← Book details Rufaffen Duma Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 19 OF 28

Sashe 19

Rufaffen Duma Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"An samo su amma gaskiya dai ana buƙatar ƙari sun yi kaɗan. Tun bayan wancan fallasar iyaye suke taka tsan-tsan akan kilace yaransu."

"To me kuke jira? Ai aiwatar da ɗaya aikin ta hanyar kwamushe su,a rikitar da ƴan gari su kwaso mana ƴan matan. Babu wanda zai zargemu."

"Daɗina da kai akwai ƙwaƙwalwa mutumina."

"Wancan harƙar fa an gama?"

"Akwai tsaro a arear amma muna ta tsara yadda zamu yi mu haƙo kayan."

"Ya kamata, DSP, jibi makaman nan da kuɗaɗen zasu shigo a rabawa yara a ci gaba da gashi. Hakin ka ne ka kula da shigowarsu lafiya. "

"An gama Boss."

"Zaku iya tafiya. Taro ya tashi."

Haka duk suka watse daga wurin.

[9/12, 10:02 PM] Ummulhair S Panisau: RUFAFFEN DUMA.
Ummulkhair S Panisau.
(Khairatup)
Karamci Writers Association.
Wattpad:Khairi_muhd
Arewabooks:Khairatup01

15

BIRNIN GWARI.

Ƙauyen Birnin Gwari kusa da kan iyakar Kaduna ne. Iska na kaɗawa, ƙananan yara na rawa a bakin wutar da aka kunna.Ƴan mata kuma suna zaune kashi-kashi suna hirar da ta shafe su.

Kawai sai jin ƙarar babura suka yi, wanan karon ƙarar ba ta babur biyu ko uku ba ce ƙarar baburan da yawa. Ji kake vrrrrrrrrrrrrrrm suka faɗo cikin ƙauyen kamar guguwar hamada. Fuskar maharan na lulluɓe da farin ƙyalle,da bindigu a hannunsu.

Jagoransu yace "ku kwashe su gabaɗaya kada ku bar ko guda ɗaya amma ku tuna kar ku kashe kowa."

Tuni kowa y firgita aka soma gudu ana ihun neman ceto ai kuwa jagoran ya saki harbi a iska aka kuma ruɗewa. Ƴan mata suka firgita,suka fara gudu,amma ƙarar harbin saman da yayi ya sa kowa ya tsaya cak a inda yake cike da fargaba da tsoro. Haka aka dinga saka ƴan mata suna hawa babur ko wann babur mace biyu ake ɗorawa cikin kuka da rawar jiki.

Haka suka kwashe ƴan mata ba tare da sun kashe ko sun daki kowa ba suka tafi suka bar su da hayaniyar kuka kawai.

Bayan tafiyarsu ,Dukansu suka zauna a ƙasa shiru kamar za a yi musu shari'a, ɗaya daga cikin mahaifin wanda aka ɗauka ya rarrafa ya zauna,ya dafe kan sa yana kiran sunan Allah cikin kuka.

Wani matashin saurayi ta miƙe yace "Ba zamu yi shiru ba! Sai mun sanarwa ƴan sanda ,sai mun bi sawunsu ko da kuwa sahun zai kai mu dajin Falgore."

Kowa yayi na'am da zancen saurayin amma cike da tsoro fal a cikin zukatan su. A daren yau dai ƙauyen ya koma musu tamkar makabarta.

Washegari!

Ina kitcen ina haɗa shayi saboda ciwon kai da ya ishe ni. Mama ta shigo da waya ta a hannunta.

"Amshi ke an ishe ni da kiɗin waya."

Maryam ta amsa tana dariya. A kunne ta kara ganin Shehnaz ce ta ke kiran ta.

"Madam!"

"Ana nan ana jiran ki maza ki shigo zaku tafi ɗauko rahoto a Birnin Gwari an sace ƴan mata sama da ashirin a daren jiya. Ina son jaridar mu ta fara wallafa labarin."

"To Madam."

