Sashe 14
Muhaseen Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Jauhar ganin dai ba zata samu abin da ta ke so ba, ga hannunta sai zafi ya ke ma ta sai kawai ta zura rigar abayarta sannan ta fito daga ɗakin, hango shi da ta yi a ƙofar fita ya saka ta bi bayansa, sam tafiyarta babu sauti shiyasa bai ji tsayuwarta ba sai ji da ya yi ta kama hanunsa ta ɗaura ƙanƙame dare da ɗaura kanta a dantsen shi wasu ruwa wanda ya tabbatar da ruwan hawaye ne na sila su na taɓa fatar hannunsa, cak ya tsaya bai yi ko motsi ba shi gaba ɗaya kanshi ya gama kullewa da Jauhar daya ɗaukowa kansa ta zame masa jangwam.
Sake ƙanƙame hannunsa ta yi tare da fashewa da kuka me ɗan sauti a wannan karon, a hankali ya ɗago da kanshi da ya yi masa nauyi sosai ya kalleta sai ya saka hannunshi ɗaya ya kamota tare da tsayar da ita a gabanshi ya tsare ta da rikitattun idanuwan shi, kallon yanda ta ke yin kukan kawai ya ke yana ji da da hali shima da ya yi kukan wataƙila ya samu sauƙin abin da ya ke ji, kama hannunta ya yi da niyar yin magan sai kawai ya ga ta kwace tare da fasa ƙara marar sauti sosai, da sauri ya sake ta yana kallon yanda ta riƙe hannun tana sabunta kukanta.
Cikin tausasa harshe ya ce da ita.
"Kin ji ciwo ne?."
Ɗaga ma shi kai ta yi alamar amsawa tana kuma kallon hannunta data tattare hannun abayar zuwa sama, shima kallon farin siririn hannun ya yi yana iya hango yanda jini ya ɗan taru a ƙasan gwuiwarta ga shi wajen yaɗan tasa alamar kumburi, sai ya ji babu daɗi a ranshi a fili kuma sai ya kalleta cike da kulawa sannan ya ce.
"Mu je a duba miki hannun kin ga ya soma kumbura."
Kallon tsakiyar idanuwansa ta yi da limsasun idanuwanta, tana hango wani da ya yi nisa sosai da rayuwarta, nisan da ta jima tana gudu wajen kamo abin amma yana sake tsere mata, yanayin shiru ya gifta a cikin kanta, yayinda taushin magarsa ya samu wawakeken fili a zuciyarta ya zauna daram, a fili kuma sai ta sake narke fuska tana son sake ganin wannan abin, ba tare da saninta ba sai ta ɗan matae hannun mw ciwo, nan take ta sake furta sautin ƙara, tare da sakin hannun da sauri azaba na baibayeta daga tsakiyar kant har ƙarƙashin ƙafafuwanta, amma ko sau ɗaya bata janye idonta daga gare shi ba, ta yi hakanne dan son sake ganin gilmawar wannan abin a cikin idannuwansa.
Da sauri ya kama hannun na ta cikin rasa abin yi, cike da kulawa ya dinga furta ma ta kalmar sannu babu ƙaƙƙautawa.
Kawai se ta faɗa jikinshi ta ƙanƙameshi da iya ƙarfinta, tana jin wani abu na mata yawo a kansa.
Kulawa abacw da ta yi ƙaura a rayuwarta, tun tashinta bata san wani abu wai shi kulawa ba, kuma bata san ya ake ji idan aka samu wannan kulawar ba, ta rayune a cikin ƙunci da kuka ita kaɗai, ita kaɗai ta ke rayuwarta a du yanda ta zo ma ta, amma a yanzu da ta ke ganin wannan abar data rasa a wajen Suhail sai zuciyarta ta sake yin rauni sosai.
Rintse idnuwansa ya yi cike da gajiyawa, a ɓangare ɗaya yana tuhumar kanshi akan yanda ya turata ta faɗi har ta ji ciwo, ga kuma tausayi da ta bashi tun a ganinshi da ita a ɗazu.
