← Book details African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals Local reading mode
READING PART 20 OF 35

Sashe 20

African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals · about 8 min read

Kulu taji abun banbarakwai,koda ta nemi dalili. Ya sanar mata Abba ya baya gari shine matsi da wahalarwa suka sanyani nayi kokarin guduwa shine ya yanke gwara ya kawoni gabanta na zauna. Jin abunda yace yasa na kalleshi kwalla ta cikamin ido,yayimin alamar cewar kada nace komai sai kawai na sunkuyar da kaina har mamakin yanda Yaya abdullah ke son kare laifin Abba nakeyi. Wane irin zuciya ce dashi har haka? Kulu ta hakikance sanin halin Raliya zata aikata abunda yafi haka acewarta,irin hakan ke sa yaro ya shiga duniya.

Yayi mana sallama bayan ya tabbatar min zai sanya mai adaidaita sahun nan ya kawomin kayana banko kalleshi ba ya lura fushi nakeyi dashi. Bai kulani ba yayi gaba,wajejan yamma sai ga mai adaidaitan ya kawo jakar kayana,ciki kuwa koda na bude na samu dubu goma a samansa. Damkasu nayi gaba daya ga Kulu.

Muna hira take shaidamin cewar da matar d'anta suke zaune da yaransu amma yanzu sunje ganin gida acan Ringim. Na nuna mata babu matsala zan iya zama. Na lura a zamanmu tana son takura kanta akan lallai sai tayimin cima mai dadi. Saida na nuna mata banaso zan iya irin rayuwarta sannan ta hakura.
Satinmu biyu tare,Salamatu da yaranta uku da mijinta suka dawo. Sunyi mamakin ganin bakuwar fuska,saida Kulu ta fahimtar da d'anta Salmanu ko ni wacece tukunna. Nan da nan kuma naga fuskar Salamatu ta chanja har ta kasa boyewa tace wai Baba ta fiye yi musu kwashe kwashe alhalin daman da yaya suke rayuwar? Kulu dai jiki yayi sanyi don ba ranar ta soma ganin rashin arziki wajen Salamatu ba hakanan d'anta kansa yana shayin matar tasa. Nidai bance musu uffan ba.

Rayuwata tana cigaba da tafiya a wajen kulu da dadi babu dadi,Yaya abdullah baya wuce sati baizo ba kafin kuma ya dauke kafa yaje Kazaure. Nan ma daya dawo ya tahomin da tsarabe tsarabe duk daga yan uwa. Banyi wani murna ba tunda dai da nayi mishi korafin tafiya dani ya nunamin kamar bayason kaini a yanzu,na lura kyamata kawai yakeyi.

Watana uku a gidan,lokacin cikin hukuncin Allah takardun Yaya abdullah sun kammalu har ma da taimakon abokinsa Rilwan ta samu aiki a wani kamfanin mahaifin Rilwan na Abuja,suka bashi karamin gida da motar kamfaninsu. Koda ya dawo ya sanarmin nayi mishi murna saidai lokacin bani da cikakkiyar lafiya. Kullum cikin zazzabi nake ga kasalar jiki. Ya kwasheni ni kadai a mashin dinsa mukaje asibiti. Koda mukaje likita ta nemi fitsarina,a tsorace na mike naje nayi na mika lab. Muna nan zaune jiki a sanyaye har aka kammala aka bamu result muka kai ga likita. Ta dago tana murmushi

"Congrats, you are pregnant."

Ihu na fasa na zube a wajen ban kara sanin meke wakana ba saidai na farka na ganni kwance a gado. Likita na tattaba goshina,tunawa da nayi da abunda naji a karshe yasa na kara sakin ihu ina fadin "Wallahi saikin zubarmin! Banaso!! Wallahi ..."

Yaya abdullah ya toshemin baki yana kuka

"Kin ja mana Tasleem! Baki kyauta mana ba."

Likita dai sannu take bina dashi.

Bayan mun fito Yaya abdullah yace bazai iya barina kuma a hannun kulu ba,dole dani zai koma Abuja ba yanda zai iya. Nidai babu bakin magana illa bakin cikin dake nukurkusata ya zamana daidai da shi kansa haushinsa nakeji. Naji duniyar na tsani kowa da komai. Mahaifiyata kadai ta fadomin a raina,kawai sai na fashe da kukan tausayawa rayuwata. Ya zataji idan tasan abunda ya sameni?

