Sashe 10
Muhaseen Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ikon Allah kenan ƙyiuya ta ke yi, to shiga da ita ma sha Allah yarinya ƴar ɗagwas da ita."
Binta ta faɗi bakinta a washe, shiga ɗakin Suhail ya yi yana jin kallo yanda aka hargitsa ɗakin da kaya babu gyara kamar bola su Zainab basa nan sun fice yawo ita kuma Binta saboda baƙar ƙazanta bata iya sharewa koda zai shekara a haka.
Sai da ya kwashe kaya sannan ya samawa Jauhar wajen zaman a saman kujera wacce du ta ɓaɓɓarke soso da katakonta a waje, zama ta yi cike da kyankyami tama maraimaice fuska ta kalli Suhail zata yi magana, sai kawai burum Binta ta hwaɗo kamar wacce aka jefo tana dashare haƙora hannunta riƙe da wani tsohon jug na roba ta cikashi da ruwa har zuba ya ke ta aje a gaban Jauhar.
"Ƴarnan ga ruwa ai ki saki jikinki kamar kina gida, za ki ji daɗin zama da mu wallahi kingammu nan bamuda wa ta matsala hannu bibiyu muke tarɓar baƙi a gidanan."
Murmushin yaƙe Jauhar ta jefeta da shi dan ita sam matar bata kwanta ma ta ba.
"Kai Suhailu nace motar waje ya za'ayi da ita kar yara su kakkarce ma ta mota dan naga sabuwace dal har kashe ido ta ke."
Cike da gajiyawa Suhail ya ce.
"A,a Umma a barta a wajen wataƙila ba jimawa zata yi ba zata tafi."
Yana gama faɗin hakan ya miƙe tsaye tare da nufar hanyar fita, da sauri Jauhar ta miƙe itama har nata yin kwallo da kofin ruwan ya tarwatse a ƙasa da hanzari da damƙi rigar Suhail ta baya har idonta ya soma tara kwalla.
"Babu inda zan je alwala zanyi in dawo, baki ji ansoma kiran sallah ba, ki zauna a wajen Umma kafin indawo."
Kamar ba zata yarda ba sai kuma ta sake shi ba tare da ta koma ta zaunaba, ita ko Binta sai ta shiga ƙoƙarin janta da fira dudan ta sake da ita.
Da yaje masallacima ya jima bai dawo ba, daya dawo ne ya iske waya acijin motar na ƙara, sai da ya kasa kunne da kyau sannan ya ji cikin motarne, kasancewae mukullen na hannunshi ya saka ya buɗe motar ya ɗauko wayar ƙirar iphone 17 darta jakarta ya gani ajiye da kuɗaɗe a barbaje sai kawai ya tatta komi ya saka a jakar sannan ya shiga gida.
Tsugunne ya hangota tsakiyar ɗaki tana jin sallamarshi tai hanzarin tashi tare da nufoshi, fuskarta face-face da hawaye, hannunshi ta kama ta riƙe gam tana sakin sababbin hawaye, baice komi ba yaja hannunta zuwa kan shimfiɗar da Binta ta yi ma ta amma taƙi zama.
"Naje wucewa naji wayarki na ruri shine na tsaya ɗauko miki na haɗo da wanna."
Ya miƙa ma ta da jakar wacce ta kasance me ɗan girma, amsae jakar ta yi tare da zazzagewa nan samabibin daloli suka shiga faɗowa tare da wa ta leda me ɗan girma, da sauri ta soma buɗe ledar ta ciro abin da ke cike, kamar ba ita ta gama kuka yanzu ba ta kalli Suhail da ƴar fara'a akan fuskarta tare da faɗin.
"Ashe nan na aje ta, abaya ce na siya ina ta nemanta bangani ba." Bata jira amsarshi ba ta shiga warwareta tare da miƙewa tsaye ta soma gwadawa da tsayinta, lafiyayyar abayace wacce daga gani ba sai amnfaɗa ba me tsada ce sosai, sai ɗaukar ido ta ke duda ba wani hasken kirki bane a tsakar gidan, linkewa ta yi sannan ta ce.
"Ina so zan yi wanka ina Bathroom?."
Ta yi maganar tana yawata idanuwanta a tsakar gidan tana neman inda za'a kira da wajen wanka........✍️
ƳAN ALBARKA A TAYA NI DA SHARE.