Ƙawa zuci abune da sam Suhail baya da shi, musamman akan jin daɗi na rayuwar duniya, rayuwarshi gaba ɗaya ta ta'laƙƙa wajen nema tare da burin faranta ran wacce ita kaɗai ya ke kallo a matsayin wani na shi, a yanzu kuma da ya shigo da Jauhar a rayuwarsa sai ya ke jin kamar akwai abin da ya ke buƙata, sai de ba zai iya cewa ga abin ba amma tabbas akwai abin da babu shi a lissafinsa kuma rayuwarsa ba zata cika ba sai da wannan abun.....✍🏻
KUYI FOLLOWING WANNAN LIKN ƊIN DOMIN SAMUN DAMAR KARANTA WANNA LITTAFIN DA ZARAR MUN ƊORA
https://whatsapp.com/channel/0029Vb8OWPtBKfi1C9DGBa13
MARYAM STAR ⭐⭐
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/DczAiFp992p78VNoV6tcMo?s=sw&p=a&mlu=3&amv=2
🌹𝙈𝙐𝙃𝘼𝙎𝙀𝙀𝙉🌹
(𝐿𝑎𝑏𝑎𝑟𝑖𝑛 𝑧𝑢𝑐𝑖𝑦𝑎 𝑚𝑒 𝑐𝑖𝑘𝑒 𝑑𝑎 𝑘𝑢𝑛𝑐𝑖, 𝑟𝑎𝑦𝑢𝑤𝑎 𝑚𝑒 𝑐𝑖𝑘𝑒 𝑑𝑎 𝑡𝑎𝑟𝑖𝑛 𝑘𝑎𝑙𝑢𝑏𝑎𝑙𝑒😔.)
𝙒𝙍𝙄𝙏𝙀 𝘽𝙔
𝙈𝘼𝙍𝙔𝘼𝙈 𝙎𝙏𝘼𝙍⭐.
💪𝙅𝘼𝙅𝙄𝙍𝙏𝘼𝙏𝙏𝙐 𝙒𝙍𝙄𝙏𝙀𝙍,𝙎 𝘼𝙎𝙎𝙊𝘾𝙄𝘼𝙏𝙄𝙊𝙉💪
✊ 𝙏𝙃𝙀 𝙎𝙃𝙄𝘿𝙊𝙍𝙄𝘼 𝙒𝙍𝙄𝙏𝙀𝙍𝙎 𝙏𝙀𝘼𝙈🤝
https://chat.whatsapp.com/Ek6DPlIu4ad0QgTfrn3rab?s=cl&p=a&ilr=4&amv=2
𝙋𝘼𝙄𝘿 𝘽𝙊𝙆
𝙎𝙀𝘼𝙎𝙊𝙉 𝙊𝙉𝙀
𝘾𝙝𝙖𝙥𝙩𝙚𝙧 12.
"Sannu zo mu je a duba miki."
Ya faɗi yana cirota daga jikinshi a hankula.
"A,ah Suhail lafiya dai mike faruwa??.".
Maganar Hamza ta tsaya lokacin da hasken fitilar ƙaramar wayarsa ya haske masa rabin fuskar Jauhar da ke gaban Suhail, da wani irin sauri ya ƙarasa yana sake hasketa da kyau.
"Kam bala'i mi zan gani kamar farar baturiya a gidanmu, ashe de Binta ta yi gaskiya."
Ya faɗa yana buɗe duka girman idanuwansa akan kyakkyawar farar fuskar Jauhar, matsawa ya kuma yi sosai tare da safa
kafaɗar Suhail mamaki bayyane akan fuskarshi.
Jauhar tuni hasken fitilar Hamza ya haske ma ta idanuwa ya zama bata gani sai faman saka hannu ta ke tana karewa, yayin da ƙyalƙyalin stons ɗin da aka yiwa rigarta ado da su suka shiga walwali, sai hakan ya bawa Suhail damar ƙare mata kallo, yana kallon yanda Allah ya zuba ruwan kyau a gareta, fara ce sol wanke hannu ka taɓa doguwa me siririn jiki, yayin da ta ke da cika a sama da ƙasa ma sha Allah, idanuwanta da ke ɗauke da ruwan hawaye a cikinsu yayin da dogayen gargasar saman idon suka jiƙe da hawayenta sai hakan ya saka idanuwanta yin kyau sosai a ganin Suhail, shagala ya yi wajen kallon yanda ta ke ƙifta idanuwan saboda hasken da ya dallare ta, har bai ji maganar da Hamza ya yi ma shi ba, sai da ya sake maimaitawa.
