Sashe 2
Muhaseen Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ka tafi mana ka tsayamin a kai ƙerere, sai ka dawo, amma kasa a ranka ni zaka fita nemowa ba kanka ba, ba zaka mallaki komi ba a rayuwa sai bayan ka wadatani ka biyani ladar rainon da nai ma ka."
Zuciyarshi a cunkushe ya soma takawa yanajin wani abu na dunƙulewa a ƙirjinsa, bai tsaya ba sai da ya fita daga gidan, a ƙofar gida ya tsaya tare da dunƙule hannayensa da ƙarfi ya soma shaƙar iska yana fesarwa daga bakinsa haɗi da fitar da huci, tazbihi ya soma yi har ya samu nauyin ƙirjinshi ya ragu sannan ya soma taka dogayen ƙafafuwansa yana yin nesa da unguwar, bai tsaya ako ina ba sai a bakin shiga wani haɗaɗɗen ƙaramin restaurant, yakai mintuna biyu a bakin shiga wajen yana kallo kayan jikinshi, shi kanshi sai da ya ji ƙyanƙyamin kanshi ya kama shi, ga zafin cefane da yatsun hannayensa ke yi, hakanan ya daure bayan ya saddar da kanshi a ƙasa ya shiga wajen, daidai wajen da aka tanada dan ma'aikata ya nufa, yana hango tarin kwanikan da aka aje dan wankewa, numfashi ya sake ja da ɗan ƙarfi ya kuma fesarwa bayan ya cika bakinshi da iska sannan ya ƙarasa wajen yana ƙaƙƙalo ɗan guntun murmushi a saman pink lips ɗinshi da suka bushe, a saidai lokacin da wani me sanye da riga fara irinta kuka ya tarbeshi da faɗin.
"Ah Suhail sai yanzu ka samu ƙarasowa, sannunka da zuwa yaukan akwai tarin aiki wallah, dan yau kasuwa tayi riba yanzu haka wajennan cike ya ke da mutane, ga aikinka can ya taru."
Ya yi ma shi maganar lokacinda ya ke yi mashi nuni da tulin wanke-wanke kuma yana bashi hannu alamar suyi musabiha, sai Suhai ya girgiza kai tare da faɗi a taƙaice.
"Assalamu alaika, kayi haƙuri hannuna babu kyau, wallahi sai yanzu na samu kaina, amma yanzu zangama aikin da yardar Allah."
Daga haka bai sake cewa komi ba ya nufi wajen haɗi da soma aikinsa bakinsa bai huta ba da ambaton Allah, sannan nauyin ƙirjinsa da maganganun Binta suka asassa ya soma kwararewa.....✍🏻
Alhamdulillah, Ayau Allah ya nufe ni da fara sabon littafi, Allah yasa yanda na fara a sa'a ingama lafiya...
Ina taya ɗaukacin al'umar musulmai barka da sallah Allah ya maimaita manah ya gwada mana wa ta shekarar.
DOKA❌❌❌
Ban amince a sauya min koda kalma ɗaya ba tare da izini na ba, wannan littafin mallakina ne, ban yarda a sarrafashi ta ko wane sigaba ba tare da amincewata ba.
NICE TAKU
MARYAM STAR⭐⭐ƳAR BAIWAR JAJIRTATTU
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/DczAiFp992p78VNoV6tcMo?s=sw&p=a&mlu=3&amv=2
🌹𝙈𝙐𝙃𝘼𝙎𝙀𝙀𝙉🌹
(𝐿𝑎𝑏𝑎𝑟𝑖𝑛 𝑧𝑢𝑐𝑖𝑦𝑎 𝑚𝑒 𝑐𝑖𝑘𝑒 𝑑𝑎 𝑘𝑢𝑛𝑐𝑖, 𝑟𝑎𝑦𝑢𝑤𝑎 𝑚𝑒 𝑐𝑖𝑘𝑒 𝑑𝑎 𝑡𝑎𝑟𝑖𝑛 𝑘𝑎𝑙𝑢𝑏𝑎𝑙𝑒😔.)
