← Book details Secondary School Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 25 OF 42

Sashe 25

Secondary School Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"To ai sai ki kira wanda kika zo wajan su amma ni bamuyi dake zaki zo ba kuma bansan ya zanyi dake ba gaskiya "Baby ko dai baka gane mai magana bane jamsy ce fa..kuma da kake maganar nakira wanda nazo wajan su wajan wa zani to idan ba kaiba suprise din ka nayi fa "Gaskiya bana bu ata idan inason ganin ki dole kinsan zan nemeki muma ahalin yanzu ma ni aiki ne dani bani da ishashshan lokacin kuma Rufaida bata da lafiya so kinga zama gidan mu bai kama kina kenan Daga haka ya katse wayar kasan cewar ya araso wajan aiki Sosai maganar Ibrahim ta atawa jamsy rai bata san me yake nufi da ita ba kenan tayi wahalar banza yake nufi ko me!kuma ma da yake maganar Rufy ba ta da lafiya meye nata acikin to Shawara ta yanke akan ta rabu dasu shi sai weekend ta neme shi su hadu *********** Yanzu haka cikin indo yayi girma sosai ya shiga wata na takwas ta dawo zama da yar tashi da yar zuwa yanzu inna ta daina fushin da ita sabida yanzu ta zama abin tausayi,sai dai abinda inna bata sani ba har yanzu indo tana ma'amala da habu sai yanzu ne da cikin ya kuma girma ta hakura shima sabida idan sunyi fama take da ciwon baya Zaune take a tsakar gida tana cin abinci,kallon inna tayi tana fa "Yanzu kenan inna idan na haihu shike nan nima na sama umma kuma zan dinga bawa yarona nono yana sha ko? Kallon ta inna tayi cike da mamakin shashancin indo wata kon ita burin ta ace mata umma kuma ta bawa yari nono yasha shi kawai take so bata san hadarin dake tare da haihuwar ba ko gudun abin kunya ita duk wannan bai dame ta ba.... "Inna nayi magana kinyi shiru ko ni bazan ba yaron nawa nono ba kuma ma ai naga baya fitar da ruwa yanzu ya zanyi kenan idan na haihu? "Banason shashancin da hauka indo ke duk wannan masifar da kika samu ba itace gaban ki ba kawai ki bawa yaro nono kike so ko...to indai haihuwa ce gaki gatanan zakici gidan kune Inna ta fa a cike da acin rai Shiru indo tayi tana suna nin maganar inna ita dai tasan batayi abinda za'a mata fa a haka ba amma ji yadda inna take mata bala'i kuma dai ane idan ta haifa dole yace mata umma kuma ta bashi nono ita ma ************Kwanan ta uku sannan ta kuma kiran Ibrahim a waya zuwa lokacin gaba aya ya manta da babin ta sabida aikin da ya shamai kai a kwana kinnan Ta nemi su hadu a wani wajan sha atawa kuma ta amince zaije dan haka take ta shirye shiryen yadda zata ja hankalinsa idan yazo tayimai maganar aure Bayan sallar magariba ya isa wajan da sukayi da shi zaune ya same ta tasha riga da wando matsatstsu sai wani yau i take ita ba ku ewa ba Tasowa tayi zata rungume shi ya daga mata hannu "kinga baki ganin cikin mutane muke ne Ya fa a yana zama cikin daya daga kujerun wajan "Kiyi sauri muyi maganar da kika ce sabida ina sauri ne zanyi ba "Nikam gaba aya na kasa gane kanka baby kwana biyu duk ka canza kamar ba kaiba gaba daya baka nuna farin ciki da gani naba ko kuma ka daina sona ne bansani ba ? "Basai sonki ne banayi ba jamsy amma yaka mata kigane nazo Lagos aiki ne bawai soyayya ba dan haka bani da ishashshan lokaci "Okay to naji,tunda haka ne to kawai ka aure ni mana ba shike nan ba kaga daga nan sai na dinga taya ka wasu aikin naka koya kace! "Eh naji amma gaskiya wannan abun bazai yiwu ba gaba aya yaushe nayi auren yanzu a kuma jin zanyi wani ai kinga da matsala "A'a toba zai ka fa a musu matar ka ba budurwa ka aura ba cutar ka akai kaga shike nan za'a bamu damar auren junan mu Ta ara sa maganar tana fari da ido cike da hango alamar nasara "Gaskiyar magana hakan bazai yiwu ba jamsy koba komai mahaifin Rufaida aminin Baba nane to bazan iya tozar ta shiba ko wani daga cikin a halinsa "Ban gane ba to yanzu me kake nufi zaka cigaba da zama ne da wacce take neman maza koya dan asara duk wani uba ai yanaso ya samawa yaranshi uwa ta gari koba haka ba Ta fa a tana tsare shi da ido dan taga yanayin fuskar shi Shiru yayi yana tunanin gaskiya ne maganar jamsy uwa ta gari ta ke bada yara na gari kuma a gaskiya kwata kwata Rufy bata dace da shi ba Kallon ta yayi kamar zai magana sai kuma yayi shiru "A'a baby kayi shiru kace wani abu mana "Haka ne maganar ki amma zanje gida inyi tunani duk yadda ta kama zamuyi waya Daga haka ya tashi yabar wajan zuciyar shi cike da tunani kala kala akan maganar jamsy Ihun farin ciki tayi ganin alamun