← Book details African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals Local reading mode
READING PART 26 OF 35

Sashe 26

African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals · about 8 min read

Daga haka ya fice, taso taji kowace mai sa'ar ce tayi nasarar samun namiji irin Haris? Da ace KB yana da kyawawan halaye irin na Haris da ta bugi kirji ta kira kanta mai sa'a. Saidai abun takaici ya zamana bashi da hali.....

'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(48)
Fuskarta ta bayyana tsananin damuwa da mamakin jin cewar wai
Haris da take zaman jira su karb'i lambar juna ya koma Kano.
Menene haka Haris yayi mata kodai mantuwa ce yayi? Inna dake
lura da ita tace
"Kin shirya zuwa gaida malam husseini daga can ki wuce gidan
mahaifiyarki,kuma kin cire mayafi kinyi zaman dirshan daga samun
labarin tafiyar Harisu. Kina nufin bazaki ba saboda shi?"
Baby ta kalli kanwarta humaira wacce duk ta shanye janbakin data
shafa mata a lebba kafin a sanyaye kuma ta janyo mayafi
wadatacce wanda ta dauka cikin kayan mamma data barsu a dakin.
"Banji dadi bane daya wuce batare da munyi sallama dashi ba.
Amma ba hakan na nufin bazanje ba. Taso muje Humaira."
Ta dauki wayoyinta fuskarnan ta baby babu walwala ta zura
takalminta mai tsini wanda sanyasu har sun zame mata jiki. Inna
dai takalmin take kallo cike da mamaki kodayake ta lura duk
takalma uku data zo dasu haka suke da tsinin dunduniya. Ta kasa
dai hakuri ta tofa
"Wai Tasleem baki tsoron wadannan takalman su karya maki
k'afa?"(Kamar dai yanda kawata Ummu Abdool ta sanya ta fad'i
cikin taron mutane koda yake farkon zuwanta birni ne👌)
Baby tayi murmushi
"Inna ai na rigaya na saba,inajin dadinsu sosai."
Inna ta tabe baki
"Oh,duk wannan tsawon naki neman k'ari kikeyi. Toh Allah Ya
tsare,sai kun dawo."
Ta amsa kafin ta fita rike da hannun Humaira wacce ta rigaya ta
mamaye zuciyarta.
Tayi mamakin samun Malam Hussein din tare da Liman a falonsa.
Ashe ma yana gidan? Suna ganinta fara'arsu ta k'aru inda Liman
yace "Ga jikar taka ai."
Cike da ladabi ta gaishesu suka amsa,Malam Hussein ya sanya
mata albarka kafin ta mike tayi musu sallama ta fita.
Duk da hakan saida ta nufi gidan ko Allah zaisa ta hadu da wanda
zai bata lambar Haris.
******
Alhaji Aliyu Hussein(mahaifin Haris, su shida iyayensu suka haifa.
Shine d'a na farko namiji,sai mace mai bi masa ta rasu, sannan
Kawu Usman,Kawu Bilal da autarsu Hajiya Barira dake aure a garin
Maradi,jamhuriyar Nijar da kuma Hajiya Mariya(mami,mahaifiyar
Kb)
Gaba dayansu mazan idan an cire Abba dake kano,suna zaune ne
anan gidan kowanne da bangarensa.
Fa'iza,Habiba 'ya'ya mata ne ga Kawu Usman,manyan mazan su
uku ne. Yasir,Abdulmalik(Babban yaya) da Faisal
Rahina,Badiyya da Atika 'ya'ya matane ga Kawu Bilal,rahina tayi
aure sauran Badiyya da atika wadanda sukayi candy. Bashi da d'a
namiji.
Sai kuma babbar diyar Hajiya barira ta fari kafin tayi aure na biyu ta