𝙒𝙍𝙄𝙏𝙀 𝘽𝙔
𝙈𝘼𝙍𝙔𝘼𝙈 𝙎𝙏𝘼𝙍⭐.
💪𝙅𝘼𝙅𝙄𝙍𝙏𝘼𝙏𝙏𝙐 𝙒𝙍𝙄𝙏𝙀𝙍,𝙎 𝘼𝙎𝙎𝙊𝘾𝙄𝘼𝙏𝙄𝙊𝙉💪
🤝𝙏𝙃𝙀 𝙎𝙃𝙄𝘿𝙊𝙍𝙄𝘼 𝙒𝙍𝙄𝙏𝙀𝙍𝙎 𝙏𝙀𝘼𝙈✊
𝙋𝘼𝙄𝘿 𝘽𝙊𝙆
𝙎𝙀𝘼𝙎𝙊𝙉 𝙊𝙉𝙀
بسم الله الرحمن الرحيم.
𝘾𝙝𝙖𝙥𝙩𝙚r 2
Zuwa lokacin da ya gama wannan tulin wanke-wanke ya samu sauƙin nauyinda zucoyarshi ta yi kaso sittin cikin ɗari, sai da ya kammala sannan ya nufi wajenda ake zuba abinci, ya amsi na shi tare da ruwan leda, sai ya samawa kanshi mutsuguni ya soma cin abinci badan yana masa daɗi ba, sai dan yunwar da ta soma saƙalar ƴan hanjinsa, bayan ya gama yayi signing tare da yin sallama da su yabar wajen, sai kuma da dare idan wani aikin ya taru.
Bayan ya firo again sai ya ƙara nausar hanya yacigaba da tafiya, bai ko saurari ƙafaguwansa da ke shaida ma sa irin gajiyar da ke tattare da su ba, bai tsaya ako ina ba sai wani waje da ake wankin motoci da mashina, canma nannaɗe ƙafar wando yayi ya soma aiki ba ji ba gani, bayan ya gaggaisa da mutanen wajen, yana jin maganganun da wasu daga cikin yaran me wajen ke faɗi a kanshi amma sam bai damu ba yaci gaba da aikinshi.
"Dan Allah Abdul jibi jikinsa du datti, kalli ƙafafuwansa yanda suka tsatstsage gwanin ƙyanƙayamin, baya wanka bare wanki, sauya maka kuwa ba'a magana, gadai mutum har mutum malam amma ƙazanta ta gama lalatashi."
Caraf wanda aka kira da Abdul ya cafe zancen tare da faɗin.
"Yo kai Mustapha in banda abinka dama wannan ai ba'a sakashi a lissafi, nasha bawa oga shawarar a sauya shi karya korar mana costomers amma ya ƙi, wai yanada amfani barinshi a wajen, yo Allah na tuba taya barin ƙazamin kamar wannan a wuri zai yi amfani."
Haka sukaita maganganu marasa daɗi akan Suhail sai de bai ko ɗaga kai ya kallesu ba, hasalima aikinshi ya cigaba da yi babu ha'inci, ko a zuci maganganunsu basu wani ɗaɗashi da ƙasa ba, dan a irin waɗanda yake ji a rana suna ninka nasu muni, kuma baya bari suyi tasiri a zuciyarshi yana ƙoƙarin sanar da kanshi cewar shi ba kamar sauran mutane bane, sam bayada ƙawazuci yana nanatawa kanshi hakan aduk sanda wani abu yaso kutsowa cikin tunaninsa.
