Sashe 13
African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals · about 8 min read
"Banza kawai."
Ya ficewarsa. Ranar haka na yini sukuku,bansan usman cikakken dan iska bane sai ranar. Duk wani kuzari bani dashi,abunda nakeji a bakin kawayena suke cewa iskancine sai ma'aurata keyi yau gashi a kaina. Haka dai na dunga kiyayewa ban kara bari munyi arba da usman ba balle Nura.
Kwanan Abba uku muka ganshi ya dawo. Washegari da safe ya fice bamusan inda ya nufa ba.
Cikin ikon Allah washegarin ranar da muka ganshi yayi fitar safe,sai ga Mamma ta dawo da Gwaggo Hajara da tayo mata rakiya. Ihun murna muka hau yi da tsalle. Mamma ita kanta farin cikin ganinmu takeyi.
Babu laifi Abba ya chanja don har girki Mamma tana karb'a. Wannan ya dagawa Raliya hankali sosai,ashe sanyin da tayi mana a baya ganin Abba yabar shiga harkarmu ne. Abba yanzu da taga har girki ya bawa Mamma sai hankalinta ya tashi. Nan kuma ta dawo da masifarta. Sai ta kintaci Mamma ta shirya fita da mota, zata hana mukulli tace motocin gidan babu mai,hakanan Mamma ke hakura ta koma don sau daya ta taba zuciya ta hau mashin saboda alokacin ba'asan da adaidaita ba, Abba ya ganta. Ranar saura kiris ya saketa Allah Ya tak'aita.
*******
Bayan shekara biyar,inada shekaru sha bakwai a duniya. Na zama cikakkiyar budurwa kuma alhamdulillah sai Allah Ya bani wani irin farin jini. Maza da mata a makarantarmu suna kaunata. A gida kuwa,har doka Mamma ta sanyamin akan babu ruwana da shiga sashen matan Nura da Usman,don kuwa anan suka tare kowannensu da matarsa su dinma matan irin gogaggun nan ne kamarsu. Hakanan ta sanyamin dokar fita da hijabi ko kuma sanya abayoyi tunda ta kula mayyar kananun kaya ce ni, duka duka manyan kayana irinsu atamfa da leshi yawanci sai anko ko kuma na dinka don sha'awa na ajiye. Yaya abdullah baya garin gaba daya, a can k'asar waje yake karatunsa,shekararsa uku acan ya zamana baifi mishi sauran shekara daya da rabi ba ya takarkare karatunsa fannin bussiness. Twins suma sun girma,fad'a tsakanina da Hamida na cacar baki wataran ma har da duka babu abunda aka fasa. Dama dama Hindu ce bana tunanin zata dauki d'abi'un uwarta duk ta fisu hakuri sannan ta kasance marar hayaniya. A makaranta ina ganin sharholiyar da Hamida keyi dukkan abunda ya hada na raye raye da kula kulan maza ba wanda bata cusa kanta ciki. Hamid ne dai ya wuce boarding school wannan ne bazance ga halinshi ba."
Baby ta gyara zama tana yamutsa fuska saboda gajiyar da hannunta ya soma yi
"Sorry."
Haris ya furta cike da kulawa,abunda bai taba yi bane. Hakan ya sanyata murmusawa shima ya mayarda martani yana mai basarwa ta hanyar shafa sumarsa.
Ta cije lebbanta na kasa mai nuni da abunda zata fada akwai ciwo(lol)
"A wannan lokacin ne,Allah Ya kawo karshen zaman Mamma da Abba,Yaya abdullah yana can wata duniya baisan abunda ke wakana ba...."
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(28)
Alokacin ina jss1,yayana ss1. Twins kuwa suna primary 4,Hindu kuma 3. Na soma hankali da fahimtar abubuwa,a fannin islamiyya ma tuni Yaya abdullah yayi haddar Al-kur'ani,sai hadisai da sauran litattafai da akeyi mishi. Nikam sauka nakeyi don ko haddar ban soma ba alokacin. Twins ne abinsu sai a hankali,don uwar tasu cikin yawon biki da suna da gaisuwar mutuwa take. Koyaushe bata fiye zama gida ba duk fitarta da yaranta take tafiya(note! Ban taba rayuwar kowa ba!). Wannan ya janyo wala wala a karatunsu na addini,malaman har korafi sukeyi don har Abba sun samu sunyi magana dashi ya nuna za'a kiyaye saidai fa bata canza zani ba.
