Sashe 16
Rufaffen Duma Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani mutum ne ya fito daga wani ɓari na gidan ya tsaya a gabansu tsam fsuskarsa a rufe take da wani baƙin kyalle . Bai yi wata magana ba kawai ya janyo wuƙa a ƙugunsa ya kai wa Maryam hari.
Smith ya yi saurin dakatar da shi ,suka fara kokawa a cikin duhu,ƙarar ƙarfe na buguwa da bango ko ƙasa.Tuni Maryam ta takure a gefe guda tana neman lambar wayar Muhamamd shi ne kaɗai ya faɗo mata a ranta.
Aikuwa cikin sa'a ta same shi nan tace mai "kai taimaka mana muna cikin matsala zasu kashe mu. "
"Kina ina Maryam ke da waye?"
A firgice ta gaya mai adireshin ta kashe wayar. Fitilar wayar ta haska nan ta ga Smith na riƙe da hannun maharin,amma bai yi aune ba ya wafce hannunsa cikin azama ya soka wuƙar a gefen cikin Smith.
"Smith" Maryam ta faɗa da ƙarfi." Da gudu tayi wurin shi amma maharin yayi tsalle ya fice ta taga.
Smith ya durƙasa ƙasa hannunsa riƙe da wurin da aka soka mai wuƙar jini na zuba kamar an yanka kaza.
"Maryam.." ya faɗa da ƙyar cikin ƙarfin hali ki tafi ,ki gudu zasu dawo na ji kamar an sa gas yana likin Maryam go save yourself."
"No! No! Smith ba zan bar ka ba. Tare muka zo tare zamu tafi." Ɗan kwalinta ta saka ta danne wurin da jinin ke zuba tana hawaye. "Ba zan bar ka ka mutu ba Smith."
Tashi tayi da ƙyar ta samu ta lallaba ta ja Smith ta soma fita da shi daga gidan ya mata nauyi amma haka take jan sa tana kuka tana jan numfashi kafin su ƙarasa fita ya suma.
Suna fita gidan ya tashi ji kake boom ƙara mai rikitarwa. Faɗuwa tayi a ƙasa ita da Smith ɗin duka tuni jikinta ya soma karkkarwa tayi kaca-kaca da jinin Smith. Da tuni suma yanzu sun ƙone a cikin wannan gidan? Tuno hakan kawai na sa ruhinta ya soma rawa.
Ji tayi kamar magana a bayansu haka ana "Ku nemo su kamar fa sun fito basu ƙone ba boss ba zai bari ba." Tana jin haka kuwa ta zare takalmanta a hankali ta dinga jan Smith daga tsallake suka raɓe a bayan wata bishiya mai yalwar ganyayyaki. Daga nan tana kallan yadda tiƙa-tiƙan mazan ke nemansu a cikin duhu. Kawo yanzu tana cike da da na sanin kin bin shawarar Smith ga shi yanzu ta yi sanadin da aka soka masa wuƙa. Da sauri ta kama pulse ɗinsa taji tana harbawa suma yayi. A tsorace take sosai.
Ta gama karaya cewa yau kam ba iya Smith ba ita kanta ba zata fita daga wannan wurin da ran ta ba.
Sai dai ƙarar mota ce ta shigo layin ta kasa kunne tana jin yadda motar ke antaya gudu.
Maharin kuwa juyawa yayi ya kalli ɗaya abokin nasa yace "Kai waye yake shigowa nan?"
Motar kuwa tsayawa tayi cak a gaban gidan Paul da ke kamawa da wuta.
Muhammad ya fito daga cikin motar da baƙar jacket a jikinsa ,hannunsa riƙe da ƙaramar bindiga yana kallon yadda wutar ke ƙara girmama. Tuni ya ji zuciyarsa ta tsinke a tunaninsa Maryam ta ƙone a ciki.
Juyawa yayi a fusace ya kalli maharan guda biyu yace "Ina Maryam? Me kuka yi mata azzalumai?" Ya nuna musu bindigar hannunsa.
Ɗayan ya gane shi ya yi tsit. Ɗayan kuma yana ƙoƙarin yayi magana sai kuma ɗayan ya riƙo hannunsa yace masa "Mu gudu wannan ba sa'anmu ba ne."