Wunin ranar haka ya ƙarar da shi da yawon aikace-aikace sai kace inji, ko inji yana tsayawa ya huta, bashi ya koma gida ba sai bayan da ya koma restaurant ya sake yin wani wanke-wanken, nan aka haɗa jimilar kuɗinsa tubu goma cis aka bashi, a hanya ya tsaya ya sayi lemo mw sanyi, yana tafiya yana shan roba ɗaya har ya shanye tas, yana jin sanyi na ratsa zuciyarsa, daga nan ya tsaya wajen mw tsire ya siyi ɗauri uku, ya koma shago ya siyi detergent da sabulun wanka, sannan ya durfafi gida agalabaici, hatta da kwayar idonsa bata ɓoye yanayin gajiyarda gangar jikinsa yayiba.
Kamar yanda ya tsammata, a lokacinda ya shiga gidan da sallama a bakinsa babu wanda ya amsha shi, ba kuma dan basa jinsa ba, hasalima duk sun ɗaga ido sun kalleshe, leda ya jefa a ɗakinsa sannan ya ƙarasa shiga a sanyaye yana kallon magidancin da ke sake haɗe fuska bayan ya ganshi, sannan ya kawar da jai gefe yana zungura baki.
"Abba da Umma barkanku da gida."
Idan sun tankashi ƙasar wajen ta tanak haka suka ɗauke kawunansu, sai Binta data kai hannu tana janyo ledojin gabansa tana bubbuɗawa tare da tame baki, tun kafin tace komi ya zaro kuɗi daga aljihunsa tare da miƙa ma ta yana fatan jin kalma ɗaya tak daga bakinta, yana so koda sau ɗayane a rana ta dinga binshi da albarka kamar yanda takewa sauran ɗiyanta, sai de shi kanshi yasan hakan ba abu ne me yiyuwaba, akan jima baiji kalmar daga bakinta ba da sunan shi ta sakawa albarka.
Ganin bata shi suke ba ya saka ya miƙe a sanyaye, sai ji yayi ɗaya daga cikin ƴan matan na faɗin.
"Am Suhail nace ba."
Juyawa tayi tare da jafeta da rikitattun idanuwansa yana kallonta, sai ta sunkui da kai saboda kwarjinin da idanuwansa masu kaifi suka yi ma ta, da wahalalliyar murya ya ce.
"Fatima ya aka yi ne?."
Tana sunne kai ta ce.
"Dama ina so ka bani kuɗi zan siyo kayan kwalliya nawa du sun tsufa wasuma sun ƙare?."
Sai da ya girgiza kai sannan ya ce da ita.
"Babu kuɗi a hannuna ki amsa a wajen Umma."
Zai juya kenan ya tsinkayi muryar Ummar na faɗin.
"Haba dan Allah, kayan kwalliyar duka nawa suke da zaka ce ta amsa a wajena, idai waɗannan kuɗaɗenne kake yiwa to wallahi sisi bazan cire ba, waye yake morar kuɗin bayan ku, du a wajen abinci da sutura sukw ƙarewa ai."
Baice komi ba ya zari dubu ɗaya ya bawa Fatimar yana fatan maganar ta tsaya iyakar nan.
"Bilkisu ɗaukowa Suhail nashi abincin."
Binta ta faɗa tana ƙidayar kuɗaɗen, tana jefa tsokar nama a baki, shiko Abba ba'a magana ya tasa nama a gaba ga lemo me sanyi yana korawa baice uffanba.
Wa ta sanƙararriyar shinkafa ce Bilki ta dire kwanonda da bakinsa yai baƙi ƙirin, saman shinkafar a bushe da alamun a buɗe ta wuni, kamar zai ce a'a sai kuma ya ɗauka gami da yin godiya ya juya ya wuce.
Bayan ya shiga ɗakinsa ya tura ƙofar, tare da kunna fitilar ƙaramar wayarsa data gama cin duniya, madannan jikinta du sun goge.
