← Book details Garkuwa Biyu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 1 OF 31

Gabatarwa

Garkuwa Biyu Part 1 Complete Hausa Novel · about 176 min read

*TYPING* 📲

✌️💔 *GARKUWA BIYU* 💔✌️


*TARE DA ALK'ALAMIN* ✍️

HASSANA D'AN LARABAWA

*MARUBUCIYAR* 👇

SANADIN HOTO
HASSANA DA HUSSAINA
CIN AMANAR RUHI
BAHAGON LAYI
BAHAGON LAYI (SABON SALO)

*DA KUMA*👇

GARKUWA BIYU

*BABI NA D'AYA DA NA BIYU*


WATTPAD:Hassana3333


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️

🖊 *PEN WRITERS ASSOCIATION*🖊️


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️


______________________________________

*~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~*


_____________________________________


https://www.facebook.com/groups/1533639276725285/


*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM*

DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN K'AI,SARKI MABUWAYI GAGARA MISALI,MAI SHEKARANJIYA DA JIYA DA YAU DA GOBE DA JIBI,WANDA YAYI MINI BAIWA YA BANI BASIRA DA HAZAK'AR RUBUTU DOMIN FAD'AKARWA DA WA'AZANTARWA DA NISHAD'ANTARWA DA ILIMANTARWA.

KAMAR YARDA AKA SABA MASOYANA YAU MA GANI NA DAWO A SHIRYE TSAF DOMIN KU,DOMIN DA BAZARKU NAKE TAKA RAWA,SOYAYYA DA ADDU'AR DA KUKE MIN TA FATAN ALKAIRI KAD'AI TA ISHENI TINK'AHO DA JIN DAD'I,INA FATAN ZAKU CIGABA,KUMA ZAKU BINI A CIKIN WANNAN LITTAFI NAWA MAI SUNA *GARKUWA BIYU* DOMIN KUJI WANE SALO YAKE D'AUKE DASHI,KUN SAN A KO DA YAUSHE SALON LITATTAFAINA SUNA SAUYAWA,TO WANNAN MA NASA SALON NA DABAN NE,ALLAH YA BANI IKON FARAWA LAFIYA KUMA NA GAMA LAFIYA.🥰🥰🥰👏👏👏🌹🌹🌹


A hankali ya shigo da motarsa cikin harabar Gidan,bayan mai gadi ya wangale masa k'aton get d'in,ya nufi parking space ,wucewar mintina biyu ya bud'e murfin motar ya zuro k'ayatattun k'afafuwansa ya sakko,hannunsa rik'e da briefcase, kyakkyawar fuskar sa sanye da glass, ya kulle motar ya tako a hankali cikin tafiyar nutsuwa da d'aukar hankali,da sauri mai gadin ya nufo shi ya zube a gabansa cikin girmama wa.

"Yallab'ai barka da dawowa"

Yayi murmushi yana gyad'a kai.
"Barka kadai Umar,ya Gidan ya wuni?dafatan komai lafiya?

Umar ya sake russunawa.

" Alhamdulillahi mun wuni lafiya,sai dai d'azu naga GARKUWA ya fito daga ciki yana kuka,amma da na tambaye shi yak'i yin magana,gashi can ma zaune a k'ofar shiga parlour "

Fuskarsa ta nuna rashin jin dad'i,ya D'an waiwaya yana hango yaron zaune ya zabga tagumi, da alamun damuwa a fuskarsa,ya dawo da kallonsa kan Umar ya D'an murmusa.

"Shikenan no problem Umar,koma wajen aikin ka zan ji damuwar da kaina".

Umar ya mik'e yana godiya,shi kuma ya fara takawa a hankali har ya isa gaban yaron D'an shekara shida,Wanda yake zaune a kan step's d'in shiga cikin parlour d'in Gidan

Ya D'an d'auki lokaci a gaban yaron yana ta kallon sa cikin damuwa da bugawar zuciya,kafin a hankali ya zame ya tsuguna gabansa,ya d'aga tattausan hannunsa ya d'ora akan hannun yaron yana zame tagumin da yayi,firgigit yaron ya d'ago kansa,yana ganin Wanda yake gaban sa da hanzari ya silalo ya fad'a k'irjinsa yana rik'e wuyansa,hawayen sa ya tsinke ya sauka kan kafad'ar mahaifinsa.

Tsawon minti biyu ya bar yaron yana kuka da shesshek'a,har sai da yaji ya lafa tukunna yasa Hannu ya d'ago shi yana kallon fuskarsa ,yasa Hannu ya share masa hawayen sa,yaron ya bishi da kallo yana k'ara kwab'e fuska zai kuma wani kukan,da sauri ya girgiza masa kai yayi magana a hankali.

"Bana son sake ganin hawaye a idanuwan HAMZA GARKUWA,kai fa jarumi ne Hamza,shi Jarumi baya kuka kullum zuciyarsa a dake take,abin da yasa ma yanzu na k'yale ka kayi domin kaji dad'i ne,ka san wani lokaci idan yaro yana kuka a kan so a barshi yayi domin wata damuwa ta yaye daga k'irjinsa,daga yanayin da naji hawayen ka sun zubo da d'umi na tabbatar na damuwa ne,shiyasa na barsu suka zuba domin kaji sauk'in damuwar,amma menene damuwarka da har ka kasa zama a cikin gida ka fito kana kuka"?

Ya sunkuyar da kai yana wasa da yatsun mahaifin nasa,yayi magana cikin muryar rauni da yarinta.

" Bana son ganin hawayen Ammina ne Abba,shine na fito nan"

"Yau ma tayi kukan ne"?

Ya tambayeshi da Hanzari.

Ya gyad'a kai yayi rau rau da idanu.

" Eh tayi sosai Abba,har idanuwanta sun yi ja"

Ya lumshe idanu ,a hankali ya ambaci.
"Innalillahi wa inna ilaihir raji'un"
Da hanzari kuma ya mik'e yaja hannun yaron yace .
"Tashi mu shiga ciki"

Yaron Ya mik'e,sannan ya mik'a Hannu yace.
"Abbana kawo jakar na rik'e maka"
Ya mik'a masa,sannan ya rungumeshi a gefensa suka shige parlourn.


Ta na zaune a d'aya daga cikin kujerun parlourn,kanta kwance akan cinyoyin ta,sallamar su bai sa ta d'ago kanta ba,suka tsaya suna dubanta suna sauke numfashi,a hankali ya juya ya kalli yaron Yayi magana a hankali.

"Tafi ka kai min jakar bedroom, daga nan kayi zamanka kayi karatu".

Ya amsa ya wuce ya na waiwayen su,har ya shige bedroom d'in,shi kuma ya tako a hankali zuwa kusa da ita ya zauna gefenta,a hankali kuma ya kai Hannu ya d'ago fuskarta da ke sunkuye yana son su had'a ido,tsigar jikinsa ta wani mik'e yarrrrr!ganin yadda idanuwanta suka yi ja sosai alamar taci kuka ba da wasa ba,ta bishi da kallo hawaye na k'ara ziraro mata,ya kai D'an yatsan sa ya share mata,sannan ya jata jikinsa a hankali ya rungumeta tsam yana ajiyar zuciya,hannunsa d'aya ya kai kan lallausan gashin kanta Wanda bai cika tsawo da yawa ba yana shafawa,d'aya hannun bisa gadon bayanta yana mata messaging.
Sai da suka d'auki tsawon lokaci a haka kafin ya d'agota daga jikinsa,ya tallabo kumatunta yana k'ok'arin jefa idanunwansa cikin nata,suna had'a idanu ta runtse nata idon,bata fiye son kallon k'wayar idon sa ba saboda maganad'isun dake fizgarta , shi kuma ya lumshe nasa idanun ya bud'e,a hankali kuma cikin maganar rad'a yace.

" Kullum na ganki cikin wannan yanayin sai nai ta tuhumar kaina anya kuwa na cancanci a kirani da GARKUWAR ki?bana son ganinki cikin damuwa ko kad'an,ki taimakawa numfashi na ki daina yawan damuwa domin nima kina sakani a damuwar,ba iya ni kad'ai ba har D'an mu da muka Haifa, me ya saki kuka a yau HIDAYA?kin tuna da k'addarar rayuwarki ne?

Ta girgiza kai a hankali hawayen ta ya kuma gangarowa,ya D'an dafe kai yace.
"Oh my God"

Sannan ya d'ago k'afafuwanta zuwa kan cinyarsa yana duba su yana mammatsawa a hankali,ya d'ago ya kalleta.

"K'afarki tana ciwo ne?ban ga kumburi a tare da ita ba,ko wani wajen nayi miki ciwo ne?

Nan ma ta girgiza kai babu magana.

" Hidaya" ya ambaci sunanta ya na mai k'ura mata idanu,ta d'ago kanta ta kalleshi.

