← Book details Namijin Zuma Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 92 OF 107

Sashe 92

Namijin Zuma Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

da duk hakan bata faru ba, wane mutum,. Driver ya budewa hajiya mommy gidan baya ta shiga yaja motar suka fice a gidan,. aunty Hafsat ta dawo Cikin gidan ta zauna a falo, haka kawai wasu kwallah suka wanke mata idanuwa na zallar tausayin Aunty Nabeelah, ga cikin jikinta, gashi ko Kafin ta fita ti-ti tasamu napep babban aiki ne, zataci tafiya sosai,duk abunnan da akeyi big hajiya bata Sani ba tana can tana baccin asara Kmr kasa. Da sauri sauri ta ringa tafiya sbda ta isa ti-ti da wuri, ga cikinta se uban motsi yakeyi,tana ta tafiyarta motar hajiya mommy tazo ta wuce fittt,.haka taci gaba da Addu'ah Allah yasa kada hajiya mommy ta rigata isa gida, dukda tasan da wuya hakan. Da sauri sauri ga uban ciki , ba halin tayi gudu da ace babu ciki jikinta da harda gudu zata hada, Amma Ina yanzu ba halin gudu, tafiyarma se a hnkli, ta tallabo kasan cikinta dayayi tsini ta kasa. A haka tayita takawa ta isa ti-ti da kyar, tayi sa'ah tana fitowa titin tasamu napep ta hau bayan ta gaya masa inda ze kaita, ba kowa a napep din, ko ciniki bata tsaya yiba sbda se uban haki takeyi, tana shiga ta jingina bayanta da napep ta kalli kafarta taga harta kuma kumbura ba karamar tafiya tayi ba, Kuma Cikin sauri da takura kai. se nishi takeyi Kawai taji me napep nacewa "Sannu hajiya, dagani kin tafiyu ga juna biyu Kuma jikinki..." Nabeelah ta shiga mamakin ya akayi ya gane akwai juna biyu jikinta, me napep,"ya akayi kasan da ciki jikina?" Nabeelah ta tambayesa Cikin mamaki da tsoro, wai namiji ya gane tanada ciki Ina maga mace, ta tabbatar ko hajiya mommy bata gane yanzu ba dole zata gane nan in taje gidan. Me napep yayi murmushi yace "Ah hajiya ai ciki ba boyeyyen abu bane, tinda na tsaya zan daukeki nagani, inda zaki ba nan zanyi ba amma sbda tausayin Cikin jikinki yasa na daukeki,,,Nima fa inada iyali yarana bakwai nasaba ganin ciki hajiya..." Nabeelah ta sauke ajiyar zuciya ita kadai tasan meke ranta ta kasa cewa komi, kawai se kallon me napep din takeyi, tana jiyo bugun zuciyar babynta a tare da ta-ta zuciyar. Kosawa tayi su isa gidan dame napep din, a kwanar shiga gidan Wani me mota baka Mercedes, yadinga biyo napep din, yazo dai-dai napep din ya zuge glass dinsa kasa, matashine dagani ko Auren fari beyi ba, Kallo daya ta masa ta dauke idanuwanta a kansa, shikam se murmushi yakeyi mata gashi kyakkyawa chocolate color, Amma be Kai Aeezad dinta kyau ba, duk sadda zataga wani namiji ko a film ne Aeezad kawai ke zuwar mata zuciya da idanuwa, data tunasa seta tuna da dadin burarsa in yana zungura mata ita. Mutunmin yace dame napep din ya tsaya Yanasan mgna da wadda ke Cikin napep din. Me napep na shirin tsayawa tace karya tsaya, dole yabi umarni dukda yaso ya samu kudi sbda yasan inya tsaya dole mutumin ze bashi Wani Abu duba da yadda ya gansa dagani zeyi alheri har me napep yasa ran yasamu ko 5k ce daga gareta ,har suka isa kofar gidan me motar na biye dasu. Nabeelah se mamaki takeyi tana tunanin to koshi bega cikin jikinnata bane yakeso ya tsayar da ita hakan ya tabbatar