Sashe 17
African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals · about 8 min read
Tun daga wannan ranar kuma sai na soma
sakewa Usman kadan kadan,nakan gaisheshi
hakanan nakan je dukkan wani aiken da
zaiyimin zuwa gidansa ko kicin din Raliya da
sauransu. Ban dai sakarmishi sosai ba,amma
babu wannan rainin sosai. Har kuwa zuwa
lokacin bai rabu da fita yawon dare ba. Nasha
ganin Meena tazo wajen Raliya tana bala'i
akan ita ta soma gajiya da bin mata irin na
Usman,mutum tamkar wanda aka yiwa asiri.
Raliya saidai ta bata hakuri don babu laifi
iyayen meena akwai naira hakanan takan
lasawa Raliya sosai domin ita din macece
wacce bata godiya ga Allah. Duk da irin arzikin
da ta hau kai tayi zaune na Abba,ga kuma
business da takeyi,hakan bai hanata hangen
na wasu ba.
Bayan watanni uku,lokacin Mamma ta kusa
shekara a gidansu,kawai na tsinci wayar Yaya
musty yana yimin albishir cewar an daurawa
Mammana aure da wani almajirin Malam. Har
tsalle nayi don murna. Yara da yawa sukanyi
bakin ciki idan uwarsu zatayi wani auren
alhalin ubansu na raye, kai koda ace baya raye
akwai yaran dake taya ubansu kishi amma
nikam baruwana ko a jikina. Daga dariya kuma
sai na fashe da kuka. Ina cewa shine ko a
gayamin nazo da wuri? Dariya yayi yace kada
na damu anan Kazaure Mamma zata zauna
duk sanda naga dama na tambayi Abba ya
barni toh nazo na ganta. Naji dadi kwarai ya
kara tambayata game da Yaya abdullah nace
mishi sauran mishi watanni uku kawai ya dawo.
Daga haka mukayi sallama tare da alkawarin
idan yaje gidan zai kirani mu gaisa da Mamma.
Ai kuwa ko awa biyu ba'ayi ba yayi kirana,na
hau bud'a karshe na saki dariya. Nayi mamaki
dana ji muryar Mamma a sanyaye har na
tambayeta ko bata farinciki da auren nan? Bata
bani amsa ba ta share da tambayar lafiyata.
Nace alhamdulillah,tace zan cigaba da
karatune? Na tabe baki "Bansani ba Mamma."
"Kamar ya baki sani ba Tasleem? Keda
mahaifinki? Kije kiyi mishi magana tun lokaci
bai kure maki ba."
Na amsa da toh saidai kuma abunda Mamma
batasani ba shine,idan har sai naje ga Abba na
gwammace nayita zama haka a gidan. Haka
mukayi sallama da ita.
Bayan kwana biyu,Meena matar Yaya Usman
ta haife tsohon cikinta ta samu d'iya mace.
Murna a wajen yan gidan ba'a magana. Nikam
ko ajikina daman ba wani mutuncinsu nake
gani ba.
*******
Bayan kwana uku da haihuwar meena,misalin
biyar na yamma,ina zaune a bakin firij na
Raliya ina gogewa,ita kuwa da yaranta suna
falon suna kallon wasan Hausa saidai ko inda
suke bana kalla ballantana film din da suke
kallo ya dauki hankalina don tun fil'azal fina
finan hausa ba burgeni sukeyi ba barni da da
kallon Indian series da Korea anan kam ko
makiyina ke kallo zan saci kallo. Sallamar
Usman ta katsesu,Hamid bai amsa ba saima
ya mike ya fice saboda a yanzu haushinsa
yakeji akaina. Bayan su hamida sun gaisheshi
ya dubi Raliya.
"Wa kike ganin ya dace ta zauna wajen Meena
ne?"
Yayi maganar tamkar da sa'arsa,Raliya bata ko
damu ba ta kyabe baki
"A'a toh,ko Dijangala ai sai ta zauna. Idan
kuwa batason aikinta ga waccan tsiyar saiku
kwasa."
Sai lokacin na dubeta kafin na watsawa Usman
mugun kallo wanda na jima banyi mishi irinsa
ba. Murmushi yayi ya dubi Raliya
"A'a dijangala shiririta ne da ita,tunda dai ga
gwaggon meena zata dunga yi musu wanka
sai Tasleem ta dunga gyare gyarem gidan."
