← Book details Muhaseen Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 15 OF 26

Sashe 15

Muhaseen Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Turɓune fuska Saleem ya yi kamar zai fashe da kuka, ya kawar da kanshi gefe yana ƙun-ƙuni.
'Ɗass-ɗass-ɗass.'
Muhaseen ya ƙyasta ƴan yatsunsa suka fitar da sautin, juyowa Saleem ya yi amma kwarjini ya hana shi kallon cikin idon Muhaseen ɗin, a maimakon haka sai ya kafe siraran pink lips ɗinshi da suka motsa kaɗan, sai kuma suka dare kyakkyawan ƙasaitacen murmushi na bayyana a samansu, lokaci ɗaya kuma soka tsuke a yanda suke, dariya me cike da jin daɗi Saleem ya sheƙe da ita, ganin murmushi a fuskar Muhaseen ba abune me sauƙi ba bare kuma dariya, dariya ita ce abu na ƙarshe da zai iya ƙirgawa a cikin ƴan yatsunsa da yasan Muhaseen ɗin ya yaɓa yi, itama dariyar tashi daban ta ke ba kamar ta sauran mutane ba.

Surutu abune da Saleem ya saba zama ya yiwa Muhaseen duda yasan ba tanka shi ya ke yi ba, amma aƙalla yasan yana saurarenshi kuma yana fahimtarshi sosai da sosai, sannan shi Saleem Allah ya yi shi cikin sahun mutane masu ɗan banzan surutu, baya iya zama bakinshi shiru ga shi da mitar tsiya, haka zai yi mitarshi ya gama amma ko Uhumm Muhaseen baya tofawa.

Yauwa kamar kullum ƙarfe takwas jerin gwanon motocinsu suka shiga yin tsere a saman titi, basu tsaya ba sai a STAR GOLD COMPANY, isar su babu jimawa aka gabatar da gagarumin sauyi, sauyin da ya gigita duniyar wasu, yayinda duniyar wasu ta cika fal da farinciki, an samu sauyin ma'aikata yayinda aka sallami wasu, wasu kuma aka ƙara musu matsayi, sannan kuma lokacin tashi bai yi ba aka sallami kowa tare da bayar da hutun kwana biyu, hutun da ya ɗarsa ayoyin tambaya a zukatan ma'aikatan.

Sai da kowa ya gaba ficewa bayan an rufe ko ina ya rage daga su sai masu gadi, sannan jerin motocinsu suka soma firfitowa a jere gwanin sha'awa su na fita daga ma'aikatar.
Runtse tafukan hannayensa ya yi yana jin ɗumin yatsunsa na ɗumama tsokar tafin hannunsa, lokaci ɗaya zuciyarshi ta sauya daga yanayin yanda ta ke dokawa, wani abu kamar tsutsa ya shiga bi ta ciki naman zuciyarshi yana kwaranya a jinin jikinshi a daidai sanda ƙwayar idansa ta yi tozali da ita, yanayin take burkin da driver ya yi da ƙarfi hayan ya saka sai da ya yo gaba sannan ya yo baya, kwata-kwata bai ji wannan ba gaba ɗaya hankalinsa na akanta.
Hannayenta duka biyun a ɗage sama yayinda ta dogara da babban ɗan yatsar ƙafarta, tsoro da firgici ya sanyata jin wani irin juyi, sai hakan ya bada salo me burgewa musamman da doguwar rigar rafae jikinta ta ɗage tare da buɗewa nan ta shiga yin juyi kamar fanka, a zahiro sai hakan ya yi kama da rawa irinta matan india, duda hakan bata gujewa abin da ta ke tsoro ba sai da ƙafarta ta gurɗe ta faɗa akan motar da ƙarfin gefen fuskarta ya daku da gaban motar nan take jini yayo tsalle daga bakinta, hakan ya yi daidai da fitowar Driver sa Saleem yayinda sauran securie suka firfito tare da zagaye wajen cikin shirin ko ta kwana.
Cike da ƙarfin hali ya ɗaga kanta bata tsaida ganinta ako ina ba sai a daidai saitin fiskarsa tada fito raɗau, yunƙurawa ta yi zata tashi amma sai wa ta azaba ta ziyarceta ba shiri ta komar da kanta.
Saleem ne ya soma kamota yana son ya tsaida ita amma sai ta gagara tsayuwa sai tangal-tangal ta ke yi, a ruɗe ya soma jera ma ta sannu yana kallon jinin da ke fita daga bakinta, ɗaga daga cikin motocin gabansu ya nufa da ita.
Ikon mallakar kanshi ne ya ƙwace daga gare shi, fararen idanuwanshi suka soma rikiɗewa su na sauya launi, yayinda ya kafe yatsun hannun Saleem da ke riƙe da ita, shi kanshi bai san abin da yake ji ba domin linzamin ikon mallakar karshi ya suɓuce daga gareshi.
Cike da amo me razanarwa gami da bada umarni a dake ya kira sunan Saleen bayan ya fita ya tsaya akan ƙafafuwansa.
"Sarki za'a wuce da ita hospital tana zubar da ji...."
Saleem bai ƙarasa faɗar abin da zai faɗa ba ganin kallon da Muhaseen ya yi ma shi ba sannan ya koma mota yabar ƙofar a buɗe.
Da sassarfa Saleem ya soma janta zuwa wajen motar ya shigar da ita gidan baya sannan ya koma mazauninya ya juyo da kanshi ta baya yana tambayarta ya jiki.
Gaba ɗaya sautin komi ya ɗauke mata lokacin da ta ji an ambaci kalmar Sarki, tana jin azaba me raɗaɗi amma hakan bai hanata buɗe idanuwanta ba ta kalleshi cikin yanar da ta baibaye idonta, daga kuma sanda ta ji an sake janta zuwa wani wajen daban sai ta soma yin yaƙi da nauyin da ke ƙoƙarin danne ta.....✍🏻