"Amma waye shi ɗin?"
Muhammad ya saki harbi a iska. Maryam ta kiɗime ta saki ihu cike da tsoro.
Da Muhamamd da maharan inda suka ji ihun suka kalla bayan bishiya.
Tuni suka soma musayar wuta a junansu. Wata mota ta kuma shigowa ita ma. Bouncers ne a ciki da bindigu. Ba sa son harbin Muhamamd su abinda suke so Maryam ce.
Muhammad ya lura suna da yawa kuma suna da makamai kawai ya yanke shawarar komawa cikin mota harinsa shi ne ya je inda Maryam take.
Yana shiga ya yi ribas kamar zai fita ne. A nan suka daina harbin dukansu suka tsaya kallonsa. Basu yi aune ba ya ci wani burki ya afka ciki da gudu daidai bishiyar ya tsaya ya fito ya tsaya a gaban motar ya ga Maryam duk tayi hurjajjan ta fita daga hayyacinta.
"Maryam ku shiga ciki."
"Ya suma."
"Waye?"
"Smith,abokin aikina tare muka zo yana ƙoƙarin ceto na suka soka mai wuƙa a ciki."
"Maryam sau nawa na gaya miki ki bar wannan taurin kan."
"Muhammad mu kai shi asibiti don Allah"
Zo ki kama bindigar nan.
Ta zaro ido ta girgiza mai kai tace "Ba zan iya ba."
"Maryam...." ya kira sunanta da wani irin tsawa.
Tashi tayi ta amsa bindigar ta na kallon maharan guda uku suma da bindigu a hannunsu suna kallonta suka bushe da dariya.
Ta haɗiyi yawu makwat ta na kallon su ita ma.
Muhammada ya ciciɓi Smith ya saka a bayan mota.
"Shiga cikin mota."
Da gudu ta zagaya ta shiga.
Shi ma ya shiga yana kallonsu suna kallonsa.
Yana jan taku ɗaya suka sa harbi sun kuma tare hanya.
Ya gama yanke shawarar ta kansu zai bi ya wuce.
Ya bawa motar wuta ya fige motar da gudu. Ganin da gaske kan su zai bi ya sa suka dare gefe ya fice daga layin.
Na cikin motar yace "Ku shigo mu bi su ku shigo."
Suka shiga sai dai ko mai irin motar Muhammmd ba su gani ba. Dole suka kama hanya suka koma.
Muhamamd kuwa na ganinsu. Dan laɓewa yayi a wani lungu don ya san zasu biyo shi ɗin.
[9/11, 8:02 PM] Ummulhair S Panisau: RUFAFFEN DUMA
Ummulkhair S Panisau.
(khairatup)
Karamci writers Association.
Wattpad:khairi_muhd.
13.
"Za mu kai shi asibiti mafi kusa. Miss ki daina kuka ki rufe wurin da kyau jini ya daina zuba."
Daman ta sa ɗankwalinta haka ta kuma dannawa tana share hawayenta ."Don Allah ka yi sauri,numfashinsa yana sauri."
Motar ta kuma ketare titi cikin gudu,fitulun titin suna wucewa kamar walƙiya.Har sai da suka isa cikin asibitin.Muhammad ya taka birki,ya fito daga motar cikin hanzari.
Da sauri ya shiga ciki yace "Emergency!"
Ma'aikatan lafiya suka fito da gado mai taya ,suka ɗauko Smith suka saka shi a kai.Marayam ta bi bayansu da gaggawa ,tana kuka da addu'a a cikin ran ta.
"Ya Allah ka cece shi." Ta faɗa da murya mai rauni da karaya.
Muhammad ya tsaya a bakin ƙofa,zufa na keto masa duk da sanyin da ake yi.
Kallon Miss yayi yace "Maryam...kar ki damu in sha Allahu za a ceto shi. Ki yi imani."
Kallonsa tayi idanuwanta cike da hawaye. "Na gode da ka zo ka taimaka mana."
Wayarta ta ji tana ringing ta manta ma da wayar a cikin aljihunta , zaro wayar tayi daga cikin aljihu. Sai dai kiran ya katse. Sai kuma saƙo ya shigo.
