← Book details African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals Local reading mode
READING PART 6 OF 35

Sashe 6

African Union Internship Program 2025: A Golden Opportunity for Young African Professionals · about 8 min read

Kukan da Baby tasha a wannan daren ne ya sanya ta tashi da matsanancin ciwon kai. Bata fito daga d'akin nan ba saida tayo sallar asubahi ta kara kwanciya bacci,a takaice dai saida rana ta fito. Ta bud'e kofa ta fito,falon babu kowa kamar yanda tayi zato,Kb ya tafi. Ko a kanta bata damu ba,ita kam idan har zancen aure ne bazai tab'a samun goyon bayanta ba. Tabbas saidai alak'arsu ta yanke anan.

Kai tsaye dakinta ta nufa,tsayawa tayi cak,ganin Kb kwance yana bacci bayan ya rungume hotonta dake ajiye gefen gadon. A hankali ta karasa ta durkusa saitin fuskarsa tana duba,murmushi dauke akan fuskarta. Lallai ba karamin so Kb yake yi mata ba,duk da cewar nata zuciyar ba wani sonshi takeyi ba sosai. Tafi daukarshi a matsayin mai biya bukatarta. A hankali ta mike ba tare da tayi yunkurin tashinsa ba. Wanka kawai ta fad'a. Bayan ta fito ta iske har lokacin kb bai farka ba,mamaki ya kamata. Kodai baiyi bacci bane daren jiya. A sannu isa gefen gadon ta zauna kafin ta jijjiga gashinta,ruwa ya fallatsar mishi a fuska. Sannu sannu ya bude ido,kafin yakai ga cewa wani abu ta mike da sauri ta koma gaban madubi

"Ya kamata ka tafi gida kafin ustaz din naka ya nemeka."

Ta karashe tana murmushi,kb ya taso ya janyota ta mike tsaye suna fuskantar juna. A karshe ya zaunar da ita gefen gado shima ya zauna. Yanda ya karanceta ko kusa bata da fushi sosai,tana da saurin hucewa,(hum).

"Na bata ranki Babyna,amma daga yau nabar zancen nan tunda har bakiso,kinji?"

Tayi murmushi kafin ta sauya salon zancen nasu. KB bai bar gidan ba sai wajen goman safe,ya k'ara tabbatarwa kansa bazai iya rabuwa da Baby ba. Ta musamman ce. Cike da nishadi ya koma gidansa.

*****

Dattijai ne guda biyu masu kimanin shekaru Sittin da d'oriya,suna zaune a kayataccen falon gidan. Kowannensu ya sha babbar riga suna hira cikin nishad'i. Lokaci guda kuma fuskar Alhaji Idris ta sauya zuwa yanayin damuwa. Wannan yasa Alhaji Aliyu tsagaita dariya ya dubeshi

"Lafiya kuwa?"

Alhaji Idris ya sauke ajiyar zuciya

"Wallahi lamarin Harisu ya soma tsoratani Alhaji. Ace yaro yak'i zancen aure,har rana mai kama da yau ya kasa kawo mana zancen da zai sanyamu farin ciki? Babu ranar da bana rokon Allah,daidai da liman saida na sanarwa domin a taimaka mana da addu'a. Kaga fa har rukiyya anyi mishi a zatonmu aljanu ne saidai ko gezau babu. Anya tafiya zata yiwu haka?"

Alhaji Aliyu yayi murmushi

"Ka gafarceni Alhaji idris,zuwa yanzu na daina ganin laifin yaron nan nafi ganin laifinku na iyayensa."

Daddy ya dubi Abba da alamun rashin fahimtar maganarsa. Abba ya jinjina mishi kai

"Kwarai ma kuwa Alhaji Idris,wannan laifin bana d'anku bane,naku ne. Kada ka manta fa,yaron nan ba shine ya haifeku ba! Akan wane dalili ne zaku zuba mishi ido sai yanda yakeso za'ayi? Ga yan uwansa nan mata a Kazaure,wadanda sukayi karatun na addini dana zamanin don me bazaku samar mishi wata a can ba? Haba jama'a,yaron nan fa ba fin karfinmu yayi ba. Yau ga dan uwansa nan har ya soma tara zuri'a shi ya zauna jiran autar mata? A'a fa,gaskiya laifi yana wajenka Alhaji."

