Sashe 10
African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals · about 8 min read
Ta kauda kanta gefe tana wani d'an tunani,shi kuwa nanata maganarta yakeyi. Tilasta ta akayi tayi karuwancin kamar ya? Haka yayita juya maganar,zuwa yanzu zai so yaji tarihinta saidai bayason yiwa mutum shishshigi a sha'anin rayuwarsa.
"Baka tambayeni inda zanje ba?"
Ta jefo mishi tambayar tana dubansa da wannan shu'uman idanuwan nata. Ya dan kalleta babu laifi ya dan saki fuska kad'an.
"Mahaifiyata zanje gani."
Baisan sadda yayi mata duban mamaki ba,tana murmushi yayinda hawaye suka kwaranyo mata ta gyada mishi kai
"Eh Haris,mahaifiyata zanje gani. A yau bana bukatar komai sai ita. Rabona da ita shekaru uku kenan."
Ya shanye mamakinsa yana maida dubansa ga titi
"A wane gari kenan?"
"KAZAURE."
Ya gangara ya sauka gefen titi,bayan mamaki daya bayyana a saman fuskarsa har da d'an murmushi. Haka kawai yaji dadin kasancewarsu 'yan gari guda. Ita kam kamar a mafarki haka take ganin murmushin da yakeyi gareta. Wannan yasa ta dan lumshe ido ta budesu domin tabbatarwar,saidai har zuwa lokacin basu gushe ba.
"Menene ya baka mamaki na kasancewata 'yar Kazaure?"
Yabar kallonta,fuska a sake yace
"Kasancewata d'an Kazaure shiyasa nayi mamaki."
Itama baby ta d'an bude ido cike da mamaki kafin ta langab'ar da kai tana marairaice murya
"Daman garinmu d'aya amma kake kyamatana?"
Yayi tsai yana dubanta,ita kam wayewar har tana neman yi mata yawa. Yanayinta ne a haka ko kuwa dai tsabar kwarewa a bariki ne?
Ya kauda wannan tunanin ta hanyar fad'in
"Ban tsanar dan uwana musulmi saidai na tsani wani hali nasa. Me kikayimin da har zan tsaneki Tasleem? Hakikanin gaskiya gurb'atacciyar rayuwa irin wacce kikeyi ne na tsana,bana kaunar dukkan mabiyanta. Babu wani burgewa a cikinta face tsantsar nadama a karshe wanda wasunku ma alokacin komai ya k'are maku babu damar tuba. Ki godewa Allah da akwai sauran numfashinki,yaci ace kinyiwa kanki fad'a da karatun ta nutsu. Kisa misali idan da ace ya zamto mutuwa ce ta riskeki yayinda kikayi hatsarin nan,wani guzuri zaki tafiyarwa Ubangijinki dashi da kikejin ya isheki kufcewa azabobinSa?"
Ta share hawayen da tun soma maganarsa suke ambaliya,idanunta yana ga kallon titi tace
"Nasani dukkan abunda ka fad'a babu k'arya aciki. Hakika rayuwar dana zab'arwa kaina ba rayuwa ce ta abun tutiya da tak'ama ba. Rayuwa ce tamkar ta dabbobi,inda mutum yake da damar yin kowane kalar sab'o ba tare da tunanin makomarmu ba. Na tafka kuskure a rayuwata Haris,saidai kamar yanda na fad'amaka,tursasani akayi."
Tun soma maganarta idanunsa ke kanta,maganarta ta karshe ta chanja yanayin duban da yake mata zuwa na rashin fahimta.
"Har ila yau,bangane manufarki ba Tasleem. Daman akan tursasa mutum ya sab'awa umarnin UbangijinSa shi kuma ya amince yabi?"
Tayi murmushi mai ciwo,ta jinjina kanta
"Bacin rai da bakin cikin kazafi da akayiwa mutum bada hakkinsa ba,ya sanyani fad'awa wannan yanayin. Abun bakin cikine ace makusantanka sune basu yarda dakai ba,har suke gaskata sharrin makiyanka. Meyasa wannan bazai dameni ba? A halitta irin tawa,na kasance mai saurin fushi da zuciya. Duk da cewar inada saurin sauka kamar yanda wasu suka fad'a,saidai na rasa yanda akayi na kasa barin abunda ya faru ya wuce a rayuwata. Babu wanda na tsana tamkar mahaifina,duk duniya babu wanda yafi bani mamaki kamar d'an uwana da muka fito ciki d'aya dashi."