"Menene? Don Allah ki fad'a min"Ya tambayeta idanuwansa cikin nata,ta fara k'ok'arin sunkuyar da kai,da hanzari ya tallabo ta ya marairaice.

" Idan baki fad'a min ba wallahi zan yi Kuka Hidaya ,a yanzu baki ji yadda k'irjina yake ciwo ba ganin hawayen ki"

Ta kwantar da kanta kan kafad'arsa tana ajiyar Zuciya,a hankali tayi magana muryarta na shak'ewa.

"Duniya cike take da mutane mabanbamta,kuma kowa da irin tasa k'addarar,wani Mummuna wani kyakkyawa,wani jarrabawarsa mai tsananin zafi ,wani kuma mai sauk'i,kowa da yadda tasa take zuwar masa a yadda Allah ya k'addara masa,ba kuma wai don ba ya son bayinsa ba yake jarrabarsu,illa domin ya gwada imanin su"

Ta D'an yi shiru tana maida numfashi,shi kam ya k'ura mata idanu,ta gyara zaman ta a jikinsa ta cigaba da magana.
"Wannan kukan da kaga ina yi k'addarar wasu na tausayawa,shiyasa nake zubar musu da hawaye"

Yayi mamaki sosai har ya kasa b'oyewa,da hanzari ya magantu.

"K'addarar wasu kuma Hidaya?yanzu akwai k'addarar da zaki tausayawa wadda ta wuce taki Hidayaa?kin manta jarrabawar ki a rayuwa ne?shin kin manta da taki k'addarar ne?wad'annan su waye da kike tausayawa k'addarar su?

Tayi murmushi mai ciwo.

" A yayin da wasu zasu tausayawa k'addarata da jarrabawata,a lokacin ne ni kuma idan naji ta wasu zan tausaya musu"

"Su wanene"? Ya tambayeta kai tsaye.

Ta amsa cikin girgiza kai.
" Ban san su ba,ban tab'a ganin su ba,Labarin su kawai na karanta ya tab'a ruhi na,kai ma kayi mamaki ko?

Ya d'aure fuska kad'an.

"Wai kina nufin daman kukan da kike yi akan karatun littafi ne?kina nufin labarin wasu kika karanta na k'arya kika zauna kina kuka?ba na hanaki zama ki karanta littafin da kika San zai saki kuka ba?yau kuma na wace marubuciyar kika karanta?

Ta bishi da kallo.

" kamar Kullum,yau ma littafin HASSANA D'AN LARABAWA na karanta mai suna SANADIN HOTO,hak'ik'a labarin ya tab'a min zuciya sosai,kamar yadda sauran litattafanta na HASSANA DA HUSSAINA DA CIN AMANAR RUHI suka tab'a min zuciya"

Haushi ya kamashi,ya fara fad'a a zafafe.

"Na rantse da Allah da zanga marubuciyar nan sai nayi shari'a da ita,akan me zata dinga saka min ke kuka?haka kawai ta zauna ta dinga rubuta k'arya tana saka ku kuka,saboda rashin aikin yi,ku rasa me zaku yiwa kuka wai sai littafi?

Yayi D'an tsaki yana zamewa ya jingina da kujerar.

Zahra tayi murmushi.

" Ba zaka gane ba ne,Abin da baka sani ba shine,ya wanci litattafan HASSANA D'AN LARABAWA Gaske ne sun faru,sannan tana duba abubuwan da suke faruwa a zamanin da muke ciki tayi rubutu a kai,Wanda zai fad'akar kuma ya nishad'antar da mutane,ni dai ina sonta,kuma ina son karanta litattafan ta domin mutum zai k'aru da wasu Abubuwan,duk da ban Santa ba ban kuma tab'a ganinta ba amma zan karb'i Numbarta wajen Sumayya domin muyi magana ni da ita,da man Sumayyan ce ta turo min litattafan na karanta"

Ya D'an yi mata kallon k'asan ido sannan ya lumshe su,a hankali kuma yasa tattausan hannunsa ya rik'o nata hannun mai kama da Auduga don laushi,ya matse a cikin tafin hannunsa,ta d'ago idanuwanta wad'anda basu kasance farare tas ba,saboda akwai wani sirki a tare dasu na lalura,ta dubeshi, fuska babu walwala idanuwansa a kanta ya fara magana.
"Zan b'atawa Sumayya rai My Hidaya,sanin kanta ne cewa duk duniya bana son ganin abin da zai saki kuka ko ya b'ata miki rai,akan me zata baki littafin da zaki karanta kiyi kuka?

Ta jawo jikinta kusa da shi ta zame ta kwantar da kanta kan yalwataccen k'irjinsa ta D'an rungumeshi ta na sauke ajiyar zuciya tace.

" Don Allah kar kaga laifinta,ni na dameta akan ta bani saboda yadda naji ana cewa litattafan sun yi dad'i,wallahi ma hanani tayi nai ta takura mata da naci shine ta bani na karanta,kuma wallahi na k'aru sosai dasu,Don Allah kayi hak'uri kar kayi wa Sumayya komai"

Yayi shiru bai ce komai ba,ta d'ago kanta tana kallon kyakkyawar fuskarsa idanuwansa a rufe,ta D'an shafi fuskarsa cikin sanyin murya tace "ka ji" yayi wal ya bud'e idanun ya sauke akan ta,ya D'an d'aga gira yayi magana a hankali"Menene?

"Kar ka yiwa Sumayya komai" ta ambata cikin shagwab'a.
"OK,ya fad'a yana yunk'urawa ya mik'e da ita a jikinsa.
" Muje bedroom wanka nake so nayi,za ki tayani ko Hidaya na?

Tayi murmushi ta na gyad'a kai sannan ta sak'alo wuyansa ta rad'a masa wata magana.
Shi ma yayi murmushi ya tsuguna gabanta yace.

"Abu mai sauk'i kenan Hidaya na,maza ki hau bayan mijinki Garkuwar ki"

Ta haye bayansa ta kwanta luf tana murmushi,shi kuma ya mik'e yana zunkud'ata suka shige bedroom suna dariya.

Hamza da ke d'akin sa yana karatu jin dariyar da iyayen sa ke yi sai yayi murmushi,hankalin sa ya kwanta,domin damuwar mahaifiyar sa ta na damun sa,ya kuma tabbatar Mahaifin sa yana k'ok'ari sosai wajen tafiyar da da uwar Ammin sa a duk lokacin da ta shiga damuwar,ya lumshe idanu ya mai da kan sa kan alk'ur'anin gaban sa ya cigaba da karatun sa cikin kwanciyar Hankali.


Comment
Share
Vote
Pls


*TYPING* 📲

✌️💔 *GARKUWA BIYU* 💔✌️


*TARE DA ALK'ALAMIN* ✍️

HASSANA D'AN LARABAWA

*MARUBUCIYAR* 👇

SANADIN HOTO
HASSANA DA HUSSAINA
CIN AMANAR RUHI
BAHAGON LAYI
BAHAGON LAYI(SABON SALO)

*DA KUMA*👇

GARKUWA BIYU


*BABI NA UKU DA NA HUD'U*

WATTPAD:Hassana3333


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️

🖊 *PEN WRITERS ASSOCIATION*🖊️


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️


______________________________________

*~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~*


_____________________________________


https://www.facebook.com/groups/1533639276725285/


Washe gari yana fita wajen Aiki sai Hidaya kawai a gidan,Hamza ma baya nan yana school,tana kwance a bedroom d'in ta hannunta rik'e da wayarta,ta kunna data ta shiga b'angaren watsapp,duba sak'onnin da suke shigo mata tayi,ba wasu masu yawa bane sosai,sak'on da ke sama ta fara dubawa sai ta tarar daga Sumayya yake,ta shiga ta duba sai taga Sumayyan na online a lokacin,amsa mata sallama tayi,Sumayya taga maganar , sai ta kuma turo mata sak'o kamar haka.

"Ykk?ina mutumi na Hamza Garkuwa?

Hidaya ta bata amsa da cewa.

" Lafiya k'alau Sumayya,ina khalifa?dafatan kuna lafiya?

"Lafiya k'alau muke, ya fita office ma.
Wai kuwa kin kammala karatun littafin nan?

Summaya ta zarce da tambayar ta,Hidaya ta bata amsa da cewa.