Tana ajiye waya ta koma falo cike da tunani. Bayan zuwan ta gidan yari a daren kuma sai a sace ƴan mata sama da ashirin me yasa? Da gaske suke ashe da suka ce basu ba ne mastermind ɗin na nan daban. Wai duk me yasa ake wannan hare-haren ne? Ba zata samu amsarta ba sai in taje Birnin Gwari.

A gurguje ta shirya ta ɗauki duk wani abu da take so tayi sallama da Mama tana sa mata albarka.

Daga can Global Times aka kwashe su don zuwa wurin da lamarin ya afku.

Ƙauyen ya cika da ƴan sanda sai tsirarun ƴan jarida.Tunda suka sauka Maryam ke bin ko ina da kallo musanmman ma jam'ar da aka kwashe ƴa'ƴansu mata abin tausayi. Kallo ɗaya zaka yi musu ka ga zallar tashin hankali a tare da su da kuma raɗaɗin da suke ji na rashin yaransu a gabansu.

Babu shakka Maryam na ɗaya daga cikin ƴan jarida mai kwazo da kuma ƙarfin hali ba wai aikin take yi don kuɗi ko suna ba,aikin take yi don tana son tayi kuma don tana son gaskiya tayi halinta. Wata dattijuwa ta samu a zaune ta rafka tagumi abin duniya ya ishe ta.

Maryam ta saita ƙaramar kyamarar ta a hannunta tace "Baba ko za ki gaya min abinda ya faru? Ina son na san komai kuma nayi miki alƙawarin kai koken ku inda duniya zata ji kuma a taya ku nemansu."

Dattijuwar nan kuwa rai-rai ta fara zayyana mata labarin yadda abin ya wakana tun zuwnasu har harbin fark da yadda aka kwashe ƴan matan da kuma hanyar da suka bi suka wuce ta nufi Kaduna-Birnin Gwari expressway. Maryam ta rubuta wannan bayanan kaitsaye zuwa ofishin DPO a Kaduna.

Wani abokin aikinta Aminu yace" Maryam ,wannan lamari ba ƙarami ba ne. Wannan hanyar ta Birnin Gwari ce duk wanda ya san ta ,ya san haɗarinta. Kina da tabbacin za ki iya shiga cikin wannan binciken?"

"Aminu idan bamu shiga ba ,wa zai kare waɗannan ƴan matan? Zan bi wannan al'amarin har sai na gano inda suke."

"Yanzu muje ofishin ƴan sanda mu samu DPO, dole ne mu bayyana musu abinda muka samo muka kuma gano. Hakan zai taimaka wajen bincike sosai.A hasashensu ma kamar dajin kuyello, aka kai ƴan matan kusa da iyaka da da jihar Zamfara.

Wannan ba rahato ba ne kawai, wannan babban labari ne da tonuwar shi zai girgiza ƙasa gabaɗaya.

*

Sam yau bata ji daga wurin Muhammad ba. Daman ita ke neman sa. Ta tari adaidaita sahu don komawa ofis kiran Shehnaz Ahmad ya shigo mata. Bata yi wata-wata ba ta ɗauki wayar kuwa. Tun kan tace wani abu ta soma yi mata magana cikin fushi.

"Wa ya ba ki izinin kai rahato station? Aika ki nayi ki kawo min rahoton don mu wallafa ba cewa nayi kije can ki nuna iyayin ki ba. Yaushe za ki fara yin aikin ki kamar sauran ne?"

"Ba laifi ba ne don na kai rahoto satation ba, lafiya da kuma samun waɗanan ƴan'matan da aka sace shi ne a gaba ba wai mu wallafa a jarida ko mu haska ba.Ni ƴar jarida ce na yarda amma kafin nan ni ƴar adam ce kamar ke kamar su kamar kowa."

"Za ki yi bayanin wannan abinda kika aikata ki dawo nan da mintuna ashirin in ba haka ba yau sai kin bar aiki."

Maida wayar cikin jakarta tayi. Ranta cike da tunane-tunane fal ranta tana mamakin yadda rashin gaskiya da son zuciya da yaɗa labarai ya kwashe son gaskiya a doron duniya kowa TRP yake so ba a son ainihin gaskiyar magana.