nasara a tafiyar tata Dan haka tace "Muje zuwa. . SECONDARY SCHOOL (Love& romantic story) Shalele ce Paid page 57&58 __________Sosai maganar da sukayi da jamsy ta sashi tunani a haka har ya dawo gida, lokacin da ya shigo Rufy ta cikin aeke mai abinci dan haka tamai sannu da zuwa sannan ta shiga dakin ta Da kallo ya bita sosai yarinyar wani zubin take jefa shi cikin tunani yadda take a nutse haka bata da haya niya baza'ai tunanin zata aikata ba Haka dai ya kwana yana wannan tunani da jamsy ta ma alamai Washe gari kuwa yana cikin karyawa hafiz yazo tare da matar shi da niyyar zata wuni wajan Rufy sosai Rufy taji da in hakan sabida ita kanta ta gaji da zaman shirin da take fama dashi gaba aya ka aici ya ishi rayuwar ta Bayan ta fitar su Ibrahim wajan aiki sosai Rufy ta saki jikin ta da matar hafiz suka sha hira a wannan yinin da sukayi tare sosai matar hafiz ta kuma fahimtar abubuwa da yawa akan Rufy Dan tunda mazan su suka fita kwata kwata batayi maganar Ibrahim ba ko sau aya haka kuma bataga ya kira ta awaya ba ita ma kuma haka sai abin ya bata mamaki dan haka ta kasa shiru tayi niyyar tanbayar ta ko suna da wata matsala a cikin zaman su "Nikuwa sister dan Allah na tanbaye ki wani abu idan ba damu ? Kallon ta Rufy tayi kafin tace "A'a ba damu tanbaye ni Allah yasa na sani "A'a wallahi kin sani sai dai idan zaki oye min Dama wani abune yake ban mamaki keda Ibrahim kamar ba auren saurayi da budurwa ba, kamar ba masoya ba,kwata kwata bakwa nuna aunar junan ku,ba nuna kulawa,bare ku dinga kewar juna Tunda nazo kwata kwata bakiyi maganar Ibrahim ko sau aya ba Ni kuwa nayi maganar hafiz yafi sau ashirin ga wayar da muke akai akai ya irani ko na irashi dan muji ya kowanne mu yake amma ke ko sau aya baki kira Ibrahim ba shima kuma haka Sannan da zasu tafi ba nuna alamar zakiyi kewar shi hasalima ko ra ashi bakiyi ba kanki na asa kika ce Adawo lafiya shike nan Shine abun wake bani mamaki wannan wanni irin aure ne haka Rufy da tayi shiru tana sauraran abinda matar hafiz take cewa murmushi tayi wanda ya tawo tare da hawayan da ya taru a idon ta Kallon ta tayi tana fa "Na yarda dake na auke ki kamar ar uwa ta dan haka zan ba i labarin rayuwa ta yau tare da abinda ko iyaye na basu sani ba Sunana Rufaida amma friend dina suna cemin Rufy ni ar Kano ce shekara ta Ashirin da biyu............. Sosai matar hafiz tayi kuka ta kuma tausa yawa Rufy fiye da tunani tabbas Rufy ta fa a sharrin awa ne kuma gashi yanzu taba bibiyar lamarin ta Kallon Rufy tayi da fuskar ta tayi jaga jaga da hawaye da majina tayi kuka kamar ranta zai fita "To yanzu ina ita jamsyn take ne? Matar hafiz ta tanbaya cike da neman arin bayani "Bazan iya ce miki ga inda take ba nasan dai mun barota a airport ranar da zamu tawo kuma ita ce wadda ta kira Ibrahim ranar da ina asibiti "Shike nan aniyar ta ta bita amma yanzu ba zamane ya kamaki ba dole ne kisan yadda zakiyi ki janyo hankalin mijin ki zuwa gare ki koda kuwa ta kasan ce ya auri jamsyn ya kasance kema kina da matsayi a zuciyar sa bawai kiyi ta tafiya a matsayin bora ba "To taya kike ganin zan samu wannan matsayin duk macen da kika ganta cikin jin dadi a gidan mijin ta to takaimai budurcin ta ni kuwa fa ! Kallon ta matar hafiz tayi tabbas abinda ta fa a gaskiya ne to amma itama idan taji gyara komai zai dawo dai dai "Karki damu zamuyi gyaran jiki wanda zai sa wajan ya matse kamar ba'a ta a shiga ba kuma dole ne ki san yadda zakiyi ki jawo hankalin mijin ki domin ko baya sonki to tabbas akwai tausayi tsakanin ku kinga nan ma wata nasarar ce Dan haka yanzu abinda zamu fara da shi shine gobe zamuje siyayya dole ki dena zama da wadan nan hijja ba zamu siyo ananan kaya domin sune zasu zama na sawar ki indai yana nan ananan kaya kuma gaskiya bazan iya sawa ba idan yana nan bare kuma na fito Rufy ta fa a kamar zatayi kuka "Ai kuwa ya zaman dole idan har munaso mu cimma bu atar mu domin duk taurin kan namiji yaga kina jujjuyamai wallahi sanu sanu zai sakko Sannan zaki fara kokarin yin hira da shi ta hakane shakuwa zata shiga tsakanin ku ke da shi To haka dai suka ara sa wannan yinin suna tattana yadda za'a samu mafita sai dai a kwai abubuwa da yawa da Rufy take ganin baza ta iya ba Da yamma tayi tare suka shiga kitchen sukayi tuwan semo da miyar ku ewa,sannan matar hafiz tasa aka dafa shayi yasha kayan amshi sabida garin da sanyi sanyi ***********Wunin yau gaba aya sai a hankula yayi aikin
Chapter 25 · 0% Book details