MARYAM STAR ⭐ ƳAR BAIWAR JAJIRTATTU WRITERS💪🏻.
Follow the MARYAM UMAR HAUSA NOVELS BOOKS LIBRARY 📚📚 channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029Vb8OWPtBKfi1C9DGBa13
🌹𝙈𝙐𝙃𝘼𝙎𝙀𝙀𝙉🌹
(𝐿𝑎𝑏𝑎𝑟𝑖𝑛 𝑧𝑢𝑐𝑖𝑦𝑎 𝑚𝑒 𝑐𝑖𝑘𝑒 𝑑𝑎 𝑘𝑢𝑛𝑐𝑖, 𝑟𝑎𝑦𝑢𝑤𝑎 𝑚𝑒 𝑐𝑖𝑘𝑒 𝑑𝑎 𝑡𝑎𝑟𝑖𝑛 𝑘𝑎𝑙𝑢𝑏𝑎𝑙𝑒😔.)
𝙒𝙍𝙄𝙏𝙀 𝘽𝙔
𝙈𝘼𝙍𝙔𝘼𝙈 𝙎𝙏𝘼𝙍⭐.
💪𝙅𝘼𝙅𝙄𝙍𝙏𝘼𝙏𝙏𝙐 𝙒𝙍𝙄𝙏𝙀𝙍,𝙎 𝘼𝙎𝙎𝙊𝘾𝙄𝘼𝙏𝙄𝙊𝙉💪
✊ 𝙏𝙃𝙀 𝙎𝙃𝙄𝘿𝙊𝙍𝙄𝘼 𝙒𝙍𝙄𝙏𝙀𝙍𝙎 𝙏𝙀𝘼𝙈🤝
https://chat.whatsapp.com/Ek6DPlIu4ad0QgTfrn3rab?s=cl&p=a&ilr=4&amv=2
𝙋𝘼𝙄𝘿 𝘽𝙊𝙆
𝙎𝙀𝘼𝙎𝙊𝙉 𝙊𝙉𝙀
𝘾𝙝𝙖𝙥𝙩𝙚𝙧 9
Bin yatsar Suhail ta yi da ido tana kallon wajen da yatsar ta nuna, ware ido ta yi sosai sai kuma ta kalle shi ta kalli wajen kamar zata yi magana sai kuma ta shanye bata ce komi ba, rigar ta sagala a kafaɗarshi sannan ta kalli Zainab da gaba ɗaya hankalinta na kan kuɗin da Jauhar ɗin ta fiddo amma bata kwashe ba.
"Am Sister please bani towel da takalmin wanka, ki haɗo min da sauran kayan wankan please."
Kallon juna Zainab da Fati suka yi sannan Zainab ta tashi ta shiga ɗaki, ba jimawa sai gata ta fito da ƙaramin kwandon wanka me ɗauke da sabulu da soso, baya Jauhar ta yi tana kallon kwandon cike da kyankyami sai kuma ta maida kallonta ga Suhail daya harɗe hannu a ƙirji fuskarshi aɗan sake yana kallon su.
"Suhail!!!!."
Ta ambaci sunan da wata irin siga, wanda hakan ya saka numfashin Suhail tsayuwar wata a ƙirjinshi, da ƙarfi ya fesar da numfashi sannan ya ɗaga mata gira ɗaya alamar ya dai?.
"Kace ta bani kayan wanka please."
Ta faɗi aɗan shagwaɓe kamar me shirin fashewa da kuka.
"Zainab bata kayan wanka." ya faɗa a taƙaice yana ɗauke gai zuwa gefe.
"Yo Suhail idan ba naka zan ɗauko ma ta ba kasan de iya wannan muke da."
Cikin rashin sanin abin yi ya ce.
"Ɗauko mata nawa ɗin."
Yana gama faɗin hakan yasoma ƙoƙarin janye hannu sa daga cikin nata, amma mi sai ta ƙara riƙeshi katamau tana girgiza kai, gaba ɗaya ya rasa abin yi zai iya cewa wannan shine first time da hannun wata mace ya taɓa jikinshi da sanin shi ba tare da ya shiryawa hakan ba, gaba ɗaya kanshi ya kulle katamau abubuwa biyu na ƙoƙarin haɗe mashi a lokaci ɗaya, cike da gajiya ya sauke idonsa akanta sannan ya ce.
"Please sakeni kije kiyi wankan."
