Sashe 25
African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals · about 8 min read
"Ni yayarki ce, kina sona?"
Humaira tana dariya tace "Eh."
Ta kara rungumeta tana kokarin danne hawayenta,burinta gari ya waye taje ga mahaifiyarta.
Daren bata iya bacci ba,sai kuka da taci k'asa k'asa tunanowa da gurb'atacciyar rayuwar datayi a baya, gashi tana kunyar yan uwanta su samu labarin. Batasan yayanta yana mugun sonta ba sai a lokacin,tunda har ya iya sanyawa 'yarsa sunanta ayanzu kam bata da burin daya wuce ta sanya yarinyar a idonta. Har zuwa lokacin bata da niyyar bud'e wayarta domin batason amsa wayar mutanenta agaban mutan gidan.
******
Baffa ya dubeshi ya ajiye littafin karatunsa
"Lafiyarka kuwa Harisu?"
Harisu ya zauna kansa a kasa
"NA SAMU MATAR AURE BAFFA.....!"
"Alhamdulillah! Wacece?"
Ya gyara zama har lokacin ransa a matukar b'ace yake.....
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(47)
Yayi kokari sosai wajen danne mugun tsanarta dake taso mishi aduk sadda ya tuna cewar ita ke haddasa rashin zaman lafiya a gidan kanwarsa.
"TASLEEM."
Ya karashe cikin d'acin zuciya,yayinda idanunsa suka kara kad'awa.
Ji yayi Baffan ya rungumoshi cikin matsanancin farin ciki wanda sanin amintar bayin Allahn a yanzu yasa ko kusa baiyi wani mamaki ba yanzun.
"Allah Ya albarkaceka a gaba daya rayuwarka Harisu,kamar kasan addu'ar dana gama yi kenan akan Allah Yasa kace kanason jikar aminina. Allah Yayi ni Husseini ban mutu ba zanga aure ya kullu tsakanin zuri'ata dana Abdulmalik? Allah na gode maKa daka amsamin addu'ata nan take. Saidai kuma harisu bazan baka auren jikata ba har sai ta amince zata aureka don haka ka tashi ka tafi zuwa gobe sai na tuntub'eta. Allah Ya tashemu lafiya."
Haris ya mike jiki babu kwari ya fice zuwa d'akin da aka tanadar masa. Kwanciya yayi akan makekan katifar sakamakon kansa da yaji yana sarawa. Anya bai kwari kansa ba kuwa?!! No! Bazai yiwu kuma yabar rayuwar Yasmeem cikin garari ba. Tabbas rayuwarta da farin cikinta sun dogara ne da Kb,burinta a duniya bai wuce Kb ba. A yau aka wayi gari Kb ya auri Tasleem,wulakanci da bakin ciki sune abunda zai biyo bayan auren ga Yasmeen. Shikam ya gwammace yayi wannan jihadin,alhalin ma a yanzu koda kud'i yana da yak'inin Baby bazata k'ara waiwayar karuwanci ba. Yana jin tsanarta a wani sashen zuciyarsa yayinda wani sashen kuma yakejin sassauci game da ita. Ya rantse sai ya rabata da Kb hanyar data dace,kb bai isa ya nemeta ba idan ta zama matarsa. Bai isa koda wasa ma ya tunkareta ba,ba wai don kishinta yakeyi ba(a fad'arsa kenan!!),sai don samawa kanwarsa 'yanci da kuma farin cikin gidan aure. Wanda bazai tabbata ba sai yayi nasarar raba wad'annan shaid'anun biyu..!
*****
Da sassafe ya kammala komai ko karyawa baiyi ba ya fito da shirinsa na komawa garin Kano domin bashi da bukatar k'ara yin tozali da Baby hakazalika hankalinsa ya tafi gaba d'aya ga kanwartasa.
Ya shiga ya samu Baffansa yana lazumi,ganinsa cikin shiri yasa Baffa watso mishi tambaya
"Harisu tafiyar ce?"
Haris ya danyi murmushi kai da ganin idanunsa kasan bai samu wadataccen bacci ba
"Tafiyarce Baffa,akwai ayyuka masu yawa da zanyi a yau in sha Allah."
"Toh madallah,game da zancen da kazo dashi kuma fa?"
