Sashe 1
Kumallon Mata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Root Entry
WordDocument
0Table
Data
[1/21, 5:06 AM] Nawarty
*HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*KUMALLON MATA....!*
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
*Labarin kumallon mata kirkirarren labarine banyishi dan wani ko wata ba idan har yayi daidai da rayuwarki/ka to bada manufa nayi ba, sannan duk sunayen garuruwan da nayi amfani dasu da sunayen halittu nasakane kawai dan nishadi da kawata labarin, Allah yasa mudace.*
*1*
***Cikin kuka take fusge fusge daga kwancen da take akan gadon asibiti ga ledar jini nan rataye ana kara mata amma hakan bai hanata yunkurin tashi ba,gefenta wata matace zaune wadda daga gani mahaifiyarta ce sai kokarin riketa take faman yi gudun kada garin wannan fusge fusgen da takeyi tajiwa kanta wani ciwon,
Cikin shasshekar kuka mai tsuma zuciya tareda tsayawa arai tace,
"Umma yanzu shikenan Abu Arqaam yarabu dani....?
Shikenan yanzu narasa masoyina?
Umma meye amfanin rayuwata?
Meye amfanin zamana agidan duniya?
Wacce irin k'addara ce wannan matsananciya.....meyasa zai barni alhalin ni ban shirya rayuwa batare dashi ba....meyasa wannan cutar ta kamani?
Watakila ma saboda ita yagujeni....nashiga uku..."
Jin surutan sunyi yawa yasa umma saurin rufe mata Baki tana jijjiga mata kai itama kwalla taf idanuwanta alamun tausayawa,
"Bahijja kiyi hakuri ki dauki k'addara kinji... insha Allah zaki samu wanda yafishi....."
"Umma bazan tab'a samun kamarshi ba..."
Kafin umma tayi magana wani matashin saurayi yashigo sanye cikin kananan kaya,ganin irin kukan da bahijja keyi da fusge fusge yasashi daka mata wata firgitacciyar tsawa,
"Hadiye wannan kukan sannan kiyiwa mutane shiru ko nayi kasa kasa dake anan....."
Babu shiri ta kama bakinta tayi shiru tare da rufe idanuwanta wadanda ke tsiyayar da hawaye,ahaka bacci ya dauketa sai faman sauke ajiyar zuciya takeyi ganin tasamu bacci yasa umma kallonshi cikin sanyin murya tace,
"Sagir meyasa kake yimata tsawa irin haka?
Baka tausayawa halin da take ciki?
Kowacece fa dole hankalinta yatashi ace ankawo lefe ansaka ranar biki amma miji yazo ya karbi abinsa....ina jin canja ra'ayi yayi yaga bai dace ya auri sikila ba...." Takarasa maganar tana goge hawayen dake zubo mata,
"Umma dan Allah kubar damuwa akan maganar nan....
Allah yabata lafiya tana samun sauki zata koma school hakan zai taimaka mata wurin rage mata damuwa...."
"Allah yabata lafiyar...."
"Amin umma"
Cikin nutsuwa da kwanciyar hankali take gudanar da komai kamar yadda tasaba,sanye take cikin kayan bacci masu taushin gaske karamar riga da dan guntun gajeren wandonta wanda bai karasa gwiwarta ba kalar ruwan hanta sai dan farin karamin hijabinta wanda ya tsaya iya kafadarta, rike take da mooper wato abun goge tiles sai faman dirjar wurin takeyi tanayi tana dan guntun tsaki sannan cikin zuciyarta tana fadin,
"Ayi yara sai dan banzan rashin ji.....
Kai wallahi yaran nan akwai kiriniya jibi duk sunbi sun bata wurin nan da water colour kamar akansu aka fara koyon zane....."
Tana ta faman mita harta kammala ta dauko abun saka daki yayi kamshi ta feffesa sannan ta sake kunna turaren kamshi na tsinke daga haka tawuce cikin kitchen tana kallon lokaci ajikin agogon dake kafe a bangon falonta, karfe 8 saura na safe agogon yanuna cikin azama tafada cikin kitchen din saboda tasan lokacin tashin yan rigamar nata yakusa, kiciniyar hada abin karyawa tafara kokarin yi ta kunna wuta ta dora tukunya.