Ku yi following ɗina a arewapen dan samun damar karanta next chapter.
👇👇👇👇👇👇
https://www.arewapen.com/u/maryamstar248

MARYAM STAR

https://chat.whatsapp.com/DczAiFp992p78VNoV6tcMo?s=cl&p=a&mlu=3&amv=2

https://www.arewapen.com/u/maryamstar248

🌹𝙈𝙐𝙃𝘼𝙎𝙀𝙀𝙉🌹
(𝐿𝑎𝑏𝑎𝑟𝑖𝑛 𝑧𝑢𝑐𝑖𝑦𝑎 𝑚𝑒 𝑐𝑖𝑘𝑒 𝑑𝑎 𝑘𝑢𝑛𝑐𝑖, 𝑟𝑎𝑦𝑢𝑤𝑎 𝑚𝑒 𝑐𝑖𝑘𝑒 𝑑𝑎 𝑡𝑎𝑟𝑖𝑛 𝑘𝑎𝑙𝑢𝑏𝑎𝑙𝑒😔.)

𝙒𝙍𝙄𝙏𝙀 𝘽𝙔
𝙈𝘼𝙍𝙔𝘼𝙈 𝙎𝙏𝘼𝙍⭐.

💪𝙅𝘼𝙅𝙄𝙍𝙏𝘼𝙏𝙏𝙐 𝙒𝙍𝙄𝙏𝙀𝙍,𝙎 𝘼𝙎𝙎𝙊𝘾𝙄𝘼𝙏𝙄𝙊𝙉💪

✊ 𝙏𝙃𝙀 𝙎𝙃𝙄𝘿𝙊𝙍𝙄𝘼 𝙒𝙍𝙄𝙏𝙀𝙍𝙎 𝙏𝙀𝘼𝙈🤝
https://chat.whatsapp.com/Ek6DPlIu4ad0QgTfrn3rab?s=cl&p=a&ilr=4&amv=2