" Na gama tun jiya wallahi,Yayi dad'i da ma'ana sosai,amma fa na sha kukan tausayin Ya Abbas da Safah Sumayya,ni yanzu ma lambar marubuciyar nake so ki bani saboda na jinjina mata akan namijin k'ok'arin da tayi wajen rubuta litattafan ta masu dad'i da k'ayatarwa,babu shirme ko kad'an"

Sumayya ta turo da emoji na dariya,sannan ta aiko text

"Ai gaskiya tana k'ok'ari sosai fa,yanzu haka wani littafin ta nake karantawa me suna BAHAGON LAYI,Wallahi Hidaya kika karanta littafin nan za ki sha dariya kamar ba gobe,tabbas Aunty Hassana D'an larabawa ta wanke mana zuciya a bisa kukan da muke sha a litattafan ta,wannan babu kuka sai dariya,jiya fa sai da khalifa ya koroni parlour wai zan hanashi bacci da dariya ta,aikuwa da na zauna ina ba shi labarin littafin sai da Yayi ciwon ciki don dariya,gaskiya littafin ya had' ba kad'an ba,cikin hikima tayi amfani da abubuwan da suke faruwa a zamanin nan ta fad'akar kuma ta nishad'antar"

Hidaya ta tura mata emoji na tsalle da murna da text kamar haka.

"Wallahi har kin sa na fara zumud'i tun kafin na karanta,ki turo min complete document d'in sa please Sumayya,kuma na san kina da numbarta tunda kina cikin group d'in ta,don Allah turo min yanzu,Allah yasa dai idan nayi mata magana ta kulani,naji an ce yawanci marubutan nan girman kai ne da su ,ba sa kula mutane"

Sumayya ta bata amsa.

"Eh ina da lambarta bari na baki,kuma wallahi zaki samu tarba ta mutunci daga gareta,gaskiya bata da wulak'anci,da kin mata magana da zarar ta gani za ta baki amsa cikin karamci,kuma ko littafin ta kike nema zata baki ba tare da jinkiri ba"

Hidaya ta tura mata emoji na tsalle da dariya,sannan ta tura text.

"Masha Allah,amma naji dad'in hakan,yanzu turo min lambar da littafin"

Sumayya ta turo mata lambar ta contact, sannan ta turo mata littafin BAHAGON LAYI,Hidaya tayi mata godiya sosai,sannan ta fita daga chart d'in su ta shiga contact d'in Hassana D'an larabawa,sai taga bata dad'e da sauka daga online ba,hakan yasa kawai ta tura mata sallama sannan ta sauka ta kashe data.

Bayan ta fita daga watsapp sai ta gyara kwanciyar ta sosai,sannan ta shiga wani app na wayarta mai suna (W P S office),ta nan take karatun document,nan da nan taje ta bud'e littafin BAHAGON LAYI,wanda Sumayya ta turo mata,ta fara karatu fuskarta d'auke da murmushi, tun a page d'in farko Hidaya ta fara tuntsira dariya sosai tamkar cikinta zai k'ulle,tayi dariya mai yawa wadda bata tab'a yin irin ta ba har da hawaye,har k'warewa take don azabar dariya,musamman da ta zo gun da Habiba take aljanun k'arya har fad'owa tayi daga gado don dariya,ta ajiye wayar ta dinga shek'a dariya kamar sabon kamun Hauka,sai da tayi mai isarta sannan ta d'auki wayar ta cigaba da karatu.

Tayi nisa sosai tana ta babbaka dariya,har ta zo in da Amina take lugudar bakin Harira,ai Hidaya ba tayi aune ba taji fitsari na Neman kufce mata a wando don dariya,da hanzari ta cillar da wayar ta mik'e da gudu Yayi bathroom, ta tsuguna tayi fitsari tayi tsarki da ruwan d'umi sannan ta fito tana maida numfashin wahalar dariya,tunda ta zo duniya bata tab'a dariya irin ta yau ba,littafin sosai ya wanke mata zuciya,kamata yayi masu lalurar damuwa da hawan jini su nema su karanta,zama tayi ta jawo wayar ta cigaba da karatu,dariya ta kuma sark'eta kamar me,amma Hidaya ta kasa hak'uri sai da ta kammala littafin BAHAGON LAYI tas kafin sallar azahar,da k'yar ta iya mik'ewa don d'auro alwala saboda yadda cikinta ya k'ulle don azabar dariya.

Bayan ta idar da sallah tayi addu'o'i sosai,musamman akan abin da ya shafi rayuwarta,sai ta jawo wayarta tana Neman layin mijinta ganin tunda ya fita bai kirata ba,kuma ta saba idan ya fita sai ya kirata sau goma ma kafin ya dawo,amma yau kamar ya san ta samu littafin da ke tayata hira bai nemeta ba,sau wajen biyar tana gwada kiran amma bai shiga ba,sai taji damuwa a ranta,domin bata son yin nesa da shi kwata kwata,amma tana tunawa da labarin matan BAHAGON LAYI sai ta k'yalk'yale da dariya har da rik'e ciki,tana cikin dariyar Hamza Garkuwa ya d'aga labulen bedroom d'in yana sallama,kawai tsayawa yayi ya bi ta da kallo bakinsa a sake,a tun tasowarsa bai tab'a ganin mahaifiyar sa cikin mad'aukakin farinciki da dariya kamar haka ba,sanin da yayi mata ma tafi bawa kuka da damuwa muhimmanci akan dariya.
Kawai sai ya cillar da school bag d'in sa ya ruga da mugun gudu ya nufe ta yana dariya shi ma,yana zuwa ya fad'a cinyar ta cike da farinciki,ya kalleta yana dariya yace.

"Ammi na waye ya saki dariya haka?"

Ta kuma tuntsirewa da dariya ta shafa kansa tace.

"Su Harira ne My boy"
Ya cigaba da kallonta yana murmushi kumatun sa na lob'awa(dimple)yace.

"Su wanene Harira Ammi na?

Ta rungume shi ta na goge Hawayen da ya fito mata na dariya,sannan tace.

" Ba ka sansu ba My boy,Labarin su na karanta shine suka bani dariya fa"

"Ammi na nima ki bani labarin,ina so nayi dariya kinji" Ya ambata yana rik'e hannun ta.

Ta dube shi sosai tana murmushi,sannan ta girgiza kai tace.

"Kar ka damu zan baka,amma sai kayi karatu mai yawa"

Ya amsa da hanzari.
"Zan yi Ammi na,I swear zan yi karatu da yawa,amma Ammi na kin daina kuka yanzu sai dariya ko?

Tausayin yaron ya kamata,da sauri ta jijjiga kai tayi murmushi tana kallon sa tace.
" insha Allah My boy na daina,yanzu tashi muje ka cire Uniform d'in ka kaci abinci tukun,kar malamin islamiyya ya zo baka kammala ba"

"To Ammi na,ya fad'a yana mik'ewa tsaye,ya nufi k'ofa ya d'auki school bag d'in sa da ya cillar ya fice daga d'akin da D'an gudun sa,ta bishi da kallo kafin ta runtse idanuwan ta ta sauke ajiyar zuciya,tana tuna Abubuwa masu d'unbun yawa da suka sark'afe rayuwarta,rayuwa kenan!duk yadda Allah ya shimfid'a maka ita haka zata kasance maka.

Bayan sallar magriba tayi karatun alk'ur'ani,Hamza ya d'auko litattafan sa suka yi bitar karatu,yaron yana cikin farinciki sosai a ranar ganin yadda mahaifiyarsa take walwala,duk da ya damu dalilin rashin ganin mahaifinsa ya dawo da wuri,tana ganin ya fara hamma ta rufe litattafan tace su je ya kwanta Yayi bacci,har d'akin sa ta raka shi ya sauya kayan bacci ta taimaka masa yayi brush,sannan ya haye D'an k'ara min bed d'in sa,tayi masa addu'a ta shafe masa a jikinsa,ta sakar masa net ta lullub'eshi da bargo,ya rufe idanuwansa,nan da nan bacci yayi awon gaba da shi,Sai da taga numfashin sa ya fara sauka alamar baccin ya d'auke shi sannan ta mik'e ta fito ta ja masa k'ofar.

Parlour ta dawo ta zauna tayi tagumi,shiru har lokacin bata ga sanyin idaniyarta ya dawo ba,har tashi tayi taje ta canja kwalliya me d'aukar hankalin ta bulbula turare da humra,amma shiru,wayoyinsa kuwa har ta gaji da kira basa tafiya,damuwa sosai ta bayyana a fuskarta,ta jawo wayar ta domin ta sake gwada kiran sa kawai sai ta tuna da littafin BAHAGON LAYI,k'ara binkito shi tayi ta fara maimaita karanta shi,kafin wani lokaci sai ga Hidaya na k'yalk'yala dariya har da birgima,har mai gadi ya bud'e wa mijin ta get ba ta ji ba,har sanda mijin nata ya shigo cikin gidan duk bata ji ba,har ya murd'a handle d'in k'ofar bedroom d'in ya shigo duk bata sani ba tana can kan bed kwance tana karatu tana d'irka dariya,cak!ya tsaya a bakin k'ofar ya tsura mata idanu cikin dukan zuciya da tsananin mamaki,me ya sa ka Hidaya wannan dariya haka?me ya dad'ad'a ruhin ta da ta samu farinciki haka?ba zai iya tuna lokacin da yaga Hidayan sa tana dariya haka ba.