koma Nijar da zama,Zahra. Wacce ke a hannun kakarsu uwargida
kuma amaryar Malam husseini,Hajja Kubra.
Kyawawan yan mata saidai na wata tafi na wata,hakan bai hanasu
sakin baki wajen kallon wacce suka tabbatar ta ketaresu a komai
ba,wacce kamshinta mai sanyi ya soma ziyartar hancinsu kafin
kyakkyawar surarta ta bayyana a gabansu gami da zazzak'ar
muryarta wacce tayi musu sallama da ita.
Gaba daya kuwa yan matan sun had'u suna masu jimamin tafiyar
Haris wanda bai zab'i d'ayansu ba. Kada ma Zahra taji
labari,yarinya mai tsananin kunya da kawaici saidai a k'asan ranta
ba k'aramin so take yiwa Haris ba. Abunda batasani ba,daman Haris
a farko kafin yazo ya kudurtawa ransa matukar anyimishi dole ya
fito da mata cikinsu toh hakika yafi ganin dacewar zab'ar Zahra. Ya
lura akwai nutsuwa da tarbiyya tattare da ita duk da dai sauran ma
akwai saidai basu da kawaici kamarta. Ko jiya da suke shawagin
nan bai ganta ba saida yasa aka kirata suka gaisa. Wannan ba
karamin dadi ya yiwa Hajja Kubra ba ganin matukar dacen data
hanga tsakanin Haris da Zahra. Hakan yasa ta kudurta yiwa Malam
zancen.
Bayan gaisuwa ta sanar dasu itace tasleem. Zahra ta tareta da
murmushi
"Wow,kece d'iyar gwaggo maryama ta Kano ko? Duk sadda naje
gidanta bamu da hira sai taki. Tabbas kinyi kama sosai da
Humeme."
Kasancewar haka take kiranta,sukayi dariya gaba daya. Bayan
gama gaisuwarsu ta nemi gaisawa da Hajja Kubra,har cikin dakinta
Zahra ta jagorance ta,itama ta nuna murnar ganin Tasleem a karshe
sukayi sallama. Ta sanya Zahra yi mata rakiya sauran sashen kafin
ta dubeta har lokacin tana murmushi haka kawai taji Zahra ta
burgeta.
"Nagode 'yar uwata,bari na karasa gidan Mamma."
"Lah bazaki shiga gidan Malam Ibrahim ba?"
Cikin rashin sani tace "Waye hakan?"
Zahra tayi dariya "Mahaifin amininin Kawu Abba ne dake garin
Kano. Kawu Abba kuma mahaifin Yaya Haris ne."
Jin wannan bayanin,Tasleem ta jinjina kanta,ta hakikance gidan
kakannin KB kenan. Gidan yana kallon juna dana kakannin Haris
suka shiga.
*****
Matansa biyu,Hajja Badi'atu da Hajja Atine. Yaransa tara cif. Hajja
badi'atu tana da biyar yayinda Hajja Atine keda hudu.
Alhaji Idris(Babangida),mahaifin Kb shine babba. Sai Safinatu,
Aisha(mahaifiyar Haris),Bello,Abdulmalik(Baba karami). Ya'yan
Hajja Badi'atu kenan. Matan duka suna gidan mazajensu. Mazan
kuwa idan an cire Daddy suna nan agidan da matansu da yaransu.
Hajja Atine kuwa,Garba,Fatima,Hafsa da Zakari. Suma duk sunyi
aure sun hayayyafa.
******
Babu inda Zahra bata shigar da tasleem ba,a inda Tasleem ta rasa
ma da wanda Kb ke kama tsakanin iyayensa. Idan ta hangi
kamanninsa da Hajja badi'atu saita hango da Malam ibrahim.
Karshe Tasleem ta yiwa Zahra godiya suka kama hanya da
kanwarta wacce tayi wayon sanin gidan mahaifiyarta."
Sai lokacin ta kunna wayarta,da kamar mintuna biyar kiran Kb ya
shigo. Wannan yasa dole ta dakata a gefen wata bishiya domin
amsa kiran nasa....!
'YAR BARIKI