"WANNAN GARGAƊI NE KAWAI. IN KUMA BA KI BAR BINCIKEN BA GARGAƊI NA GABA SAI YA FI WANNAN."
Jikin Maryam yayi sanyi. Ta juya ta kalli Muhammad.
Maryam ta zauna a kujerar bakin ɗakin Tiyatar. Hannunta har yanzu akwai jini a jiki. Zuciyarta na rawa,idan tana kallon ƙofar ɗakin da aka rufe. Muhammad ya tsaya a tsaye daga gefe kamar mai gadin ɗakin. Hannunsa cikin aljihun wandon sa,idanuwansa na bin ko wanne motsi kamar mai shirin duk wani haɗari.
Bayan awa ɗaya aka buɗe ƙofar ɗakin, likitan ya fito yana cire safar hannu ya ce "Ku ne kuka kawo shi?"
"Eh." Maryam ta faɗa da sauri tana miƙewa. "Yaya yake?"
Likitan yace "Mun dakatar da zubar jinin. Wuƙar ta kusa taɓa masa zuciya amma bata kai nan ba. Yanzu mun maida shi ICU ,amma har yanzu bi farfaɗo ba. Yana buƙatar kulawa sosai da hutu."
Maryam ta ji wani nauyi ya sauka daga zuciyarta. Ta dafe ƙirjin ta tace "Alhamdu lillahi."
"Duk wannan abin saboda ni ya faru da Smith. Da ban ce muje ba da ƙila yana gidansa a kan gadonsa yana bacci."
Muhammad ya gigrgiza kai yace "Kar ki ɗora laifin hakan a kan ki. Duk wanda ya ke son ganin gaskiya ta bayyana, dole ya fuskanci haɗararruka a hanya. Amma wannan ba zai sa ki karaya ba. Ya zame miki wani tsani da kwarin guiwa wurin ganin kin cimma nasara shi ne ramuwar da za ki yi wa Smith."
Maryam ta kalle shi tace "sun ce min na daina wannan binciken."
Wannan yana nufun sun tsorata da ke ,kuma tabbas binciken ki yana kan hanya akwai wata manakisa da ake ɓoyewa."
"Nima na gamsu da hakan."
"Maryam,na tabbata akwai wanda ke ɓoye wani abu babba. Kuma ba za su yi ƙasa a guiwa ba, don ganin ba mu gano komai akan ku ba. Dole ne mu yi gaggawa kafin su kuma kawo miki wani harin."
Miƙewa tayi tsaye ta tsaya bakin ƙofar ICU. Idanuwanta cike da hawaye,amma ta daure ,lokaci guda kuma ta juya tace "To me za mu fara yi?"
"Zo ki zauna." Ya nuna mata wuri.
"Gaya min komai me ya faru a gidan Paul ɗin?"
"Kwanfutar sa muka samu muna buɗewa kuma anyi hacking ɗinta bamu samu komai a ciki ba. Sai wasu takardu su ma sun tsufa ba masu amfani ba ne ba sai....." sai kuma ta zaɓi da tayi shiru bata son ta faɗawa kowa komai yanzu ta sa a ranta ba zata dinga gaywa kowa komai ba."
"Sai me kuma?"
"Ba komai iya su kenan kuma sun ƙone a gidan Paul."
Wata ma'aikaciyar jinya ce ta tsaya a gabansu tace "Kece Maryam?"
Maryam ta ɗaga kai ta kalleta tace "Ni ce."
"Ok. Wani a waje yana son ganin ki."
"Wanne ne zai zo gani na a asibiti a wannan lokacin?"
"Ban sani na bai gaya min sunan sa ba. Yace akwai saƙon da zai baki."
Maryam ta kalli Muhammad ta kalli Nas. Muhammad ya ɗaga mata kai alamar taje.
"Ba matasala?"
"Zan biyo bayan ki na baki kariya."
Hanyar da Nas ɗin ta bi nan suka bi. A harabar asibitin suka tsaya.Wani mutum suka gani a tsaye sanye da hula mai rufe fuska da facemask.Ta matsa kusa, mutumin ya ajiye wata ƙaramar jaka a ƙasa sannan ya juya ya bar wurin ba tare da yace uffan ba.