Kayan jikinshi ya shiga cirewa yanajin yanda suke tashin warin rana da ƙura, ƙaƙƙarfan numfashi ya saki yana jin wani sanyi na ratsa shi sanadiyar fitar da kayan da yayi, kai tsaye ya fita waje tare da ɗauka botiki ya saka kayan, ya zauna ya wanke su tas sannan ya shiga wanka, duda baya son wanka da ruwan sanyi amma bashida yanda zai yi hakanan yake yi dana sanyin, yanda ruwan ke sauka a jikinshi haka yake jin gakiya na baibayeshi, idonshi har lumshewa yake sanda ya fito daga wankan, best da boxer kawai ya iya sakawa addu'ar barcima rabi da rabi yayi, nannauyan barci ya ɗaukeshi, a can sama-sama ya dinga jiyo muryar Binta kamar tana faɗa, sai de baya iya gane abin da take faɗa, kuma yanajin kamar mutum a kanshi amma bai iya buɗe idoba saboda nauyin barci, a cikin barcinne kawai ya ke damun sauƙi, ananne yake samu isashen hutu, shiyasa baya kai dare sosai ba tare da dawo gida ba.
ASOKORO
MABATA MAIN HOUSE.
"Tasss, tasssss" kake jin ƙarar lafiyayun tagwayen maruka na sauka a lausasan kuncin wa ta budurwa.
Tsit duniyarta ta tsaya gaba ɗaya, azaba da raɗaɗin zuci dana mari suka haɗe ma ta a waje ɗaya, soma ja da baya-baya ta yi tana girgiza kanta da taji kamar baya jikinta, kafin cikin sarƙewar murya ta soma faɗin.
"Ni Papah, ni, niii! marina fa ka yi, akan wannan abar."
Ta faɗa tana yin nuni da wa ta lukutar yarinya da ke tsaye a wajen hannunta riƙe da taddy tana zunɓura ƙaramin bakinta.
A hasale wanda aka kira da Papah ya ce.
"Na mareki, nace na mareki ɗin Jauhar, bama iya mari ba, zan iya yi miki abin da yafi mari matuƙar kika sake ɗaga ƙazamin hannunki akan ƴata, ita ɗin ƴata ce, banida kamarta, zan wulaƙanta du wanda ya taɓa min ita ko waye shi, na faɗa na ƙara faɗa bakida wani amfani a rayuwata, bakida amfani a cikin zuriyata ni LAMINU GABATA.
Zuciyarshi a cunkushe ya soma takawa yanajin wani abu na dunƙulewa a ƙirjinsa, bai tsaya ba sai da ya fita daga gidan, a ƙofar gida ya tsaya tare da dunƙule hannayensa da ƙarfi ya soma shaƙar iska yana fesarwa daga bakinsa haɗi da fitar da huci, tazbihi ya soma yi har ya samu nauyin ƙirjinshi ya ragu sannan ya soma taka dogayen ƙafafuwansa yana yin nesa da unguwar, bai tsaya ako ina ba sai a bakin shiga wani haɗaɗɗen ƙaramin restaurant, yakai mintuna biyu a bakin shiga wajen yana kallo kayan jikinshi, shi kanshi sai da ya ji ƙyanƙyamin kanshi ya kama shi, ga zafin cefane da yatsun hannayensa ke yi, hakanan ya daure bayan ya saddar da kanshi a ƙasa ya shiga wajen, daidai wajen da aka tanada dan ma'aikata ya nufa, yana hango tarin kwanikan da aka aje dan wankewa, numfashi ya sake ja da ɗan ƙarfi ya kuma fesarwa bayan ya cika bakinshi da iska sannan ya ƙarasa wajen yana ƙaƙƙalo ɗan guntun murmushi a saman pink lips ɗinshi da suka bushe, a saidai lokacin da wani me sanye da riga fara irinta kuka ya tarbeshi da faɗin.
"Ah Suhail sai yanzu ka samu ƙarasowa, sannunka da zuwa yaukan akwai tarin aiki wallah, dan yau kasuwa tayi riba yanzu haka wajennan cike ya ke da mutane, ga aikinka can ya taru."
Ya yi ma shi maganar lokacinda ya ke yi mashi nuni da tulin wanke-wanke kuma yana bashi hannu alamar suyi musabiha, sai Suhai ya girgiza kai tare da faɗi a taƙaice.
