← Book details Muhaseen Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 23 OF 26

Sashe 23

Muhaseen Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tsaye ya ke a gaban wani baro da aka shaƙe tab da kayan gwangwan suna ta tafka ciki, kamar daga sama ya hango Salamatu ta taho a guje, ɓata fuska ya yi a daidai sanda take gab da ƙarasowa wajen ya tare da ta faɗin.
"Ke dan Ubanki bana hana ki fitowa a haka ba, jibe ki kamar mahaukaci kai ko kallabi babu."
Cikin shesheƙar gudun da ta yi ta ce.
"Baba ka zo gida ba lafiya, Umma ce ta faɗi tanata wani abu na ban tsoro."
Salati ya rafka tare da kiran wani yaro ya ce da shi ya zo suyi ciniki zai je ya dawo.
A hanzarce ya bi bayan Salamatu sai zabga sauri ya ke kamar zai tashi sama, ga gaban shi da ke ta faɗuwa.
Yanda Salamatu ta barta haka ta isketa yashe a ƙasa, isowar Mamman babu jimawa ko gama shiga ɗakin bai yi ba kan shi ya sara da wani irin ƙarfi nan take ya durƙushe a ƙasa sannan cikin wata iriyar murya wacce sam bata yi kama da tashi ba aka soma faɗin.
"Allah ya ja zamanin Gimbiya kuma Sarauniya, takawar ki lafiya giwar Amale, ambuga da ke am barki kece a gaba kece a baya maƙiyanki fadawanki."
Haka aka ci gaba da jeranto kirari ga Umma da ke kwance har lokacin, yayin da Mamman ke gurfane kan shi a ƙasa.
Gaba ɗaya sai mutanen ɗakin suka sha jinin jikin su, domin dai sun fara fahimtar abin da ke faruwa da alama Umma nada iskokai kuma sune suka tashi yanzu haka.
Fitsari ne kawai ya rage Uwale taba yi ba dan tana da mugun tsoron Aljannu, bugu da ƙari kuma wata ƙara da suka soma jiyowa na tashi daga saman ɗakin busa ce irinta algaita da kuma ƙarar takun dawakai harma da haniniyarsu, gaba ɗaya ƙarar kamar a cikin ɗakin ake yin ta, sai da suka toshe kunnuwansu da sautin ke shiga sosai har yana ƙoƙarin saka musu ciwon kai.

BAYAN MINTUNA ARBA'IN.
Sannu a hankula Umma ta shiga buɗe idanuwanta a hankula, yayin da haske ranar da ya soma shigowa ɗakin ya yi jagora wajen sukar idanuwanta, da sauri ta sake kulle su tana jin yanda hasken ya shiga cikin su kai tsaye, mitsa ƙafarta ta soma yi wacce ta ji kamar an kunce ta daga ɗaurin gwaggwaɓar sarƙa, sai kuma ta ɗaga hannunta da shima ya yi mata nauyi sosai, tambayar zuciyarta ta soma yi.
'Shin mike faruwa da ita.'
Sannan ta yunƙura tare da tashi zaune ɗangwara gwas, ware fararen idanuwanta ta yi tare da bin mutanen da suka baibayeta da kallo irinna, 'Mi kuke yi a nan.'
Bama kallon da suke yi mata bane abin ɗaure kai sannun da suke jeranta mata gamu da fatan sauƙi shi yafi komi dagula lissafinta.
Tana so ta buɗe baki ta yi magana amma ƙarfin jini irinna Sarauta da ke yawo a sassan jiki da jijiyoyinta ha hana faruwar hakan, dafe kanta ta yi da ƙarfi kafin ta ce cikin rarrabewar harshe.
"Mi nike yi anan, su waye ku."
Tsit masarrafar tunanin Najla wacce ke durƙushe a gaban Ummar ta tsaya cak da aiki lokacin da Ummar ta jefo wannan tambayar, ba wai bata san Ummar ba ɗaya daga cikin ahalin gidan ba ce, sarai ta san da hakan kuma bata manta ba sai de a yanayin yanda Ummar ta yi maganar sai ta ruɗar da ita, sau uku tana buɗe baki zata yi magana amma kuma sai hakan ya gagara, ga wani kwarjinin Ummar da ya cika lakin gaba ɗaya.
"Ummana."
Najla ta ƙwato maganar daga can ƙasan numfashin ta dake barazanar ɗaukewa a ko wanne lokaci.
Kalmar Umma kalma ce da tasan ana amfani da ita wajen kiran wacce ta taka matsayin uwa, ko kuma aka raɗa mata wannan sunan, sai de a iya sanin ta sam batada wanda ya taɓa koda kwatanta kiranta da wannan sunan ba, a yanzu kuma da aka kirata da sunan sai ta ji wani abu me nauyi ya faɗo daga zuciyarta ya shiga bajewa a ƙirjinta, yayin da kanta ya sara da ƙarfin gaske nan take shuɗaɗun abubuwa suka shifa dawowa a kwanyar ta daki-daki.