Raliya bata musa ba domin duk yanda zan
kuntata a rayuwa shi tafi kauna. Tace
"Hakan ma yayi,ke! Idan kin kammala ki tattaro
kayanki ki koma gidan Usman har sai matarsa
ta gama wanka sannan zaki dawo."
Bance uffan ba don bakin ciki,a matukar fusata
ta kammala aikin na mike na shiga daki. Haka
na tattaro kayan na fito. Hamida mukayi arba
da ita ta tuntsire da dariya gami da yimin
gwalo"Haka zaki k'are." Kamar nace mata wani
abu saidai na fasa nayi gaba,Raliya har lokacin
tana falon banko kalleta ba nayi gaba abina a
fusace.
Saida nazo daidai garden na zube anan na
fashe da kuka,wai haka rayuwata zata k'are?
Wane irin uba gareni da bai daukeni komai ba?
Ya manta da ya haifeni ne har ya banzatar dani
a gidansa ya maidani wofi? Ace yan aiki ma
sun fini daraja da kima a gidannan? Na daga
kaina nakai duba da d'an lilon da muka saba
wasa da Yayana. Haka zaiyita cillani yana
goyani muna zagaye garden dinnan muna
dariya. Ba zato naji an dafani ta baya,nayi
azamar juyowa ganin Usman bansan lokacin
da naja tsaki ba nayi kokarin mikewa yayi
saurin dawowa ta gabana.
"Haba Tasleem,ashe tsanar da kika yimin har
takai ace kije ki taimakawa matata ki zauna
kina kuka? Duk cikinmu waye mai tausayinki
bayan ni? Haba Tasleem,banji dadi ba wallahi."
Ganin yanayin fuskarsa sai naga kamar ban
kyauta ba,nace
"Ni ba gidanka ko matarka na tsana ba ai,irin
wannan rainin hankalin da akeyimin a gidan
ubana ne na kasa gane dalilinsa. Bansan kuma
me na tsarewa mutane ba."
Na karashe cikin tsiwa,yayi dariya ya kawo
hannu zai dora kan lebbana nayi azamar ja da
baya,cikin tsoron yanayin kallon da yakemin
"Tasleem komai naki abun sha'awa ne wallahi.
Ni bana k'inki,inason ganin kanwata a kusa
dani shine ma dalilin da yasa na nemi alfarmar
zuwanki. Kiyi hakuri inajin dadin yanda kika
kware a gyara muhalli. Meena KAZAMAR GIDA
ce, banason ganin gidan nan da kazanta. Don
Allah kanwata wallahi tana yin arba'in I
promise you zaki komo gida."
Bance komai ba na mike na dauki jakata nayi
gaba yana magana ko juyowa banyi,menene
saukin da nan da can din?
****
Baby ta numfasa,hawayenta ya karu wani yana
bin wani. Haris ya miko mata (handkerchief)
dinsa,tasa hannu ta karb'a saidai bata da
niyyar share hawayen. Ta dubi Haris wanda
shima ya gaji da waigenta ya karkato gaba
daya yana duban fuskarta don jin dadin hirar.
"Haris a wannan zuwan nawa ne gidan Usman
komai na rayuwata ya soma tabarbarewa.
Yanda akayi kuwa shine......."
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(34)
"Usman ya dunga jana a jiki da wasa da dariya musamman idan ba idon matarsa a wajen. Tun ina daure masa har dai na hakikance dagaske tausayina yakeji kuma kauna ta don Allah yakemin. Hakan ya zamana na amince cewar bashi da wata manufa akaina. Yaya Abdullah kuwa munfi sati lokacin bamuyi magana dashi ba don bana samun kudin da zan sayi data,hakanan shima bansan meya hanashi kirana ba.
Wahala iri iri babu banayi a hannu meena,ni ce kula da jaririyarta da taci sunan uwar meena wato Sadiya suke kiranta da Ummi. A farko Usman so yayi ya sanya sunan mahaifiyarsa saidai ta murje idanunta tace sam bazata amince ba,UWA TAFI UWA don haka saidai a sanya sunan nata uwar. Haka dai Usman ya goyi bayanta,dayake itama Raliyar irin dukiyar da ake kawowa Meena daga gidansu a matsayinta na wacce ta haifi jikar fari ya hargitsa mata kai tace bakomai abi tsarin da Meena da takeso.