Ta tsagaita ta dubi Haris wanda shima idanunsa ke kanta cikin rashin sanin inda ta dosa da maganganunta.
"Kada kayi mamaki idan kaji cewar mahaifina sananne ne a fad'in jahar Kano ba b'oyayye ba."
Ai sai ya kasa dauke ido a kanta,yayinda ta cigaba da yi mishi murmushin nan wanda ke k'ona zuciyarta. Haris ya numfasa
"Idan kinga babu damuwa,ko zaki iya bayyanamin labarinki Tasleem?"
Ta d'anyi shiru tamkar bazatace komai ba,can kuma ta karkato jikinta sosai tana mai lankwasar da kafafuwanta a saman kujera. Idanuwanta suna duban na Haris, yayin da fuskarta ta chanja kala zuwa ja. Murmushi ta k'ak'alo ta jefamishi
"Zakaji tarihina,zakaji wacece ni Haris. Na yarda dakai dari bisa dari."
Ta jingina kanta jikin kujera ta tsurawa sitiyari ido kafin ta bud'i bakinta ta soma magana...
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(23)
"Mahaifina Doctor Abba Waziri,d'a a wajen marigayi Wazirin Kano,Alhaji Ma'aruf Waziri.(ahuwan kanawa..lol)."
Haris ya fiddo ido kadan yana dubanta cikin razana,Doctor Abba Waziri? Shi kuwa ya za'ayi ya kasa saninsa? Babban likita kuma kwararre a fannin k'ashi. Dukkan fad'in garin kano harma da yawa daga sauran garuruwa ansan da zamansa. Ko marigayi mahaifinsa,Alhaji Ma'aruf Wazirin kano,baiyi sunan da d'an nasa yayi ba. Wajen taimakon mutane da kiyaye lafiyarsu.
Baby ta cigaba da zancenta bata ko damu da razanar data sauka a saman fuskarsa ba.
"Mahaifiyata kuwa,Hajiya Maryam Abdulmalik,haifaffiyar Kazaure ce. D'iya a wajen babban limamin masallacin juma'a na Kazaure,Malam Abdulmalik Hussein."
Ai sai Haris ya k'ara sarewa,Malam Abdulmalik Hussein,babban aminin kakansa ne na wajen uba. A iyakar saninsa,gidansa ya zamto na mahaddata Al-k'ur'ani. Suna da nutsuwa yaransa hakanan kowannensu suna zaune ne a gabansa. Duk shine ya aurar da yaransa. Kenan Gwaggo Maryama itace mahaifiyar Tasleem? Unbelievable!
Sai lokacin ne ma idanuwansa suka soma hasko masa kamannin Gwaggo maryama a fuskar Tasleem.
Hawaye akan fuskarta
"Wad'annan bayin Allah biyun,sune sukayi silar samuwata a duniya da ikon Allah.
Mahaifana sunyi rayuwa cike da jin dadi a matsayinsu na ma'aurata kafin Allah Ya albarkacesu da samun d'a namiji,Abdullah. Yaya abdullah yana da shekara d'aya a duniya,kakanmu Alhaji Ma'aruf ya rasu aka nad'a Yayan mahaifina,Alhaji Nasir akan karagar mulki.
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(25)
Mamma tana nan zaune har na kusan mintuna sai gasu sun fito suna dariya. Abba yayi shirinsa na tafiya asibiti yayinda briefcase dinsa ke a hannun Raliya tana takowa da murmushi dauke saman fuskarta. Mamma duk da haushinta da takeji ta kasa cewa uffan akan wannan al'amari,saidai ta daure fuska. Wai ma duk a banza,Abba baisan tana yi ba. Har ya nufo teburin sai Raliya tayi saurin magana,wai me yake nufi ne? Bazaici wainar da tayi mishi ba? Ga mamakin Mamma sai ya juya ya dubeta ya bata hakuri cewar zaije yaci wainar Raliya kada tayi fushi. Mamma kai kawai ta gyada mishi,ta kasa cewa uffan har suka fice.
A ranar kuma,da daddare tana zaune a falonta,Abba yayi kiran wayarta yana nemanta. Ba musu ta tafi da tsohon ciki,ta nufi sashensa. Turus tayi ganin matasan da basu wuce ashirin da wani abu ba,zaune saman kujera tare dasu Abba da Raliya sai hira akeyi da dariya. Abba ya ankara da shigowarta,ya dubeta kafin yayi mata iznin shigowa. Ta karasa ta zauna a gefensa. Abba ya dubi samarin
"Banji kun gaisheta ba?"