"Suhail wai ina ka samo wannan cikar ne, gaskiya an tafi da ni wallahi."
Maganar Suhail ce ta dawo da shi duniyar zahiri, da sauri ya janye idonshi daga kanta ya kuma janye hasken wayar Hamza ba tare da ya ce komi ba ya juya zuwa cikin gida, da sauri Jauhar ta bi bayanshi tare da jerawa da shi tana sauke ajiyar zuciya, saura kaɗan ta yi karo da bango kasancewar sam bata gani, da taimakon Suhail daya janyo ta baya ta lura da abin da ke shirin faruwa.
Hamza ma biyo bayansu ya yi yana ta faman washe baki ganin zuƙeƙiyar Baby a gidansu.
Zai iya ƙirga sau nawa ya taɓa shiga ɗakin Suhail tun tasowarsu, du da gida ɗaya suke amma sam baya shiga sabgogin Suhail ɗin, dan a kullum yana kallon kansa a matsayin gaba da Suhail.
BANANA ISLAND
Sautin shiru ne ya gifta ta cikin kansa, yayinda masarrafar tunaninsa ta soma dawowa aiki, sannu a hankali abubuwa masu tarin yawa suka soma giftawa ta cikin kansa, cikin ikon Allah ya soma motsawa tare da buɗe idanuwanshi, ya jima kwance a wajen bai gama dawowa hayyacinsa ba sai bayan shuɗewar mintuna, yunƙurawa ya yi da niyar tashi zaune amma mi, a maimakon ya ji an rirriƙe shi kamar baya sai ya ji ya yunƙura ya miƙe sawai da shi, ko da ya tashi tsaye sai ya ji shi ya tsayu akan diga-diganshi yana jin kamar an cire wani abu me kama da ƙaton dutse da ya danne shi, juyi ya soma yi yana dudduba jikinshi da kyau, abin mamaki sai ya ke jinshi a cikakken mutum kamar kowa, da sassarfa ya soma takawa zuwa gaban wawakeken miro, tae ya ke kallon idanuwansa da suka sauya launi daga jajaye zuwa farare tas kamar madara, lumshe su ya yi tare da sake buɗewa, amma still sai ya sake ganin sun washe sun yi fari tas kamar yanda suke a can baya, yawatawa da idanuwansa ya soma yi a duka sassan jikinsa ta jikin miro amma kuma sai ya sake ganin wasu sauye-sauyen a tattare da shi, akwai wani baƙin abu da yake firfitowa a jikinsa musamman a saitin jijiyoyi amma sanzu daya dudduba baiga komi ba, babu su duk sun ɓace.
Komawa da baya ya yi ya zauna daɓas a san bed cikin wani irin yanayi, da sauri ya tashi tare da kallon fari ƙar ɗin zanin gadon amma amma mi, sai yaga babu wannan jikin da ya zubar, shanye mamakinsa ya yi tare da kwashe zanin ya kai shi laundry ya aje, sannan ya shiga toilet ya sake yin wanka ya fito jallabiya kawai ya saka ya fita jin ƙarar alarm ɗin lokacin sallar asuba na dokawa.
Yawata idanuwansa ya ke akan tarin ma'aikatan gidan maza da ke ta firfitowa domin zuwa sallah, sai ya ji wani alfahari na kama shi gami da jin daɗin yanda du wani makusancinsa baya wasa da yin sallah akan lokaci.
Yau da ƙarfinsa ya ke gabatar da ibada cike da shauƙi, fuskarshi a sake babu komi a cikinta babu wannan ɗaurewar da ya ke kuma babu murmushi ammadai a sake ta ke, hatta ma'aikansa yau sunga sauyi domin kuwa musabiha ya dinga yi da su hand to hand lokacin da aka fito daga sallah.
Saleem kuwa bakinshi har kunne sosai ya karanci sauyi daga wajen oganshi, ko da suka koma cikin gida umarni Muhaseen ya bayar akan a dafa abinci me rai da motsi a yi sadaka.
"Sarki."
Saleem ya kira shi muryarsa da alamun nishaɗi a ciki.
"Uwummm."
Ya amsa shi tare da ɗaga fararen idanuwansa ya zuba su akan Saleem ɗin.
"Ko da sau ɗaya ne dan Allah."