Wanki kuwa babu ranar da hannuna baya taba ruwa,hakanan daidai da undies din Meena ni nake aikin wanke mata su. Sau daya na taba gigin yi mata musu akan wankin ta jibgeni ba tare da kowa yayi yunkurin cetona ba. Hakanan nayi jinyata na warke domin alokacin Usman baya garin yaje daurin auren abokinsa a Zaria kamar yanda ya shaidamin.
Bakar ranar da bazan mance ba itace ranar da babu kowa a sashen usman sai ni. Gwaggo ta raka meena asibiti don allurar da zata kai Ummi,ina zaune a falo zaune kan kujera ina hutawa sanin da nayi matar gidan batanan balle kuma ta gani tunda dai ta rigaya ta sanyamin dokar hawa kujerunta nikam gajiya da aikin dana kammala yasa na shimfide saman kujerar ina kallon tashar Zeeworld da suke hasko series dinnan na Destiny wanda an riga anyimin nisa sakamakon jimawa da nayi ban kalla ba. Yawo naji wani abu kamar hannu yana yimin a kunnena nayi azamar mikewa zaune don ba karamin firgita nayi ba. Ganin Usman yasa nayi murmushi kadan ban kawo komai a raina ba na gaisheshi hade da tambayar
"Yaushe ka shigo?"
Wani kallo yake watsomin,hakan yasa cike da mamaki na dubi shigar dake jikina naga babu inda na kuskuro da shigar banza. Na kara dubansa "Lafiya dai baban ummi?"
Ya basar yana mai mikewa tsaye da dariya
"Lafiyar kenan Kanwata,kallonki nakeyi ina tausayawa rayuwarki. Ace ke kam baki da wani hutu sai masu gidan basunan kike da yancin sakewa tamkar ba gidan mahaifinki ba?"
Nayi murmushi ina mai jin dadin yanda Usman ke nuna damuwarsa akaina,alokacin na ayyana cewar ko na manta kowa bazan mance kaunar da Usman ya nunamin ba alokacin da dukkan gidan suka juyamin baya.
"Ayya,bakomai Baban ummi wataran sai labari fa."
Yayi dariya yace "Hakane kanwata,kiyi kallo abinki domin kuwa ina maki albishir cewar matar gidan bazata shigo yanzu ba don zata biya ta gidansu." Naji wani sanyin dadi shi kuwa yayo hanyar dakinsa na maida kaina ga kallo. Jimawa kadan ya fito ya shiga kicin bayan ya chanja suturar jikinsa zuwa doguwar jallabiya. Ban damu da sanin abunda zai aikata a kicin ba,a cewata ma,ai gwara kada ya matsamin ya barni na dan huta kafin hakimar tasa ta dawo. Hankalina ya nutsa sosai ga kallo saidai naji alamar ajiye kwalin a kusa dani. Hakan yasa na juyo na dubeshi,murmushi ya sakarmin yana kurbar lemon kwalin na Chi exotic dake hamnunsa,yayimin nuni da ido ga lemon da yake ajiye akan tebur kusa dani.
"Bismillah kina kallona,nasan rowa irin ta Meena bazaisa ta baki damar daukar abun sha ba. Bari na dan kwanta kafin nan da la'asar." Ya mike ya shige daki,nayi murmushi don nasan gaskiya ya fada. Meena rowan tsiya ne da ita,koda bak'i tayi sai sun nemi ruwa sannan ake basu balle akaima ga lemo. Na dubi kwalin lemun ina tunanin yaushe ma rabona dana samu yancin shan lemun kwali duk da a baya katon katon babu irin wanda Abba baya ajiyewa Mamma. Na dauka na bude na sha sosai,inayi ina kallo. Tsayawa nayi cak yayinda kaina yayimin nauyi,na ajiye kwalin lemun na dafe kaina ina mai runtse ido. A hankali na soma fita hayyacina,tun ina jiyo muryoyin dake fitowa a tv har dai na daina ji da ganin komai."
sakewa Usman kadan kadan,nakan gaisheshi
hakanan nakan je dukkan wani aiken da
zaiyimin zuwa gidansa ko kicin din Raliya da
sauransu. Ban dai sakarmishi sosai ba,amma
babu wannan rainin sosai. Har kuwa zuwa
lokacin bai rabu da fita yawon dare ba. Nasha
ganin Meena tazo wajen Raliya tana bala'i
akan ita ta soma gajiya da bin mata irin na
Usman,mutum tamkar wanda aka yiwa asiri.