Yaji ransa ya b'aci tunawa da batun aurensa da Baby wanda ya k'ak'abawa kansa,
"Baffa na baku nan da karshen sati,duk abunda kuka yanke in sha Allah zan dawo sai naji."
Ya jinjina kansa
"Ai shikenan,lallai kuma ka gayawa iyayenka maza ina bukatar ganinsu idan zaku dawo ku dawo tare. Allah Ya tsare hanya. Ka shiga kuyi sallama da aminin nawa ko?"
"Amin." Daga haka Haris ya fice batare da yayi na'am da zancen baffa na karshe ba,bayan ya yiwa mutan gidan sallama ya fita,yan matan da bai zab'a ba kenan!
Yana sane ya share batun zuwa gidan liman,ya tayar da motarsa wacce tun jiya da yamma yasa aka wanke mishi tayi k'al. Ya zauna kenan yana kokarin daura seat belt ya hango wata sark'a a k'asan mazaunin kusa da direba. Hannu yasa ya dauka,ba shakka sark'a ce da baby ke ado da ita a k'afarta. Zuciyarsa ta d'an sosu,ji yayi kuma yana kewar rashin abokiyar hira a kusa dashi. Saidai tunawa da yayi da kanwarsa da halin da take ciki yasa yayi azamar ajiye sark'ar a saman kujera ya kunna karatun kur'ani mai girma yayi ribas ya d'auki hanya...sai Kanon Dabo.....!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(49)
"Ya akayi Kabir?"
Ya lumshe ido ya sauke ajiyar zuciya cikin jin dadin muryar daya jima yana kewarta.
"Idan da abunda yafi tashin hankali da matsanancin damuwa tsanani,toh kin sanyani a ciki Babyna. Nayi mugun kewarki har na zama tamkar zararre wanda hakan ke nema ta shafi mu'amalata da kowa da kuma aikina. Where have you been for so long? Kinsan irin halin da na shiga?"
Ta numfasa cike da takaicinsa,ita kam yanzu haushi ma yake bata,ta dan ja karamin tsaki
"Banson takura ne Kabir,na d'anyi tafiya bana zaton dawowata nan kusa ma."
"What?!!"
Ya fad'a da k'arfi yana mikewa zaune daga kishingid'ar da yayi a daya daga cikin kujerun na babban airport dake birnin tarayyar Abuja,alokacin yana shirin zuwa Kano ne domin amsa kiran iyayensa duk akan matar da sai daga baya ya gane rashin kyautatawarsa gareta. Yayi kokarin saita kansa ganin yanda mutanen wajen suka zubomishi ido gaba daya. Cikin tattausar murya yace
"Meyasa kikeson tayarmin da hankali babyna? Jikina ya bani kina tare da wani shegen shiyasa kika chanjamin. Wai me yake baki? Me kuma yake maki da bana iya kokarina wajen yi maki?"
Hawaye suka surnano daga idanuwan Baby,ba wai na wani abu bane sai jin tsanar kanta da kanta. Wai har itace yau ake gayawa haka? Karuwa ta gaske ake daukarta. A fusace tace
"Nabar wannan rayuwar kabir! Bana tunanin daga yau zaka kara ganina ballantana akai ga kaji muryata! Bakai ba,kowanene nabarshi har abada na gane wannan rayuwar ba rayuwa ce..."
Dariyar daya sanya kamar wani zautacce yasa Baby tsayawa cak, hakazalika mutanen dake zaune tare dashi suka zubamishi ido domin zuwa lokacin baiko damu dasu ba.
"Karya kikeyi?! You can never live without me baby! Ke d'in tawa ce, baki isa kiyimin YANKAR KAUNA ba! Dani dake babu mai rabamu,kuma ki sani, ina nan ina jiranki. Ki ajiye a ranki baki da miji sai ni! Saina aureki kota halin k'ak'a sai na cigaba da gabatar da rayuwa dake!"
Ta katse wayar gaba daya a fusace ta fiddo sim ta tauneshi ta furzar. Kawai sai ta durkushe ta fashe da kuka.
"Adda menene?"
Maganar Humaira ya ankarar da ita a inda suke, ta share hawayenta ta mike tana kokarun kakalo murmurshi
"Bakomai kanwata,muje."