Yafi minti biyar tsaye yana ta kallon ta bata saniba,shauk'i na d'iban sa zuwa gareta,k'afafuwan sa har wani rawa suke tamkar ba zasu d'auki gangar jikin sa ba,a matuk'ar kasalan ce ya bud'e murya da k'yar ya ambaci sunan ta.

"Hidaya naaaaaaa".


Comment
Share
Vote
pls


*TYPING*📲

✌️💔 *GARKUWA BIYU* 💔✌️

*TARE DA ALK'ALAMIN* ✍️

HASSANA D'AN LARABAWA

*MARUBUCIYAR* 👇

SANADIN HOTO
HASSANA DA HUSSAINA
CIN AMANAR RUHI
BAHAGON LAYI
BAHAGON LAYI (SABON SALO)

*DA KUMA*

GARKUWA BIYU


*BABI NA BIYAR DA NA SHIDA*


WATTPAD:Hassana3333


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️

🖊 *PEN WRITERS ASSOCIATION*🖊️


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️


______________________________________

*~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~*


_____________________________________


https://www.facebook.com/groups/1533639276725285/


Jin sautin muryar sa ya sa ta waiwayo ta kalleshi,fuskarta cike da Annashuwa tana k'yalk'yala dariya,yana niyyar takowa domin isa gare ta ta riga shi mik'ewa,da sassarfa ta nufo shi,ya ware hannayensa ya runtse idanu yana son jin ta a cikin ji kin shi,tana zuwa a maimakon ta fad'a ji kin shi kawai sai ta tsuguna gaban sa ta d'ora kanta kan cikin shi,sannan ta rungume k'ugun shi ta d'ora bakin ta dai dai saitin cibiyar shi ta D'an ciza,ya saki Y'ar k'ara kad'an yasa Hannu yana rik'o kanta,sannan ya za me a hankali ya tsuguna gaban ta kamar yadda take a tsugune tana doka masa murmushi me k'ayatarwa.

Hannun ta ya rik'o da Hannu d'aya,d'aya hannun kuma ya dafe cikin shi da shi yana D'an yamutsa fuska yana marairaicewa,cikin wata irin kasala ya fara magana.

"Wannan cizon da kika min idan kika tsige cibiyar za ki rasa ta wasa Hidaya na,ni da na tawo da hanzarin rungumar ki,kawai kuma sai ki tarbeni da cizo?

Ta matse yatsun sa a hannunta har suka ba da k'ara,ya lumshe idanu yana ajiyar zuciya, ta kai yatsan shi guda d'aya bakin ta tana tsotsa,yaji wani zirrr a ji kin shi,da sauri ya fad'a jikinta yana rungume sosai da sakin ajiyar zuciya,sai da ta tabbatar ta gama sanyayar masa da jiki sannan ta tanka.

" ka san dalilin da ya sa na cije ka?"

Ya ka sa magana illa girgiza mata kai da yayi yana lafe a jikinta,ta d'ago shi daga jikinta suna kallon juna sannan tace.

"Hukunci nayi maka fa,tunda ka fita yau ka manta da sha'ani na,baka kirani a waya ba,baka dawo da wuri ba,kawai ka rataye ni ina ta shan sharafina da kokawar tunanin halin da kake ciki"

Ya D'an girgiza kai yana gyara zama a k'asa,sannan ya jawo ta jikin shi ya kwantar kan cinyoyin shi yana shafa kanta,a hankali cikin k'aramar murya ya fara magana.

"Idan akwai ranar da za ta riske ni a fad'in duniyata wadda za ta kasance cikin mantawa da sha'anin ki,zan rok'i Allah ya d'auki raina kafin zuwan ranar,na sha mantawa da kai na fa!amma ba zan iya mantawa da ke ba Hidaya na,"

Yana direwa ta tare shi da tambaya.

"To menene ya tsayar da kai haka?"

Ya numfasa yana yawo da hannuwan sa a jikin ta.

"Yana daga cikin sha'anin ki,batun kwangilar ginin masallaci da makarantar islamiyyar nan ne,shine na tsaya muna tattaunawa da masu Aikin,domin a hanzarta kammalawa da wuri kamar yadda kike so,wayoyi na na kashe su ne saboda kar a dameni da kira,zuciyata ta k'agauta wajen son cika umarnin ki"

Ta jijjiga kai tana jin sonsa na k'aruwa a ruhinta,ya d'ago ta suna kallon juna,tana shirin magana ya riga ta.

"Na jima banga farinciki da walwala a tare da ke kamar yau ba?don Allah Hidaya na me ya faru da ke?sanar da ni da hanzari,ni ma ina son tayaki farincikin"

Maganar sa ya sa ta tuna da littafin,dariya ta k'ara kamata,ta kwashe da dariya ta fad'a jikinsa,yayi baya ya fad'i kwance,ta haye ruwan cikin shi tana dariya sosai kamar zautacciya,kawai shi ma sai ya biye mata ya kama dariyar,ganin dariyar Hidayan wani k'atoton abin alfahari ne a gareshi,sun jima suna dariya kafin da k'yar su tsagaita,da k'yar ta iya magana.

"Me yasa kake dariya?" Ta tambayeshi.

"Dariyar ki ce ta sakani dariya,Da za ki tausayawa d'okina da kin gajarce min shi ta hanyar sanar da ni dalilin yawan dariyar ki a yau,Hidaya na me ya saki dariya haka yau?" Ya tambaye ta.

Kai tsaye ta bashi Amsa.

"Hassana D'an larabawa ce"

A kwance suke amma sai da ya mik'e da hanzari yana tallafar ta jikin shi,ya tsura mata idanu cikin mamaki ya furta cewa.

"Wannan Marubuciyar me saki kuka wai?"

Ta jijjiga kai tana Murmushi,ta zarce da ba shi amsa.

"Ita ce,yau na yi dariyar da ban tab'a yin irin ta ba, wani littafin ta na karanta wai shi BAHAGON LAYI,ban tab'a cin karo da littafi mai sanya nishad'i kamar sa ba,ta cikin Hikima da sanya nishad'i a zukatan mutane ta fad'akar a kan Mata masu wata irin halayya da ke faruwa a wannan Zamanin,Cizon da nayi maka ma a cikin littafin na koyo yanda ake cizon mutum a Cibiya,shine na gwada" ta k'arasa da dariya.

Shi ma yayi dariya yana ta kallonta,dad'i na kwarara a ransa,cikin nishad'i yayi magana.

"Allah ya sa ka mata da alkairi ya biya mata buk'atun ta na alkairi,Hak'ik'a ta gama yi min komai tunda ta sakaki a farinciki,a baya Haushin ta nake ji saboda kukan da take sa ki,amma yanzu ta wanke laifin ta,kamata ma yayi na bata babban tukuici,dan haka wane tukuici kike ganin ya kamata nayi mata? Ya ambata cike da murna da zumud'i.

Tayi murmushi sosai ta zarce da tambayar sa tace.

" Amma ni ma za ka bani tukuicin farincikin ko?"

Ya rik'o kafad'unta cikin shauk'in Soyayya yana lumlumshe idanu ya fara magana.

"Eh zan baki!ai ke kyautar kaina ma zan miki gabad'aya,domin bani da abin da zan iya biyan ki da shi na wannan farincikin"

"Aikuwa kana da shi….!Ta katse shi.

Ya sumbaci goshinta ya cilla idanuwansa cikin nata yana k'ara lumshe wa.

"Da gaske?to menene?fad'i ko menene na yarje miki Hidaya na"

Ta sanyaya murya tana kwanciya a k'irjin shi tace.

"Abin da za ka biya ni da shi shine,ka amince min na bawa Anty Hassana D'an larabawa LABARI NA,domin ta rubuta shi,ina so al'umma da da ma su karanta domin su D'auki wani babban darasi a ciki,kamar yadda dukkan litattafan ta suke d'auke da darussa masu d'umbun yawa,ni ma ina so Labarin mu ya shiga sahun Labaran da za a k'aru da su a fad'in Duniya,Don Allah ka yarje min kayi min wannan Alfarmar,hakan zai k'ara sawa na tabbatar kai d'in GARKUWAR HIDAYA NE".

Ba k'aramar razana yayi da jin maganar ta ba,tamkar an buga masa guduma a kansa yaji.
A rikice ya d'ago ta cikin wata iriyar razana,idanuwan sa a warwaje yake kallon ta maganar ta nayi masa kuwwa a kunnuwan sa,kallon ta yake yi tamkar wani tab'ab'b'e bakin sa a sake ,yana maida wani irin numfashi da k'yar,bai tab'a tunanin abin da Hidaya zata furta ba kenan,da baiyi gangancin ba ta tabbaci akan zai yi mata ba,me yasa Hidaya tayi wannan tunanin?me yasa take son fallasa sirrin su har duniya ta sani?ya a kayi wannan tunanin ya shiga k'wak'walwar kanta?gaskiya ba zai iya ba,ba zai iya cikawa Hidaya burin ta ba…….!