"Assalamu alaika, kayi haƙuri hannuna babu kyau, wallahi sai yanzu na samu kaina, amma yanzu zangama aikin da yardar Allah."
Daga haka bai sake cewa komi ba ya nufi wajen haɗi da soma aikinsa bakinsa bai huta ba da ambaton Allah, sannan nauyin ƙirjinsa da maganganun Binta suka asassa ya soma kwararewa.....✍🏻
Alhamdulillah, Ayau Allah ya nufe ni da fara sabon littafi, Allah yasa yanda na fara a sa'a ingama lafiya...
Ina taya ɗaukacin al'umar musulmai barka da sallah Allah ya maimaita manah ya gwada mana wa ta shekarar.
DOKA❌❌❌
Ban amince a sauya min koda kalma ɗaya ba tare da izini na ba, wannan littafin mallakina ne, ban yarda a sarrafashi ta ko wane sigaba ba tare da amincewata ba.
NICE TAKU
MARYAM STAR⭐⭐ƳAR BAIWAR JAJIRTATTU
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/DczAiFp992p78VNoV6tcMo?s=sw&p=a&mlu=3&amv=2
🌹𝙈𝙐𝙃𝘼𝙎𝙀𝙀𝙉🌹
(𝐿𝑎𝑏𝑎𝑟𝑖𝑛 𝑧𝑢𝑐𝑖𝑦𝑎 𝑚𝑒 𝑐𝑖𝑘𝑒 𝑑𝑎 𝑘𝑢𝑛𝑐𝑖, 𝑟𝑎𝑦𝑢𝑤𝑎 𝑚𝑒 𝑐𝑖𝑘𝑒 𝑑𝑎 𝑡𝑎𝑟𝑖𝑛 𝑘𝑎𝑙𝑢𝑏𝑎𝑙𝑒😔.)
𝙒𝙍𝙄𝙏𝙀 𝘽𝙔
𝙈𝘼𝙍𝙔𝘼𝙈 𝙎𝙏𝘼𝙍⭐.
💪𝙅𝘼𝙅𝙄𝙍𝙏𝘼𝙏𝙏𝙐 𝙒𝙍𝙄𝙏𝙀𝙍,𝙎 𝘼𝙎𝙎𝙊𝘾𝙄𝘼𝙏𝙄𝙊𝙉💪
🤝𝙏𝙃𝙀 𝙎𝙃𝙄𝘿𝙊𝙍𝙄𝘼 𝙒𝙍𝙄𝙏𝙀𝙍𝙎 𝙏𝙀𝘼𝙈✊
𝙋𝘼𝙄𝘿 𝘽𝙊𝙆
𝙎𝙀𝘼𝙎𝙊𝙉 𝙊𝙉𝙀
بسم الله الرحمن الرحيم.
𝘾𝙝𝙖𝙥𝙩𝙚r 2
Zuwa lokacin da ya gama wannan tulin wanke-wanke ya samu sauƙin nauyinda zucoyarshi ta yi kaso sittin cikin ɗari, sai da ya kammala sannan ya nufi wajenda ake zuba abinci, ya amsi na shi tare da ruwan leda, sai ya samawa kanshi mutsuguni ya soma cin abinci badan yana masa daɗi ba, sai dan yunwar da ta soma saƙalar ƴan hanjinsa, bayan ya gama yayi signing tare da yin sallama da su yabar wajen, sai kuma da dare idan wani aikin ya taru.
Bayan ya firo again sai ya ƙara nausar hanya yacigaba da tafiya, bai ko saurari ƙafaguwansa da ke shaida ma sa irin gajiyar da ke tattare da su ba, bai tsaya ako ina ba sai wani waje da ake wankin motoci da mashina, canma nannaɗe ƙafar wando yayi ya soma aiki ba ji ba gani, bayan ya gaggaisa da mutanen wajen, yana jin maganganun da wasu daga cikin yaran me wajen ke faɗi a kanshi amma sam bai damu ba yaci gaba da aikinshi.
