← Book details Muhaseen Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 26 OF 26

Sashe 26

Muhaseen Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Allah ya taimake ka ka gafarce ni ban yi hakan da wata manufa ba na yi hakanne dan kawarda idon masharanta, kuma ina da burin sanar da kai amma kuma wasu abubuwa da suke faruwa da ni ya saka na kasa sanar maka."
A ɗimauce ya soma tambayata abubuwanda ke faruwa, nu kuma ban ɓoye masa ba na sanar da shi.
"Allah ya taimake ka haƙiƙa ina fuskantar barazana akan wannan cikin, ga shi ina yawan yin mugayen mafarkai da kuma firgita, abin yana tsorata ni sosai shi yasa na kasa sanar da kai banaso ka sake ƙwallafa ranka akan ciki kuma daga baya muzo shima mu rasa shi."

"Tabbas kin aikata laifi me girma na ɓoye min abin da ke faruwa da ke, kuma tabbas kin cancanci hukunci saboda haka na yanke hukunci za ki je can Masarautar Katsina ki raini cikin a can, zaki tafi da kyautar dawakai biyar shanu goma tare da ɗanyar gorl wannan masoni ne na hukuncin gagarumin laifin da kika aikata."
Faɗawa jikin shi na yi tare da jeranto godiya sinƙi-sinƙi farinciki fal raina.
Kamar yanda ya faɗa hakan ce ta faru, kai tsaye a washe gari aka tashi da labarin zuwana Katsina, bayan na yu sallama na tafi ne labarin ina da shigar ciki ya baibaye Masarauta, labarin daya ɗimauta zukatan munafukai da kuma azzalumai, daga ciki akwai babbar azzaluma wacce sam babu Allah a ranta wato Gimbiya Zainaba, idan ana neman ƴan tawagar shailan na kurkusa to a sakata a sahun farko, domin zaluncinta na shallake gaban kwatance.
Daga ranar da labarin ya risketa bata sake barci cikin salama ba, inda ta dinga shiga tana fita wajen ganin ta kassara min rayuwa, a ɗa can tana zuwarmin a mafarki amma a ɓoye, amma a yanzu a zahiri nike ganinta kuma a siffar ban tsoro ga shi yanzu tsoratar da ni da ake yi abin ya ninka na baya, dan ma dai na duƙufa da addu'a sannan a gidana kullum cikin taya ni suke, takanas ake dafa abinci sutura harma da kuɗaɗe aka dinga sadaka da niyyar Allah ya kare ni da abin da ke cikina.

Cikin ikon Ubangiji mabuwayi me rahama da jin ƙan bayinsa a ranar wata juma'a bayan cikina ya shiga watan haihuwa, kuma a ranar na samu baƙuncin Me martaba da ke zuwa duba ni duk ƙarshen mako, muna zaune muna gaisawa ciwo ya ci ƙarfina, dama dauriya kawai nike yi, nan take aka yi asibitin masarautarmu da ni.
Mutane ko ta ina antaru anata addu'ar Allah ya sauke ni lafiya, yayinda na kasance tare da Me martaba Sarki a ɗakin haihuwa inda kusan a tare muke yin gumurzun ni da shi.
Bayan awanni huɗu ƙwarara Allah ya sauke ni lafiya, bayan na haifi santalelen yaro namiji da ƴan mintuwa wata naƙudar ta sake taso min gadan-gadan ba'a rufe mintuna a shirin ba ana sake direwa Me martaba wani yaron.
Bazan iya misilta muku murna da farincikin da garuruwa guda biyu suke ciki ba, Me martaba kuwa ba'a magana ko gyara yaran ba'a gama yi ba ya ɗauke su cikin jini ya rungume yana kukan farin ciki tare da jeranta kirari da godiya ga Allah."