Ya marairaice fuska kamar zai yi kuka.
Daga gira Muhaseen ya yi alamar tamba.
"Murmushi, ina so inga murmushi akan fuskarka aƙalla koda sau ɗaya ne."
Ya faɗa yana sake marairaicewa.
Ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya Muhaseen ya yi tare da aje hannayensa akan cinyoyinshi ya kafe Saleem da mayun idanuwanshi masu cike da kwarjini.
Sake ƙanƙame hannunsa ta yi tare da fashewa da kuka me ɗan sauti a wannan karon, a hankali ya ɗago da kanshi da ya yi masa nauyi sosai ya kalleta sai ya saka hannunshi ɗaya ya kamota tare da tsayar da ita a gabanshi ya tsare ta da rikitattun idanuwan shi, kallon yanda ta ke yin kukan kawai ya ke yana ji da da hali shima da ya yi kukan wataƙila ya samu sauƙin abin da ya ke ji, kama hannunta ya yi da niyar yin magan sai kawai ya ga ta kwace tare da fasa ƙara marar sauti sosai, da sauri ya sake ta yana kallon yanda ta riƙe hannun tana sabunta kukanta.
Cikin tausasa harshe ya ce da ita.
"Kin ji ciwo ne?."
Ɗaga ma shi kai ta yi alamar amsawa tana kuma kallon hannunta data tattare hannun abayar zuwa sama, shima kallon farin siririn hannun ya yi yana iya hango yanda jini ya ɗan taru a ƙasan gwuiwarta ga shi wajen yaɗan tasa alamar kumburi, sai ya ji babu daɗi a ranshi a fili kuma sai ya kalleta cike da kulawa sannan ya ce.
"Mu je a duba miki hannun kin ga ya soma kumbura."
Kallon tsakiyar idanuwansa ta yi da limsasun idanuwanta, tana hango wani da ya yi nisa sosai da rayuwarta, nisan da ta jima tana gudu wajen kamo abin amma yana sake tsere mata, yanayin shiru ya gifta a cikin kanta, yayinda taushin magarsa ya samu wawakeken fili a zuciyarta ya zauna daram, a fili kuma sai ta sake narke fuska tana son sake ganin wannan abin, ba tare da saninta ba sai ta ɗan matae hannun mw ciwo, nan take ta sake furta sautin ƙara, tare da sakin hannun da sauri azaba na baibayeta daga tsakiyar kant har ƙarƙashin ƙafafuwanta, amma ko sau ɗaya bata janye idonta daga gare shi ba, ta yi hakanne dan son sake ganin gilmawar wannan abin a cikin idannuwansa.
Da sauri ya kama hannun na ta cikin rasa abin yi, cike da kulawa ya dinga furta ma ta kalmar sannu babu ƙaƙƙautawa.
Kawai se ta faɗa jikinshi ta ƙanƙameshi da iya ƙarfinta, tana jin wani abu na mata yawo a kansa.
Kulawa abacw da ta yi ƙaura a rayuwarta, tun tashinta bata san wani abu wai shi kulawa ba, kuma bata san ya ake ji idan aka samu wannan kulawar ba, ta rayune a cikin ƙunci da kuka ita kaɗai, ita kaɗai ta ke rayuwarta a du yanda ta zo ma ta, amma a yanzu da ta ke ganin wannan abar data rasa a wajen Suhail sai zuciyarta ta sake yin rauni sosai.
Rintse idnuwansa ya yi cike da gajiyawa, a ɓangare ɗaya yana tuhumar kanshi akan yanda ya turata ta faɗi har ta ji ciwo, ga kuma tausayi da ta bashi tun a ganinshi da ita a ɗazu.