mata dame napep din nada kallon kwa-kwaf babbar Addu'ar ta Allah yasa ba Maye bane me napep din. Me napep din na tsayawa, tana sauka a napep din me motar ma ya tsaya Yana fadin "Baiwar Allah ni sanki nake da Aure..." Nabeelah ta kalli cikin dake jikinta a cikin hijjabi, tana mamaki ta mikawa me napep din dubu dayar kawai, tafiyar tata batafi ta 700 ba ko a drop ne, wai danma akwai tsadar fuel, Sam ba Wani uban nisa. Nabeelah ta shige gidan da hanzari bayan ta mikawa me napep din kudin se godiya yakeyi ganin ta bashi dubu daya, itade ta shige Nan ta barsu waje shida me napep dayayi tafiyarsa tuni. Me motar Wanda ya jima kofar gidan yana jiran fitowarta kana ya juya ya bar kofar gidan. Nabeelah na Shiga cikin gidan ta tsaya ta saita kanta sosai a gate din farko ta kara gyara hijjabinta, kana ta nufa cikin gidan se gaisawa sukeyi da masu gadi wadanda da kyar suka ganeta sbda kibar da tayi. Tana isowa packing space taga motar Hajiya mommy seda gabanta ya fadi yau tasan zatasha wulakanci sosai,. Haka jiki a sanyaye ta nufa part din Hajiya mommy bakinta dauke da sallama, ta isa palonta bayan an mata iso se Addu'ah takeyi a ranta kada a gane cikin jikinta. A palon ta tadda naeema zaune ta saki uban jiki, Hajiya mommy ma zaune se faman karkada kafa takeyi Daman jiran isowar nabeelah takeyi, se manyan aminanta guda biyu hajiya naja'atu da hajiya samira, sauran basu karaso ba tukunna, yau babban sha'ani za ayi na cikar babban shagon hajiya mommy shekara goma da budewa. Sai Karfe shida na yamma za a fara. Na'eema da kyar ta iya gane nabeelah wadda ta zube kasan ta fara gaida kowa dake palon harda naeema, wadda keta kallanta tana yatsina fuska kmr taga zawo, Nan da Nan ta hade Rai kmr taga mutuwa, gabaki daya se taji ta Kuma tsanar Nabeelah fin ada ta rasa dalilin hakan, ko amsa gaisuwarta batayi ba. Hajiya mommy ta rufeta da masifa da zagi da tozarci na rashin karasowar da batayi ba da wuri har ta bari ta rigata karasowa. Seda hajiya naja'atu ta bata hkri kana ta sassauta.Nabeelah tabata hkri ta mata banza, ta mike ta nufi hanyar kitchen hajiya mommy tace"Baraka zata nuna miki komi, kar Wanda yasa Miki hannu ke zakiyi duk aikin musammanma girkin Kuma inaso abincina yayi dadih..." Nabeelah ta juyo tace toh Cikin ladabi. Ta nufa kitchen jiki na rawa, ta tadda masu Aiki suka gaggaisa duk nutsuwarta bata jikinta tunani takeyi ta yaya zatayi wannan uban aikin gata da uban hijjabi jikinta. Bata tsaya bata lokaci ba,ta fita kitchen din waje, ta hada wutar itace, tin a nan se nishi kawai takeyi tana motsa kafa da kyar, gashi ba d'an tayi sbda tace kar wanda ya tayata a barta tayi ita kadai, kaf kawayenta sunasan abincin nabeelah shiyasa take zuwa duk satin ta girka in zatayi taro da kawayen nata. Haka ta hada wutar ba karamin wahala tasha ba ga wutar damuna azabar wahala ce da ita,seda tasha fama wutar kafin ta kama, ga hayaki idanuwanta sukayi red sosai, haka ta daure, ta dakko tukunya lamba ashirin ta daura kan wutar , da kyar ta dauko tukunyar, fried rice ta fara daurawa, kana ta sake kunna wata wutar ta daura jallof rice, tana Aikin tana gumi Gashi ba sauri Sbda a takure take ga nauyin cikin ga nauyin hijjabi duk ta gaji