Tafiya takeyi saidai komai na kalaman kabir yana dawo mata,taji ta tsani kanta. Inama za'a maido hannun agogo baya,inama inama zai zamana wannan kaddarar zata shafe a tarihin rayuwarta. Kai inama ace Abbanta bai auri Raliya ba har ma hakan yayi sanadin fad'awarsu ha'ula'i. Haka tayi ta tunane tunane jikinta babu laka har suka iso gidan auren Mamma. Baki ta saki ganin makeken gidan wanda bata taba zaton anan Kazaure za'a samu gida mai kyawun fasali kamar na turawa ba. Humaira ta katseta tana jan hannunta
"Nan ne gidan fa Adda."
Wata yarinya suka soma cin karo da ita tasha d'amara,ta cika eyeshadow a saman idonta,ga kuma jan baki data maka. Lukuta ce ta gaske,tana tsallenta kamar ba budurwa ba tana b'alla rake. Ganinsu yasa tayi d'if tana bazo ido. Kafin ta washe baki ganin Humaira
":Yar Humeme,wacece wannan kamar baturiya?"
Baby murmushi kawai takeyi ganin yarinyar,kamar dai tana da matsalar yarinta amma irin wannan kwalliyar ai an bar yayinsu.
"Addana ce, daga birni."
Yarinyar ta cuno baki. Wani saurayi mai shekaru sha takwas ya iso wajensu yace
"Kedai kam Safiya bazaki bar shiririta ba,inace anti tace ki tafi gidanku kibar fitowa idan kaka tana bacci? Wannan yar birni ce,kinga ma yanda ake kwalliya ba irin naki ba."
Ya karashe suna dariya har baby wacce abun ya bata dariya,wacce aka kira da Safiya ta murguda baki ta k'ara b'antalar rake
"Oho dai,Ali nuhu ma kansa yace mata suna kauye."
"Yauwa d'an k'arasa mana."
Ta harareshi tayi gaba tana tsalle tsallenta tace
"Akwai wanka."
Ta fice, saurayin ya dubi baby sukayi dariya. Ya dan russuna ya gaisheta gami da tambayar wanda take nema. Kafin ta bashi amsa humaira ta cafe
"Yaya Nura,addana ce ta Kano."
Ya kalli humaira ya kalleta,tabbaa yaga kama ya kara washe baki
"Yaya tasleem,right?"
Ta lumshe ido hadi da jinjina mishi kai lokaci daya. Ai sai ya sheka da gudu
"Kai ka kai,amma yau ni zan soma kaiwa antinmu albishir."
Jin haka Humaira ma tabi bayansa a guje. Dariya baby tayi ta mara musu baya tana mai zumudin yin tozali da mahaifiyarta....
******
Haris cike da mamaki ya dubi Yasmeen bayan sun keb'e a farfajiyar gidan inda tayo mishi rakiya zai koma ofis lokacin karfe ukun rana.
"Ashe kina da hankali har haka little? Kwarai banyi tsammanin zaki iya b'oyewa iyayenmu ainahin abunda ya had'aku da KB ba."
Yasmeen tayi murmushi mai ciwo
"Bari kawai yayana,wallahi inason Yaya kabir kai kanka shaida ne. Gani nayi a yanda kawai Daddy ya dauki zafi jin cewar yace na dawo ba tare da wani dalili ba(kamar yanda ta fad'a musu kenan don kare mijinta),kar kaso kaga yanda ya fusata sai faman bud'e wuta yakeyi. Ya kake tunanin idan sunji har marina yayi akan karuwarsa? Ba yanda za'ayi nayi gangancin da za'a rabani dashi. Kaima ina rok'onka don Allah kada ka nunamishi kasan zancen."
Ya kara tsintar kansa da kauna da matsanancin tausayin kanwar tasa, shi kuwa ya za'ayi yayi gangancin barin Tasleem ta ruguza farincikinta? Bazai yiwu ba. Ya numfasa
"Baki da matsala dani little,saidai ina rok'onki da ki rage son d'a namiji har haka kada ya zame maki babbar matsala fiye da yanzu. Ki cigaba da addu'a Allah Yayi mana magani. Bari na tafi, Abba yana jirana."
Ta tareshi
"Af,baka sanarmin wacce ka zab'o mana matsayin antin tawa ba? Kodai zatona ya zama gaskiya,Zahra ce?"
Yayi murmushin dole
"No.. Baki canka ba."
Ta dan nuna damuwarta,ganin ta bude baki zata k'ara magana ya bude motarsa ya fad'a
"Ke kyaleni kinji ko? Sai mun dawo da yamma."