"Dan Allah Abdul jibi jikinsa du datti, kalli ƙafafuwansa yanda suka tsatstsage gwanin ƙyanƙayamin, baya wanka bare wanki, sauya maka kuwa ba'a magana, gadai mutum har mutum malam amma ƙazanta ta gama lalatashi."
Caraf wanda aka kira da Abdul ya cafe zancen tare da faɗin.
"Yo kai Mustapha in banda abinka dama wannan ai ba'a sakashi a lissafi, nasha bawa oga shawarar a sauya shi karya korar mana costomers amma ya ƙi, wai yanada amfani barinshi a wajen, yo Allah na tuba taya barin ƙazamin kamar wannan a wuri zai yi amfani."
Haka sukaita maganganu marasa daɗi akan Suhail sai de bai ko ɗaga kai ya kallesu ba, hasalima aikinshi ya cigaba da yi babu ha'inci, ko a zuci maganganunsu basu wani ɗaɗashi da ƙasa ba, dan a irin waɗanda yake ji a rana suna ninka nasu muni, kuma baya bari suyi tasiri a zuciyarshi yana ƙoƙarin sanar da kanshi cewar shi ba kamar sauran mutane bane, sam bayada ƙawazuci yana nanatawa kanshi hakan aduk sanda wani abu yaso kutsowa cikin tunaninsa.
Wunin ranar haka ya ƙarar da shi da yawon aikace-aikace sai kace inji, ko inji yana tsayawa ya huta, bashi ya koma gida ba sai bayan da ya koma restaurant ya sake yin wani wanke-wanken, nan aka haɗa jimilar kuɗinsa tubu goma cis aka bashi, a hanya ya tsaya ya sayi lemo mw sanyi, yana tafiya yana shan roba ɗaya har ya shanye tas, yana jin sanyi na ratsa zuciyarsa, daga nan ya tsaya wajen mw tsire ya siyi ɗauri uku, ya koma shago ya siyi detergent da sabulun wanka, sannan ya durfafi gida agalabaici, hatta da kwayar idonsa bata ɓoye yanayin gajiyarda gangar jikinsa yayiba.
Kamar yanda ya tsammata, a lokacinda ya shiga gidan da sallama a bakinsa babu wanda ya amsha shi, ba kuma dan basa jinsa ba, hasalima duk sun ɗaga ido sun kalleshe, leda ya jefa a ɗakinsa sannan ya ƙarasa shiga a sanyaye yana kallon magidancin da ke sake haɗe fuska bayan ya ganshi, sannan ya kawar da jai gefe yana zungura baki.
"Abba da Umma barkanku da gida."
Idan sun tankashi ƙasar wajen ta tanak haka suka ɗauke kawunansu, sai Binta data kai hannu tana janyo ledojin gabansa tana bubbuɗawa tare da tame baki, tun kafin tace komi ya zaro kuɗi daga aljihunsa tare da miƙa ma ta yana fatan jin kalma ɗaya tak daga bakinta, yana so koda sau ɗayane a rana ta dinga binshi da albarka kamar yanda takewa sauran ɗiyanta, sai de shi kanshi yasan hakan ba abu ne me yiyuwaba, akan jima baiji kalmar daga bakinta ba da sunan shi ta sakawa albarka.
Ganin bata shi suke ba ya saka ya miƙe a sanyaye, sai ji yayi ɗaya daga cikin ƴan matan na faɗin.
"Am Suhail nace ba."
Juyawa tayi tare da jafeta da rikitattun idanuwansa yana kallonta, sai ta sunkui da kai saboda kwarjinin da idanuwansa masu kaifi suka yi ma ta, da wahalalliyar murya ya ce.
"Fatima ya aka yi ne?."
Tana sunne kai ta ce.