Wataranar juma'a da yamma na dawo daga gidan Waziri inda nakai ziyara ga aminiyata Juwairiyya,misalin karfe biyar da mintuna ne,direba ya faka. Na fito ina duban wasu matasa biyu tare da Hamza anan kusa da motar Hamza suna hira da kyakyata dariya. D'aya gajere ne,bak'i saidai kalar fatar ta haskaku tamkar dai na yan gidan hutu. Bashi da wani kyau na azo a gani yayinda d'ayan kuwa ya kasance dogo yana da d'an haske. Sannan yayi kama matuka da Raliya. Bazasu wuce talatin da wani abu ba,kansu wani dan iskan aski ne na yan duniya. Gashi duk sun matse cikin kananun kaya masu wanduna iyaka gwuiwa. Na dauke kaina kamar ban gansu ba zan shige gida. Tsawar da Hamza ya dakamin ce ta rud'a tunanina,na dubeshi. Jajayen idanunsa ya shiga zaremin,yace naje. Ba musu ta isa jiki yana rawa.
"Don ubanki baki iya gaisar da mutane ba? Ko bakiga Nura da Usman bane? Kina daukarsu bare ne? Toh don ubanki sun fiki matsayi a gidan nan."
Jin abunda yace na zumburo baki,a ganina rainin hankali ne ace wani can ya fika alhalin gidan ubanka ne. Naji an kaimin hauri da k'afa a bakin. Nura ne,gajeran ciki. Ya zaromin ido
"Barta Yaya hamza,ashe har wannan lokacin wannan yar iskar yarinyar bata nutsu ba. Tun tana 'yar ficikarta take tsula tsiya a gidan nan. Toh don ubanki tunda muka dawo garin nan keda gyatumar taki zaku magantu. Tashi kibar nan!"
Ya dakamin tsawa,ai da gudu gudu nayi ciki cikin ihun kuka. A falo na zube inata bori,Kulu da Mamma suka fito suna tambayar ko lafiya? Yaya abdullah kuwa bai nan yana tare da abokansa na unguwa suna ball. Na shaida musu abunda ya faru,Mamma taja tsaki
"Allah Ya kyauta."
Daga haka tayi gaba bata ko damu da wankemin jinin dake d'iga daga bakina ba. Kulu ta kamani mukayi bandakina ta wankemin bakin tsaf sannan ta sanyani na chanja kayan kasancewar sun b'aci da jini.
Result din Nura da Usman ba wani kyau sukayi ba,tun dawowarsu ma banda yawo da suka sanya a gaba basu da wani aiki. Ga yan mata da suke yiwa b'arin naira. Bayan bautar kasarsu Raliya ta sanya Abba ya nema musu aikin yi saidai babu wanda akayi dacen samarwa. A karshe tace ya basu jari. Nan ya basu kudade da yawa don suyi sana'a koda kasuwanci ne. Saidai ba wanda ya yunk'ura,karshe ma mota suka saya kowanne da tasa. Rayuwarsu ta baya sai abunda ya k'aru,neman mata kamar me don hatta da shaye shaye sukan d'an tab'a. Mamma tasha gargad'ina akan kar na kuskura koda wasa na dunga shiga sashensu. Baruwana dasu, naji gargadinta sosai duk da inajin haushinsu. A duniya babu wadanda na tsana bayan Abba sai su. Tsakanin Mamma da Abba kuwa,har ta manta rabon da Abba ya zauna sukayi hirarsu cikin nishadi har ma ya nemi shawararta akan wani aiki nasa, ko kuma ya sanar da ita abunda yake niyyar yi ko kuma yayi. Zuwa lokacin ma Mamma bata damuwa,idan da sabo yaci ace ta saba domin kuwa abun gaba yakeyi. Na takaice maka saida ya zamana Abba ko girkin Mamma bayaci,sam Mamma bata da kwana a gidan. Kiyayyarsa gareta tamkar an k'ara ne. Domin hana kawo abinci sashensa yayi,yace tayi zamanta a nata sashen idan yana da bukata ai yasan inda take amma anan ita ya lura bata da aiki sai korafi akan abunda baikai ya kawo ba. Tun ina zuwa sashen Abba da kaina duk da kwab'ar Mamma har nazo na daina domin ko kallo ban isheshi ba. Zafi ya hadewa Mamma,gashi ita ba suruka ba balle takai k'ara don tun Abba yan karami mahaifiyarsa ta rasu. Shi kadai ne a wajen mahaifiyarsa,a hannun mahaifiyar Alhaji Nasir,uwargida a wajen marigayi Waziri Ma'aruf wato mahaifinsu Abba,ya tashi. Itace komai nasa kafin itama ciwon sugar yayi ajalinta. Mahaifiyar Gwaggo sarai ita kadaice tsohuwar data rage a matan Waziri,sai yaransa su goma sha biyar cif. 'Ya'ya goman duk na uwargidan ne,sai Abba cikon na sha daya sannan ya yan amaryar waziri,uwar Gwaggo sarai,itace mai yara hudu.