Humaira tana dariya tace "Eh."
Ta kara rungumeta tana kokarin danne hawayenta,burinta gari ya waye taje ga mahaifiyarta.
Daren bata iya bacci ba,sai kuka da taci k'asa k'asa tunanowa da gurb'atacciyar rayuwar datayi a baya, gashi tana kunyar yan uwanta su samu labarin. Batasan yayanta yana mugun sonta ba sai a lokacin,tunda har ya iya sanyawa 'yarsa sunanta ayanzu kam bata da burin daya wuce ta sanya yarinyar a idonta. Har zuwa lokacin bata da niyyar bud'e wayarta domin batason amsa wayar mutanenta agaban mutan gidan.
******
Baffa ya dubeshi ya ajiye littafin karatunsa
"Lafiyarka kuwa Harisu?"
Harisu ya zauna kansa a kasa
"NA SAMU MATAR AURE BAFFA.....!"
"Alhamdulillah! Wacece?"
Ya gyara zama har lokacin ransa a matukar b'ace yake.....
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(47)
Yayi kokari sosai wajen danne mugun tsanarta dake taso mishi aduk sadda ya tuna cewar ita ke haddasa rashin zaman lafiya a gidan kanwarsa.
"TASLEEM."
Ya karashe cikin d'acin zuciya,yayinda idanunsa suka kara kad'awa.
Ji yayi Baffan ya rungumoshi cikin matsanancin farin ciki wanda sanin amintar bayin Allahn a yanzu yasa ko kusa baiyi wani mamaki ba yanzun.
"Allah Ya albarkaceka a gaba daya rayuwarka Harisu,kamar kasan addu'ar dana gama yi kenan akan Allah Yasa kace kanason jikar aminina. Allah Yayi ni Husseini ban mutu ba zanga aure ya kullu tsakanin zuri'ata dana Abdulmalik? Allah na gode maKa daka amsamin addu'ata nan take. Saidai kuma harisu bazan baka auren jikata ba har sai ta amince zata aureka don haka ka tashi ka tafi zuwa gobe sai na tuntub'eta. Allah Ya tashemu lafiya."
Haris ya mike jiki babu kwari ya fice zuwa d'akin da aka tanadar masa. Kwanciya yayi akan makekan katifar sakamakon kansa da yaji yana sarawa. Anya bai kwari kansa ba kuwa?!! No! Bazai yiwu kuma yabar rayuwar Yasmeem cikin garari ba. Tabbas rayuwarta da farin cikinta sun dogara ne da Kb,burinta a duniya bai wuce Kb ba. A yau aka wayi gari Kb ya auri Tasleem,wulakanci da bakin ciki sune abunda zai biyo bayan auren ga Yasmeen. Shikam ya gwammace yayi wannan jihadin,alhalin ma a yanzu koda kud'i yana da yak'inin Baby bazata k'ara waiwayar karuwanci ba. Yana jin tsanarta a wani sashen zuciyarsa yayinda wani sashen kuma yakejin sassauci game da ita. Ya rantse sai ya rabata da Kb hanyar data dace,kb bai isa ya nemeta ba idan ta zama matarsa. Bai isa koda wasa ma ya tunkareta ba,ba wai don kishinta yakeyi ba(a fad'arsa kenan!!),sai don samawa kanwarsa 'yanci da kuma farin cikin gidan aure. Wanda bazai tabbata ba sai yayi nasarar raba wad'annan shaid'anun biyu..!
*****
Da sassafe ya kammala komai ko karyawa baiyi ba ya fito da shirinsa na komawa garin Kano domin bashi da bukatar k'ara yin tozali da Baby hakazalika hankalinsa ya tafi gaba d'aya ga kanwartasa.
Ya shiga ya samu Baffansa yana lazumi,ganinsa cikin shiri yasa Baffa watso mishi tambaya
"Harisu tafiyar ce?"
Haris ya danyi murmushi kai da ganin idanunsa kasan bai samu wadataccen bacci ba
"Tafiyarce Baffa,akwai ayyuka masu yawa da zanyi a yau in sha Allah."
"Toh madallah,game da zancen da kazo dashi kuma fa?"
Yaji ransa ya b'aci tunawa da batun aurensa da Baby wanda ya k'ak'abawa kansa,
"Baffa na baku nan da karshen sati,duk abunda kuka yanke in sha Allah zan dawo sai naji."