Anutse take yin aikinta duk ta karkata hankalinta kan kwababbiyar fulawa mai dakakken naman da take nadawa tana sakawa cikin mai domin soyawa taji wata lafiyayyar runguma daga bayanta,
"Ohh Allah......
Antashi kuma..."
Tafada batare da ta juya ba amma ta tsaya cak da abinda takeyi sakamakon rikon da yayi mata dan ba karamar kasala ya haifar mata ba,
Kiss yabata akumatunta sannan ya kwantar da kansa saman kafadarta,
"Good morning baby...."
"Morning, kabarni nayi aikina kaje ka kula da yaranka please..." Tafada ahankali tana kokarin zamewa daga rikon da yayi Mata,
"Nidai a'a naki wayon...., kibarshi karki wahalar da kanki zan samo mana abinda zamu ci"
"Karka damu yanzu zan kammala..."
Bai saketa ba har lokacin yana rikeda ita ga abinda take soyawa yasoyu yana neman fara konewa,
"Sakeni to inkarasa aikina..."
Dan sakinta yayi amma ba gaba dayaba sai dai yaja dan baya kadan, juyawa tayi ta dan kalleshi daga shi sai yan kananan kayan baccinshi riga armless da wando dukkansu masu santsi sky blue,
"Kullum ina fada maka amma bakaji kadaina wannan tabarar da kake yi idan ba hakaba wallahi watarana yaranka zasu gani.....
Har yanzu kai yarone"
Murmushi yayi yana kallon bayanta, gaskiya Bilkisu bazata taba canjawa ba daga kaunar girmanta da take dashi son girmanta ajininta yake.
Bata jira yayi magana ba taci gaba da aikinta tana yi tana ture hannunshi daga jikinta zuwa can ta juyo ta kalleshi amma basu hada idoba,
"Dan Allah baby ka barni ingama aikin nan....."
Sumarshi ya shafa sannan ya dan jingina da jikinta kadan,
"Gaskiya ni takura min za ayi...." Yafada cikin shagwaba,
"Wai kamanta yau weekend ne?
Muna tare fa har dare...."
"Yes.....
Yau ranata ce, namanta ne fa sai ina ganin kamar zaki fita office....
Kuma da zarar kin dawo agajiye kike dawo min sai dai kiyita bacci bakya moruwa"
"No yau ina tare dakai har gobe har jibi saboda babu aiki Monday..."
Tun kafin ta karasa fada ya rukunkumeta yana kissing dinta tako ina daga bisani yasaketa yana dariya yafita daga cikin kitchen din ya nufi dakin baccin yaransu, kamar yadda ya tsammata duk dinsu bacci sukeyi sai Mimi kadai wadda itace yar karamarsu domin bata wuce wata tara ba zuwa goma, tana ganinshi tafara murna tana faman yimasa gwaranci, daukarta yayi sannan yafara tashin yaran daya bayan daya yana yimusu wanka,shiryasu yayi tsaf cikin kayan makaranta na tahfiz daidai lokacin mahaifiyar tasu tashigo rikeda kayan karin kumallonsu, ganin yawan aikin da yarage mata yasata sakin ajiyar zuciya cikin farin ciki tafurta,
"Thank you bae....
Hanfa kuyi sauri kuci amikaku tahfiz...
Sauri please...."
Da kanshi ya zauna yana hada musu tea cikin sauri suke yin komai har yaran suka kammala, dukkan abunda suke bukata dan tafiya makaranta ta hada musu cikin jakunkunansu,daya bayan daya tarinka binsu tana sumbatarsu akumatu tana yimusu addu'ar dawowa lafiya, saida yajira suka gama sannan ya kama hannunsu zuwa waje domin drivern dake kaisu makaranta tuni yadade awurin yana jiransu akan idonshi suka tafi suna ta faman daga masa hannu, ciki yajuya bayan yarufe gidan.
Tana zaune dakin yara kamar yadda yabarsu tana feeding din mimi zama yayi agabanta yana shafa kan mimi ita kuma yana kallonta,
Da ido ta tambayeshi ma'anar kallon da yake yimata, murmushi yayi mata ya lumshe ido,
"Yanzu kin sallami kowa saura ni..."
Girgiza Kai tayi tana murmushi sannan ta mika masa mimi,
"Karbi yarka zanyi wanka....."