Ƙawa zuci abune da sam Suhail baya da shi, musamman akan jin daɗi na rayuwar duniya, rayuwarshi gaba ɗaya ta ta'laƙƙa wajen nema tare da burin faranta ran wacce ita kaɗai ya ke kallo a matsayin wani na shi, a yanzu kuma da ya shigo da Jauhar a rayuwarsa sai ya ke jin kamar akwai abin da ya ke buƙata, sai de ba zai iya cewa ga abin ba amma tabbas akwai abin da babu shi a lissafinsa kuma rayuwarsa ba zata cika ba sai da wannan abun.....✍🏻
KUYI FOLLOWING WANNAN LIKN ƊIN DOMIN SAMUN DAMAR KARANTA WANNA LITTAFIN DA ZARAR MUN ƊORA
https://whatsapp.com/channel/0029Vb8OWPtBKfi1C9DGBa13
MARYAM STAR ⭐⭐
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/DczAiFp992p78VNoV6tcMo?s=sw&p=a&mlu=3&amv=2
🌹𝙈𝙐𝙃𝘼𝙎𝙀𝙀𝙉🌹
(𝐿𝑎𝑏𝑎𝑟𝑖𝑛 𝑧𝑢𝑐𝑖𝑦𝑎 𝑚𝑒 𝑐𝑖𝑘𝑒 𝑑𝑎 𝑘𝑢𝑛𝑐𝑖, 𝑟𝑎𝑦𝑢𝑤𝑎 𝑚𝑒 𝑐𝑖𝑘𝑒 𝑑𝑎 𝑡𝑎𝑟𝑖𝑛 𝑘𝑎𝑙𝑢𝑏𝑎𝑙𝑒😔.)
𝙒𝙍𝙄𝙏𝙀 𝘽𝙔
𝙈𝘼𝙍𝙔𝘼𝙈 𝙎𝙏𝘼𝙍⭐.
💪𝙅𝘼𝙅𝙄𝙍𝙏𝘼𝙏𝙏𝙐 𝙒𝙍𝙄𝙏𝙀𝙍,𝙎 𝘼𝙎𝙎𝙊𝘾𝙄𝘼𝙏𝙄𝙊𝙉💪
✊ 𝙏𝙃𝙀 𝙎𝙃𝙄𝘿𝙊𝙍𝙄𝘼 𝙒𝙍𝙄𝙏𝙀𝙍𝙎 𝙏𝙀𝘼𝙈🤝
https://chat.whatsapp.com/Ek6DPlIu4ad0QgTfrn3rab?s=cl&p=a&ilr=4&amv=2
𝙋𝘼𝙄𝘿 𝘽𝙊𝙆
𝙎𝙀𝘼𝙎𝙊𝙉 𝙊𝙉𝙀
𝘾𝙝𝙖𝙥𝙩𝙚𝙧 12.
"Sannu zo mu je a duba miki."
Ya faɗi yana cirota daga jikinshi a hankula.
"A,ah Suhail lafiya dai mike faruwa??.".
Maganar Hamza ta tsaya lokacin da hasken fitilar ƙaramar wayarsa ya haske masa rabin fuskar Jauhar da ke gaban Suhail, da wani irin sauri ya ƙarasa yana sake hasketa da kyau.
"Kam bala'i mi zan gani kamar farar baturiya a gidanmu, ashe de Binta ta yi gaskiya."
Ya faɗa yana buɗe duka girman idanuwansa akan kyakkyawar farar fuskar Jauhar, matsawa ya kuma yi sosai tare da safa
kafaɗar Suhail mamaki bayyane akan fuskarshi.
Jauhar tuni hasken fitilar Hamza ya haske ma ta idanuwa ya zama bata gani sai faman saka hannu ta ke tana karewa, yayin da ƙyalƙyalin stons ɗin da aka yiwa rigarta ado da su suka shiga walwali, sai hakan ya bawa Suhail damar ƙare mata kallo, yana kallon yanda Allah ya zuba ruwan kyau a gareta, fara ce sol wanke hannu ka taɓa doguwa me siririn jiki, yayin da ta ke da cika a sama da ƙasa ma sha Allah, idanuwanta da ke ɗauke da ruwan hawaye a cikinsu yayin da dogayen gargasar saman idon suka jiƙe da hawayenta sai hakan ya saka idanuwanta yin kyau sosai a ganin Suhail, shagala ya yi wajen kallon yanda ta ke ƙifta idanuwan saboda hasken da ya dallare ta, har bai ji maganar da Hamza ya yi ma shi ba, sai da ya sake maimaitawa.
"Suhail wai ina ka samo wannan cikar ne, gaskiya an tafi da ni wallahi."
Maganar Suhail ce ta dawo da shi duniyar zahiri, da sauri ya janye idonshi daga kanta ya kuma janye hasken wayar Hamza ba tare da ya ce komi ba ya juya zuwa cikin gida, da sauri Jauhar ta bi bayanshi tare da jerawa da shi tana sauke ajiyar zuciya, saura kaɗan ta yi karo da bango kasancewar sam bata gani, da taimakon Suhail daya janyo ta baya ta lura da abin da ke shirin faruwa.