Ya jinjina kansa
"Ai shikenan,lallai kuma ka gayawa iyayenka maza ina bukatar ganinsu idan zaku dawo ku dawo tare. Allah Ya tsare hanya. Ka shiga kuyi sallama da aminin nawa ko?"
"Amin." Daga haka Haris ya fice batare da yayi na'am da zancen baffa na karshe ba,bayan ya yiwa mutan gidan sallama ya fita,yan matan da bai zab'a ba kenan!
Yana sane ya share batun zuwa gidan liman,ya tayar da motarsa wacce tun jiya da yamma yasa aka wanke mishi tayi k'al. Ya zauna kenan yana kokarin daura seat belt ya hango wata sark'a a k'asan mazaunin kusa da direba. Hannu yasa ya dauka,ba shakka sark'a ce da baby ke ado da ita a k'afarta. Zuciyarsa ta d'an sosu,ji yayi kuma yana kewar rashin abokiyar hira a kusa dashi. Saidai tunawa da yayi da kanwarsa da halin da take ciki yasa yayi azamar ajiye sark'ar a saman kujera ya kunna karatun kur'ani mai girma yayi ribas ya d'auki hanya...sai Kanon Dabo.....!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(49)
"Ya akayi Kabir?"
Ya lumshe ido ya sauke ajiyar zuciya cikin jin dadin muryar daya jima yana kewarta.
"Idan da abunda yafi tashin hankali da matsanancin damuwa tsanani,toh kin sanyani a ciki Babyna. Nayi mugun kewarki har na zama tamkar zararre wanda hakan ke nema ta shafi mu'amalata da kowa da kuma aikina. Where have you been for so long? Kinsan irin halin da na shiga?"
Ta numfasa cike da takaicinsa,ita kam yanzu haushi ma yake bata,ta dan ja karamin tsaki
"Banson takura ne Kabir,na d'anyi tafiya bana zaton dawowata nan kusa ma."
"What?!!"
Ya fad'a da k'arfi yana mikewa zaune daga kishingid'ar da yayi a daya daga cikin kujerun na babban airport dake birnin tarayyar Abuja,alokacin yana shirin zuwa Kano ne domin amsa kiran iyayensa duk akan matar da sai daga baya ya gane rashin kyautatawarsa gareta. Yayi kokarin saita kansa ganin yanda mutanen wajen suka zubomishi ido gaba daya. Cikin tattausar murya yace
"Meyasa kikeson tayarmin da hankali babyna? Jikina ya bani kina tare da wani shegen shiyasa kika chanjamin. Wai me yake baki? Me kuma yake maki da bana iya kokarina wajen yi maki?"
Hawaye suka surnano daga idanuwan Baby,ba wai na wani abu bane sai jin tsanar kanta da kanta. Wai har itace yau ake gayawa haka? Karuwa ta gaske ake daukarta. A fusace tace
"Nabar wannan rayuwar kabir! Bana tunanin daga yau zaka kara ganina ballantana akai ga kaji muryata! Bakai ba,kowanene nabarshi har abada na gane wannan rayuwar ba rayuwa ce..."
Dariyar daya sanya kamar wani zautacce yasa Baby tsayawa cak, hakazalika mutanen dake zaune tare dashi suka zubamishi ido domin zuwa lokacin baiko damu dasu ba.
"Karya kikeyi?! You can never live without me baby! Ke d'in tawa ce, baki isa kiyimin YANKAR KAUNA ba! Dani dake babu mai rabamu,kuma ki sani, ina nan ina jiranki. Ki ajiye a ranki baki da miji sai ni! Saina aureki kota halin k'ak'a sai na cigaba da gabatar da rayuwa dake!"
Ta katse wayar gaba daya a fusace ta fiddo sim ta tauneshi ta furzar. Kawai sai ta durkushe ta fashe da kuka.
"Adda menene?"
Maganar Humaira ya ankarar da ita a inda suke, ta share hawayenta ta mike tana kokarun kakalo murmurshi
"Bakomai kanwata,muje."