Kwarai dukkansu matan sun watsar da Mamma,hatta da Gwaggo Sarai mai kawo mata tsegumin auren da Abba zaiyi a farko. Matar Waziri mai ci a yanzu,Alhaji Nasir,Hajiya Hajara. Itace suke mutunci sosai da Mamma don shekarunta bai wuce na Mamma ba. Itace kuma k'arama ta uku a matansa. Ita ta kasance mahaifiyar Juwairiyya.
Wannan kenan!!!
Mamma ta rame ta rasa meke mata dadi,Abdullah shine mai rarrashinta. Akwai sadda naji yana bata shawarar kodai zataje Kazaure ta sanarwa Malam? Don lokacin bai zama limamin juma'a ba,marigayi Malam Abubakar ne Limamin. Mamma tak'i. Yaya abdullah shine abokin shawararta wasu lokutan yanda ta suka shak'u ko ni da nake mace ba muyi wannan shak'uwar ba.
Rayuwa na tafiya da dadi babu dadi. Saida muka samu hutun watanni uku na makarantar boko,ina shirin shiga jss2 Yaya abdullah kuwa zai shiga Ss2,mukaje Kazaure ziyaran kakannina. Yan uwan mamma babu wanda bai firgita da ganin yanda ta koma ba. Sukayita tambaya tana cewa babu komai. Har Malam ma haka ta fada mishi. A karshe ta sanyamu a d'aki ni da abdullah ta k'ara kwab'armu akan kada mu sake mu gayamusu halin da take ciki. Ai kuwa bayan ta fita ziyarar yar uwarta. Naje na samu Malam,ina kuka na zayyane mishi komai na yanda Mamma ke rayuwa a gidan nan don har yan aikin Raliya sun fita muhimmanci a wajen Abba. Ga rashin kunya da yaran Raliya sukeyi mata,babu mai ganin girmanta musamman ma manyan. Malam ya fusata ainun,yace nabar kukan bari ta dawo. Ai kuwa Mamma tana dawowa nabar gidan da zummar lekawa gidan kanwar Mamma,Gwaggo Nusaiba......
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(30)
"Maganar da nakeyi maka har ila yau,bansan takamaiman silar rabuwar iyayena. Abunda zan iya tunawa shine. Adaidai wannan lokacin da sakin ke daf da faruwa,Mamma ta shiga wani irin yanayi na yawan tunani da kuka. Nasha kamata a daki tana kuka,tambayar duniya nayi mata tak'i sanar dani. Ga Abba ma bai shiga sha'aninta,na fahimci ran girkinta saidai tayi mishi abinci takai ta juyo bata zuwa inda yake. Ta rame gaba daya, zuwa lokacin nayi hankali nasan menene ya kamata hakan yasa ban sanarwa Yaya abdullah ba duk kuwa da cewa muna yawan chatting dashi yayita bani labarin wata budurwarsa da yake fatan aurarta,Hidaya. Itama 'yar Kano ce karatu ya kaita London. Na gaji da ganin halin da Mamma ke ciki wannan yasa na tambayi kulu ko tana da masaniya saidai ta tabbatar min babu abunda Mamma ta gayamata,itama ta tambayeta amma ta nuna mata bakomai.