Lumshe idanuwanta tayi cike da gajiya. A hankali take mayar da numfashi.
Ita fa ta sani zuciyarta ta ƙuna, kuma ta sani ba ita kaɗai ba ce take samun matsala daga wurin ubangidanta ba, amma wannan karon, mahanar Shehnaz ta shige ta fiye da sauran lamura. Wannan fa magana ke ta yara mata da aka kwashe an rasa ina aka kai su amma ita ta rahoton kawai take. Mtsw ta saki tsaki ta sa hannu tana murza idanuwanta. Mai adaidaita sahu na sauke ta ta sallame shi ta shiga cikin farfajiyar ma'aikatar ta su.

Kallo ta ga ana bin ta da shi hakan yasa ta gane akwai matsalar da gaske dai. Ko kwankwasa ƙofar bata yi ba ta tura ta shiga dake ita ma a sama take fuskokin mutanen ƙauyen kawai take gani na mata gizo yadda suka kasance hopless and tired akan lamuran duniya gabaɗaya.

Shehnaz na zauna a kan kujera ,hannunta riƙe da biro tana sa hannu a kan takardu tamkar ba ita bace yanzu ta kirata tana mata masifa ba.

"Na dawo." Ta faɗa a hankali amma da murya mai cike da ƙwarin guiwa.

Shehnaz ta ɗago kai ta kalle ta,idanuwanta suka nuna mamakin irin sautin da tayi amfani da shi wurin yi mata magana ba shakku ba fargaba.

"Bayanan fa?" Ta tambayeta kaitsaye ita ma.

Kujera ta ja ta zauna ba tare da an bata izinin zaman ba. Haɗe hannuwanta tayi ta ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya.

"Madam Shehnaz wannan fa ba labari ba ne da za mu buga don mu samu kuɗi ba ne. Na ga tsoro da tashin hankali a cikin idanuwan iyayen yaran nan da aka kwashe,na ga yadda iyayensu suke roƙon Allah suna kuka da hawayensu."

"Bayani nace ki bani ba wa'azin ki nake son ji ba."

"Idan na dawo ofis don na rubuta labari kamar ba komai ne ya faru ba ,to ban yi aikin da zuciyata ke so ba."

Shehnaz ta kama haɓa tana kallon ƙarfin halin Maryam. Sai da ta gama nazarin ta tsab sannan ta janye idon ta gefe sannan ta ce mata. "In na fahimta kin fi so ki rasa aikin ki saboda abubuwan da ba ruwanki da su?"

"Idan aikin jarida shi ne kawai naɗa labarai domin samun riba ba don kawo sauyi ba, to ban san me amafanin shigata wannan sana'ar ba." Ta miƙe tsaye.

Shehnaz ta yi shiru na wasu sakannni bata ce komai ba sai da ta ga da gaske zata fita daga Ofis ɗin sannan tace "Maryam"

Maryam ta tsaya a bakin ƙofa.

Shehnaz tace "kin tabbata kin yarda da kan ki muma za ki iya kare kan ki?"

"Na tabbata.Ina tare da gaskiya babu abinda zai same ni. Kuma zan ci gaba har sai na gano waɗanda ke da hannu a wannan kwashe yaran."

Ta fita daga ofishin ba tare da ta kalli ko ina ba. A zuciyarta ta riga ta yanke shwarar wannan lamarin ba labari ba ne a wurin ta kawai gwagwarmaya ce."

Kan teburin ta ,ta koma ta zauna ,wayarta tayi ƙara. Sunan ta kalla a hankali ta furta "DSP Hamza."

Ɗaukar wayar tayi tace "Yallabai."

"Muna da wata shaida na san zai taimaka miki."

"Yallabai. Me aka samu?"

"Mun kama wani yaro ana zargin da sa hannunsa da satar yaran nan a daren jiya."

"Kai Yallabai na ji daɗin wannan labarin."

"Za ki iya zuwa?"

Tuni ta suri jakarta ta miƙe a lokaci guda tace "Yallabai na taho ma."
Chapter 19 · 0% Book details