Nisawa Umma ta yi tare da kallon fuskar Mamman da ta sauya da wani yanayi me kama da al'ajabi, sai kuma ta karkata kanta zuwa wajen da Najla wacce ta yi mutuwar zaune ta ke sai ta share hawayen idonta sannan ta janyo hannun Najla zuwa kuda da ita, Najla wacce gaba ɗaya tasha jinin jikinta lokacin da Umma ta janyo ta sai ta lumshe idon ta wasu hawaye na tsinke mata.
Ɗaura kanta Umma ta yi a saman cinyarta tare da shaga kanta sannan ta ci gaba daga inda ta tsaya.

"Bayan na farfaɗo ya dawo hayyacina na riski lafiyayyun kyawawan tagwayen yarana, waɗanda suka saka ni zubarda hawaye ina godiya ga Allah da yayi nufin zuwansu duniya duk da irin ƙalubalen gami da tsoron dana shiga lokacin da nike ɗauke da su a cikina.
Matsowa Me martaba ya yi tare da ɗaga min gadon na ɗan yi sama, sannan ya ɗauko yaran gaba ɗayansu ya saka min a gefe da gefe na, fuskar shi ƙunshe da yalwatacciyar fara'a.
Lokacin da ɗumin su ya ratsa ni sai da na lumshe idanuwana sannan na ɗaura idona akan ɗaya daga cikin yara.
Idon shi a buɗe tar yana ɗan kyaftasu yana kallon fuskar Me martaba, nima kallon Me martabar na yi kamar zan yi magana sai ya riga ni da faɗin.
"Hhhhh wannan ai shine Magaji, domin tun zuwan shi duniya ya fara sanin mahaifi sa, bara ki gani in kauce zai rufe idon shi ne."
Kamar wasa ya kauce zuwa ƙasa sai ga yaron ya yamutse fuska gami da maida idon shi ya rufe, dariya muka yi gaba ɗayanmu mutanen da ke cikin ɗakin muna al'ajabin wannan yaro, Me martaba na ɗagowa yaron ya sake buɗe idon shi.

Kwanana ɗaya a asibiti aka sallame ni domin ina cikin ƙoshi kafiya ni da yarana, kwana ɗaya na ƙara a Katsina muka tattara muka koma Masarauta dan Me martaba ya matsa akan mu koma, sosai aka haɗa shagali wajen tarbarmu, a ranar na sake gasgata irin soyayyar da Me martaba ke yi min, nan aka dinga tururuwa dangi da ƴan uwa harma da sauran manya ana zuwa ganin yara, kuma duk wanda ya zo ba zai zo hannu biyu ba da gagarumar kyautar da za'a yiwa yaran, tun zuwan su duniya Me martaba yayi musu huɗuba da suna Hassan da Husaini, sai de an ɓoye sunan aka saka musu inkiya Muhaseen da Suhail, haihuwar yarannan ya sake buɗe min ƙofofin arziƙi, yayinda nima ba'a barni a baya ba wajen samun manyan kyaututtuka daga jama'a na tayani murna.
A ranar suna kuwa shagalin da aka sha ba zai misaltuba, dan kuwa anci uban nera a ranar, kowa da ke garin Kano sai da yasan da ansamu ƙaruwar yara a gidan Me martaba sarki Muhusin Salis.

Bayan anyi taron suna ni da sauran dangina muka yi zaman ƙirga abin da na samu, sai da na girgiza lokacin da aka lissafa min miloyoyin dana samu, da kuma wanda yarana suka samu, iya tsabar kuɗaɗe kenan banda gonaki da kuma shanaye da raƙumma, harma da kaji na hausa da akuyoyi, ji nayi lissafin yafi ƙarfin kaina dan haka sai na kirayi Me martaba ya zo, nace zan raba komi biyu zan ba shi rabi, ni da yarana sai mu ɗauki sauran rabin, amma fafur yaƙi amincewa, sai ma bada shawarar fara kasuwanci me gwaɓi da yayi min tayi, domin juya dukiyata ta ƙara bunƙasa, sosai sauran ƴan uwana suka yi na'am da hakan, basu koma ba sai da aka gama tsara komi aka kasafta dukiyar, inda aka zuba mana hannayen jari a manyan kamfanonin da ke ƙasarnan harma da sayranƙasashe, yayi da na yi rubutu da saka hannu akan na damƙa hagorancin gaba ɗaya dukiyar ga babban ɗana Muhaseen, ko bayan bana raye ya ci gaba da kulawa da dukiyar kar ya raba tashi data ɗan uwansa, a lokacin dariya mutanen da ke wajen suka yi min, ganin yaron da ke da ƴan ƙwanaki a duniya amma har na fara ɗira ma shi nauyu, sai da na ware waɗanda zan kyautar ga sauran jama'ar gidan da kuma wanda na fitar domin ayi sadaka da abin da zai taimaki sauran jama'ar gari, sannan muka tattara muka koma Katsina.