Haka dai muka koma mukayi sallama da kulu bayan Yaya ya cikata da kudi yayi mata godiya. Ita kanta salamatu saida ya bata,ba kunya ta karba da rawar jiki.

A karshe muka koma ya ajiye mashin din daya aro na makocinmu kuma abokinsa sannan ya tsayar mana da adaidaita sai tasha domin tuni daman kayansa suna tashar a hannun wani amintaccensa.

*****
Baby ta tsagaita hadi da jan majina,fuskarta tayi jazur tamkar kosai kamar yanda fuska da fararen kwayar idanun Haris suka sauya launi zuwa ja.
Zuwa lokacin shi kanshi hawayen yake fitarwa. Ta cigaba

"Haris wannan shine silar zamana a Abuja na shekara daya da watanni a gidan Yayana da matarsa Hasinat."
'YAR BARIKI

©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)

(38)

Watanmu shida cif a garin Abuja,babu yanda na iya cikina ya girma ya fito so sai. Akan bakin cikin ganinsa ya sanya Yaya abdullah kauracewa yini a gidan,kasancewar estate ne wajen akwai mutane da dama saidai ba wanda ke shiga harkar wani sosai. Kullum rufe nake da hijabi zunb'ulele saboda nauyin da nakeji musamman ma na yayana. Shima baya yini a gidan. Wataranar laraba ne na tashi da matsanancin ciwon mara da baya. Lokacin kuwa karfe uku na rana ga Yaya abdullah bai dawo gidan ba. Sai murkususu nakeyi a tsakar falon ina salati a zuci don bakin nawa ma mutuwa yayi murus. Na rasa yanda zanyi,cikin ikon Allah sai ga Yaya abdullah bayan nakai tsawon awa daya ina abu daya. Jaka da ledar dake a hannunsa ya yasar ya nufoni a guje.
"Lafiya tasleem? Haihuwar ce?"

Na gyada kai ina runtse ido don babu baki, ya fita a guje ya bude motarsa sannan yazo ya daukeni ya sanyani ciki. Har ya bude motar zai shiga ya dubeni a rikice "Kin hada kayan dana kawo na baby kuwa?"

Ban iya magana ba,ya fita da sauri saidai yayi mamakin ganin yanda ya kawomin haka suke a ledar ban fidda komai ba. Ya kinkimo ledar karshe da ya rasa abunyi ya kinkimo harda akwatin kayana kasancewar nak'i jerasu a kwaba don komai ba burgeni yakeyi ba a lokacin. Haka muka isa asibiti,nidai ina motar nan tunda wani azababben ciwo ya murdomin na saki k'ara na sume bansan me ya wakana ba. Bayan farkawata kuwa na ganni kwance a gado wai ashe aiki akayimin aka fiddo jaririn. Saidai kuma baizo da rai ba. Bansan sadda nayi hamdala ba sa'ilin da nos ta shaidamin hakan,ta taimaka ta gyarani tsaf sannan aka chanja min daki. Mintuna kalilan ina nan kwance ina hawayen farin ciki,Yaya abdullah ya shigo da wani wanda kallo daya nayi mishi na fahimci cewa Rilwan ne. Na kauda kaina daga dubansu. Yaya abdullah ya riko hannuna yana murmushi "Sannu kanwata,ya jikin?"

Murmushi kawai nayi mishi,kafin shima Rilwan ya matso yana min sannu. Na amsa a nutse, sallamar wata matashiyar budurwa ce ta katsemu. Ta shigo dauke da kwando,a bayanta kuma wani saurayi ne ya tsuke cikin kananun kaya askin kanshi kadai sun wadatar su nunawa mutum irin matasan nan ne masu wankan kwalabo. Suka karaso ciki,nayi yunkurin mikewa da azama naga budurwar ta ajiye kwandon ta iso wajena.

"Sorry." Ta fada cikin muryarta na gogaggun yan boko. Ta jinginamin filo na kwantar da bayana akai. A hankali na gaishesu suka amsa min.