Sai lokacin dukkansu suka hau kwasar gaisuwa,Mamma ta amsa. Bayan ya kira sunanta,ya shaida mata yaran Raliya ne,da Hamza,Nura da kuma Usman. Anan gidan zasu cigaba da rayuwarsu kasancewarsu marayun da ubansu ya rasu. Zai dauki nauyin karatunsu da komai ma na rayuwarsu. Maganar ta daki Mamma,sai lokacin ta k'ara gaskata magana gwaggo sarai. Ta boye mamakinta tayi mishi fatan alheri akan niyyarsa sannan tayi mishi alk'awarin itama zata daukesu tamkar Abdullah d'anta. Bazata bambantasu ba kamar yanda ya nema. Abba yaji dadi,yace su bata girmanta a matsayinta na matarsa. Suma kamar gaske sukayi na'am. Daga haka ta tashi ta koma.
Zamanta da Raliya kuwa zama ne ba yabo ba fallasa,Raliya aikinta bai wuce jaye jayen fad'a ba duk da ba sashe d'aya suke ba. Tsakaninta da Abba ma ya chanja,ya zamana mukullan motar gidan a hannunta suke,acewarsa itace babba don ta girmeta. Mamma batace komai ba ta bisu hakanan.
Babbar matsalar data soma tayarwa Mamma hankali,bai wuce kwananta da yake kaiwa ga Raliya ba. Ya chanja mata kullum cikin daure dauren fuska. Abdullah bashi da damar sakewa da Abba kamar a baya,ya zamana bai fiye janshi da wasa ba.
Cikin wannan yanayin na rashin samun kulawar miji,abunda bai kai ya kawo ba zai hau ta da fad'a marar dalili koda a gaban 'yan aiki ne. Nakuda ya kamata,gatanan ita d'aya a d'aki. Da abun yaci tura ta lalubo wayarta ta kira Abba. Cikin magagin bacci ya amsa,jin cewar tana nakuda ne ya wartsakar dashi domin har lokacin akwai burbushin sonta a ransa. Haka ya taso Raliya na biye dashi."
Baby ta dakata tayi dariyar takaici gami da kwafa
"Ta hana akai uwata asibiti,shegiyar taso ta kasheni Allah Yayi zan fito duniya na zame mata annoba."
Haris dai kallon Baby yakeyi,murmushi kawai yayi jin abunda ta fad'a kafin ta cigaba.....
Sorinku...bana gida ne...sai zuwa dare in sha Allah.
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(24)
"Mamma,wato mahaifiyata. Sunan da muke kiranta dashi kenan,tana dauke da cikina ne babu zato Abba ya soma shirye shiryen aure. Sam,Mamma bata tayar da hankalinta ba kasancewarta mace tagari,wacce take da ilimin addini kuma take aiki dashi. Ta bashi goyon baya sosai har kuma a yanda ta labartamin yazo yana jin kunyarta ba kuma ya fasa batun auren nasa ba.
Hankalin Mamma bai tashi ba har saida labari ya risketa ta hanyar kanwar Abba,Gwaggo Sarai akan wacce Abba zai aura ba yarinya bace. Asalima a girme ta girmeshi nesa ba kusa ba sannan tana da manyan 'ya'ya maza har su uku sai kuma mace d'aya dake gidan mijinta. A yanda Gwaggo Sarai ta ji harda yaran Abba yayi na'am zai rike mata su tunda dai marayune mahaifinsu ya rasu gashinan su d'in basu kasance masu kudi ba. Wannan babban taimako ne zaiyi. Tun alokacin ma ya zamana shine komai na karatunsu,domin kuwa sun kusan yin watanni uku suna tare da Abba kafin ya sanarwa Mamma halin da suke ciki. Wannan shine ya d'agawa Mamma hankali saidai ta nunawa Gwaggo Sarai hakan ba damuwa bace tunda a irin girma na gidan Abba da kuma tazara dake tsakanin sasunan guda uku sai mutum yayi abunda zaiyi babu wanda yaga wani tsakaninsu. Sai bayan tafiyar Gwaggo Sarai ne hankalin Mamma ya tashi,ta nemi yin shawara da aminiyarta wacce bani da masaniyar ko har yanzu suna tare,wato Hajiya Aisha,itama 'yar Kazaure ce kamar yanda Mamma ta gayamin. Ta sanar da ita halin da take ciki,Hajiya Aisha ta bata shawara akan ta dage da addu'a domin dai idan ta d'aga hankalinta babu ribar da zata tsinta a ciki. Haka dai Mamma ta nutsu ta zubawa sarautar Allah ido. Lokacin kuwa Abdullah babu inda baya yawonsa ya soma wayo.