MAFARIN ƘADDARA.

Komi ya faru ne a tsakiyyar daren ranar takata, inda Sarauniya Aishatu ta farka daga barcin da ya ɗauke ba tare data shiryawa hakan ba, idan ba zata manta ba tana kwance ne asaman gadonta na alfarma yayinda tagwayen yaranta ke shimfiɗe a kusa da su, ba zata iya tuna abin da ya sakata mancewa da azkar da kuma alwalar da take yi duk daren duniya musamman idan zata kwanta barci ba, kawai de taji kasala na baibaye ta yayin da Jakadiya ta kawo mata yaranta tagwayen da suka yi marice a fadar Sarki, kafin barci ya ɗauke ta ta kasance cikin yi musu wasanni kamar yanda ta sabar musu duk farkon dare kafin suyi barci, kuma zata tuna yanda ta mulke jikunan su da ruwan addu'ar da aka tanada domin su.
Ta farka a furgice cikin barcin daya kwasheta yayin da ta soma ji ana kiran sunanta ta ko wace kusurwa da ke ɗaƙin, a gigice ta farka cike da razani ta soma juye-juye tana neman wanda ke kiran nata, sai de kuma muryoyi ne mabanbantan data gasa tantancewa, ga wani abu me kama da magana da ke janta zuwa hanyar fita, daga ita sai rigar barcin jikinta ta soma takawa cikin hanzari tana yin hanyar fita daga ɗakin, sai da ta gama ficewa daga manyan falukan gidan ta fita cikin tsakar gida sannan ta kai dubanta gabas da yamma kudu da arewa amma ta rasa hanyar da zata bi ta fice zuwa wajen da ake kiranta, kiran da idan ta ji shi take jin kwanyarta na tafarfasa tana fita daga hayyacinta, idonta ne ya sauka akan dogon ginin katangar wajen, bata yi wata-wata ba ta nufi wajen gaban-gaban ta ɗane katangar tare da doma haurawa har ta samu ta haye da kyar, dira ta yi a ƙasa cikin rashin sa'a sai ta dira akan ƙafarta ta haggu nan ta amsa da tsananin azaba, amma jin ana sake jiranta ya saka ta miƙe tana ɗingisa ƙafar ta soma takawa a wahale, juyawa ta yi tare da kallon bayan ginin masarautar sai kawai taga wuta me tartsatsi na tashi da sauri ta kawar da kanta tare da cigaba da tafiya.
Ba zata iya misilta tsayin lokacin data kwashe tana tafiya ba, sai de zata iya ƙiyasta baƙar azabar da ta ke cikin sha a tafiyar da take yi, gazawa ta risketa ne a daidai lokacin da sautin wannan muryar ta ɗauke gaba ɗaya, nan take ta fice a hayyacinta tare da durƙushewa a ƙasan wajen da bata damu da ko ina bane, nan take ta baje tana dakin numfarfashi, tana iya ganin hasken da ke hasketa tun daga can nesa ta cikin idanuwanta da suka yi biji-biji, kuma tana jin sanda wani abu me ƙara ya ja ya tsaya a kusa da ita, abin da bata tantance ba shine, shin motar ta bi ta kanta koko.?.....✍🏻

ALHAMDULILLAH MUNA GAB DA KAMMALA FREE PAGE ZAMU SHIGA PAID PAGES KU GARZAYA KU BIYA KUƊAƊEN KU DOMIN SAMUN DAMAR KARANTA WANNAN LABARIN TUN DAGA FARKO HAR ƘARSHE.

MARYAM STAR⭐⭐ƳAR BAIWAR JAJIRTATTU WRITERS

Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/DczAiFp992p78VNoV6tcMo?s=sw&p=a&mlu=3&amv=2
🌹𝙈𝙐𝙃𝘼𝙎𝙀𝙀𝙉🌹
(𝐿𝑎𝑏𝑎𝑟𝑖𝑛 𝑧𝑢𝑐𝑖𝑦𝑎 𝑚𝑒 𝑐𝑖𝑘𝑒 𝑑𝑎 𝑘𝑢𝑛𝑐𝑖, 𝑟𝑎𝑦𝑢𝑤𝑎 𝑚𝑒 𝑐𝑖𝑘𝑒 𝑑𝑎 𝑡𝑎𝑟𝑖𝑛 𝑘𝑎𝑙𝑢𝑏𝑎𝑙𝑒😔.)