"Amaryarmu,da alama garin na Abuja yayi maki dadi shiyasa daga sati gashi kin kusa yin wata."

Cewar rilwan ya fada yana duban matashiyar nan wacce tuni na daina tunanin inda nasan fuskarta saboda na fahimci itace dai Hasinar Yaya abdullah. Saidai wanda suke tare dinne mai shegen kallo,ban sani ba. Dariyar Hasina ta katsemin tunani

"Wai kai ina ruwanka ne? Baka ganin Abdul dina yana jinyar kanwarmu,haka kake so na tafi na barshi duk su wahala? Ayya na manta ma,ban maki gaisuwa ba sister,ya hakurin rashin bebinmu? Allah Yaji kansa."

Nayi mamakin yanda Yaya abdullah bai boye musu cewar haihuwa nayi ba,sai duk na tsargu na dauka ya gama sanar dasu dukkan abunda ya shafi rayuwata.

"HAYAT kaji kanwar taka ko? Ya kamata ka dunga taka mata burgi irin wannan love haka?" Rilwan ne ya fada ganin ban amsa zancen Hasina ba. Yaya abdullah dai murmushi kawai yakeyi,ta dubesu

"Don Allah ku fita kuna matsawa kanwata da hayaniya gashi ko abinci bata ci."

Haka suna dariya suka fice, ni kuwa Allah Allah nakeyi su fita saboda bayan tsarguwa da nayi harma da kauracewa mayen kallon da Hayat ke watsomin wanda yana daga cikin abunda na tsana.

Hasinat ta hadamin tea ta zubamin chickensoup da suka taho dashi haka ta taimaka ta dunga bani da zafi zafi babu laifi naci sosai.

A karshe dai bayan su Yaya sun shigo akayita hira da dariya,nikam kallonsu kawai nakeyi,anan na fahimci cewar an kusa sanya ranar auren Yaya da hasina. Babu laifi na lura tana da mutunci,kamar bazatayi hayaniya ba. Allah Allah nakeyi su fita na tambayi Yaya abdullah abunda ya sanarwa Hasina a kaina. Saidai fa koda suka tafi na tambayeshi,nayi bakin cikin jin cewar ya sanar da ita wai nayi aurena mijina ya rasu ya barni da ciki yanzu ma na haihu d'an babu rai. Koda nayi tunani daga baya na fahimci rufamin asiri yayi.

Bayan wata daya da yin hakan,Yaya abdullah yayimin batun komawa makaranta,naji dadi kwarai saidai na nuna mishi ya bari ya kammala hada lefansa tunda a kansa yake. Yayi naam da batuna. Kullum muna waya da Mamma da mutan Kazaure kowannensu na lura a zatonsu ina kano ne basu san cewar ina tare da yayana ba. Gaba daya suna da labarin lefan da Yaya abdullah ke hadawa. Bayan ya kammala ya zaunar dani yace zaije dashi ya kaiwa Raliya ko ba komai tana ganin kimarsa yanzu da yayi kudi amma hakan ba damuwarsa bace shi dai su mika lefansa gidansu Hasinat. Baki kawai na tab'e bance uffan ba. Idan ma ba don Allah take jan yayana a jiki ba ita ya shafa yanzu kam na fidda kaina da lamuran gidansu Yaya Abdullah don ya tashi daga gidanmu.

Ranar da aka kai lefa da kayan saka rana ya shaidamin nan da wata uku za'ayi bikinsa. Na tayashi murna. Saidai sabon al'amarin da yake niyyar bullowa cikin rayuwata ya dagamin hankali,banason wata soyayya,asalima ba burgeni takeyi ba alokacin. Amma hakanan Yaya Rilwan ya shiga cusa kansa gareni,tun ina ja baya har dai Yaya abdullah yace kada na damu ya amince da rilwan amininsa ne kada na wulakantashi a hankali sai a rabu. Wannan yasa na sakarwa Yaya rilwan harma nake sauraronsa. Alokacin kuma yayana ya hau gyaran gida bayan ya soma kokarin nemamin admission.

Bayan sati uku aka samar min,na soma zuwa nan jami'ar Abuja inda na soma karatuna a fannin shari'ah.

BAYAN WATANNI HUDU
Chapter 20 · 0% Book details