Smith ya yi saurin dakatar da shi ,suka fara kokawa a cikin duhu,ƙarar ƙarfe na buguwa da bango ko ƙasa.Tuni Maryam ta takure a gefe guda tana neman lambar wayar Muhamamd shi ne kaɗai ya faɗo mata a ranta.
Aikuwa cikin sa'a ta same shi nan tace mai "kai taimaka mana muna cikin matsala zasu kashe mu. "
"Kina ina Maryam ke da waye?"
A firgice ta gaya mai adireshin ta kashe wayar. Fitilar wayar ta haska nan ta ga Smith na riƙe da hannun maharin,amma bai yi aune ba ya wafce hannunsa cikin azama ya soka wuƙar a gefen cikin Smith.
"Smith" Maryam ta faɗa da ƙarfi." Da gudu tayi wurin shi amma maharin yayi tsalle ya fice ta taga.
Smith ya durƙasa ƙasa hannunsa riƙe da wurin da aka soka mai wuƙar jini na zuba kamar an yanka kaza.
"Maryam.." ya faɗa da ƙyar cikin ƙarfin hali ki tafi ,ki gudu zasu dawo na ji kamar an sa gas yana likin Maryam go save yourself."
"No! No! Smith ba zan bar ka ba. Tare muka zo tare zamu tafi." Ɗan kwalinta ta saka ta danne wurin da jinin ke zuba tana hawaye. "Ba zan bar ka ka mutu ba Smith."
Tashi tayi da ƙyar ta samu ta lallaba ta ja Smith ta soma fita da shi daga gidan ya mata nauyi amma haka take jan sa tana kuka tana jan numfashi kafin su ƙarasa fita ya suma.
Suna fita gidan ya tashi ji kake boom ƙara mai rikitarwa. Faɗuwa tayi a ƙasa ita da Smith ɗin duka tuni jikinta ya soma karkkarwa tayi kaca-kaca da jinin Smith. Da tuni suma yanzu sun ƙone a cikin wannan gidan? Tuno hakan kawai na sa ruhinta ya soma rawa.
Ji tayi kamar magana a bayansu haka ana "Ku nemo su kamar fa sun fito basu ƙone ba boss ba zai bari ba." Tana jin haka kuwa ta zare takalmanta a hankali ta dinga jan Smith daga tsallake suka raɓe a bayan wata bishiya mai yalwar ganyayyaki. Daga nan tana kallan yadda tiƙa-tiƙan mazan ke nemansu a cikin duhu. Kawo yanzu tana cike da da na sanin kin bin shawarar Smith ga shi yanzu ta yi sanadin da aka soka masa wuƙa. Da sauri ta kama pulse ɗinsa taji tana harbawa suma yayi. A tsorace take sosai.
Ta gama karaya cewa yau kam ba iya Smith ba ita kanta ba zata fita daga wannan wurin da ran ta ba.
Sai dai ƙarar mota ce ta shigo layin ta kasa kunne tana jin yadda motar ke antaya gudu.
Maharin kuwa juyawa yayi ya kalli ɗaya abokin nasa yace "Kai waye yake shigowa nan?"
Motar kuwa tsayawa tayi cak a gaban gidan Paul da ke kamawa da wuta.
Muhammad ya fito daga cikin motar da baƙar jacket a jikinsa ,hannunsa riƙe da ƙaramar bindiga yana kallon yadda wutar ke ƙara girmama. Tuni ya ji zuciyarsa ta tsinke a tunaninsa Maryam ta ƙone a ciki.
Juyawa yayi a fusace ya kalli maharan guda biyu yace "Ina Maryam? Me kuka yi mata azzalumai?" Ya nuna musu bindigar hannunsa.
Ɗayan ya gane shi ya yi tsit. Ɗayan kuma yana ƙoƙarin yayi magana sai kuma ɗayan ya riƙo hannunsa yace masa "Mu gudu wannan ba sa'anmu ba ne."
"Amma waye shi ɗin?"