Kasa magana yayi illa kallon da yake ta bin ta da shi,har ta gaji da jiran cewar sa ta matso ta sake nutsa kanta a cikin k'irjin shi,tayi magana a hankalin.

"Baka ce komai ba kayi shiru?ka amince min?

Girgiza kai yayi duk da ba kallon fuskarsa take ba,jin alamun motsin da jikinsa ke yi yasa ta d'ago ta k'ura masa idanu tana jiran Amsar sa.

Da k'yar ya iya fizgo magana bayan ya sunkuyar da kansa k'asa.

" Kiyi Hak'uri Hidaya na,ba zan iya amincewa da buk'atar ki ba"

Ta zaro idanu tana dafe k'irjinta,a rud'e tace.

"Why…"
"Ba na son abin da zai fallasa sirrin rayuwar mu ne,kiyi Hak'uri da wannan buk'atar ki fad'i wata zan miki kinji"

Hankalin ta ya tashi ganin tana son rasa damarta,ta marairai ce tana rok'on sa.

"Ba fallasuwar Sirri ba ne,babu Wanda zai san labarin mu a ka rubuta fa,za a sauya abubuwa da yawa ta yadda wad'anda suka San mu ma ko sun karanta ba za su gane labarin mu ba ne,Don Allah ka amince min,wannan ce kad'ai buk'ata ta a gareka ka daure ka cika min burina"

Ya d'ago ya kalleta idanuwan sa har sun fara sauya kala,ba k'aramar razana yayi ba da yaga idanuwanta har sun ciko da hawaye,ya rik'o ta cikin sauri cike da damuwa yace.

"Ki bar wannan tunanin please,muyi maganar da za ta yiwu, don gaskiya wannan ba zata yiwu ba"

Ta fashe da kuka ta fizge jikinta ta mik'e da hanzari,a gigice ya mik'e yana k'ok'arin kamata,amma ta goce ta nufi k'ofa ta fice daga d'akin da gudu,ya rud'e ya gigice saboda baya son damuwar ta ko kad'an,da hanzari ya taka ya fice ya bita yana k'wala kiran sunan ta.

"Hidaya!Hidaya!please Hidaya na tsaya ki saurare ni….!


Comments
Share
Vote
Pls


*TYPING*📲

✌️💔 *GARKUWA BIYU* 💔✌️

*TARE DA ALK'ALAMIN* ✍️

HASSANA D'AN LARABAWA

*MARUBUCIYAR* 👇

SANADIN HOTO
HASSANA DA HUSSAINA
CIN AMANAR RUHI
BAHAGON LAYI
BAHAGON LAYI (SABON SALO)

*DA KUMA*

GARKUWA BIYU


*BABI NA BAKWAI DA NA TAKWAS*


WATTPAD:Hassana3333


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️

🖊 *PEN WRITERS ASSOCIATION*🖊️


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️


______________________________________

*~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~*


_____________________________________


https://www.facebook.com/groups/1533639276725285/


Wani d'aki da ke falon ta shige da gudu tana kuka,tana shiga ta kulle k'ofar ma Dan kar ya biyo ta,gadon d'akin ta fad'a tana cigaba da kuka sosai,babu abin da take buk'ata a wannan lokacin kamar ya yarje mata a rubuta labarin su,amma me yasa ya k'i? Me yasa ya ke jayayya da hakan?.

Har bakin k'ofar ya zo hankalinsa a tashe ya fara buga k'ofar yana kiran sunan ta da rok'on ta akan ta bud'e k'ofar,amma tayi mirsisi ta cigaba da kukan ta,kukan da yake tafasa zuciyar sa da k'irjin sa,babu irin rarrashin da bai yi mata akan ta bud'e k'ofar ba ,tana jin sa tayi masa shiru sai shesshek'ar kukan ta da yake jiyo wa,a hankali ya d'ora kansa jikin k'ofar yana sauke ajiyar zuciya a jejjere,idanuwan sa suka ciko da hawaye,muryar sa da rauni sosai ya fara magana.

"Please Hidaya na ki bud'e min k'ofa,bana son wani Abu ya faru da ke,kin sani ciwon ki baya son damuwa da tashin hankali,Don girman Allah kiyi hak'uri ki bud'e min muyi magana ta fahimta kinji"

Ta na jin sa amma ta share shi,ita fa idan ba furtawa yayi cewar ya amince ba ba zata bud'e k'ofar ba,haka yayi ta magiya amma funfurus tak'i kula shi,duk da zuciyar ta na ciwo akan k'in sauraren sa,tana yi mata gargad'i da tunasar wa da cewa"Hidaya ki Amsawa GARKUWAR KI,kin sani babu wani Abu mai muhimmanci a rayuwar sa da ya kai ki a wannan lokaci,ya kamata ki tausaya masa kar ki sa ka shi a damuwa"

D'ora hannun ta tayi dai dai saitin zuciyarta ta na hawaye,sannan ta fara magana da zuciyar kamar mai magana da Wanda ke kusa da ita.

"My heart kar ki zargeni da saka GARKUWATA cikin damuwa,kawai ina tauna tsakuwa ne domin Aya taji tsoro,idan ba hakan nayi ba ba zai fuskance ni har ya yarje min Abin da nake so ba".

Ya fi minti talatin yana aikin buga k'ofar cikin damuwa,ganin tak'i bud'ewa kawai sai ya zame ya zauna a bakin k'ofar,ya jingina da k'ofar ya runtse idanuwan sa yana tuna Abubuwa kala kala,a irin Abubuwa da k'addarorin da suka sark'afe rayuwar Hidaya ya kamata ya amince da maganar ta ko domin ta samu farinciki,duk da shi ta sa zuciyar bata son hakan,amma tilas yayi hak'uri da na sa muradin domin cika muradin Hidaya,idan fa har yana so ya cigaba da dawwama da amsa sunan GARKUWAR HIDAYA.

Yadda Zuciyar sa take cikin tunani haka ta Hidaya ta kasance,haka nan ta ta zuciyar ta fi tasa shiga rud'u sosai,Abubuwa da yawa sun faru da rayuwar ta Wanda za ta so mutanen duniya su yi Alk'alanci a kan rayuwar ta da duniyar ta,Mutane guda biyu ne suka amsa sunan GARKUWAR HIDAYA,sune suka taka muhimmiyar rawa na zamantowa GARKUWARTA a rayuwa,sun mata komai ,sun kare ta,sun tsare ta,sun tarairayeta,sun rungume ta,a lokacin da take cikin tsaka mai wuya tun daga Yarinta har zuwa girman ta ko domin saboda Soyayya da raunin ta,had'i da wata gingimemiyar lalura me girma da ta zamo k'addarar ta,a fahimtar Hidaya idan a kace GARKUWA to ana nufin mutumin da ya jib'anci al'amuran ka,kuma ya taimake ka a rayuwa,yayi k'ok'arin tsareka da duk wani sharri da zai sameka,ya hanaka kuka,ya rasa Abubuwa da dama a rayuwar sa domin ya farantawa taka rayuwar,yayi k'ok'arin tsare maka mutuncin ka,ya hak'ura da bin son zuciyar sa domin ya farantawa taka zuciyar,ya gwammace ya rasa Abubuwa masu muhimmanci na rayuwar sa domin ya kyautata taka rayuwar,idan abin farinciki ya sameka ya kan fika murna,idan damuwa ko bak'inciki ya sameka ya kan fika shiga tashin hankali,wannan shi ake kira da GARKUWAR MUTUM,haka nan yawan ci akan samu mutum d'aya ya zamo GARKUWAR mutum,ko ya zama GARKUWAR Mutane da yawa,amma ita Hidayan GARKUWAR ta sun kasance guda BIYU,wad'anda suka taka muhimmiyar rawa a rayuwar ta da duniyar ta,har ta kasa bambance shin wanene ya canacanta a kira shi da GARKUWA ta farko?dalilin da yasa take son Mutane su karanta tarihin rayuwar ta kenan!ko domin su bambance a cikin mutane guda biyun wanene ya dace a kira shi da GARKUWAR HIDAYA?