Ya ficewarsa. Ranar haka na yini sukuku,bansan usman cikakken dan iska bane sai ranar. Duk wani kuzari bani dashi,abunda nakeji a bakin kawayena suke cewa iskancine sai ma'aurata keyi yau gashi a kaina. Haka dai na dunga kiyayewa ban kara bari munyi arba da usman ba balle Nura.
Kwanan Abba uku muka ganshi ya dawo. Washegari da safe ya fice bamusan inda ya nufa ba.
Cikin ikon Allah washegarin ranar da muka ganshi yayi fitar safe,sai ga Mamma ta dawo da Gwaggo Hajara da tayo mata rakiya. Ihun murna muka hau yi da tsalle. Mamma ita kanta farin cikin ganinmu takeyi.
Babu laifi Abba ya chanja don har girki Mamma tana karb'a. Wannan ya dagawa Raliya hankali sosai,ashe sanyin da tayi mana a baya ganin Abba yabar shiga harkarmu ne. Abba yanzu da taga har girki ya bawa Mamma sai hankalinta ya tashi. Nan kuma ta dawo da masifarta. Sai ta kintaci Mamma ta shirya fita da mota, zata hana mukulli tace motocin gidan babu mai,hakanan Mamma ke hakura ta koma don sau daya ta taba zuciya ta hau mashin saboda alokacin ba'asan da adaidaita ba, Abba ya ganta. Ranar saura kiris ya saketa Allah Ya tak'aita.
*******
Bayan shekara biyar,inada shekaru sha bakwai a duniya. Na zama cikakkiyar budurwa kuma alhamdulillah sai Allah Ya bani wani irin farin jini. Maza da mata a makarantarmu suna kaunata. A gida kuwa,har doka Mamma ta sanyamin akan babu ruwana da shiga sashen matan Nura da Usman,don kuwa anan suka tare kowannensu da matarsa su dinma matan irin gogaggun nan ne kamarsu. Hakanan ta sanyamin dokar fita da hijabi ko kuma sanya abayoyi tunda ta kula mayyar kananun kaya ce ni, duka duka manyan kayana irinsu atamfa da leshi yawanci sai anko ko kuma na dinka don sha'awa na ajiye. Yaya abdullah baya garin gaba daya, a can k'asar waje yake karatunsa,shekararsa uku acan ya zamana baifi mishi sauran shekara daya da rabi ba ya takarkare karatunsa fannin bussiness. Twins suma sun girma,fad'a tsakanina da Hamida na cacar baki wataran ma har da duka babu abunda aka fasa. Dama dama Hindu ce bana tunanin zata dauki d'abi'un uwarta duk ta fisu hakuri sannan ta kasance marar hayaniya. A makaranta ina ganin sharholiyar da Hamida keyi dukkan abunda ya hada na raye raye da kula kulan maza ba wanda bata cusa kanta ciki. Hamid ne dai ya wuce boarding school wannan ne bazance ga halinshi ba."
Baby ta gyara zama tana yamutsa fuska saboda gajiyar da hannunta ya soma yi
"Sorry."
Haris ya furta cike da kulawa,abunda bai taba yi bane. Hakan ya sanyata murmusawa shima ya mayarda martani yana mai basarwa ta hanyar shafa sumarsa.
Ta cije lebbanta na kasa mai nuni da abunda zata fada akwai ciwo(lol)
"A wannan lokacin ne,Allah Ya kawo karshen zaman Mamma da Abba,Yaya abdullah yana can wata duniya baisan abunda ke wakana ba...."
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(28)
Alokacin ina jss1,yayana ss1. Twins kuwa suna primary 4,Hindu kuma 3. Na soma hankali da fahimtar abubuwa,a fannin islamiyya ma tuni Yaya abdullah yayi haddar Al-kur'ani,sai hadisai da sauran litattafai da akeyi mishi. Nikam sauka nakeyi don ko haddar ban soma ba alokacin. Twins ne abinsu sai a hankali,don uwar tasu cikin yawon biki da suna da gaisuwar mutuwa take. Koyaushe bata fiye zama gida ba duk fitarta da yaranta take tafiya(note! Ban taba rayuwar kowa ba!). Wannan ya janyo wala wala a karatunsu na addini,malaman har korafi sukeyi don har Abba sun samu sunyi magana dashi ya nuna za'a kiyaye saidai fa bata canza zani ba.