Raliya saidai ta bata hakuri don babu laifi
iyayen meena akwai naira hakanan takan
lasawa Raliya sosai domin ita din macece
wacce bata godiya ga Allah. Duk da irin arzikin
da ta hau kai tayi zaune na Abba,ga kuma
business da takeyi,hakan bai hanata hangen
na wasu ba.
Bayan watanni uku,lokacin Mamma ta kusa
shekara a gidansu,kawai na tsinci wayar Yaya
musty yana yimin albishir cewar an daurawa
Mammana aure da wani almajirin Malam. Har
tsalle nayi don murna. Yara da yawa sukanyi
bakin ciki idan uwarsu zatayi wani auren
alhalin ubansu na raye, kai koda ace baya raye
akwai yaran dake taya ubansu kishi amma
nikam baruwana ko a jikina. Daga dariya kuma
sai na fashe da kuka. Ina cewa shine ko a
gayamin nazo da wuri? Dariya yayi yace kada
na damu anan Kazaure Mamma zata zauna
duk sanda naga dama na tambayi Abba ya
barni toh nazo na ganta. Naji dadi kwarai ya
kara tambayata game da Yaya abdullah nace
mishi sauran mishi watanni uku kawai ya dawo.
Daga haka mukayi sallama tare da alkawarin
idan yaje gidan zai kirani mu gaisa da Mamma.
Ai kuwa ko awa biyu ba'ayi ba yayi kirana,na
hau bud'a karshe na saki dariya. Nayi mamaki
dana ji muryar Mamma a sanyaye har na
tambayeta ko bata farinciki da auren nan? Bata
bani amsa ba ta share da tambayar lafiyata.
Nace alhamdulillah,tace zan cigaba da
karatune? Na tabe baki "Bansani ba Mamma."
"Kamar ya baki sani ba Tasleem? Keda
mahaifinki? Kije kiyi mishi magana tun lokaci
bai kure maki ba."
Na amsa da toh saidai kuma abunda Mamma
batasani ba shine,idan har sai naje ga Abba na
gwammace nayita zama haka a gidan. Haka
mukayi sallama da ita.
Bayan kwana biyu,Meena matar Yaya Usman
ta haife tsohon cikinta ta samu d'iya mace.
Murna a wajen yan gidan ba'a magana. Nikam
ko ajikina daman ba wani mutuncinsu nake
gani ba.
*******
Bayan kwana uku da haihuwar meena,misalin
biyar na yamma,ina zaune a bakin firij na
Raliya ina gogewa,ita kuwa da yaranta suna
falon suna kallon wasan Hausa saidai ko inda
suke bana kalla ballantana film din da suke
kallo ya dauki hankalina don tun fil'azal fina
finan hausa ba burgeni sukeyi ba barni da da
kallon Indian series da Korea anan kam ko
makiyina ke kallo zan saci kallo. Sallamar
Usman ta katsesu,Hamid bai amsa ba saima
ya mike ya fice saboda a yanzu haushinsa
yakeji akaina. Bayan su hamida sun gaisheshi
ya dubi Raliya.
"Wa kike ganin ya dace ta zauna wajen Meena
ne?"
Yayi maganar tamkar da sa'arsa,Raliya bata ko
damu ba ta kyabe baki
"A'a toh,ko Dijangala ai sai ta zauna. Idan
kuwa batason aikinta ga waccan tsiyar saiku
kwasa."
Sai lokacin na dubeta kafin na watsawa Usman
mugun kallo wanda na jima banyi mishi irinsa
ba. Murmushi yayi ya dubi Raliya
"A'a dijangala shiririta ne da ita,tunda dai ga
gwaggon meena zata dunga yi musu wanka
sai Tasleem ta dunga gyare gyarem gidan."