Wucewar Awa d'aya cif Hidaya na cikin tunane tunane,a lokacin ne kuma ta daina jin motsin mijin nata a bakin k'ofar d'akin ta,ciwon kai sosai take ji kamar kan ta zai tsage,barci ya k'i ziyartar idanuwan ta,a hankali ta mirgina ta mik'e zaune ta rik'e kan nata da hannuwa biyu,Jim kad'an sannan ta mik'e tsaye tana jin juwa kamar za ta fad'i, a hankali ta isa bakin k'ofar ta tsaya,ta D'an sa ka kunnuwanta jikin k'ofar tana son jiyo motsin sa,shiru ko saukar numfashin sa bata ji ba,d'ora hannun ta tayi akan mabud'in k'ofar ta murza key ta bud'e a hankali,yanayin jikinta da taji yana son sauyawa shiyasa take son shan magani,kuma maganin yana parlour, A hankali ta fito daga bedroom d'in tana takawa cikin sand'a har ta isa tsakiyar Parlour'n in da magungunan suke akan center table,kwata kwata bata lura da shi ba yana kwance akan doguwar kujera rigingine,ya rufe fuskarsa da hannayensa sa,d'aukan maganin tayi ta juya a hankali za ta koma d'akin,shi kam daman idanun sa biyu,kuma tun fitowar ta yake kallonta da k'asan idanu,kuma ya san bata ankara da shi ba da ba zata fito ba,sai da tazo dab da shi zata gota shi sannan ya d'ago hannun sa guda d'aya ya rik'o nata hannun,a rikice kuma a tsarace ta zabura saboda abin ya zo mata bagatatan!ta waiwaya da sauri ta na duban sa amma idanuwan sa a runtse suke,ta cigaba da kallon k'ayatacciyar fuskarsa ta ragowar hasken fitilar da ta haskake parlour'n ,a hankali ya soma Jan hannun ta har ya dangana ta da jikin shi yana daga kwance,kan k'irjin shi ya d'ora ta ya kwantar da ita,a tare suka sauke ajiyar zuciyar da ta zo musu,ya sa Hannu yana shafa bayanta har lokacin idanuwan sa a rufe,a hankali cikin raunin murya ya soma magana.

"Me za ki yi da magani cikin Daren nan"?

Tayi shiru babu amsa tana sakin Numfashi,bai damu da shirun ta ba ya sake jefa mata wata tambayar.

" Ba kya jin dad'i ne ?wani gurin na yi miki ciwo ko?"

Sai lokacin ta D'an gyad'a kai a hankali,yayi ajiyar zuciya ya mik'e zaune tare da ita a jikinsa,tana kan cinyoyin sa ya rungume ta a k'irjin shi yana shafa kumatun ta.

"Kina son saka mu a damuwa ko?ban da haka ai kin san ciwon ki baya buk'atar yawan damuwa Hidaya,ita fa Lafiya GARKUWAR jiki ce,ana buk'atar mutum ya dinga yawan kulawa da ita a ko yaushe,kin san wahalar da kike sha idan ciwon ya tashi ,ba ke kad'ai ba,har da ni da na kasance GARKUWAR ki"

Danshin da yaji a k'irjin shi ya sa shi d'ago kanta da hanzari yana duban fuskar ta,hawaye sosai idanuwan ta ke fitar wa,Hannu ya sa ya share mata hawayen yayi miskilin murmushi yace.

"Me kike so?Har yanzun zuciyar ki na nan akan bakan ta na son a rubuta Labarin mu?"

Da sauri ta gyad'a kai alamar haka ne.

Ya rik'o kafad'un ta yana yi mata wani kallo da ta kasa fassarashi,cikin shauk'in k'auna ya kai harshen sa kan fuskarta ya fara lasar hawayen ta yana shanyewa,sai da ya lashe tsaf yana ta faman sakin ajiyar zuciya sannan ya jefata k'irjin shi ya rungume ta tsam,da wata irin murya ya fara ambatar.

"Na amince Hidaya,wallahi na amince Hidaya na,idan har hakan zai faranta Zuciyar ki".

Wani farinciki ya ziyarci zuciyar ta da ta jima ba taji irin shi ba,Ruk'unk'ume shi tayi cikin murna tana rungumar sa,ya tarbeta shi ma suka karad'e junan su da runguma da sumbata kamar su cinye juna,ganin farincikin ta shine abin da yafi so a rayuwa, idan Hidaya na farinciki ya kan ji tamkar an masa kyautar Aljanna ne.

Wucewar mintuna Hidaya na zuba masa kalaman godiya da Soyayya,shiru yayi yana sauraron ta idanuwansa lumshe,zak'in kalaman na ratsa k'wak'walwar shi,sai da ta kammala sannan ya fara mayar mata da raddi,raddin da bai yi kala ko kama da nata ba,raddin da ya shallake tunanin ita kanta Hidayan,raddin da duk k'uncin da zuciya take ciki muddin aka nufeta da shi sai ta raunana ta girgiza,kafin wani lokaci sai ga ma'auratan suna shirin sumewa a fagen SOYAYYAH……!


Comment
Share
Vote
Pls


*TYPING*📲

✌️💔 *GARKUWA BIYU* 💔✌️

*TARE DA ALK'ALAMIN* ✍️

HASSANA D'AN LARABAWA

*MARUBUCIYAR* 👇

SANADIN HOTO
HASSANA DA HUSSAINA
CIN AMANAR RUHI
BAHAGON LAYI
BAHAGON LAYI (SABON SALO)

*DA KUMA*

GARKUWA BIYU


*BABI NA TARA DA NA GOMA*


WATTPAD:Hassana3333


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️

🖊 *PEN WRITERS ASSOCIATION*🖊️


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️


______________________________________

*~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~*


_____________________________________


https://www.facebook.com/groups/1533639276725285/


*** Ranar sun kwana cikin farinciki tare da faranta ran juna,Hidaya ta dage sosai wajen nuna masa kulawa da godiyar ta gareshi,shi kansa yayi mamakin Hidaya a ranar,domin wasu abubuwan da tayi masa bata tab'a kwatanta yi masa ba,Daren ya sa ka shi cikin darare masu muhimmanci a rayuwar sa.

Sai bayan da Hidaya tayi bacci ne sannan zuciyar sa ta shiga tunani akan wasu abubuwa iri iri da suka wanzu,kawai ya tsinci kansa ne da zubda hawaye mai k'una da zafi,yayi kuka sosai Wanda ya jima bai yi irinsa ba,kuka na kewa da ciwon zuciya,duk da abubuwa sun daidai ta a gareshi amma ba zai tab'a mantawa da baya ba,har sai lokacin da ya koma ga mahaliccin shi.

Kukan sa yayi yawa har ya fara bayyana,ganin Hidaya na motsi ya sa shi had'iyewa ya rufe baki,ya k'ura mata ido yana kallon yadda take bacci cikin kwanciyar hankali,ta k'ara kyawu a idanuwansa,ya kai Hannu ya shafi fuskarta yana tuna yadda ta rikice masa yanzu ta rud'a shi ta rud'a kanta,ya lumshe idanu yana jin tsigar jikin shi na tashi musamman da ya tuna wani Abu da tayi masa Wanda kad'an ya rage ya sumar da shi saboda shauk'i,Hidayan sa Muradin sa,yana rok'on Allah ya tsawaitawa Hidaya kwanakin ta na duniya har ya riga ta mutuwa,duk da Hidayan ta kasance mai lalura!amma kuma kad'an daga ikon Allah ne ya d'auki ran mai lafiya ya bar Mara lafiya.

Sai da k'arfe biyu da mintuna na dare yayi sannan ya iya zare jikin shi daga na Hidaya,ya sa ka mata pillow sannan ya iya mik'ewa ya shige bathroom domin ya tsaftace jikin shi,har lokacin Hawaye yana ratso fatar idanuwan sa,a haka yayi wankan sa na tsarki sannan ya d'aura Alwala ya fito,jallabiya me dogon Hannu ya sa ka da gajeren wando ,ya feshe jikin shi da turare mai sanyin k'amshi,darduma ya shimfid'a ya hau domin sallar nafila,sai ya waiwaya ya kalli Hidayan,har lokacin bacci take cikin kwanciyar hankali tana rungume da pillow a k'irjin ta,yayi murmushi ya sa Hannu ya goge k'wallar idanuwan sa sannan ya kabbara sallah.

Ya dad'e yana sallah hawaye bai bar zuba a idanuwan sa ba,har ya kammala ya d'auki alk'ur'ani ya fara karantawa yana kuka,sosai zuciyar sa tayi rauni,ya karanta izifi biyu sannan ya rufe alk'ur'anin ya soma jero addu'o'i na larabci da Hausa,yana zuwa kan wata addu'a kawai sai ya kife kansa kan gwiwoyin sa yana malalar da hawaye,da k'yar ya iya k'arasa addu'ar ya shafa.

Bai koma bacci ba!kawai sai ya d'auki carbi yana yi wa Annabi (S A W)salati da kirari,idanuwan sa na kan Hidaya,yana zaune ya tuna da HAMZA GARKUWA,kwata kwata bai saka shi a idanuwan sa ba tun da ya dawo gidan,har gashi dare ya tsala,rigimar Hidaya ta mantar da shi komai!mik'ewa yayi a hankali ya fito daga bedroom d'in su zuwa na Hamzan,ba zai iya jurewa zama bai ganshi ba,ya san shi kansa yaron da tunanin sa yayi bacci,tunda tun safe rabon da su ga juna balle suyi magana,yana isa bakin k'ofar yasa Hannu ya bud'e d'akin ya shiga a hankali,ya kai Hannu kan makunnin fitila ya kunna,haske ya gauraye d'akin sosai.