Daddy yayi murmushi

"Gadanga kenan,zamanin nan da kake gani ba'a yiwa yara auren dole,ba irin zamanin mu bane wanda ko fuskar matanmu bamu gani ba sai bayan an mik'o mana su gidajenmu. Wannan zamanin za'a kuntata rayuwar yaro ne kawai."

"Nima bance kuyi mishi dolen ba idi(ya fada cikin zolaya kasancewar sunan da yake kiranshi kenan a baya da kuma wasu lokutan na yanzu),ku turashi kuce yaje ya zab'a idan yaso sai ya sanar maku wacce ta kwanya mishi ko kuwa?"

Daddy yayi dariya

"Gaskiyane,sai ayi hakan toh. Fatanmu Allah Yasa mu dace."

Abba ya amsa da amin. Daga haka hira ta mik'a.......!

'YAR BARIKI

©Rufaida Omar

(14)

Misalin karfe sha biyu da rabi na dare,baby tafe akan hanyarta na zuwa birthdayparty na Hibba da saurayinta ya had'a mata. Taci kwalliya har ta gaji da had'uwa. Kid'a ke tashi kawai a motar,saidai cak motar ta soma kokarin tsayawa. Karshe ta tsaya cak akan titin daya kasance shiru tamkar babu mutane sai tsilli tsillin motoci suke wucewa. Ta buga sitiyari da k'arfi ganin mai ne ya k'are mata. Shaf ta mance cewar Dalal ta ari motar taje kasuwa da ita dazu,gashi babu alamun masu siyarda mai a kusa. Wayarta ta dauko,ta kira lambar Hibba,yana ta ringing bata dauka ba. Hakanan Manal da Dalal. Ta tabbatar dukkansu hankulansu yana wajen party. Taja karamin tsaki kafin ta soma duban hanya taga ko zata samu mai taimakonta.

Tafe yake a hanyarsa ta komawa gida daga meeting da yayi (attending) na aikinsu. A gajiye yake saboda ya mance rabon da yakai war haka baiyi bacci ba. Hannu ya gani an sanya mishi ana tsayar dashi. Ya duba dakyau,mace ce,kuma da alama motarta ce ta sami matsala. Ba tare daya lura da ko wacece ba,ya samu waje ya faka domin shi ya dauka ma kabila ce duba da yanayin suturar dake jikinta na gown marar hannu ga kuma gashi a waje.

"Sannu,please ko..."

Sauran maganar ya makale a fatar bakinta ganin Haris. Shi kanshi baisan ita bace saida ya fito daga cikin motarsa suka nufo juna.

Zallar kyawun fuskarsa ta k'ara fitowa a lokacin daya tamketa,ya juya da niyyar komawa motarsa ya tafi. Tayi azamar tarar gabanshi,cikin marairaicewa tace

"Domin Allah ka tausayamin mana bestfriend,wallahi ka tafi ka barni anan za'a saceni ne. Man motata ya k'are ne."

Sai lokacin ya lura ashe harda hudin hanci gareta,ta maka barima fara akan hancin. Ganin yanda ta marairaice ne ya sanyashi kauda kansa,baice komai ba ya gifta ya shige motarsa. Har ta fidda ran cewa zai taimaketa taji yana mata hon. Cikin sauri ta dauki wayoyinta da fos dinta. Ta rufe gilasan motar ta kulleta ruf sannan ta nufi motar tasa. Sai lokacin hankalinta yakai ga lambar motar,nan da nan ta tunano inda ta santa. Ashe shine ya taba binta a guje sadda ta tuk'o motar Kb. Murmushi ta danyi kafin ta zagaya ta bud'e gaban motar ta shiga. Nan da nan kamshinsu ya mamaye motar, har suka rasa fahimtar na wanda yafi tashi.

"Nagode bestfriend."

"Haris sunana."

Ya fada cikin fusata. Ta dubeshi ganin yanda yayi kicin kicin,ta kad'a idanuwanta

"Ok,Haris."

"Ina zan kaiki?"

"Tahir."

Baisan sadda ya dubeta ba,itama har lokacin idanuwanta na kansa. Saidai baice komai ba ya fisgi motar a fusace,gudu yakeyi kamar zai tashi sama,baby kuwa ko a jikinta. To yau ya soma sanin gudu a mota ne? Kallonsa kawai takeyi cike da mamakin irin kyawu na Haris. Bayan haka ma,tafi mamakin yanda duk haduwarta ko kallo bata isheshi ba. Toh ita kuwa iyakar zamanta a rayuwa bata taba ganin namijin daya ganta bai kara kallo ba saboda zubin da halittar da Allah Yayi gareta.