Wataranar juma'a da yamma na dawo daga gidan Waziri inda nakai ziyara ga aminiyata Juwairiyya,misalin karfe biyar da mintuna ne,direba ya faka. Na fito ina duban wasu matasa biyu tare da Hamza anan kusa da motar Hamza suna hira da kyakyata dariya. D'aya gajere ne,bak'i saidai kalar fatar ta haskaku tamkar dai na yan gidan hutu. Bashi da wani kyau na azo a gani yayinda d'ayan kuwa ya kasance dogo yana da d'an haske. Sannan yayi kama matuka da Raliya. Bazasu wuce talatin da wani abu ba,kansu wani dan iskan aski ne na yan duniya. Gashi duk sun matse cikin kananun kaya masu wanduna iyaka gwuiwa. Na dauke kaina kamar ban gansu ba zan shige gida. Tsawar da Hamza ya dakamin ce ta rud'a tunanina,na dubeshi. Jajayen idanunsa ya shiga zaremin,yace naje. Ba musu ta isa jiki yana rawa.
"Don ubanki baki iya gaisar da mutane ba? Ko bakiga Nura da Usman bane? Kina daukarsu bare ne? Toh don ubanki sun fiki matsayi a gidan nan."
Jin abunda yace na zumburo baki,a ganina rainin hankali ne ace wani can ya fika alhalin gidan ubanka ne. Naji an kaimin hauri da k'afa a bakin. Nura ne,gajeran ciki. Ya zaromin ido
"Barta Yaya hamza,ashe har wannan lokacin wannan yar iskar yarinyar bata nutsu ba. Tun tana 'yar ficikarta take tsula tsiya a gidan nan. Toh don ubanki tunda muka dawo garin nan keda gyatumar taki zaku magantu. Tashi kibar nan!"
Ya dakamin tsawa,ai da gudu gudu nayi ciki cikin ihun kuka. A falo na zube inata bori,Kulu da Mamma suka fito suna tambayar ko lafiya? Yaya abdullah kuwa bai nan yana tare da abokansa na unguwa suna ball. Na shaida musu abunda ya faru,Mamma taja tsaki
"Allah Ya kyauta."
Daga haka tayi gaba bata ko damu da wankemin jinin dake d'iga daga bakina ba. Kulu ta kamani mukayi bandakina ta wankemin bakin tsaf sannan ta sanyani na chanja kayan kasancewar sun b'aci da jini.
Result din Nura da Usman ba wani kyau sukayi ba,tun dawowarsu ma banda yawo da suka sanya a gaba basu da wani aiki. Ga yan mata da suke yiwa b'arin naira. Bayan bautar kasarsu Raliya ta sanya Abba ya nema musu aikin yi saidai babu wanda akayi dacen samarwa. A karshe tace ya basu jari. Nan ya basu kudade da yawa don suyi sana'a koda kasuwanci ne. Saidai ba wanda ya yunk'ura,karshe ma mota suka saya kowanne da tasa. Rayuwarsu ta baya sai abunda ya k'aru,neman mata kamar me don hatta da shaye shaye sukan d'an tab'a. Mamma tasha gargad'ina akan kar na kuskura koda wasa na dunga shiga sashensu. Baruwana dasu, naji gargadinta sosai duk da inajin haushinsu. A duniya babu wadanda na tsana bayan Abba sai su. Tsakanin Mamma da Abba kuwa,har ta manta rabon da Abba ya zauna sukayi hirarsu cikin nishadi har ma ya nemi shawararta akan wani aiki nasa, ko kuma ya sanar da ita abunda yake niyyar yi ko kuma yayi. Zuwa lokacin ma Mamma bata damuwa,idan da sabo yaci ace ta saba domin kuwa abun gaba yakeyi. Na takaice maka saida ya zamana Abba ko girkin Mamma bayaci,sam Mamma bata da kwana a gidan. Kiyayyarsa gareta tamkar an k'ara ne. Domin hana kawo abinci sashensa yayi,yace tayi zamanta a nata sashen idan yana da bukata ai yasan inda take amma anan ita ya lura bata da aiki sai korafi akan abunda baikai ya kawo ba. Tun ina zuwa sashen Abba da kaina duk da kwab'ar Mamma har nazo na daina domin ko kallo ban isheshi ba. Zafi ya hadewa Mamma,gashi ita ba suruka ba balle takai k'ara don tun Abba yan karami mahaifiyarsa ta rasu. Shi kadai ne a wajen mahaifiyarsa,a hannun mahaifiyar Alhaji Nasir,uwargida a wajen marigayi Waziri Ma'aruf wato mahaifinsu Abba,ya tashi. Itace komai nasa kafin itama ciwon sugar yayi ajalinta. Mahaifiyar Gwaggo sarai ita kadaice tsohuwar data rage a matan Waziri,sai yaransa su goma sha biyar cif. 'Ya'ya goman duk na uwargidan ne,sai Abba cikon na sha daya sannan ya yan amaryar waziri,uwar Gwaggo sarai,itace mai yara hudu.