"Baka tambayeni inda zanje ba?"
Ta jefo mishi tambayar tana dubansa da wannan shu'uman idanuwan nata. Ya dan kalleta babu laifi ya dan saki fuska kad'an.
"Mahaifiyata zanje gani."
Baisan sadda yayi mata duban mamaki ba,tana murmushi yayinda hawaye suka kwaranyo mata ta gyada mishi kai
"Eh Haris,mahaifiyata zanje gani. A yau bana bukatar komai sai ita. Rabona da ita shekaru uku kenan."
Ya shanye mamakinsa yana maida dubansa ga titi
"A wane gari kenan?"
"KAZAURE."
Ya gangara ya sauka gefen titi,bayan mamaki daya bayyana a saman fuskarsa har da d'an murmushi. Haka kawai yaji dadin kasancewarsu 'yan gari guda. Ita kam kamar a mafarki haka take ganin murmushin da yakeyi gareta. Wannan yasa ta dan lumshe ido ta budesu domin tabbatarwar,saidai har zuwa lokacin basu gushe ba.
"Menene ya baka mamaki na kasancewata 'yar Kazaure?"
Yabar kallonta,fuska a sake yace
"Kasancewata d'an Kazaure shiyasa nayi mamaki."
Itama baby ta d'an bude ido cike da mamaki kafin ta langab'ar da kai tana marairaice murya
"Daman garinmu d'aya amma kake kyamatana?"
Yayi tsai yana dubanta,ita kam wayewar har tana neman yi mata yawa. Yanayinta ne a haka ko kuwa dai tsabar kwarewa a bariki ne?
Ya kauda wannan tunanin ta hanyar fad'in
"Ban tsanar dan uwana musulmi saidai na tsani wani hali nasa. Me kikayimin da har zan tsaneki Tasleem? Hakikanin gaskiya gurb'atacciyar rayuwa irin wacce kikeyi ne na tsana,bana kaunar dukkan mabiyanta. Babu wani burgewa a cikinta face tsantsar nadama a karshe wanda wasunku ma alokacin komai ya k'are maku babu damar tuba. Ki godewa Allah da akwai sauran numfashinki,yaci ace kinyiwa kanki fad'a da karatun ta nutsu. Kisa misali idan da ace ya zamto mutuwa ce ta riskeki yayinda kikayi hatsarin nan,wani guzuri zaki tafiyarwa Ubangijinki dashi da kikejin ya isheki kufcewa azabobinSa?"
Ta share hawayen da tun soma maganarsa suke ambaliya,idanunta yana ga kallon titi tace
"Nasani dukkan abunda ka fad'a babu k'arya aciki. Hakika rayuwar dana zab'arwa kaina ba rayuwa ce ta abun tutiya da tak'ama ba. Rayuwa ce tamkar ta dabbobi,inda mutum yake da damar yin kowane kalar sab'o ba tare da tunanin makomarmu ba. Na tafka kuskure a rayuwata Haris,saidai kamar yanda na fad'amaka,tursasani akayi."
Tun soma maganarta idanunsa ke kanta,maganarta ta karshe ta chanja yanayin duban da yake mata zuwa na rashin fahimta.
"Har ila yau,bangane manufarki ba Tasleem. Daman akan tursasa mutum ya sab'awa umarnin UbangijinSa shi kuma ya amince yabi?"
Tayi murmushi mai ciwo,ta jinjina kanta
"Bacin rai da bakin cikin kazafi da akayiwa mutum bada hakkinsa ba,ya sanyani fad'awa wannan yanayin. Abun bakin cikine ace makusantanka sune basu yarda dakai ba,har suke gaskata sharrin makiyanka. Meyasa wannan bazai dameni ba? A halitta irin tawa,na kasance mai saurin fushi da zuciya. Duk da cewar inada saurin sauka kamar yanda wasu suka fad'a,saidai na rasa yanda akayi na kasa barin abunda ya faru ya wuce a rayuwata. Babu wanda na tsana tamkar mahaifina,duk duniya babu wanda yafi bani mamaki kamar d'an uwana da muka fito ciki d'aya dashi."
Ta tsagaita ta dubi Haris wanda shima idanunsa ke kanta cikin rashin sanin inda ta dosa da maganganunta.
"Kada kayi mamaki idan kaji cewar mahaifina sananne ne a fad'in jahar Kano ba b'oyayye ba."