𝙒𝙍𝙄𝙏𝙀 𝘽𝙔
𝙈𝘼𝙍𝙔𝘼𝙈 𝙎𝙏𝘼𝙍⭐.

💪𝙅𝘼𝙅𝙄𝙍𝙏𝘼𝙏𝙏𝙐 𝙒𝙍𝙄𝙏𝙀𝙍,𝙎 𝘼𝙎𝙎𝙊𝘾𝙄𝘼𝙏𝙄𝙊𝙉💪

✊ 𝙏𝙃𝙀 𝙎𝙃𝙄𝘿𝙊𝙍𝙄𝘼 𝙒𝙍𝙄𝙏𝙀𝙍𝙎 𝙏𝙀𝘼𝙈🤝
https://chat.whatsapp.com/Ek6DPlIu4ad0QgTfrn3rab?s=cl&p=a&ilr=4&amv=2

𝙋𝘼𝙄𝘿 𝘽𝙊𝙆
𝙎𝙀𝘼𝙎𝙊𝙉 𝙊𝙉𝙀

𝘾𝙝𝙖𝙥𝙩𝙚𝙧 20
Last page
Tsugunnawa a gabanta matuƙin motar ya yi tare da soma faɗin.
"Baiwar Allah lafiyarki ƙalau kuwa, Innalillahi wa'inna ilaihi raju'u."
Sai kuma ya tashi tsaye tare da soma zagaye wajen yana dube-dube ko zai iya ganin ɗan uwanta wataƙila hatsari suka yi a mota, amma har ya ƙaraci dube-duben shi bai ga kowa ba kuma bai ga wata alama da ke nuni da anyi hatsari akan hanyar ba.
Dama haka ya ke, ya yi sabo da ganin tashin hankula iri-iri sannan shi mutum ne me tsananin tausayi baya tsoro ko shakkar za'a iya cutar da shi garin taimako, dan haka sai ya koma wajen ta ya ciciɓe ta ya saka a mota ya bawa motar wuta cike da warewa yaci gaba da tuƙi, kasancewar lokacin dare ne sai ya samu damar sharara gudu yanda ya ke so yana yi yana hangen ta ganin bata motsa ba amma kuma tana numfashi a wahalce.
Sai gab da subahi suka ida cikin garin Legos kai tsaye ya wuce wata unguwa wacce mutane keta hada-hadarsu kamar rama, a daidai wani ɗan surƙuƙin gida ya ci burki tare da matsa horn da ƙarfi, nan take wata mata ita da wasu yara suka firfito daga ciki fuskokinsu cike da fara'a suka shiga yi ma shi barka da hanya, sai de ganin yanayin fuskar shi da alamu damuwa da kuma buɗe bayan ragwargwaɓaɓɓiyar motar da ya yi wata mata ta bayyana a kwance ya saka su kallon juna da alamun tambaya.
"Uwale zo ku kama ku shiga da ita ciki."
Ya faɗa yana gudawa daga wajen motar, babu musu Uwale da waɗanan ƴan matan suka kama ta zuwa ciki, sai de kuma yanzu numfashinta na fita da wani irin sauti me kamar nishi irinna azaba ko fita a hayyaci, basu kula da sun kama ƙafarta me ciwo ba sai da suka kai ta cikin gidan suka shimfiɗe hasken aci balbal ya haske ta a nanne wata budurwa ta saki ƙara ganin yanda ƙafar ta haye ta kumbura suntum.
"Innalillahi Kawu Mamman kalli yanda ƙafarta ta ji ciwo."
Da ya matsa kusa da ita sosai nan take ya hango gocewar da ƙashin ƙafarta ya yi, bai kuma yi jinkiri ba ya dire kofin ruwan da aka bashi ya soma tattaɓa ƙafar.
"Uwale kawo min jakar aikina."
Da hanzari wacce ya kira da Uwale ta tashi tare da shiga wani ɗaki babu jimawa ta fito hannunta ɗauke da jakar, a ladabce ta miƙa ma shi jakar.
Babu ɓata lokaci ya soma gyara mata ƙafar, in banda nishi babu abin da take yi sai kuma ruwan hawaye da ke zirara daga cikin idanuwanta.
Chapter 23 · 0% Book details