Taka burki da yayi,ya maidota hayyacinta. Wannan ya sanyata kauda kanta daga barin kallonsa. Ta duba,kwarai sun iso kofar hotel din.

"Rayuwar da kika zab'awa kanki ina mai tabbatar maki akwai ranar k'in dillanci. Sam,wannan bai dace da musulma ba. Kin maida kanki kasuwar da kowa yake da damar shiga. Kin zubda k'imarki ta d'iya mace akan son duniya wanda bazai kwatoki daga azabar Allah da kwanciyar kabari ba. Kiyi tunani,matan aure nawa kika dauki hakkinsu wajen nasarar dauke hankulan mazajensu a kansu? Allah bazai kyaleki ba,da rai da lafiyarki muddin baki tuba ba sai kinga sakayya. Idan zina abun yi ce kije kiyi tayi,ke da karya baku da bambanci."

Yayi shiru yana mai duban titi,murya a kausashe ya kara magana

"Get out."

Kamar wacce aka daskarar,gaba daya ta gaza motsi. Bata ce mishi uffan ba. Jin tayi shiru ya sanyashi juyowa da niyyar fad'a,abun mamaki hawaye ya gani suna zuba daga kwayar idanun Baby. Tayi azamar sharesu,murmushi ta k'ak'alo ta jefeshi dashi

"Nagode da taimakon da kayi gareni,Allah Ya kaika gida lafiya."

Daga haka tayi saurin ficewa tayi ciki,saidai kana dubanta zaka fahimci a sanyaye take ko daga yanayin tafiyarta. Ko kadan bata bashi tausayi ba,saidai har ya tafi yana mamakin yanda akayi kalamansa suka sanyata hawaye. Karshe dai ya watsar a cewarsa,munafunci ne. Wanda yayi nisa bazai tab'a jin kira ba....!

'YAR BARIKI

©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)

(15)

"Kiyi tunani,matan aure nawa kika dauki hakkinsu wajen nasarar dauke hankulan mazajensu a kansu? Allah bazai kyaleki ba,da rai da lafiyarki muddin baki tuba ba sai kinga sakayya."

Har zuwa yanzu da take kwance a gadon d'akin na hotel d'in,ita kad'ai. Wadannan kalaman ke yawo a kwakwalwarta. Damuwar da ta yawaita a zuciyarta ya hanata zuwa bangaren da ake fatin hibba,hakan yasa ta kama d'aki da zummar ta kwana da safe tayi gida. Batayi iya runtsawa ba kalaman Haris sun shigeta matuka. Ta tuno yanayin fuskarsa wanda ke nuni da tsantsar takaicinsa na halin da rayuwarta ke ciki. Bata taba cin karo da wanda ya nuna kyama a harkar rayuwarta ba kamar shi.

"Nan da kike ganinsa ustaz ne,ya fiye takura kansa baison ya more rayuwarsa."

Kalaman Kb akan Haris suka fad'o mata. Tabbas ta yarda da hakan,Haris kamilin mutum ne wanda bai sha'awar rayuwar da suke ganin itace ta arziki a garesu.

*****

Da zarar ya runtse ido,ita yake gani. Bai manta sa'adda ta dubeshi fuska dauke da ruwan hawaye wanda yasan na munafunci ne. Amma meyasa ta kasa b'acewa tunaninsa,bai manta sadda ta fice a motar ba jiki a sanyaye. Toh hakan yana nufin taji nasiharsa ne ko kuwa? Amma ai inda ace ta dauki zancensa,babu abunda zaisa ta shiga hotel d'in. Ya dafa goshinsa yana mai runtse ido,bayason ya dunga tunanin wacce bazata amfaneshi da komai ba. Hakan yasa ya mike tsam yayo alwala ya soma nafila duk domin kaucewa tunanin wacce ko sunanta bai sani ba.

******

"Gobe zan koma Abuja,inaso muyi wata magana ne."

Ya tsayar da rubuce rubucensa sannan ya dago fararen idanunsa ya saukesu akan Kb,fuska ba walwala.

"Na'am,ina sauraronka."
'YAR BARIKI

©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)

(16)

Kb ya numfasa yana mai sassauta muryarsa,ba tare daya yarda ya dubi kwayar idanun Haris ba ya soma magana
Chapter 6 · 0% Book details