𝙋𝘼𝙄𝘿 𝘽𝙊𝙆
𝙎𝙀𝘼𝙎𝙊𝙉 𝙊𝙉𝙀

𝘾𝙝𝙖𝙥𝙩𝙚𝙧 13
Addu'a abace da ta jima tana yi, musamman akan cikar burukanta, bayan ta yi addu'ar tana tsayuwa da yaƙini akan Allah zai amsata ko ba lokacin ba, ta tsayu akan komi daren daɗewa addu'arta zata karɓu.
Kamar dai yanzu da ta ke jin cewa babbar addu'ar da ta ɗauki tsayin lokaci tana yi tun bayan data mallaki hankalin kanta ta amsu, sai de kuma idanuwanta da take alfahari da su akoda yaushe, takanyi godiya ga Allah idan ta gansu a jikin madubi, sannan tana alfahari da lafiyar da Allah ya wadata idanuwanta da ita, ciwon ido cuta ce da iya saninta bata taɓa yin ta, sai de idonta na sauya launi lokaci bayan lokaci musamman idan ta shiga yanayi.
A yanzu da idanwanta suka zama shamaki wajen kallon cikar burinta, sai ta ji wani sanyi ya baibayeta nan take ta yi ƙasa da kanta idonta na cika da hawaye, ɗisar farin ruwa me sulki da launin jah a saman ƙafarshi ya saka tsigogin jikinshi mimmiƙewa suna matsewa tare da fitar da ruwan gumi, da kyar ya danne ajiyar zuciyar da ke son kwace ma shi, ya sake maida hankali wajen kallon gaban motar.
Hawaye ta ci gaba da saki ko zata samu nauyin da zuciyarta ta yi ya ragu, wataƙila idanuwanta ma daga yau sun daina, taɓe-taɓe ba halinta bane takanga abu ya burge ta amma bata fiye kai hannu da sunan ta taɓa ba, amma a yau a kuma yanzu sai ta ji tana so ta taɓa, badan komi ba sai dan tabbatarwa, bata tsaya shawara da kwanyarta ba ta biyewa zuciyarta ya aika abin da bata yi ba, yayin da alƙalin ƙaddara ya rubuta ƙaddaruwarsa tun kafin wanzuwarta a duniya.
Yam...yam...yam, tsigar jikinshi ya shiga mimmiƙewa, ya yinda wani ɗumi me shige da irin ɗumin da mutum ke kasancewa bayan saukar zazzaɓi daga jikinsa ya baibaye shi nan take.
A lokacin da ɗumin tattausan tafin hannunta ya sauka akan hannunsa, rintse ido ya yi da ƙarfi yana ƙoƙarin saita kanshi, kafin ya lalubo abin yi, ya sake tsinkayar ɗumin lallausan hannunta na yawo a hannunsa tana gaba tana baya da shi, da mugun gudu ya yi nasarar kwato kansa ya dawo hayyacinsa, ba tare da sanin abin da zai biyo baya ba ya saka nashi hannun tare da dakatar da ita, sai kawai ya tsinci kanshi da matse hannunta gam a cikin nashi hannun.

Bayan lokaci me tsayi yau shi Muhaseen ne riƙe da hannun wa ta, wa ta macce wacce sam baida alaƙa da ita ta kusa ko ta nesa, mu'amala da mata ba ɗabi'arsa bace hasalima ko wajen aiki bai fiye yin aiki da su ba, ba kuma dan babu su a companys ɗin shi ba, sai dan yana nesanta kansa da su saboda wani dalili na daban.

Ko da shine bai da lafiya bai fiye shiga asibiti ba, koda ta kama ya shiga to Saleem ne ke bayani akan abin da ke damunsa ko da kuwa ba hakan bane yakan yi shiru yana saurarensu baya cewa komi, shiyasa ya fi so akira ma shi Doctor har gida ya duba shi, amma yanzu bayan isarsu da kanshi ya ja hannunta daya matse a cikin na shi bai tsaya ko inaba sai a gaban kwararen Doctor wanda ake ji da shi a asibitin, sai ya tsinkayo muryashi na jawabi akan abin da ya faru, kuma ya yi tsayin daka har aka gyara mata buguwar da gefen kanta ya yi tare da yin dresing ɗin ƙananun raunukan da ta ji a gefen idonta.

Iya shirun da ta yi kawai bata ce ko kanzil ba tun bayan afkuwar lamarin, abin ya shiga zuciyarshi da wani abu, wani abu wanda ba zai fassara shi nan take ba tare da ya nutsu ya yi nazari ba.
Ko bayan daya tabbatar da komi ya tafi daidai, bai so ya tafi ya barta ba amma babu yanda zaya yi aiyukan da ke gabanshi kaɗai sun ishe shi, ga kiran gaugawa da aka yi ma shi daga Company na ƙirar ƙarafuna, hakan ya saka ya tafi yana jin kewar wani abu wanda ke tattare da ita.

Kallon gefe da gefe na unguwar ta su ta yi tana Allah-Allah akan wani ya leƙo ya ganta ba dan komi ba sai dan ya zame mata shaidar gani da ido idan ta je gida ta bayar da labarin aka ƙaryata ta.
Sai de bata samu kowa ba sai mutanen da ke hada-hadarsu a wajen hakan ya saka ta saɓi ledar da aka shaƙe mata da fruit da kuma magunguna ta yi lungun gidansu kamar zata kifa.

Kamar kullum yau ma tana zaune ita kaɗai tana sana'ar data sabarwa kanta wato tazbihi, ihun da Najla ta kwalla tare da ɗanewa jikinta ne ya zaburar da ita, a kiɗime ta soma faɗin.
"Innalillahi Najla mi ke faruwa ne, lafiya?."
Ta yi tambayar tana riƙe Najlar da kyau tare da raba idanuwanta a bakin ƙofa tana jiran ta ga shigowar abin da ya biyota.

Cikin shehseƙar murya Najla ta ce.
Chapter 15 · 0% Book details