Hamza ma biyo bayansu ya yi yana ta faman washe baki ganin zuƙeƙiyar Baby a gidansu.
Zai iya ƙirga sau nawa ya taɓa shiga ɗakin Suhail tun tasowarsu, du da gida ɗaya suke amma sam baya shiga sabgogin Suhail ɗin, dan a kullum yana kallon kansa a matsayin gaba da Suhail.
BANANA ISLAND
Sautin shiru ne ya gifta ta cikin kansa, yayinda masarrafar tunaninsa ta soma dawowa aiki, sannu a hankali abubuwa masu tarin yawa suka soma giftawa ta cikin kansa, cikin ikon Allah ya soma motsawa tare da buɗe idanuwanshi, ya jima kwance a wajen bai gama dawowa hayyacinsa ba sai bayan shuɗewar mintuna, yunƙurawa ya yi da niyar tashi zaune amma mi, a maimakon ya ji an rirriƙe shi kamar baya sai ya ji ya yunƙura ya miƙe sawai da shi, ko da ya tashi tsaye sai ya ji shi ya tsayu akan diga-diganshi yana jin kamar an cire wani abu me kama da ƙaton dutse da ya danne shi, juyi ya soma yi yana dudduba jikinshi da kyau, abin mamaki sai ya ke jinshi a cikakken mutum kamar kowa, da sassarfa ya soma takawa zuwa gaban wawakeken miro, tae ya ke kallon idanuwansa da suka sauya launi daga jajaye zuwa farare tas kamar madara, lumshe su ya yi tare da sake buɗewa, amma still sai ya sake ganin sun washe sun yi fari tas kamar yanda suke a can baya, yawatawa da idanuwansa ya soma yi a duka sassan jikinsa ta jikin miro amma kuma sai ya sake ganin wasu sauye-sauyen a tattare da shi, akwai wani baƙin abu da yake firfitowa a jikinsa musamman a saitin jijiyoyi amma sanzu daya dudduba baiga komi ba, babu su duk sun ɓace.
Komawa da baya ya yi ya zauna daɓas a san bed cikin wani irin yanayi, da sauri ya tashi tare da kallon fari ƙar ɗin zanin gadon amma amma mi, sai yaga babu wannan jikin da ya zubar, shanye mamakinsa ya yi tare da kwashe zanin ya kai shi laundry ya aje, sannan ya shiga toilet ya sake yin wanka ya fito jallabiya kawai ya saka ya fita jin ƙarar alarm ɗin lokacin sallar asuba na dokawa.
Yawata idanuwansa ya ke akan tarin ma'aikatan gidan maza da ke ta firfitowa domin zuwa sallah, sai ya ji wani alfahari na kama shi gami da jin daɗin yanda du wani makusancinsa baya wasa da yin sallah akan lokaci.
Yau da ƙarfinsa ya ke gabatar da ibada cike da shauƙi, fuskarshi a sake babu komi a cikinta babu wannan ɗaurewar da ya ke kuma babu murmushi ammadai a sake ta ke, hatta ma'aikansa yau sunga sauyi domin kuwa musabiha ya dinga yi da su hand to hand lokacin da aka fito daga sallah.
Saleem kuwa bakinshi har kunne sosai ya karanci sauyi daga wajen oganshi, ko da suka koma cikin gida umarni Muhaseen ya bayar akan a dafa abinci me rai da motsi a yi sadaka.
"Sarki."
Saleem ya kira shi muryarsa da alamun nishaɗi a ciki.
"Uwummm."
Ya amsa shi tare da ɗaga fararen idanuwansa ya zuba su akan Saleem ɗin.
"Ko da sau ɗaya ne dan Allah."
Ya marairaice fuska kamar zai yi kuka.
Daga gira Muhaseen ya yi alamar tamba.
"Murmushi, ina so inga murmushi akan fuskarka aƙalla koda sau ɗaya ne."
Ya faɗa yana sake marairaicewa.
Ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya Muhaseen ya yi tare da aje hannayensa akan cinyoyinshi ya kafe Saleem da mayun idanuwanshi masu cike da kwarjini.