← Book details Nama Ya Dahu Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 41 OF 60

Sashe 41

Nama Ya Dahu Part 2 Complete Hausa Novel · about 3 min read

karɓarta. Da ƙyar Faty ta shawo kaina na yarda na amshi kuɗi da sarƙar, dan na miƙa mata nace ta mayar mishi ma ni bana so. "Sarƙar ki saka a wuyanki da'iman kar kiyi wasarere da'ita dan sai a sace. Kuɗi kuma ki adana abinki. Amman wallahi da nice Salim yace yana so da aure, da a mugun guje zan aureshi in watsar da rayuwarnan da nake ciki. Ke kuwa har wanne irin miji kika tanadarma kanki a gida najeriya da kika ƙi amincewa da Salim? Mazan mu sun banbanta da mazan Larabawa, ina miki kwaɗayin shiga cikin babbar daular da har muma zamu dangwali arziki. Akwai Alawiyya data zauna tare dani Balarabe take aure,itama daga Najeriya tazo aikatau, ya ganta tana aiki a gidansu kamar wasa ya aureta yaransu biyu du maza. Duk shekara iyayenta da ƙannenta suna zuwa aikin Hajji, iyayenta sun zama masu arziki. Iyabo ki zauna ki nutsu tsam babu fa wanda yaƙi daɗi" Ni dai nayi jigum inata faman jujjuya maganganun a kaina amman kaina yaƙi ɗauka. Soyayyar Yaya Hamma kawai nake ji tana dukan raina, ina kuma hasaso dimuwar da zai shiga in labarin soyayyata ko aurena da salim ya je kunnuwansu. Wata zuchiyar tace dani. "Ki tsaya kallon ruwa kwaɗo yai miki ƙafa. Kul ki yi nazari dan gudun yin ba wan ba ƙanin. Ki ƙi Salim, ki koma Najeriya batun soyayyarki da Hamma yasha ruwa, ko kiga Daso a gidanshi tunda dama ba furta miki kalmar so yayi ba. Ba wani alƙawari yardadde ku ka yi ba." Sai naji gabana yana dokawa da ƙarfi. Ni dai ji kawai nayi asuba tayi ina daga zaunannan ko kwanciya ban yi ba. Ina yin Sallah saina kwanta bacci. A cikin baccin naji ana ɗaɗamun duka, ina buɗe idanuna muka haɗa idanu da Hajiya. "Maza tashi ki haɗo kayanki, an turo mota zaki koma bakin aikinki." Bani da zaɓi haka na haɗa kayana na fito tsamo_tsamo. A fitowata sai gani ga Uwani kaciɓus. Tayi baƙi idanunta yayi zuru_zuru. Yanayin yadda na ganta a zahirin gaskiya hankali yayi matuƙar tashi. Hannun juna muka kama. Buɗar bakin Uwani maganarta ta farko tace. "Allah yayi zamu gana ne Iyabo. Amman kinga daga nan Najeriya zan koma, inaso in mutu a ƙasata cikin dangina da gatana." Kuka na fashe dashi nace. Uwani ki zauna a wajen Faty ki bani lokaci zan dawo bazaki koma ke kaɗai ba Uwani." "Dalla wuce ni ki bani waje, zaki tsayar dasu kina baiwa" Cewar Hajiya. Ina kuka ina waigen Uwani har gaban motar gidan aikina. Uwani ki mun alƙawarin ba zaki tafi ki barni ba" Ina faɗar haka na shiga mota. Ya ilahi. Azaba, damuwa, ciwon baya dana ƙirji babu irin wanda a ciki ban ɗanɗaneshi ba. Ga tunani Uwani daya addabi ruhina.✍🏻 MRS BUKHARI Su iyabo suna ganin jalala
Chapter 41 · 0% Book details