A can naci gaba da rainon ƴaƴana cike da kulawa, bani na koma Kano ba sai da suka yi wayo sosai, ko bayan dana koma munci gaba da rayuwarmu cikin kwanciyar hankali sam bana fuskantar matsalar komi daga wajen mijina, ga ƴaƴana da suke wuni a faɗa musamman Muhaseen da sam bashi da rigima, saɓanin Suhail da ke da ƙallafar uwa, ko fita aka yi da shi baya jimawa ake dawo da shi in shayar da shi (Yanzu na gane wani abu, shin masu karatu kuma kun gane ko kuwa🤔).

Rayuwa ta miƙa sosai, abubuwa masu daɗi da marasa daɗi sun faru, masu daɗin sun fi yawa akan marasa daɗin, marasa daɗin basu wuce yanda nike fuskantar barazana ni da yarana ba daga wajen abokan zamana, ga shi na gagara sanar da kowa damuwata, mugayen mafarkai gami da gane-gane babu wanda bana yi har tsoro nike dare yayi ace zan kwanta.

Ba zan mance ranar data zama rana mafi muni a gare ni ba, ranar Muhaseen da Suhail suka cika shekaru biyu da watanni, mun zauna a turaka ni da Me martaba muna lissafin ribar da ake samu a kasuwancina, sai ya ke bani shawara akan mu kafa kamanoni a kudu, ana samun alkairi sosai, ban ha da nisa ba na amince nace ma shi ko bayan bana raye yayi abin da ya dace kawai, ashe duk abin da muke yi Gimbiya Zainaba na laɓe tana jinmu, domin ranar ita zata amshi turaka, kuma lokacin fitata ya yi, ban ƙara jimawa ba na yi ma shi sallama na tashi da yarana na fice, ɗan turus na yi lokacin dana ganta a baki ƙofa tana jefami mugun kallo, amma ban ce komi ba na raɓata na fice gabana na faɗuwa.

Bazan mance ba a ranar ne naji ana kiran sunana lokacin nayi shirin barci ni da yarana ina musu wasa barci ya ɗauke ni, a ranar ne naji zan iya mutuwa idan ban fita daga Masarautar Kano ba, hankalina ya gushe tunanina yayi ƙaura na gagara gane komi illa bin umarnin da ake bani ta hanyar kiran sunana, ban san abin da ya faru daga nan ba kawai de na farka na ganni a wannan gidan, idan ban manta ba."
Ta kai ƙarshen maganar tana gashewa da kukan kewar yaranta data tuna a yanzu, tare da damƙar gashi kan Najla a cikin hannunta tana murzawa....✍🏻

Alhamdulillahi a yau Allah ya nufe ni da gama MUHASEEN littafi na ɗaya, zamu ɗora a littafi na biyu wanda ya kasance littafin kuɗi ne.

Ƴar uwa idan har kina so mu warware zaren cakwakiyar wannan libari tare da ke to ki garzaya ki biya kuɗin wannan labbarin naira 500 kacal kema ki mallaki na ki

9136291920
MARYAM UMAR
OPAY.

Shaidar biya a wannan layin.
09112636748

Karku bari a barku a baya ni ce taku har kullum me son ganin farin cikinku.

MARYAM STAR⭐⭐

SAI MUN HAƊU A LITTAFU NA GABA 2
Chapter 26 · 0% Book details