Karbarta yayi sannan cikin bata fuska yace,
"Baby dan Allah jirani muyi tare mana....."
"A'a gaskiya kowa yayi nashi.."
Shi dariya ma tabashi saboda yanda tayi saurin fita daga dakin, mimi ya rungume yana jijjigata,falo suka koma ya kwantar da ita akirjinshi yana shafar bayanta babu jimawa tayi bacci, kwantar da ita yayi yanufi bedroom, tana gaban mirror tana kiciniyar daura dan kwalin atamfar dake jikinta dinkin riga da skirt, ta cikin mirror din ta kalleshi shima ita yake kallo,
"Kin kyau baby....
Kawo indaura miki.."
"Nagode...."
Dan kwalin ya karbe kamar dagaske daura mata din zaiyi daga nan inda take zaune ya kinkimeta da duk karfinshi, zillewa tafara kokarin yi amma takasa tarasa sai yaushe fahad zai daina wannan yarintar tashi kwata kwata baya girma fahad din shekaru shida baya shine dai yanzu bai canja ba.
Sosai ta bata fuska tana harararshi, da murmushi yamayar mata martanin hararar da take yimasa,
"Basaida nace kijirani muyi wankan tareba kika ki.....
Yanzu kinga sai muyi tare"
Makale kafada tayi tana girgiza kai saboda ita yanzu bata wani rawar kan yin wanka tare dashi tun bayan da ta hahhaihu duk stretch marks suka bata mata jiki ko ina sun futo rado rado ahakanma dan tana amfani da mayuka da sabulai masu kyau dan rage tasirunsu ne,
"Wai meyasa yanzu ake guduna ne?
Uhmm baby?"
"Dan Allah katashi kaje kayi wanka bae...."
"Zo muyi tare.....
Dake zaifi"
Girgiza kai tayi amma bai hakuraba saida ya kinkimeta suka shiga toilet din tare gaba daya yagama fahimtarta yasan abinda yasa mafi yawan lokuta bata yarda suyi wanka tare saboda yanzu jikinta ya canja shiyasa akoda yaushe shikuma yake nuna mata shi ita din yakeso bawai halittarta ba kuma har gobe bai canja ba, irin tsokanar da yasata agaba yana yimata acikin bathroom dinne yasata warewa itama ta wartsake tana ramawa wannan dalilinne yasasu daukar lokaci mai tsawo acikin bathroom din suna wasa da ruwa, bayan dogon lokaci suka fito tana goye abayanshi,
"Duk ranar da nayi kwalliya saika bata min kake jin dadi fahad......" Tafada cikin shagwaba,
"Tukwici ai nake bayarwa ko kin manta bahaushe yace yaba kyauta tukwici?
Thank u hajjaju....."
Harararshi tayi ta mike ta ciro wata yar karamar riga tunda tayi kwalliyar yabata gara tasaka masa kayan da yafiso yaje yakaraci fitinarshi dan akoda yaushe indai suna tare yafi son abar mishi kayanshi afili yana hangowa, itafa yanzu harta saba da rigimar fahad da shagwabarshi,rigar tasaka wacce bata da wani girman kirki iya cinya milk colour mai dan karamin hannu sannan bata da kauri mai budadden kirji, rungumeta yayi ta baya sai kuma ya sassauta rikon da yayi mata,
"Yunwa nakeji baby....
Muje kibani abinci"
Agogo ta kalla 12 na rana harda yan wasu mintuna,
"Ba dole kaji yunwa ba, fitina duk ta cika ma mutum ciki..."
"Kai baby......."
"To goyani muje...."
Baiyi musuba ya sunkuya tahau bayanshi suka fita falo, mimi na kwance inda yabarta har lokacin bacci takeyi, sauke Bilkisu yayi yamatsa gaban yarinyar yana kare mata kallo yayinda ita kuma Bilkisu tashiga kitchen, ada yana ganin kamar duk cikin yaran mimi ce kadai ta dauko kamar Bilkisu kadan amma yanzu itama duk ta juye kamar yan uwanta wato kamarshi, murmushi yayi ya murza yan yatsun yarinyar yana kallon bakinta irin nashi sak dan tsut dashi,
"Bakin yarinyar nanma irin nawane...."
"Bakin rashin kunya....".
Tafada daidai lokacin da ta karaso rikeda babban faranti.