Bata so hakan ba sam amma babu yanda zata yi hakanan ta sake shi tana ji kamar idan ya matsa daga wajenta wani abu marar daɗi zai iya faruwa da ita.
Ta ɗauki mintuna biyu tana kallon kewayen kamar ba zata shiga ba, ko mi ta tuna sai kuma ta shiga.
Lumshe ido Suhail ya yi yanajin kanshi naɗan sara mashi na surutun da ya yi me ɗan tsayi, dan surutu ba al'adarsa bace ko a wajen kasuwancinshi baya surutu sosai sai idan ta kama balle a gida da bawani samun sakin fuska ya ke ba, damƙar rigar data sagala mashi yayi tare da nufar wajen da ta zazzage jakarta, akan idonshi gaya Fati ta zare dala ɗaya baice da ita komi ba ya shiga tattara sauran yana mayar mata a jakar, sai lokacin yai danasanin ɗauko ma ta jakar kamar ya manta da su waye ƴan gidansu, musamman idan sukaga kuɗi ko waje me maiƙo.
Sautin hito ne ya daki dodon kunansa a daidai sanda ya ɗago yana zuge zif ɗin jakar, Hamza ya gani tsaye a bayanshi cikin shiga irinta gayu, kannan an tara suma an mummurɗeta kamar ƙuda wai ahakan du cikin gayu ne, yana wani boƙarewa ya kankwashe murya irin guy ɗinan sannan ya ce.
"Hi Suhail naga wata farar sol me kwarjini a waje, shine ake sanar min wai ai kai kazo da ita shine nace harka ta samu ba zaka neme ni ba haba Broth ka daina haka, kasan mu masu fita cilling dole sai da irin wanna, ammafa wallahi tayi iya yi wannan daidai wankan gobe wallahi Allah, to ya ne guy zaka yi mana ehhhh yane ni da freinds ɗina muɗan fantama."
Hamza ya yi maganar yana lallankwashe jiki.
Murya a sanyaye Suhail ya ce
"Haba Hamza sau nawa zan yi maka magana akan rashin yin sallama, sai kace gidan arna zaka shigo mana kana fito."
"Kuturun..... waye kuma Hamza ba daɗin ji, gaskiya Suhail kana min yawa fa iya wuya ya zaka dinga kurana da wannan sunan kamar wani lezy gaskiya karka sake bana so, idan ba zaka kira ni da Handsome ba to ka daina kirana nayafe wallahi."
Ya faɗa yana sauya fuska daga fara'a zuwa ɗaure fuska.
Girgiza kai kawai Suhail ya yi tare da nufar ɗakin sa yana nemawa Hamza sauƙi a lamurransa.
Binta data laɓe daga tagar ɗaki tana leƙensu ta kwalla kiran Hamza da sauri haɗe da yafito shi tana ƴar murya, a maimakon ya hanzarta sai ya tsaya ƙanun surutai kafin ya shiga ɗakin.
LEGOS NIGERIA
AGEGE.
"Ƙwarfeshi ta baya,,,, yauwa naushi cikinshi, lanƙwasa hannayensa ka dira ta kansa,, yeeeeeeeeeeeee Zaki, Zaki, Zaki, Sarkina ka yi nasara kamar dai kullum."
A bin da ɗan mitsitsin bakinta ke faɗi kenan da ƙarfin sauti, yayinda siraran hannayenta suka shiga mommotsawa tare da kai duka a duk inda ta samu, gaba ɗaya zanin jikinta ya nannaɗe, fararen cinyoyinta a waje.
Kallon-kallo mutanen da ke tsaitsaye cirko-cirko kusa da ita suka soma yi, cikinsu an rasa wanda zai kusanceta, a zahiri barci ta ke amma doke-doken da take kaiwa da iya ƙardinta zaisa ka zaci iskokai gareta suka tashi.
Wani kyamusashe magidancine ya matsa kuda da ita, a daidai sanda ta ɗaga ƙafarta da iya ƙarfinta ta kai zazzafan harbi, ya yi ƙoƙarin kaucewa amma bai samu nasara ba, sai da ta kwaɗa mashi ƙafa a gefen fuska kamar ba bamiji ba yai gefe tare da kwalla ƙara yana soshe-soshe, yayinda hankulan mutanen yajen ya koma kanshi nan aka shiga jajanta ma shi.