Hamza na kwance kan D'an k'ara min bed d'in sa yana ta bacci lullub'e da bargo,numfashin sa na sauka a hankali,cikin wani irin taku ya k'arasa gaban yaron ya zauna bakin bed d'in,k'ura masa idanu yayi kafin ya sa Hannu ya shafa kan shi zuwa kyakkyawar fuskar shi da D'an k'ara min bakin shi,ya sunkuya ya sumbaci goshin shi,sannan ya dinga karanto addu'o'i na kariya daga shaid'anu yana tofa mi shi yana shafa mi shi a jikin shi.

Ya jima a d'akin kafin ya fito ya koma bedroom d'in su,a lokacin wasu masallatan sun fara kiran sallar Farko,ya tarar Hidaya ta farka tana laluben sa tana kiran sa cikin k'aramar murya,da Hanzari ya k'arasa kusa da ita yana kamata ya rik'e ta a jikin shi ya rungume ta yana fad'in.

"Kin ganni nan fa,kin farka?me kike so?

Ta kwantar da kanta a k'irjin shi,cikin k'aramar murya tace.

" Zan sha Ruwa".

Da Hanzari ya jinginata da gadon ya mik'e ya fice daga bedroom d'in,Jim kad'an ya dawo da ruwan faro a hannun sa da cup me D'an girma,da kansa ya tsiyayi ruwan ya ba ta ta shanye,ya kuma tsiyaya ya sake bata shi ma ta shanye,ya dad'a mata ta sha rabi ta rage rabi ta na sauke ajiyar zuciya.

Ya dire cup d'in kan bedside, ya waiwayo yana jawo ta jikin shi,kafin yayi magana ta riga shi magana.

"Ina kaje…!?

Ya kai Hannu yana wasa da kunnen ta yace.

" Na je na yiwa GARKUWA addu'a ne,kuma na gan shi,ban samu ganin sa ba da na dawo saboda rigimar ki"

Tayi murmushi ta na gyara kwanciyar a jikin shi ta na lumshe idanu za ta koma bacci,da sauri ya d'ago ta yana kallon cikin idanuwan ta yana hura mata iskar bakin shi.

"Wake up My Hidaya,kinji masallaci can ana kiran Sallah,yanzu za a yi assalatu,tashi nayi miki wanka saboda kar mu rasa Sallah.

Ta na langab'e a jikin shi ya d'auketa har bathroom, da kansa yayi mata wanka saboda jikinta babu k'wari,sai da ya kammala mata sannan ya d'aura mata towel,ta yi brush tare da d'aura alwala,shi ma ya sake alwala sannan suka fito.

Doguwar riga mai hijab ya d'auko mata ya saka mata,sannan yace tayi raka'atanil fijr saboda assalatu tayi,yana ganin ta tayar da sallah yayi sauri ya fice ya nufi d'akin Hamza ya tashe shi,yaron bacci cike a idanuwan sa amma haka ya tashi,ya raka shi bakin toilet ya karanta masa addu'ar shiga band'aki,shi ma ya fad'a,sannan suka shiga,ya sa masa MacLean a brush ya wanke bakin shi,sannan ya fito ya bar shi yayi fitsari da alwala,yana tsaye har ya fito,ya taimaka masa ya cire masa sleeping dress d'in sa ya ba shi Pakistan na riga da wando ya saka,sannan ya kama hannun sa suka fice zuwa masallaci domin sallatar sallar Asuba.

Sun D'an jima har sai da gari ya fara Haske sannan suka dawo gidan,a ktcheen suka tarar da Hidaya ta na k'ok'arin d'ora break fast,ga abincin school da take girkawa Hamza,da sauri Hamza ya nufe ta yana rungume k'ugunta yana murmushi,ita ma tayi masa murmushi ta na Jan karan hancin sa,ya zame ya durk'usa ya gaishe ta.

"Ina kwana Ammi na?"

"Lafiya k'alau!dafatan ka tashi lafiya?" Ta amsa tana kallon sa.

Ya waiwaya ya dubi mahaifinsa da ya jingina da drower d'in ktcheen yana ta kallonsu fuskarsa k'unshe da fara'a,sannan ya juya ya kalli Hidaya yace.

"Eh!na tashi lafiya Ammi na….yau fa har mafarkin granny nayi,yaushe za ta dawo ne…?

" Ta kusa insha Allah"

Mahaifin sa ya ba shi Amsa,sannan ya matso ya durk'usa gabansa ya rik'o hannuwan sa yace.

"Mu je na taya ka shiryawa kar ka makara a school,ka ga Ammin ka dai girki take yi ".

" To daddy"Hamza ya amsa yana murmushi.

Jan hannun sa yayi suka nufi bakin k'ofa,a hankali ya waiwayo ya dubi Hidaya da ke tsaye tana bin su da kallo,wani irin kallo yayi mata tare da kanne mata ido d'aya,ya D'an turo bakin sa alamar sumbatar ta,murmushi tayi tana lumshe idanu,har suka fice daga ktcheen d'in ta juya ta cigaba da aikin ta,zuciyar ta cike da farin ciki.

Bayan ta kammala da kanta ta taya mijin nata Shiryawa a hanzar ce,saboda yadda masu aikin kwangila suka dame shi da waya,tare da Hamza ya fita ya sauke shi School sannan ya wuce.

Ita kam Hidaya sai da ta kammala komai na Aikin gidan sannan ta hakimce a kan kujerar parlour'n ta,ta d'auki phone d'in ta ta bud'e data ta shiga b'angaren WhatsApp, sak'onni suka dinga shigowa a jejjere,cikin ikon Allah taci karo da abin da take so,wato Amsa sallama daga Hassana D'an Larabawa,da hanzari ta bud'e sak'on,sai taga a lokacin ma tana online,fuskar ta ta cika da fara'a,zumud'i ya ishe ta,hannun ta na rawa ta fara k'ok'arin rubuta sak'o domin tura wa Marubuciya HASSANA D'AN LARABAWA.....!


Comment
Share
Vote
Pls


*TYPING*📲

✌️💔 *GARKUWA BIYU* 💔✌️

*TARE DA ALK'ALAMIN* ✍️

HASSANA D'AN LARABAWA

*MARUBUCIYAR* 👇

SANADIN HOTO
HASSANA DA HUSSAINA
CIN AMANAR RUHI
BAHAGON LAYI
BAHAGON LAYI (SABON SALO)

*DA KUMA*

GARKUWA BIYU


*BABI NA GOMA SHA D'AYA DA NA GOMA SHA BIYU*


WATTPAD:Hassana3333


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️

🖊 *PEN WRITERS ASSOCIATION*🖊️


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️


______________________________________

*~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~*


_____________________________________


https://www.facebook.com/groups/1533639276725285/


"Ina fatan ina magana da marubuciya Anty Hassana D'an Larabawa?"

Abin da Hidaya ta rubuta ta tura kenan.

Sak'on yana tafiya cikin minti d'aya taga alamun Hassana D'an Larabawa na typing alamun dawo da amsa,ta fara murmushi tana jiran ganin amsa.

"Eh ita ce sister,da wa nake magana?"

Hassana D'an Larabawa ta rubutowa Hidaya ,har da emoji mai nuna alamun murmushi.

Hidaya taji dad'i ta mayar mata da amsa.

"Sunana Fatima,amma ana yi min lak'abi da Hidaya,ni masoyiyar ki ce kuma masoyiyar rubutun ki,saboda na k'aru da Abubuwa da dama a cikin su,nayi kuka sosai,haka nan nayi dariya musamman a BAHAGON LAYI,domin jiya har cizon da Habiba tayi wa Malam Arabi a cibiyar sa sai da na gwada akan Mijina ni ma"

Hassana tana karanta sak'on Hidaya ta turo emoji na zare idanu da mamaki,sannan ta turo sak'o.

"Mijin ki kuma?haba Y'ar uwa Fatima! Ai ban rubuta Dan ki kwaikwaya kiyi wa mijinki ba,sai dai kuma idan cizon Soyayya ne"

Hidaya tayi dariya ta gyara zaman ta har da kashigid'a,sannan ta tura Amsa kamar haka.

"Wallahi Anty Laifi yayi min ne,shiyasa na rama da cizo"

Hassana ta tura alamun dariya da sak'o.

"Ayya Fatima!mazajen mu ai sai muna hak'uri da su daman,Allah dai ya kyautata zamantakewar mu da su?

" Ameen Anty Hassana"

Hidaya ta amsa da hakan.Sannan ta sake tura sak'o.