Muhammad ya saki harbi a iska. Maryam ta kiɗime ta saki ihu cike da tsoro.
Da Muhamamd da maharan inda suka ji ihun suka kalla bayan bishiya.
Tuni suka soma musayar wuta a junansu. Wata mota ta kuma shigowa ita ma. Bouncers ne a ciki da bindigu. Ba sa son harbin Muhamamd su abinda suke so Maryam ce.
Muhammad ya lura suna da yawa kuma suna da makamai kawai ya yanke shawarar komawa cikin mota harinsa shi ne ya je inda Maryam take.
Yana shiga ya yi ribas kamar zai fita ne. A nan suka daina harbin dukansu suka tsaya kallonsa. Basu yi aune ba ya ci wani burki ya afka ciki da gudu daidai bishiyar ya tsaya ya fito ya tsaya a gaban motar ya ga Maryam duk tayi hurjajjan ta fita daga hayyacinta.
"Maryam ku shiga ciki."
"Ya suma."
"Waye?"
"Smith,abokin aikina tare muka zo yana ƙoƙarin ceto na suka soka mai wuƙa a ciki."
"Maryam sau nawa na gaya miki ki bar wannan taurin kan."
"Muhammad mu kai shi asibiti don Allah"
Zo ki kama bindigar nan.
Ta zaro ido ta girgiza mai kai tace "Ba zan iya ba."
"Maryam...." ya kira sunanta da wani irin tsawa.
Tashi tayi ta amsa bindigar ta na kallon maharan guda uku suma da bindigu a hannunsu suna kallonta suka bushe da dariya.
Ta haɗiyi yawu makwat ta na kallon su ita ma.
Muhammada ya ciciɓi Smith ya saka a bayan mota.
"Shiga cikin mota."
Da gudu ta zagaya ta shiga.
Shi ma ya shiga yana kallonsu suna kallonsa.
Yana jan taku ɗaya suka sa harbi sun kuma tare hanya.
Ya gama yanke shawarar ta kansu zai bi ya wuce.
Ya bawa motar wuta ya fige motar da gudu. Ganin da gaske kan su zai bi ya sa suka dare gefe ya fice daga layin.
Na cikin motar yace "Ku shigo mu bi su ku shigo."
Suka shiga sai dai ko mai irin motar Muhammmd ba su gani ba. Dole suka kama hanya suka koma.
Muhamamd kuwa na ganinsu. Dan laɓewa yayi a wani lungu don ya san zasu biyo shi ɗin.
[9/11, 8:02 PM] Ummulhair S Panisau: RUFAFFEN DUMA
Ummulkhair S Panisau.
(khairatup)
Karamci writers Association.
Wattpad:khairi_muhd.
13.
"Za mu kai shi asibiti mafi kusa. Miss ki daina kuka ki rufe wurin da kyau jini ya daina zuba."
Daman ta sa ɗankwalinta haka ta kuma dannawa tana share hawayenta ."Don Allah ka yi sauri,numfashinsa yana sauri."
Motar ta kuma ketare titi cikin gudu,fitulun titin suna wucewa kamar walƙiya.Har sai da suka isa cikin asibitin.Muhammad ya taka birki,ya fito daga motar cikin hanzari.
Da sauri ya shiga ciki yace "Emergency!"
Ma'aikatan lafiya suka fito da gado mai taya ,suka ɗauko Smith suka saka shi a kai.Marayam ta bi bayansu da gaggawa ,tana kuka da addu'a a cikin ran ta.
"Ya Allah ka cece shi." Ta faɗa da murya mai rauni da karaya.
Muhammad ya tsaya a bakin ƙofa,zufa na keto masa duk da sanyin da ake yi.
Kallon Miss yayi yace "Maryam...kar ki damu in sha Allahu za a ceto shi. Ki yi imani."
Kallonsa tayi idanuwanta cike da hawaye. "Na gode da ka zo ka taimaka mana."
Wayarta ta ji tana ringing ta manta ma da wayar a cikin aljihunta , zaro wayar tayi daga cikin aljihu. Sai dai kiran ya katse. Sai kuma saƙo ya shigo.