©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)

(50)

Hankalinsa idan yayi dubu ya tashi,Allah Allah yakeyi jirginsu ya tashi yaje ya nemi inda baby take ya dauketa koda ta halin k'ak'a ne. Shaf ya manta da dalilin zuwansa Kano akan matarsa ce,ana kiran masu tafiya Kano yayi zumbur ya mike yayi gaba.

Baby tana neman rainamishi hankali,shi kam bayajin zai iya rabuwa da ita a yanzu. Ko me za'ayi saidai iyayensa su amince su aura masa ita koda na watanni ukun ne yanda kungiyarsu tace idan yaso daga baya zai san yanda zai fiddata cikin shaid'anin kungiyar nan.

******
Da gudu ta isa ga Mamma wacce ke tsaye tana sauraron maganar Nura da humaira duk bata gama yarda dasu ba. Jin tasleem a jikinta tana kuka yasa ta tsaya cak,itama hawayen ne suka cika idanunta. Sallamar dattijon ta katsesu,duk suka waiga suna amsawa. Yayi tsai ganin bakuwar fuska,kafin ya jefo tambaya,nura ya amsata

"Adda tasleem ce fa Dad,'yar anti ta birni."

Fara'arsa ta k'aru,fari fari ne da silkin bak'i,dogo ne yana da jiki. Ganin Mamma ta nufeshi gami da amsar ledar hannunsa a ladabce ya fahimtar da baby lallai shine mijin Mammanta. Murmushinta ya fad'ad'u itama had'e da hawayen farin cikin ganin irin sauyin da Allah ya yiwa mammanta. Tun kafin yakai ga k'araso kusa da ita ta zube gwuiwoyinta k'asa ta gaisheshi

"Ina kwana Kawu."

Ya mikar da ita ta hanyar riko hannunta yana 'yar dariya

"Ashe bazaki bani matsayin uba ba tasleem? Toh ni kuma na daukeki matsayin d'iyata tun kafin na sakaki a kwayar idona. Kiyi kirana da Dad kema amma banjin dadin uncle dinnan."

Mamaki ya kamata tana dariyar farin ciki,kawai saita fashe da kuka,ashe wataran zata samu wannan soyayya irinta uba? Alhamdulillah.

Dad ya katseta ta hanyar duban Mamma fuskarsa ta cika da farin ciki

"Yau duk abunda za'ayi a gidan nan na fannin girke girke da shaye shaye ya zamana yazo daidai da ra'ayin d'iyata kada ayi abunda bataso."

Daga haka ya dubeni

"Menene abun kuka my daughter? Sai kisa naji kamar bakyayin uban dani."

Tayi azamar share hawayenta ta dubi mamma wacce murmushi kawai takeyi tana kallonta kafin ta maida dubanta ga Dad

"Ba haka bane Dad,kukan murna nakeyi."

Ya dafe kanta cikin murmushin yace

"Ya isa hakanan kada yayi yawa kuma. Bari na shiga ciki."

Ya mike ya nufi sama. Baby ta zauna saman kujera tana dariya tace

"Mamma nayi maki murna."

Ta harareta kadan,nura yaja hannun humaira yana fad'in

"Yar kanwata zo mu amso alawa wajen Dad."

Suka haye saman tare,Mamma da Baby suma saman suka nufa d'akin Mamma.
Ta dubi hannun diyarta

"Ya naga kamar hannun naki a kumbure?"

Ta d'an dubi hannun,ashe fa dazu da zatayi wanka ta fidda bandage din,ta dan tabe baki kadan

"Buguwa nayi kuma har yanzu yanamin zafi kadan kadan. Amma da sauki,mamma ya sunan dad din nawa? Ke daya ce a wajensa ne? Waye wannan nuran shima d'anki ne?"

Mamma tayi dariya
"Tambaya uku lokaci d'aya?"

Baby tayi dariya itama

"Allah kuwa mamma ke d'ince duk kin chanja kin k'ara kyau kamar baki da kishiya."

Ta fada don a zatonta wannan katon gidan bazai yiwu ace mata daya ciki ba. Kuma daman a baya gwaggo Hajara ta fadamata yana da iyali.

"Kema kinyi chanjawar data bani mamaki tasleem,kamar ba 'yar makaranta ba anya kina karatun ma?"

Mamma ta fada tana binta da kallon zargi. Tasleem ta diririce sai kuma ta basar da sakin 'yar dariya,mamma tayi tagumi ganin d'iyartata harda b'ulin hanci haka kawai jikinta yayi sanyi duk da tasan kwalliya ce.

"Kai mamma,muda muke karatu. Kuma fa shekara nawa rabonmu da juna kinga dole fa na chanja maki. Don Allah gayamin mamma."

Mamma ta sauke ajiyar zuciya

"Alhaji Kamal Hassan sunansa,kafin ya aureni yana da mace guda daya,Hajiya Aisha. Tana da yaranta manyan maza biyu,suna karatu a turai,sai budurwa d'aya,tana aure a Minna. Sai kuma nura wanda a wajen haihuwarsa Allah Ya dauki ranta. Tun bayan rasuwarta Alhaji yak'i aure har Allah Ya kawo mutuwar aurena ya amince zai aureni bayan da yazo gaida Liman ya ganni yace yana so. Humaira sunan matarsa taci muke kiranta hakan. Kinji tambayarki. Inaso kema ki amsamin tawa tambayar. Menene ainahin abunda ke faruwa? Jikina yana bani akwai abunda keda Abdullah kuke b'oyemin,hakanan nayi mamaki don ko d'azu munyi waya dashi bai bani labarin zuwanki Kazaure ba. Ya cemin mahaifinki na kwance tsawon watanni biyu baijin dadi shine ke d'awainiya dashi,duk sadda na tambayeshi ko kinzo dubashi daga makaranta sai ya hau yimin kame kame. Tasleem ko bakwa jituwa da yayan naki ne?"
Chapter 26 · 0% Book details