"Wayyo Allah ta gama da ni ta kasara min muƙamuƙi munafukar, wayyo Allah, wayyo na bani na lalace ni Mamman."
Binta ta faɗi bakinta a washe, shiga ɗakin Suhail ya yi yana jin kallo yanda aka hargitsa ɗakin da kaya babu gyara kamar bola su Zainab basa nan sun fice yawo ita kuma Binta saboda baƙar ƙazanta bata iya sharewa koda zai shekara a haka.
Sai da ya kwashe kaya sannan ya samawa Jauhar wajen zaman a saman kujera wacce du ta ɓaɓɓarke soso da katakonta a waje, zama ta yi cike da kyankyami tama maraimaice fuska ta kalli Suhail zata yi magana, sai kawai burum Binta ta hwaɗo kamar wacce aka jefo tana dashare haƙora hannunta riƙe da wani tsohon jug na roba ta cikashi da ruwa har zuba ya ke ta aje a gaban Jauhar.
"Ƴarnan ga ruwa ai ki saki jikinki kamar kina gida, za ki ji daɗin zama da mu wallahi kingammu nan bamuda wa ta matsala hannu bibiyu muke tarɓar baƙi a gidanan."
Murmushin yaƙe Jauhar ta jefeta da shi dan ita sam matar bata kwanta ma ta ba.
"Kai Suhailu nace motar waje ya za'ayi da ita kar yara su kakkarce ma ta mota dan naga sabuwace dal har kashe ido ta ke."
Cike da gajiyawa Suhail ya ce.
"A,a Umma a barta a wajen wataƙila ba jimawa zata yi ba zata tafi."
Yana gama faɗin hakan ya miƙe tsaye tare da nufar hanyar fita, da sauri Jauhar ta miƙe itama har nata yin kwallo da kofin ruwan ya tarwatse a ƙasa da hanzari da damƙi rigar Suhail ta baya har idonta ya soma tara kwalla.
"Babu inda zan je alwala zanyi in dawo, baki ji ansoma kiran sallah ba, ki zauna a wajen Umma kafin indawo."
Kamar ba zata yarda ba sai kuma ta sake shi ba tare da ta koma ta zaunaba, ita ko Binta sai ta shiga ƙoƙarin janta da fira dudan ta sake da ita.
Da yaje masallacima ya jima bai dawo ba, daya dawo ne ya iske waya acijin motar na ƙara, sai da ya kasa kunne da kyau sannan ya ji cikin motarne, kasancewae mukullen na hannunshi ya saka ya buɗe motar ya ɗauko wayar ƙirar iphone 17 darta jakarta ya gani ajiye da kuɗaɗe a barbaje sai kawai ya tatta komi ya saka a jakar sannan ya shiga gida.
Tsugunne ya hangota tsakiyar ɗaki tana jin sallamarshi tai hanzarin tashi tare da nufoshi, fuskarta face-face da hawaye, hannunshi ta kama ta riƙe gam tana sakin sababbin hawaye, baice komi ba yaja hannunta zuwa kan shimfiɗar da Binta ta yi ma ta amma taƙi zama.
"Naje wucewa naji wayarki na ruri shine na tsaya ɗauko miki na haɗo da wanna."
Ya miƙa ma ta da jakar wacce ta kasance me ɗan girma, amsae jakar ta yi tare da zazzagewa nan samabibin daloli suka shiga faɗowa tare da wa ta leda me ɗan girma, da sauri ta soma buɗe ledar ta ciro abin da ke cike, kamar ba ita ta gama kuka yanzu ba ta kalli Suhail da ƴar fara'a akan fuskarta tare da faɗin.
"Ashe nan na aje ta, abaya ce na siya ina ta nemanta bangani ba." Bata jira amsarshi ba ta shiga warwareta tare da miƙewa tsaye ta soma gwadawa da tsayinta, lafiyayyar abayace wacce daga gani ba sai amnfaɗa ba me tsada ce sosai, sai ɗaukar ido ta ke duda ba wani hasken kirki bane a tsakar gidan, linkewa ta yi sannan ta ce.
"Ina so zan yi wanka ina Bathroom?."
Ta yi maganar tana yawata idanuwanta a tsakar gidan tana neman inda za'a kira da wajen wanka........✍️
ƳAN ALBARKA A TAYA NI DA SHARE.
MARYAM STAR ⭐ ƳAR BAIWAR JAJIRTATTU WRITERS💪🏻.