WordDocument
0Table
Data
[1/21, 5:06 AM] Nawarty
*HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*KUMALLON MATA....!*
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
*Labarin kumallon mata kirkirarren labarine banyishi dan wani ko wata ba idan har yayi daidai da rayuwarki/ka to bada manufa nayi ba, sannan duk sunayen garuruwan da nayi amfani dasu da sunayen halittu nasakane kawai dan nishadi da kawata labarin, Allah yasa mudace.*
*1*
***Cikin kuka take fusge fusge daga kwancen da take akan gadon asibiti ga ledar jini nan rataye ana kara mata amma hakan bai hanata yunkurin tashi ba,gefenta wata matace zaune wadda daga gani mahaifiyarta ce sai kokarin riketa take faman yi gudun kada garin wannan fusge fusgen da takeyi tajiwa kanta wani ciwon,
Cikin shasshekar kuka mai tsuma zuciya tareda tsayawa arai tace,
"Umma yanzu shikenan Abu Arqaam yarabu dani....?
Shikenan yanzu narasa masoyina?
Umma meye amfanin rayuwata?
Meye amfanin zamana agidan duniya?
Wacce irin k'addara ce wannan matsananciya.....meyasa zai barni alhalin ni ban shirya rayuwa batare dashi ba....meyasa wannan cutar ta kamani?
Watakila ma saboda ita yagujeni....nashiga uku..."
Jin surutan sunyi yawa yasa umma saurin rufe mata Baki tana jijjiga mata kai itama kwalla taf idanuwanta alamun tausayawa,
"Bahijja kiyi hakuri ki dauki k'addara kinji... insha Allah zaki samu wanda yafishi....."
"Umma bazan tab'a samun kamarshi ba..."
Kafin umma tayi magana wani matashin saurayi yashigo sanye cikin kananan kaya,ganin irin kukan da bahijja keyi da fusge fusge yasashi daka mata wata firgitacciyar tsawa,
"Hadiye wannan kukan sannan kiyiwa mutane shiru ko nayi kasa kasa dake anan....."
Babu shiri ta kama bakinta tayi shiru tare da rufe idanuwanta wadanda ke tsiyayar da hawaye,ahaka bacci ya dauketa sai faman sauke ajiyar zuciya takeyi ganin tasamu bacci yasa umma kallonshi cikin sanyin murya tace,
"Sagir meyasa kake yimata tsawa irin haka?
Baka tausayawa halin da take ciki?
Kowacece fa dole hankalinta yatashi ace ankawo lefe ansaka ranar biki amma miji yazo ya karbi abinsa....ina jin canja ra'ayi yayi yaga bai dace ya auri sikila ba...." Takarasa maganar tana goge hawayen dake zubo mata,
"Umma dan Allah kubar damuwa akan maganar nan....
Allah yabata lafiya tana samun sauki zata koma school hakan zai taimaka mata wurin rage mata damuwa...."
"Allah yabata lafiyar...."
"Amin umma"
Cikin nutsuwa da kwanciyar hankali take gudanar da komai kamar yadda tasaba,sanye take cikin kayan bacci masu taushin gaske karamar riga da dan guntun gajeren wandonta wanda bai karasa gwiwarta ba kalar ruwan hanta sai dan farin karamin hijabinta wanda ya tsaya iya kafadarta, rike take da mooper wato abun goge tiles sai faman dirjar wurin takeyi tanayi tana dan guntun tsaki sannan cikin zuciyarta tana fadin,
"Ayi yara sai dan banzan rashin ji.....
Kai wallahi yaran nan akwai kiriniya jibi duk sunbi sun bata wurin nan da water colour kamar akansu aka fara koyon zane....."
Tana ta faman mita harta kammala ta dauko abun saka daki yayi kamshi ta feffesa sannan ta sake kunna turaren kamshi na tsinke daga haka tawuce cikin kitchen tana kallon lokaci ajikin agogon dake kafe a bangon falonta, karfe 8 saura na safe agogon yanuna cikin azama tafada cikin kitchen din saboda tasan lokacin tashin yan rigamar nata yakusa, kiciniyar hada abin karyawa tafara kokarin yi ta kunna wuta ta dora tukunya.