Kwarai dukkansu matan sun watsar da Mamma,hatta da Gwaggo Sarai mai kawo mata tsegumin auren da Abba zaiyi a farko. Matar Waziri mai ci a yanzu,Alhaji Nasir,Hajiya Hajara. Itace suke mutunci sosai da Mamma don shekarunta bai wuce na Mamma ba. Itace kuma k'arama ta uku a matansa. Ita ta kasance mahaifiyar Juwairiyya.
Wannan kenan!!!
Mamma ta rame ta rasa meke mata dadi,Abdullah shine mai rarrashinta. Akwai sadda naji yana bata shawarar kodai zataje Kazaure ta sanarwa Malam? Don lokacin bai zama limamin juma'a ba,marigayi Malam Abubakar ne Limamin. Mamma tak'i. Yaya abdullah shine abokin shawararta wasu lokutan yanda ta suka shak'u ko ni da nake mace ba muyi wannan shak'uwar ba.
Rayuwa na tafiya da dadi babu dadi. Saida muka samu hutun watanni uku na makarantar boko,ina shirin shiga jss2 Yaya abdullah kuwa zai shiga Ss2,mukaje Kazaure ziyaran kakannina. Yan uwan mamma babu wanda bai firgita da ganin yanda ta koma ba. Sukayita tambaya tana cewa babu komai. Har Malam ma haka ta fada mishi. A karshe ta sanyamu a d'aki ni da abdullah ta k'ara kwab'armu akan kada mu sake mu gayamusu halin da take ciki. Ai kuwa bayan ta fita ziyarar yar uwarta. Naje na samu Malam,ina kuka na zayyane mishi komai na yanda Mamma ke rayuwa a gidan nan don har yan aikin Raliya sun fita muhimmanci a wajen Abba. Ga rashin kunya da yaran Raliya sukeyi mata,babu mai ganin girmanta musamman ma manyan. Malam ya fusata ainun,yace nabar kukan bari ta dawo. Ai kuwa Mamma tana dawowa nabar gidan da zummar lekawa gidan kanwar Mamma,Gwaggo Nusaiba......
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(30)
"Maganar da nakeyi maka har ila yau,bansan takamaiman silar rabuwar iyayena. Abunda zan iya tunawa shine. Adaidai wannan lokacin da sakin ke daf da faruwa,Mamma ta shiga wani irin yanayi na yawan tunani da kuka. Nasha kamata a daki tana kuka,tambayar duniya nayi mata tak'i sanar dani. Ga Abba ma bai shiga sha'aninta,na fahimci ran girkinta saidai tayi mishi abinci takai ta juyo bata zuwa inda yake. Ta rame gaba daya, zuwa lokacin nayi hankali nasan menene ya kamata hakan yasa ban sanarwa Yaya abdullah ba duk kuwa da cewa muna yawan chatting dashi yayita bani labarin wata budurwarsa da yake fatan aurarta,Hidaya. Itama 'yar Kano ce karatu ya kaita London. Na gaji da ganin halin da Mamma ke ciki wannan yasa na tambayi kulu ko tana da masaniya saidai ta tabbatar min babu abunda Mamma ta gayamata,itama ta tambayeta amma ta nuna mata bakomai.