Follow the MARYAM UMAR HAUSA NOVELS BOOKS LIBRARY 📚📚 channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029Vb8OWPtBKfi1C9DGBa13
🌹𝙈𝙐𝙃𝘼𝙎𝙀𝙀𝙉🌹
(𝐿𝑎𝑏𝑎𝑟𝑖𝑛 𝑧𝑢𝑐𝑖𝑦𝑎 𝑚𝑒 𝑐𝑖𝑘𝑒 𝑑𝑎 𝑘𝑢𝑛𝑐𝑖, 𝑟𝑎𝑦𝑢𝑤𝑎 𝑚𝑒 𝑐𝑖𝑘𝑒 𝑑𝑎 𝑡𝑎𝑟𝑖𝑛 𝑘𝑎𝑙𝑢𝑏𝑎𝑙𝑒😔.)
𝙒𝙍𝙄𝙏𝙀 𝘽𝙔
𝙈𝘼𝙍𝙔𝘼𝙈 𝙎𝙏𝘼𝙍⭐.
💪𝙅𝘼𝙅𝙄𝙍𝙏𝘼𝙏𝙏𝙐 𝙒𝙍𝙄𝙏𝙀𝙍,𝙎 𝘼𝙎𝙎𝙊𝘾𝙄𝘼𝙏𝙄𝙊𝙉💪
✊ 𝙏𝙃𝙀 𝙎𝙃𝙄𝘿𝙊𝙍𝙄𝘼 𝙒𝙍𝙄𝙏𝙀𝙍𝙎 𝙏𝙀𝘼𝙈🤝
https://chat.whatsapp.com/Ek6DPlIu4ad0QgTfrn3rab?s=cl&p=a&ilr=4&amv=2
𝙋𝘼𝙄𝘿 𝘽𝙊𝙆
𝙎𝙀𝘼𝙎𝙊𝙉 𝙊𝙉𝙀
𝘾𝙝𝙖𝙥𝙩𝙚𝙧 9
Bin yatsar Suhail ta yi da ido tana kallon wajen da yatsar ta nuna, ware ido ta yi sosai sai kuma ta kalle shi ta kalli wajen kamar zata yi magana sai kuma ta shanye bata ce komi ba, rigar ta sagala a kafaɗarshi sannan ta kalli Zainab da gaba ɗaya hankalinta na kan kuɗin da Jauhar ɗin ta fiddo amma bata kwashe ba.
"Am Sister please bani towel da takalmin wanka, ki haɗo min da sauran kayan wankan please."
Kallon juna Zainab da Fati suka yi sannan Zainab ta tashi ta shiga ɗaki, ba jimawa sai gata ta fito da ƙaramin kwandon wanka me ɗauke da sabulu da soso, baya Jauhar ta yi tana kallon kwandon cike da kyankyami sai kuma ta maida kallonta ga Suhail daya harɗe hannu a ƙirji fuskarshi aɗan sake yana kallon su.
"Suhail!!!!."
Ta ambaci sunan da wata irin siga, wanda hakan ya saka numfashin Suhail tsayuwar wata a ƙirjinshi, da ƙarfi ya fesar da numfashi sannan ya ɗaga mata gira ɗaya alamar ya dai?.
"Kace ta bani kayan wanka please."
Ta faɗi aɗan shagwaɓe kamar me shirin fashewa da kuka.
"Zainab bata kayan wanka." ya faɗa a taƙaice yana ɗauke gai zuwa gefe.
"Yo Suhail idan ba naka zan ɗauko ma ta ba kasan de iya wannan muke da."
Cikin rashin sanin abin yi ya ce.
"Ɗauko mata nawa ɗin."
Yana gama faɗin hakan yasoma ƙoƙarin janye hannu sa daga cikin nata, amma mi sai ta ƙara riƙeshi katamau tana girgiza kai, gaba ɗaya ya rasa abin yi zai iya cewa wannan shine first time da hannun wata mace ya taɓa jikinshi da sanin shi ba tare da ya shiryawa hakan ba, gaba ɗaya kanshi ya kulle katamau abubuwa biyu na ƙoƙarin haɗe mashi a lokaci ɗaya, cike da gajiya ya sauke idonsa akanta sannan ya ce.
"Please sakeni kije kiyi wankan."
Bata so hakan ba sam amma babu yanda zata yi hakanan ta sake shi tana ji kamar idan ya matsa daga wajenta wani abu marar daɗi zai iya faruwa da ita.