Anutse take yin aikinta duk ta karkata hankalinta kan kwababbiyar fulawa mai dakakken naman da take nadawa tana sakawa cikin mai domin soyawa taji wata lafiyayyar runguma daga bayanta,
"Ohh Allah......
Antashi kuma..."
Tafada batare da ta juya ba amma ta tsaya cak da abinda takeyi sakamakon rikon da yayi mata dan ba karamar kasala ya haifar mata ba,
Kiss yabata akumatunta sannan ya kwantar da kansa saman kafadarta,
"Good morning baby...."
"Morning, kabarni nayi aikina kaje ka kula da yaranka please..." Tafada ahankali tana kokarin zamewa daga rikon da yayi Mata,
"Nidai a'a naki wayon...., kibarshi karki wahalar da kanki zan samo mana abinda zamu ci"
"Karka damu yanzu zan kammala..."
Bai saketa ba har lokacin yana rikeda ita ga abinda take soyawa yasoyu yana neman fara konewa,
"Sakeni to inkarasa aikina..."
Dan sakinta yayi amma ba gaba dayaba sai dai yaja dan baya kadan, juyawa tayi ta dan kalleshi daga shi sai yan kananan kayan baccinshi riga armless da wando dukkansu masu santsi sky blue,
"Kullum ina fada maka amma bakaji kadaina wannan tabarar da kake yi idan ba hakaba wallahi watarana yaranka zasu gani.....
Har yanzu kai yarone"
Murmushi yayi yana kallon bayanta, gaskiya Bilkisu bazata taba canjawa ba daga kaunar girmanta da take dashi son girmanta ajininta yake.
Bata jira yayi magana ba taci gaba da aikinta tana yi tana ture hannunshi daga jikinta zuwa can ta juyo ta kalleshi amma basu hada idoba,
"Dan Allah baby ka barni ingama aikin nan....."
Sumarshi ya shafa sannan ya dan jingina da jikinta kadan,
"Gaskiya ni takura min za ayi...." Yafada cikin shagwaba,
"Wai kamanta yau weekend ne?
Muna tare fa har dare...."
"Yes.....
Yau ranata ce, namanta ne fa sai ina ganin kamar zaki fita office....
Kuma da zarar kin dawo agajiye kike dawo min sai dai kiyita bacci bakya moruwa"
"No yau ina tare dakai har gobe har jibi saboda babu aiki Monday..."
Tun kafin ta karasa fada ya rukunkumeta yana kissing dinta tako ina daga bisani yasaketa yana dariya yafita daga cikin kitchen din ya nufi dakin baccin yaransu, kamar yadda ya tsammata duk dinsu bacci sukeyi sai Mimi kadai wadda itace yar karamarsu domin bata wuce wata tara ba zuwa goma, tana ganinshi tafara murna tana faman yimasa gwaranci, daukarta yayi sannan yafara tashin yaran daya bayan daya yana yimusu wanka,shiryasu yayi tsaf cikin kayan makaranta na tahfiz daidai lokacin mahaifiyar tasu tashigo rikeda kayan karin kumallonsu, ganin yawan aikin da yarage mata yasata sakin ajiyar zuciya cikin farin ciki tafurta,
"Thank you bae....
Hanfa kuyi sauri kuci amikaku tahfiz...
Sauri please...."
Da kanshi ya zauna yana hada musu tea cikin sauri suke yin komai har yaran suka kammala, dukkan abunda suke bukata dan tafiya makaranta ta hada musu cikin jakunkunansu,daya bayan daya tarinka binsu tana sumbatarsu akumatu tana yimusu addu'ar dawowa lafiya, saida yajira suka gama sannan ya kama hannunsu zuwa waje domin drivern dake kaisu makaranta tuni yadade awurin yana jiransu akan idonshi suka tafi suna ta faman daga masa hannu, ciki yajuya bayan yarufe gidan.
Tana zaune dakin yara kamar yadda yabarsu tana feeding din mimi zama yayi agabanta yana shafa kan mimi ita kuma yana kallonta,
Da ido ta tambayeshi ma'anar kallon da yake yimata, murmushi yayi mata ya lumshe ido,
"Yanzu kin sallami kowa saura ni..."
Girgiza Kai tayi tana murmushi sannan ta mika masa mimi,
"Karbi yarka zanyi wanka....."