Ai sai ya kasa dauke ido a kanta,yayinda ta cigaba da yi mishi murmushin nan wanda ke k'ona zuciyarta. Haris ya numfasa
"Idan kinga babu damuwa,ko zaki iya bayyanamin labarinki Tasleem?"
Ta d'anyi shiru tamkar bazatace komai ba,can kuma ta karkato jikinta sosai tana mai lankwasar da kafafuwanta a saman kujera. Idanuwanta suna duban na Haris, yayin da fuskarta ta chanja kala zuwa ja. Murmushi ta k'ak'alo ta jefamishi
"Zakaji tarihina,zakaji wacece ni Haris. Na yarda dakai dari bisa dari."
Ta jingina kanta jikin kujera ta tsurawa sitiyari ido kafin ta bud'i bakinta ta soma magana...
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(23)
"Mahaifina Doctor Abba Waziri,d'a a wajen marigayi Wazirin Kano,Alhaji Ma'aruf Waziri.(ahuwan kanawa..lol)."
Haris ya fiddo ido kadan yana dubanta cikin razana,Doctor Abba Waziri? Shi kuwa ya za'ayi ya kasa saninsa? Babban likita kuma kwararre a fannin k'ashi. Dukkan fad'in garin kano harma da yawa daga sauran garuruwa ansan da zamansa. Ko marigayi mahaifinsa,Alhaji Ma'aruf Wazirin kano,baiyi sunan da d'an nasa yayi ba. Wajen taimakon mutane da kiyaye lafiyarsu.
Baby ta cigaba da zancenta bata ko damu da razanar data sauka a saman fuskarsa ba.
"Mahaifiyata kuwa,Hajiya Maryam Abdulmalik,haifaffiyar Kazaure ce. D'iya a wajen babban limamin masallacin juma'a na Kazaure,Malam Abdulmalik Hussein."
Ai sai Haris ya k'ara sarewa,Malam Abdulmalik Hussein,babban aminin kakansa ne na wajen uba. A iyakar saninsa,gidansa ya zamto na mahaddata Al-k'ur'ani. Suna da nutsuwa yaransa hakanan kowannensu suna zaune ne a gabansa. Duk shine ya aurar da yaransa. Kenan Gwaggo Maryama itace mahaifiyar Tasleem? Unbelievable!
Sai lokacin ne ma idanuwansa suka soma hasko masa kamannin Gwaggo maryama a fuskar Tasleem.
Hawaye akan fuskarta
"Wad'annan bayin Allah biyun,sune sukayi silar samuwata a duniya da ikon Allah.
Mahaifana sunyi rayuwa cike da jin dadi a matsayinsu na ma'aurata kafin Allah Ya albarkacesu da samun d'a namiji,Abdullah. Yaya abdullah yana da shekara d'aya a duniya,kakanmu Alhaji Ma'aruf ya rasu aka nad'a Yayan mahaifina,Alhaji Nasir akan karagar mulki.
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(25)
Mamma tana nan zaune har na kusan mintuna sai gasu sun fito suna dariya. Abba yayi shirinsa na tafiya asibiti yayinda briefcase dinsa ke a hannun Raliya tana takowa da murmushi dauke saman fuskarta. Mamma duk da haushinta da takeji ta kasa cewa uffan akan wannan al'amari,saidai ta daure fuska. Wai ma duk a banza,Abba baisan tana yi ba. Har ya nufo teburin sai Raliya tayi saurin magana,wai me yake nufi ne? Bazaici wainar da tayi mishi ba? Ga mamakin Mamma sai ya juya ya dubeta ya bata hakuri cewar zaije yaci wainar Raliya kada tayi fushi. Mamma kai kawai ta gyada mishi,ta kasa cewa uffan har suka fice.
A ranar kuma,da daddare tana zaune a falonta,Abba yayi kiran wayarta yana nemanta. Ba musu ta tafi da tsohon ciki,ta nufi sashensa. Turus tayi ganin matasan da basu wuce ashirin da wani abu ba,zaune saman kujera tare dasu Abba da Raliya sai hira akeyi da dariya. Abba ya ankara da shigowarta,ya dubeta kafin yayi mata iznin shigowa. Ta karasa ta zauna a gefensa. Abba ya dubi samarin
"Banji kun gaisheta ba?"