Raliya bata musa ba domin duk yanda zan
kuntata a rayuwa shi tafi kauna. Tace
"Hakan ma yayi,ke! Idan kin kammala ki tattaro
kayanki ki koma gidan Usman har sai matarsa
ta gama wanka sannan zaki dawo."
Bance uffan ba don bakin ciki,a matukar fusata
ta kammala aikin na mike na shiga daki. Haka
na tattaro kayan na fito. Hamida mukayi arba
da ita ta tuntsire da dariya gami da yimin
gwalo"Haka zaki k'are." Kamar nace mata wani
abu saidai na fasa nayi gaba,Raliya har lokacin
tana falon banko kalleta ba nayi gaba abina a
fusace.
Saida nazo daidai garden na zube anan na
fashe da kuka,wai haka rayuwata zata k'are?
Wane irin uba gareni da bai daukeni komai ba?
Ya manta da ya haifeni ne har ya banzatar dani
a gidansa ya maidani wofi? Ace yan aiki ma
sun fini daraja da kima a gidannan? Na daga
kaina nakai duba da d'an lilon da muka saba
wasa da Yayana. Haka zaiyita cillani yana
goyani muna zagaye garden dinnan muna
dariya. Ba zato naji an dafani ta baya,nayi
azamar juyowa ganin Usman bansan lokacin
da naja tsaki ba nayi kokarin mikewa yayi
saurin dawowa ta gabana.
"Haba Tasleem,ashe tsanar da kika yimin har
takai ace kije ki taimakawa matata ki zauna
kina kuka? Duk cikinmu waye mai tausayinki
bayan ni? Haba Tasleem,banji dadi ba wallahi."
Ganin yanayin fuskarsa sai naga kamar ban
kyauta ba,nace
"Ni ba gidanka ko matarka na tsana ba ai,irin
wannan rainin hankalin da akeyimin a gidan
ubana ne na kasa gane dalilinsa. Bansan kuma
me na tsarewa mutane ba."
Na karashe cikin tsiwa,yayi dariya ya kawo
hannu zai dora kan lebbana nayi azamar ja da
baya,cikin tsoron yanayin kallon da yakemin
"Tasleem komai naki abun sha'awa ne wallahi.
Ni bana k'inki,inason ganin kanwata a kusa
dani shine ma dalilin da yasa na nemi alfarmar
zuwanki. Kiyi hakuri inajin dadin yanda kika
kware a gyara muhalli. Meena KAZAMAR GIDA
ce, banason ganin gidan nan da kazanta. Don
Allah kanwata wallahi tana yin arba'in I
promise you zaki komo gida."
Bance komai ba na mike na dauki jakata nayi
gaba yana magana ko juyowa banyi,menene
saukin da nan da can din?
****
Baby ta numfasa,hawayenta ya karu wani yana
bin wani. Haris ya miko mata (handkerchief)
dinsa,tasa hannu ta karb'a saidai bata da
niyyar share hawayen. Ta dubi Haris wanda
shima ya gaji da waigenta ya karkato gaba
daya yana duban fuskarta don jin dadin hirar.
"Haris a wannan zuwan nawa ne gidan Usman
komai na rayuwata ya soma tabarbarewa.
Yanda akayi kuwa shine......."
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(34)
"Usman ya dunga jana a jiki da wasa da dariya musamman idan ba idon matarsa a wajen. Tun ina daure masa har dai na hakikance dagaske tausayina yakeji kuma kauna ta don Allah yakemin. Hakan ya zamana na amince cewar bashi da wata manufa akaina. Yaya Abdullah kuwa munfi sati lokacin bamuyi magana dashi ba don bana samun kudin da zan sayi data,hakanan shima bansan meya hanashi kirana ba.
Wahala iri iri babu banayi a hannu meena,ni ce kula da jaririyarta da taci sunan uwar meena wato Sadiya suke kiranta da Ummi. A farko Usman so yayi ya sanya sunan mahaifiyarsa saidai ta murje idanunta tace sam bazata amince ba,UWA TAFI UWA don haka saidai a sanya sunan nata uwar. Haka dai Usman ya goyi bayanta,dayake itama Raliyar irin dukiyar da ake kawowa Meena daga gidansu a matsayinta na wacce ta haifi jikar fari ya hargitsa mata kai tace bakomai abi tsarin da Meena da takeso.
