waye Kb ba,kuma baya fatan tasan wannan boyayyen al'amarin,daidai da iyayensu baiso zancen yaje wurinsu. Shi kam,sai inda karfinsa ya k'are akan ganin rayuwar amininsa kuma dan uwansa ya daidaita.....!

*****

Misalin (1:00am) na dare......

'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(12)
Kwance suke a dakinta kan makeken gadonta,tayi
matashi da cinyarsa.
"Babyna."
Ba tare data amsa ba ta dago idanuwanta
lumsassu ta dubeshi,ya sanya hannu yana wasa
da girarta kafin yace
"Inason muyi wata magana ne."
Batace komai ba,sai kallo da take binsa
dashi,wannan ya bawa Kb damar cigaba da
zancensa.
"Kinga dai a yanzu babu damar haduwa a gidan
ko? Sannan yanzu idanun Haris a kaina yake na
tabbatar bai gamsu cewar na rabu dake da gaske
ba."
Ya danyi shiru kamar mai nazari,kafin ya riko
hannunta yana cigaba da duban kwayar idanunta
masu k'ara dulmiyar dashi kogin kaunarta.
"Abu ne da bazan taba iya aikatawa ba,saidai
zuwa yanzu ina tsoron kada Haris yakai k'arata
wajen iyayenmu....."
"Menene dangantakarku da guy dinnan ne? Na
lura ka bashi matsayi da yawa a rayuwarka KB."
Baby ta katseshi ta hanyar jefo mishi wannan
tambayar. Murmushi yayi ya shafi gashin dokin
dake kanta wanda sai yace shi dai tunda yasan
baby bai taba ganin iyakar jelar gashinta
ba,baisani ba tana da yawan gashin ko babu.
"Haris Aliyu kenan,iyayenmu aminan juna
ne,wannan yasa mukayi sabo dashi sosai fiye da
tunanin mai tunani. Ya kasance dan uwana
wanda bama boyewa juna sirri. Nan da kike
ganinsa ustaz ne,ya fiye takura kansa baison ya
more rayuwarsa."
Kb ya dan tabe baki kafin ya cigaba
"Abunda zai baki mamaki ma,har yau bai taba
sanin diya mace ba sannan har zuwa yanzu yak'i
aure a cewarsa gareni,baiga wacce tayi mishi
bane."
Baby ta lumshe ido kafin ta muskuta ta juyawa
Kb baya
"Karancin wayewa ke damunsa,saidai kasan wani
abu? Da ace nice kai babu wanda ya isa hanani
yin abunda nake ra'ayinsa. Kaban mamaki KB,
akan wannan guy din saika rabu dani."
"No baby,ni wanene da zan bar mace irinki?
Wannan karya ne. Shiyasa na samo mana
mafita,kawai ki nutsu ki saurareni please."
Har lokacin idanuwanta a rufe suke,haka kawai
take tsintar kanta da tunano kyakkyawar halittar
fuskar HARIS,
"Ina sauraronka."
"Zaki aureni Tasleem?"
Cikin matukar razana ta bude idanuwanta,kafin ta
mike zaune tana duban kwayar idanuwan
Kabir,kwarai babu alamun wasa a abunda yace.
Gabanta ya shiga faduwa haka kawai,yayi azamar
matsowa ya riko hab'anta
"Wallahi Tasleem zan iya aurenki,babu kyankyami
ko wani abu. Sonki nakeyi,bazaki gane yanda na
shaku da soyayyarki..."
Ta cire hannunshi ta juya mishi baya gami da
sauke kafarta akan gadon,har lokacin bugun
zuciyarta bai daidaita ba
"Na gayamaka tun a farkon mu'amalarmu kafin
muyi nisa haka. Kamar yanda ka taba zuwarmin
da batu irin wannan a yanzun ma amsar d'aya
ce,bazan iya aurenka ba."
Kb hankalinshi ya tashi,kaunarta na kara karfi a
zuciyarsa. Zuwa yanzu ya amincewa kansa lallai
ba sha'awa kawai yake yiwa Baby tasleem
ba,harda soyayya. Hannunta cikin nasa,yayinda
kalar kwayar idanunsa suka sauya launi saboda
tsabar tashin hankali na jin maganar dake dake
fitowa a bakin baby.
"Me kikeso a rayuwa wanda har yanzu baki samu
ba? Wallahi ki fad'amin ko menene shi zan
mallaka maki Tasleem dan har zaki yarda na
killaceki a gidana ya zamana ni kadai nake da
hakki akanki. Ya zamana kinbar mu'amala da
kowa. Wallahi tasleem zan iya mallaka maki
dukkanin dukiyata matukar hakan zaisa ki amince
dani matsayin mijinki. Please ki....."
Ta mike a fusace
"Ya isheni Kb!!!!"
Ta dakatar dashi kafin ta watsa mishi duban da
tunda suke tare bata taba yi mishi ba. Duba ne na
raini da wulakanci,
"Bazaka taba samun biyan bukatar nan ba. Na
tsani aure! Bazan taba yinshi ba!! Babu komai a
rayuwar aure sai tozarci da wulakanci! Wannan
ikrarin da kakeyi na kana sona,zai tafi da zarar na
kasance matarka."
Kb ya nufeta da niyyar rikowa tayi azamar
dakatar dashi ta hanyar daga mishi hannu. Daga
haka ta fice da gudu tabar dakin. Bata shige
ko'ina ba sai d'akin Dalal ta sanya mukulli jikin
kofar ta rufe. Kuka takeyi sosai wanda ya tada
hankalin kb dake tsaye daga waje yana jiyo
sautin kukan nata.
"Please baby i'm sorry,indai maganar aure ne
bazan k'ara yi maki ba."
Ita kuwa baby,ita kadai tasan me me kalmar aure
yake tunano mata.
Daren babu wanda yayi kwanan farin ciki a
cikinsu.
'YAR BARIKI

©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)

(13)
Chapter 5 · 0% Book details