Karbarta yayi sannan cikin bata fuska yace,
"Baby dan Allah jirani muyi tare mana....."
"A'a gaskiya kowa yayi nashi.."
Shi dariya ma tabashi saboda yanda tayi saurin fita daga dakin, mimi ya rungume yana jijjigata,falo suka koma ya kwantar da ita akirjinshi yana shafar bayanta babu jimawa tayi bacci, kwantar da ita yayi yanufi bedroom, tana gaban mirror tana kiciniyar daura dan kwalin atamfar dake jikinta dinkin riga da skirt, ta cikin mirror din ta kalleshi shima ita yake kallo,
"Kin kyau baby....
Kawo indaura miki.."
"Nagode...."
Dan kwalin ya karbe kamar dagaske daura mata din zaiyi daga nan inda take zaune ya kinkimeta da duk karfinshi, zillewa tafara kokarin yi amma takasa tarasa sai yaushe fahad zai daina wannan yarintar tashi kwata kwata baya girma fahad din shekaru shida baya shine dai yanzu bai canja ba.
Sosai ta bata fuska tana harararshi, da murmushi yamayar mata martanin hararar da take yimasa,
"Basaida nace kijirani muyi wankan tareba kika ki.....
Yanzu kinga sai muyi tare"
Makale kafada tayi tana girgiza kai saboda ita yanzu bata wani rawar kan yin wanka tare dashi tun bayan da ta hahhaihu duk stretch marks suka bata mata jiki ko ina sun futo rado rado ahakanma dan tana amfani da mayuka da sabulai masu kyau dan rage tasirunsu ne,
"Wai meyasa yanzu ake guduna ne?
Uhmm baby?"
"Dan Allah katashi kaje kayi wanka bae...."
"Zo muyi tare.....
Dake zaifi"
Girgiza kai tayi amma bai hakuraba saida ya kinkimeta suka shiga toilet din tare gaba daya yagama fahimtarta yasan abinda yasa mafi yawan lokuta bata yarda suyi wanka tare saboda yanzu jikinta ya canja shiyasa akoda yaushe shikuma yake nuna mata shi ita din yakeso bawai halittarta ba kuma har gobe bai canja ba, irin tsokanar da yasata agaba yana yimata acikin bathroom dinne yasata warewa itama ta wartsake tana ramawa wannan dalilinne yasasu daukar lokaci mai tsawo acikin bathroom din suna wasa da ruwa, bayan dogon lokaci suka fito tana goye abayanshi,
"Duk ranar da nayi kwalliya saika bata min kake jin dadi fahad......" Tafada cikin shagwaba,
"Tukwici ai nake bayarwa ko kin manta bahaushe yace yaba kyauta tukwici?
Thank u hajjaju....."
Harararshi tayi ta mike ta ciro wata yar karamar riga tunda tayi kwalliyar yabata gara tasaka masa kayan da yafiso yaje yakaraci fitinarshi dan akoda yaushe indai suna tare yafi son abar mishi kayanshi afili yana hangowa, itafa yanzu harta saba da rigimar fahad da shagwabarshi,rigar tasaka wacce bata da wani girman kirki iya cinya milk colour mai dan karamin hannu sannan bata da kauri mai budadden kirji, rungumeta yayi ta baya sai kuma ya sassauta rikon da yayi mata,
"Yunwa nakeji baby....
Muje kibani abinci"
Agogo ta kalla 12 na rana harda yan wasu mintuna,
"Ba dole kaji yunwa ba, fitina duk ta cika ma mutum ciki..."
"Kai baby......."
"To goyani muje...."
Baiyi musuba ya sunkuya tahau bayanshi suka fita falo, mimi na kwance inda yabarta har lokacin bacci takeyi, sauke Bilkisu yayi yamatsa gaban yarinyar yana kare mata kallo yayinda ita kuma Bilkisu tashiga kitchen, ada yana ganin kamar duk cikin yaran mimi ce kadai ta dauko kamar Bilkisu kadan amma yanzu itama duk ta juye kamar yan uwanta wato kamarshi, murmushi yayi ya murza yan yatsun yarinyar yana kallon bakinta irin nashi sak dan tsut dashi,
"Bakin yarinyar nanma irin nawane...."
"Bakin rashin kunya....".
Tafada daidai lokacin da ta karaso rikeda babban faranti.