Wanki kuwa babu ranar da hannuna baya taba ruwa,hakanan daidai da undies din Meena ni nake aikin wanke mata su. Sau daya na taba gigin yi mata musu akan wankin ta jibgeni ba tare da kowa yayi yunkurin cetona ba. Hakanan nayi jinyata na warke domin alokacin Usman baya garin yaje daurin auren abokinsa a Zaria kamar yanda ya shaidamin.
Bakar ranar da bazan mance ba itace ranar da babu kowa a sashen usman sai ni. Gwaggo ta raka meena asibiti don allurar da zata kai Ummi,ina zaune a falo zaune kan kujera ina hutawa sanin da nayi matar gidan batanan balle kuma ta gani tunda dai ta rigaya ta sanyamin dokar hawa kujerunta nikam gajiya da aikin dana kammala yasa na shimfide saman kujerar ina kallon tashar Zeeworld da suke hasko series dinnan na Destiny wanda an riga anyimin nisa sakamakon jimawa da nayi ban kalla ba. Yawo naji wani abu kamar hannu yana yimin a kunnena nayi azamar mikewa zaune don ba karamin firgita nayi ba. Ganin Usman yasa nayi murmushi kadan ban kawo komai a raina ba na gaisheshi hade da tambayar
"Yaushe ka shigo?"
Wani kallo yake watsomin,hakan yasa cike da mamaki na dubi shigar dake jikina naga babu inda na kuskuro da shigar banza. Na kara dubansa "Lafiya dai baban ummi?"
Ya basar yana mai mikewa tsaye da dariya
"Lafiyar kenan Kanwata,kallonki nakeyi ina tausayawa rayuwarki. Ace ke kam baki da wani hutu sai masu gidan basunan kike da yancin sakewa tamkar ba gidan mahaifinki ba?"
Nayi murmushi ina mai jin dadin yanda Usman ke nuna damuwarsa akaina,alokacin na ayyana cewar ko na manta kowa bazan mance kaunar da Usman ya nunamin ba alokacin da dukkan gidan suka juyamin baya.
"Ayya,bakomai Baban ummi wataran sai labari fa."
Yayi dariya yace "Hakane kanwata,kiyi kallo abinki domin kuwa ina maki albishir cewar matar gidan bazata shigo yanzu ba don zata biya ta gidansu." Naji wani sanyin dadi shi kuwa yayo hanyar dakinsa na maida kaina ga kallo. Jimawa kadan ya fito ya shiga kicin bayan ya chanja suturar jikinsa zuwa doguwar jallabiya. Ban damu da sanin abunda zai aikata a kicin ba,a cewata ma,ai gwara kada ya matsamin ya barni na dan huta kafin hakimar tasa ta dawo. Hankalina ya nutsa sosai ga kallo saidai naji alamar ajiye kwalin a kusa dani. Hakan yasa na juyo na dubeshi,murmushi ya sakarmin yana kurbar lemon kwalin na Chi exotic dake hamnunsa,yayimin nuni da ido ga lemon da yake ajiye akan tebur kusa dani.
"Bismillah kina kallona,nasan rowa irin ta Meena bazaisa ta baki damar daukar abun sha ba. Bari na dan kwanta kafin nan da la'asar." Ya mike ya shige daki,nayi murmushi don nasan gaskiya ya fada. Meena rowan tsiya ne da ita,koda bak'i tayi sai sun nemi ruwa sannan ake basu balle akaima ga lemo. Na dubi kwalin lemun ina tunanin yaushe ma rabona dana samu yancin shan lemun kwali duk da a baya katon katon babu irin wanda Abba baya ajiyewa Mamma. Na dauka na bude na sha sosai,inayi ina kallo. Tsayawa nayi cak yayinda kaina yayimin nauyi,na ajiye kwalin lemun na dafe kaina ina mai runtse ido. A hankali na soma fita hayyacina,tun ina jiyo muryoyin dake fitowa a tv har dai na daina ji da ganin komai."