kafin aje ko ina,. Inna sadiya dake gefe tana yanka salad Se sannu take mata ba kowa a gurin duk masu aikin sun kama gabansu zuwa nasu ayyukan, Nabeelah ta amsa da yawah. Innah sadiya dayace daga masu dafa abinci a gidan, kawai Taya Nabeelah takeyi yankan salad din ganin ayyukan sun mata yawa,sannan se kallanta takeyi ganin Kmr tanada ciki,DUk yadda Nabeelah ta kaiga fama da hijjabi seda inna sadiya ta gane akwai ciki jikinta abinka da babbar mace, mamaki inna sadiya tashigayi kan yaushe nabeelah tayi aure basu Sani ba?" Haka kawai inna sadiya se taji tausan Nabeelah, ta tashi kawai tasa mata hannu a Aikin, Nabeelah tace ta barshi, inna sadiya tace "Bari in tayaki ba komi insha Allahu..." Aiko Nabeelah taji dadih, Nan inna tasa mata hannu har suka gama Hajiya mommy bata leko ba tana can falon tana fama da baki wanda keta danno kai, tini gida ya cika da mata taf,. Nabeelah da innah suka kammala komi suka gyara kitchen, Nabeelah ta nufa gyaran gidan ita kadai da kyar, take aikin Amma haka seda ta gyara ko Ina,Hajiya mommy tace har tsakar gida ta share, Aiko haka ta share tsakar gidan da kyar, ranar de haka Nan ta wuni tsaye, se aikin azaba takeyi, Nan gidan akasha party , Hall taso tayi abubuwanta Amma Alhaji sunusi ya dinga rokonta kartaje hall da kyar ta yadda,. DUk cukowar gidan babu Dan uwan Hajiya mommy sede bare, bata gayyaci Yan uwanta ba, ko uwarta bata gayyataba, Sbda batasan azo a zubda mata mutumci a cikin manyan mutane, kawai Sbda su talakawa ne, kar suzo su addabi masu kudi da Karnin talauci, acewarta, ita fa Sam ba Wani zuwa ma gidansu takeyi ba, tinda ta auri Alhaji sunusi kimanin shekaru goma Sha biyar bata je gidan iyayensa sau hudu ba, se Alhaji sunusi yayi ta lallashi take zuwa, ko tunawa tayi da yadda gidansu yake da muni da Karnin talauci se taji tashin zuciya,in kaga an Kai Wani Abu Arziki gidansu to daga Alhaji sunusi ne Amma ita kan Ina bata taba aika musu dakomiba, hana karya de sadda ubanta ya kwanta ciwo rai hannun Allah ta aika musu da kudi dubu hamsin, Amma ita ko zuwa batayi ba, sede ta kirasa ta gaidasa sama-sama, harga Allah tinda ta shigo daula bata fatan zuwa cikin karnin talauci,. Sannan bata bawa Wani nata fuskar zuwa nata gidan ba,abinka da uwa, uwarta ta taba zuwa sbda ta ganta kawai, tabi ta hade rai,batade furta abaki ba, sede ta nuna a fuskarta daga ranar Mamanta bata Kuma zuwa ba, sede tanata binta da Adduar shiriya, sbda zuwanta gidan ta fuskanci se yadda tayi da mijin Kuma tasan aikin asiri ne kawai,ita da kanta uwar ta-ta tasan yarta bata da hali,. A wata shekara gidansu ya ruguje, seda Alhaji sunusi yase musu gida Amma ita sede ta bisu da Allah kyauta,ubanta kullum cikin tsine mata yakeyi, danma uwar na tausarsa, ita Sam bazata iya tsine mata ba sede ta bita da Addu'ah kawai. Hajiya Rafi'ah zatama kawayenta hidimar 5m sbda a fita kunya harkar girma da isa, ita a dole ga matar me kudi, ta baza gwala-gwalai a wuya da hannu ayita isa, Amma bazata iyama uwarta da ubanta hidimar 100k ba, duk kusancinta da kawaye bata taba nuna musu gidan su ba sede tace iyayenta sun rasu. har karfe sha-biyu na dare Nabeelah na tsaye da sauran masu Aikin sbda
Chapter 92 · 0% Book details