"Dama ina so ka bani kuɗi zan siyo kayan kwalliya nawa du sun tsufa wasuma sun ƙare?."
Sai da ya girgiza kai sannan ya ce da ita.
"Babu kuɗi a hannuna ki amsa a wajen Umma."
Zai juya kenan ya tsinkayi muryar Ummar na faɗin.
"Haba dan Allah, kayan kwalliyar duka nawa suke da zaka ce ta amsa a wajena, idai waɗannan kuɗaɗenne kake yiwa to wallahi sisi bazan cire ba, waye yake morar kuɗin bayan ku, du a wajen abinci da sutura sukw ƙarewa ai."
Baice komi ba ya zari dubu ɗaya ya bawa Fatimar yana fatan maganar ta tsaya iyakar nan.
"Bilkisu ɗaukowa Suhail nashi abincin."
Binta ta faɗa tana ƙidayar kuɗaɗen, tana jefa tsokar nama a baki, shiko Abba ba'a magana ya tasa nama a gaba ga lemo me sanyi yana korawa baice uffanba.
Wa ta sanƙararriyar shinkafa ce Bilki ta dire kwanonda da bakinsa yai baƙi ƙirin, saman shinkafar a bushe da alamun a buɗe ta wuni, kamar zai ce a'a sai kuma ya ɗauka gami da yin godiya ya juya ya wuce.
Bayan ya shiga ɗakinsa ya tura ƙofar, tare da kunna fitilar ƙaramar wayarsa data gama cin duniya, madannan jikinta du sun goge.
Kayan jikinshi ya shiga cirewa yanajin yanda suke tashin warin rana da ƙura, ƙaƙƙarfan numfashi ya saki yana jin wani sanyi na ratsa shi sanadiyar fitar da kayan da yayi, kai tsaye ya fita waje tare da ɗauka botiki ya saka kayan, ya zauna ya wanke su tas sannan ya shiga wanka, duda baya son wanka da ruwan sanyi amma bashida yanda zai yi hakanan yake yi dana sanyin, yanda ruwan ke sauka a jikinshi haka yake jin gakiya na baibayeshi, idonshi har lumshewa yake sanda ya fito daga wankan, best da boxer kawai ya iya sakawa addu'ar barcima rabi da rabi yayi, nannauyan barci ya ɗaukeshi, a can sama-sama ya dinga jiyo muryar Binta kamar tana faɗa, sai de baya iya gane abin da take faɗa, kuma yanajin kamar mutum a kanshi amma bai iya buɗe idoba saboda nauyin barci, a cikin barcinne kawai ya ke damun sauƙi, ananne yake samu isashen hutu, shiyasa baya kai dare sosai ba tare da dawo gida ba.
ASOKORO
MABATA MAIN HOUSE.
"Tasss, tasssss" kake jin ƙarar lafiyayun tagwayen maruka na sauka a lausasan kuncin wa ta budurwa.
Tsit duniyarta ta tsaya gaba ɗaya, azaba da raɗaɗin zuci dana mari suka haɗe ma ta a waje ɗaya, soma ja da baya-baya ta yi tana girgiza kanta da taji kamar baya jikinta, kafin cikin sarƙewar murya ta soma faɗin.
"Ni Papah, ni, niii! marina fa ka yi, akan wannan abar."
Ta faɗa tana yin nuni da wa ta lukutar yarinya da ke tsaye a wajen hannunta riƙe da taddy tana zunɓura ƙaramin bakinta.
A hasale wanda aka kira da Papah ya ce.
"Na mareki, nace na mareki ɗin Jauhar, bama iya mari ba, zan iya yi miki abin da yafi mari matuƙar kika sake ɗaga ƙazamin hannunki akan ƴata, ita ɗin ƴata ce, banida kamarta, zan wulaƙanta du wanda ya taɓa min ita ko waye shi, na faɗa na ƙara faɗa bakida wani amfani a rayuwata, bakida amfani a cikin zuriyata ni LAMINU GABATA.