"WANNAN GARGAƊI NE KAWAI. IN KUMA BA KI BAR BINCIKEN BA GARGAƊI NA GABA SAI YA FI WANNAN."
Jikin Maryam yayi sanyi. Ta juya ta kalli Muhammad.
Maryam ta zauna a kujerar bakin ɗakin Tiyatar. Hannunta har yanzu akwai jini a jiki. Zuciyarta na rawa,idan tana kallon ƙofar ɗakin da aka rufe. Muhammad ya tsaya a tsaye daga gefe kamar mai gadin ɗakin. Hannunsa cikin aljihun wandon sa,idanuwansa na bin ko wanne motsi kamar mai shirin duk wani haɗari.
Bayan awa ɗaya aka buɗe ƙofar ɗakin, likitan ya fito yana cire safar hannu ya ce "Ku ne kuka kawo shi?"
"Eh." Maryam ta faɗa da sauri tana miƙewa. "Yaya yake?"
Likitan yace "Mun dakatar da zubar jinin. Wuƙar ta kusa taɓa masa zuciya amma bata kai nan ba. Yanzu mun maida shi ICU ,amma har yanzu bi farfaɗo ba. Yana buƙatar kulawa sosai da hutu."
Maryam ta ji wani nauyi ya sauka daga zuciyarta. Ta dafe ƙirjin ta tace "Alhamdu lillahi."
"Duk wannan abin saboda ni ya faru da Smith. Da ban ce muje ba da ƙila yana gidansa a kan gadonsa yana bacci."
Muhammad ya gigrgiza kai yace "Kar ki ɗora laifin hakan a kan ki. Duk wanda ya ke son ganin gaskiya ta bayyana, dole ya fuskanci haɗararruka a hanya. Amma wannan ba zai sa ki karaya ba. Ya zame miki wani tsani da kwarin guiwa wurin ganin kin cimma nasara shi ne ramuwar da za ki yi wa Smith."
Maryam ta kalle shi tace "sun ce min na daina wannan binciken."
Wannan yana nufun sun tsorata da ke ,kuma tabbas binciken ki yana kan hanya akwai wata manakisa da ake ɓoyewa."
"Nima na gamsu da hakan."
"Maryam,na tabbata akwai wanda ke ɓoye wani abu babba. Kuma ba za su yi ƙasa a guiwa ba, don ganin ba mu gano komai akan ku ba. Dole ne mu yi gaggawa kafin su kuma kawo miki wani harin."
Miƙewa tayi tsaye ta tsaya bakin ƙofar ICU. Idanuwanta cike da hawaye,amma ta daure ,lokaci guda kuma ta juya tace "To me za mu fara yi?"
"Zo ki zauna." Ya nuna mata wuri.
"Gaya min komai me ya faru a gidan Paul ɗin?"
"Kwanfutar sa muka samu muna buɗewa kuma anyi hacking ɗinta bamu samu komai a ciki ba. Sai wasu takardu su ma sun tsufa ba masu amfani ba ne ba sai....." sai kuma ta zaɓi da tayi shiru bata son ta faɗawa kowa komai yanzu ta sa a ranta ba zata dinga gaywa kowa komai ba."
"Sai me kuma?"
"Ba komai iya su kenan kuma sun ƙone a gidan Paul."
Wata ma'aikaciyar jinya ce ta tsaya a gabansu tace "Kece Maryam?"
Maryam ta ɗaga kai ta kalleta tace "Ni ce."
"Ok. Wani a waje yana son ganin ki."
"Wanne ne zai zo gani na a asibiti a wannan lokacin?"
"Ban sani na bai gaya min sunan sa ba. Yace akwai saƙon da zai baki."
Maryam ta kalli Muhammad ta kalli Nas. Muhammad ya ɗaga mata kai alamar taje.
"Ba matasala?"
"Zan biyo bayan ki na baki kariya."
Hanyar da Nas ɗin ta bi nan suka bi. A harabar asibitin suka tsaya.Wani mutum suka gani a tsaye sanye da hula mai rufe fuska da facemask.Ta matsa kusa, mutumin ya ajiye wata ƙaramar jaka a ƙasa sannan ya juya ya bar wurin ba tare da yace uffan ba.