Tafiya takeyi saidai komai na kalaman kabir yana dawo mata,taji ta tsani kanta. Inama za'a maido hannun agogo baya,inama inama zai zamana wannan kaddarar zata shafe a tarihin rayuwarta. Kai inama ace Abbanta bai auri Raliya ba har ma hakan yayi sanadin fad'awarsu ha'ula'i. Haka tayi ta tunane tunane jikinta babu laka har suka iso gidan auren Mamma. Baki ta saki ganin makeken gidan wanda bata taba zaton anan Kazaure za'a samu gida mai kyawun fasali kamar na turawa ba. Humaira ta katseta tana jan hannunta
"Nan ne gidan fa Adda."
Wata yarinya suka soma cin karo da ita tasha d'amara,ta cika eyeshadow a saman idonta,ga kuma jan baki data maka. Lukuta ce ta gaske,tana tsallenta kamar ba budurwa ba tana b'alla rake. Ganinsu yasa tayi d'if tana bazo ido. Kafin ta washe baki ganin Humaira
":Yar Humeme,wacece wannan kamar baturiya?"
Baby murmushi kawai takeyi ganin yarinyar,kamar dai tana da matsalar yarinta amma irin wannan kwalliyar ai an bar yayinsu.
"Addana ce, daga birni."
Yarinyar ta cuno baki. Wani saurayi mai shekaru sha takwas ya iso wajensu yace
"Kedai kam Safiya bazaki bar shiririta ba,inace anti tace ki tafi gidanku kibar fitowa idan kaka tana bacci? Wannan yar birni ce,kinga ma yanda ake kwalliya ba irin naki ba."
Ya karashe suna dariya har baby wacce abun ya bata dariya,wacce aka kira da Safiya ta murguda baki ta k'ara b'antalar rake
"Oho dai,Ali nuhu ma kansa yace mata suna kauye."
"Yauwa d'an k'arasa mana."
Ta harareshi tayi gaba tana tsalle tsallenta tace
"Akwai wanka."
Ta fice, saurayin ya dubi baby sukayi dariya. Ya dan russuna ya gaisheta gami da tambayar wanda take nema. Kafin ta bashi amsa humaira ta cafe
"Yaya Nura,addana ce ta Kano."
Ya kalli humaira ya kalleta,tabbaa yaga kama ya kara washe baki
"Yaya tasleem,right?"
Ta lumshe ido hadi da jinjina mishi kai lokaci daya. Ai sai ya sheka da gudu
"Kai ka kai,amma yau ni zan soma kaiwa antinmu albishir."
Jin haka Humaira ma tabi bayansa a guje. Dariya baby tayi ta mara musu baya tana mai zumudin yin tozali da mahaifiyarta....
******
Haris cike da mamaki ya dubi Yasmeen bayan sun keb'e a farfajiyar gidan inda tayo mishi rakiya zai koma ofis lokacin karfe ukun rana.
"Ashe kina da hankali har haka little? Kwarai banyi tsammanin zaki iya b'oyewa iyayenmu ainahin abunda ya had'aku da KB ba."
Yasmeen tayi murmushi mai ciwo
"Bari kawai yayana,wallahi inason Yaya kabir kai kanka shaida ne. Gani nayi a yanda kawai Daddy ya dauki zafi jin cewar yace na dawo ba tare da wani dalili ba(kamar yanda ta fad'a musu kenan don kare mijinta),kar kaso kaga yanda ya fusata sai faman bud'e wuta yakeyi. Ya kake tunanin idan sunji har marina yayi akan karuwarsa? Ba yanda za'ayi nayi gangancin da za'a rabani dashi. Kaima ina rok'onka don Allah kada ka nunamishi kasan zancen."
Ya kara tsintar kansa da kauna da matsanancin tausayin kanwar tasa, shi kuwa ya za'ayi yayi gangancin barin Tasleem ta ruguza farincikinta? Bazai yiwu ba. Ya numfasa
"Baki da matsala dani little,saidai ina rok'onki da ki rage son d'a namiji har haka kada ya zame maki babbar matsala fiye da yanzu. Ki cigaba da addu'a Allah Yayi mana magani. Bari na tafi, Abba yana jirana."
Ta tareshi
"Af,baka sanarmin wacce ka zab'o mana matsayin antin tawa ba? Kodai zatona ya zama gaskiya,Zahra ce?"
Yayi murmushin dole
"No.. Baki canka ba."
Ta dan nuna damuwarta,ganin ta bude baki zata k'ara magana ya bude motarsa ya fad'a
"Ke kyaleni kinji ko? Sai mun dawo da yamma."