Ta ɗauki mintuna biyu tana kallon kewayen kamar ba zata shiga ba, ko mi ta tuna sai kuma ta shiga.
Lumshe ido Suhail ya yi yanajin kanshi naɗan sara mashi na surutun da ya yi me ɗan tsayi, dan surutu ba al'adarsa bace ko a wajen kasuwancinshi baya surutu sosai sai idan ta kama balle a gida da bawani samun sakin fuska ya ke ba, damƙar rigar data sagala mashi yayi tare da nufar wajen da ta zazzage jakarta, akan idonshi gaya Fati ta zare dala ɗaya baice da ita komi ba ya shiga tattara sauran yana mayar mata a jakar, sai lokacin yai danasanin ɗauko ma ta jakar kamar ya manta da su waye ƴan gidansu, musamman idan sukaga kuɗi ko waje me maiƙo.
Sautin hito ne ya daki dodon kunansa a daidai sanda ya ɗago yana zuge zif ɗin jakar, Hamza ya gani tsaye a bayanshi cikin shiga irinta gayu, kannan an tara suma an mummurɗeta kamar ƙuda wai ahakan du cikin gayu ne, yana wani boƙarewa ya kankwashe murya irin guy ɗinan sannan ya ce.
"Hi Suhail naga wata farar sol me kwarjini a waje, shine ake sanar min wai ai kai kazo da ita shine nace harka ta samu ba zaka neme ni ba haba Broth ka daina haka, kasan mu masu fita cilling dole sai da irin wanna, ammafa wallahi tayi iya yi wannan daidai wankan gobe wallahi Allah, to ya ne guy zaka yi mana ehhhh yane ni da freinds ɗina muɗan fantama."
Hamza ya yi maganar yana lallankwashe jiki.
Murya a sanyaye Suhail ya ce
"Haba Hamza sau nawa zan yi maka magana akan rashin yin sallama, sai kace gidan arna zaka shigo mana kana fito."
"Kuturun..... waye kuma Hamza ba daɗin ji, gaskiya Suhail kana min yawa fa iya wuya ya zaka dinga kurana da wannan sunan kamar wani lezy gaskiya karka sake bana so, idan ba zaka kira ni da Handsome ba to ka daina kirana nayafe wallahi."
Ya faɗa yana sauya fuska daga fara'a zuwa ɗaure fuska.
Girgiza kai kawai Suhail ya yi tare da nufar ɗakin sa yana nemawa Hamza sauƙi a lamurransa.
Binta data laɓe daga tagar ɗaki tana leƙensu ta kwalla kiran Hamza da sauri haɗe da yafito shi tana ƴar murya, a maimakon ya hanzarta sai ya tsaya ƙanun surutai kafin ya shiga ɗakin.
LEGOS NIGERIA
AGEGE.
"Ƙwarfeshi ta baya,,,, yauwa naushi cikinshi, lanƙwasa hannayensa ka dira ta kansa,, yeeeeeeeeeeeee Zaki, Zaki, Zaki, Sarkina ka yi nasara kamar dai kullum."
A bin da ɗan mitsitsin bakinta ke faɗi kenan da ƙarfin sauti, yayinda siraran hannayenta suka shiga mommotsawa tare da kai duka a duk inda ta samu, gaba ɗaya zanin jikinta ya nannaɗe, fararen cinyoyinta a waje.
Kallon-kallo mutanen da ke tsaitsaye cirko-cirko kusa da ita suka soma yi, cikinsu an rasa wanda zai kusanceta, a zahiri barci ta ke amma doke-doken da take kaiwa da iya ƙardinta zaisa ka zaci iskokai gareta suka tashi.
Wani kyamusashe magidancine ya matsa kuda da ita, a daidai sanda ta ɗaga ƙafarta da iya ƙarfinta ta kai zazzafan harbi, ya yi ƙoƙarin kaucewa amma bai samu nasara ba, sai da ta kwaɗa mashi ƙafa a gefen fuska kamar ba bamiji ba yai gefe tare da kwalla ƙara yana soshe-soshe, yayinda hankulan mutanen yajen ya koma kanshi nan aka shiga jajanta ma shi.
"Wayyo Allah ta gama da ni ta kasara min muƙamuƙi munafukar, wayyo Allah, wayyo na bani na lalace ni Mamman."