Sai lokacin dukkansu suka hau kwasar gaisuwa,Mamma ta amsa. Bayan ya kira sunanta,ya shaida mata yaran Raliya ne,da Hamza,Nura da kuma Usman. Anan gidan zasu cigaba da rayuwarsu kasancewarsu marayun da ubansu ya rasu. Zai dauki nauyin karatunsu da komai ma na rayuwarsu. Maganar ta daki Mamma,sai lokacin ta k'ara gaskata magana gwaggo sarai. Ta boye mamakinta tayi mishi fatan alheri akan niyyarsa sannan tayi mishi alk'awarin itama zata daukesu tamkar Abdullah d'anta. Bazata bambantasu ba kamar yanda ya nema. Abba yaji dadi,yace su bata girmanta a matsayinta na matarsa. Suma kamar gaske sukayi na'am. Daga haka ta tashi ta koma.
Zamanta da Raliya kuwa zama ne ba yabo ba fallasa,Raliya aikinta bai wuce jaye jayen fad'a ba duk da ba sashe d'aya suke ba. Tsakaninta da Abba ma ya chanja,ya zamana mukullan motar gidan a hannunta suke,acewarsa itace babba don ta girmeta. Mamma batace komai ba ta bisu hakanan.
Babbar matsalar data soma tayarwa Mamma hankali,bai wuce kwananta da yake kaiwa ga Raliya ba. Ya chanja mata kullum cikin daure dauren fuska. Abdullah bashi da damar sakewa da Abba kamar a baya,ya zamana bai fiye janshi da wasa ba.
Cikin wannan yanayin na rashin samun kulawar miji,abunda bai kai ya kawo ba zai hau ta da fad'a marar dalili koda a gaban 'yan aiki ne. Nakuda ya kamata,gatanan ita d'aya a d'aki. Da abun yaci tura ta lalubo wayarta ta kira Abba. Cikin magagin bacci ya amsa,jin cewar tana nakuda ne ya wartsakar dashi domin har lokacin akwai burbushin sonta a ransa. Haka ya taso Raliya na biye dashi."
Baby ta dakata tayi dariyar takaici gami da kwafa
"Ta hana akai uwata asibiti,shegiyar taso ta kasheni Allah Yayi zan fito duniya na zame mata annoba."
Haris dai kallon Baby yakeyi,murmushi kawai yayi jin abunda ta fad'a kafin ta cigaba.....
Sorinku...bana gida ne...sai zuwa dare in sha Allah.
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(24)
"Mamma,wato mahaifiyata. Sunan da muke kiranta dashi kenan,tana dauke da cikina ne babu zato Abba ya soma shirye shiryen aure. Sam,Mamma bata tayar da hankalinta ba kasancewarta mace tagari,wacce take da ilimin addini kuma take aiki dashi. Ta bashi goyon baya sosai har kuma a yanda ta labartamin yazo yana jin kunyarta ba kuma ya fasa batun auren nasa ba.
Hankalin Mamma bai tashi ba har saida labari ya risketa ta hanyar kanwar Abba,Gwaggo Sarai akan wacce Abba zai aura ba yarinya bace. Asalima a girme ta girmeshi nesa ba kusa ba sannan tana da manyan 'ya'ya maza har su uku sai kuma mace d'aya dake gidan mijinta. A yanda Gwaggo Sarai ta ji harda yaran Abba yayi na'am zai rike mata su tunda dai marayune mahaifinsu ya rasu gashinan su d'in basu kasance masu kudi ba. Wannan babban taimako ne zaiyi. Tun alokacin ma ya zamana shine komai na karatunsu,domin kuwa sun kusan yin watanni uku suna tare da Abba kafin ya sanarwa Mamma halin da suke ciki. Wannan shine ya d'agawa Mamma hankali saidai ta nunawa Gwaggo Sarai hakan ba damuwa bace tunda a irin girma na gidan Abba da kuma tazara dake tsakanin sasunan guda uku sai mutum yayi abunda zaiyi babu wanda yaga wani tsakaninsu. Sai bayan tafiyar Gwaggo Sarai ne hankalin Mamma ya tashi,ta nemi yin shawara da aminiyarta wacce bani da masaniyar ko har yanzu suna tare,wato Hajiya Aisha,itama 'yar Kazaure ce kamar yanda Mamma ta gayamin. Ta sanar da ita halin da take ciki,Hajiya Aisha ta bata shawara akan ta dage da addu'a domin dai idan ta d'aga hankalinta babu ribar da zata tsinta a ciki. Haka dai Mamma ta nutsu ta zubawa sarautar Allah ido. Lokacin kuwa Abdullah babu inda baya yawonsa ya soma wayo.