"Naji dad'i sosai da kika saurare ni har nayi magana mai tsawo da ke,hakan ya nuna min abin da ake fad'a akan marubuta ba gaskiya bane,ana yawan cewa kuna da wulak'anci idan akayi muku magana bakwa amsawa mutum,ni kuma yanzu sai naga Ashe ba haka abin yake ba,ba a taru an zama d'aya ba"

Sak'on ya D'an yi minti uku ba tare da Hassana ta duba ba,sai can ta duba ta fara rubuto amsa.

"Sorry Fatima na D'an amsawa wasu magana ne kin jini shiru,Ai gaskiya ya kamata Mutane su dinga yiwa marubuta uzuri,saboda wani zubin suna da ayyuka a gabansu,ga rubutu,hakan yasa idan akayi musu magana ta kan d'auki lokaci babu amsa,amma tabbas akwai masu shariyar,kuma suma muna k'ok'arin nusar da su cewar su dinga kyautata mu'amalar su da mutane,saboda duk mai sonka ya gama yi maka komai a rayuwa,ni ina girmama masoyina,domin bani da abin da zan biya shi da shi na nuna soyayyar sa gareni"

Hidaya na ganin amsar ta jijjiga kai tayi murmushi, sosai ta sake jin k'aunar Hassana D'an Larabawa a ranta,hakan yasa ta kuma tura sak'o.

"Gaskiya hakane Anty Hassana,wannan maganar ta ki ta sa na kuma jin k'aunar ki a raina da fatan zumunci ya k'ullu tsakanina da ke,amma akwai tambayar da nake so nayi miki idan babu damuwa"

Hassana ta dawo da Amsa.

"Babu damuwa,Allah ya sa na sani,kuma Allah ya bani ikon Amsawa".

Hidaya ta rubuta ta tura.

" Da gaske littafin SANADIN HOTO true life story ne?"

Hassana D'an Larabawa ta tura emoji na dariya da sak'o.

"Tabbas haka ne,Labarin littafin ya faru da gaske,kamar yadda labarin CIN AMANAR RUHI ya faru da gaske"

Hidaya ta D'an zaro idanu ta gyara zama ta tura emoji na mamaki da sak'o.

"Amma gaskiya nayi mamaki Anty Hassana!saboda banga kin rubuta cewa true life story ba ne,kar kiga na dame ki da tambaya pls menene dalilin hakan?"

Hassana ta tura wa Hidaya Amsa.

"Akwai dalili da yawa gaskiya,kad'an daga ciki shine,na san labarin SANADIN HOTO ya tab'awa mutane zuciya da yawa,duk da ban fad'i cewar gaske bane,to ya kike tunani idan na bayyana shi a matsayin gaskiya ne?kinga zai zaunawa mutane a zuciya suyi ta tunanin abin zuciyar su tana yin ba dad'i,sannan ana samun wasu matsalolin da dama akan Rubuta true life story,kad'an kenan daga abin da yasa ban cika rubuta wa ba"

Hidaya ta amsa .

"Hakane gaskiya!to idan babu damuwa ina son na tattauna wata magana ne da ke Anty Hassana,idan har za ki bani damar hakan"

Sai da sak'on yayi minti biyu sannan Hassana ta dawo da Amsa.

"Ina sauraren ki babu damuwa,ina da isasshen lokaci a yanzu babu abin da nake yi"

Hidaya ta turo da emoji na tsalle da murna,sannan ta fara Rubuta sak'o ta tura.

"Anty Hassana tunda na fara karanta litattafanki nake jin kin shiga zuciyata,domin babu wani littafin ki da za a karanta ba tare da an k'aru ba,kina duba abubuwan da suke faruwa kiyi rubutun akai ba tare da shirme ba,haka nan babu batsa sai yawan addini da kike sakawa,kamar littafin CIN AMANAR RUHI wani wa'azi ne me zaman kansa,haka nan ragowar litattafan ki,a lokacin da nake karantawa babu abin da nake hangowa sai tawa rayuwar da k'addarorin da suka sark'afeta,na tabbatar da mutane za su ji labarina akwai muhimman Abubuwa da za su k'aru da su a cikin Labarin,domin ya tattara komai,idan nace komai to ina nufin komai d'in,da na zauna nayi tunani sai naga ni ba Marubuciya ba ce,kin san kowa da baiwar sa,k'ila ni idan na Rubuta Labarina ba zai kai inda nake so ba,haka nan ba zai yi armashi kamar yadda idan ke ce kika Rubuta zai yi ba,shiyasa na zab'eki a matsayin wadda ya dace ta Rubuta Labarina,kuma ina fata da d'okin jin amsa wadda zata sakani farinciki daga gareki".

Hassana D'an Larabawa ta jima tana Nazari akan sak'on Hidaya kafin ta bata Amsa da cewa.

"Naji dad'i Sosai da kika zab'o ni a cikin dubun dubatar Marubuta domin na Rubuta Labarin ki,duk da dai ban san me Labarin ya k'unsa ba,sai dai akwai sharad'i akan Hakan….!

" Wane sharad'i ne Anty Hassana?" Hidaya ta tambaya.

"Akwai Yanayin Labarin da Hannuna baya Rubutawa,Musamman Labari na Batsa ko Wanda ba zai amfani al'umma ba,domin duk abin da muka rubuta abin tambaya ne,mu na mantawa da Lahirar mu mu na bin rud'in duniya,bayan gidan Lahira shine tabbas a garemu,kamar yadda Allah (S W A)yace a cikin alk'ur'anin sa mai Girma.

"وماھذہ الحیٰوة الدنیا الا لھو ولعب ،وإن الدار الاّخرة لھی الحیوان،لو کانوایعلمون"

(Rayuwar wannan duniya ,ba komai ba ce ,face wasa da wargi.Lallai gidan Lahira shi e rayuwar,da Mutane suna da ilimi).

Zan saurari Labarin ki idan har Wanda ya kamata a rubuta ne to zan rubuta ko domin Mutane su k'aru da shi,hakan ma kuma a bisa wani sharad'in na cewa har sai na tabbatar da amincewar Mijinki wajen Rubuta Labarin,domin a yanzu shine yake iko da ke,a k'ark'ashin sa kike,idan har wad'annan sharud'an suka cika to babu Haufi da yardar Allah zan Rubuta Labarin ki domin Duniya ta karanta.

Dad'i ya kwarara a Zuciyar Hidaya,ta dinga tura stickers da emojis na murna da jin dad'i da dariya,daga k'arshe ta Rubuta sak'o ta tura.

"Insha Allahu zaki sameni mai cika sharud'an ki Anty Hassana,ban tunkare ki ba har sai da na fara samun amincewar mijina,da izininsa komai zai tabbata,haka nan Labari na bai shafi Batsa ko wani Abu da bai kamata ba,Hasali ma ni bana karanta litattafan Batsa,domin suna cutar da mutum da idanuwan sa,haka nan masu Rubutawa na kan yi mamakin yadda suke tak'ark'arewa suna rubuta abin da ba zai amfanesu ba balle ya amfanar da al'umma,illa ma su dinga jawowa Kansu fushin Allah,haka nan su tarawa Kansu zunubai a maimakon lada"

Hassana D'an Larabawa tayi murmushi ta rubuta Amsa.

"Naji dad'in Maganarki akan Mijinki,sai dai duk da hakan zan k'ara bincike akan hakan kafin komai ya fara wakana insha Allah,Batun rubutun Batsa kuma mu na nan mu na yiwa masu yi addu'a da fatan Allah ya shirye su su daina,idan har suka tuba suka daina Allah zai yafe musu ya karb'i tuban su,domin Allah yana cewa.

"یأیھا الذین ءامنوا توبوا الی اللہ توبة نصو حا عسیٰ ربکم ان یکفر عنکم سیٸاتکم"

(Ya ku wad'anda suka yi imani ku tuba zuwa ga Allah tuba na gaskiya,tabbas Ubangijinku zai gafarta muku laifuffukan ku).

Haka nan a wata ayar ya sake cewa.

"و ھو الذی یقبل التوبة عن عبادہ و یعفوا عن السیٸات و یعلم ما تفعلون"

(Shine Wanda yake karb'ar tuba daga wajen bayinsa,kuma yake yin afuwa game da munanan aiyuka).

Dan haka mu na yi musu addu'a da wasiyya da suji tsoron Allah a duk in da suke,su tuba,Allah zai gafarta musu,Allah ya gafarta mana gabad'ayan mu.

Hidaya ta ji dad'in tattaunawar su har bata san lokaci ya k'ure ba,kiran wayar ta da mijin ta yayi ne yasa ta yiwa Hassana D'an Larabawa Sallama,da Alk'awarin zuwa Anjima za su sake had'uwa online ko ta kira ta.

Hassana ta bata Amsa da cewa.

"To babu laifi Fatima,Madalla,Allah ya kai mu lokacin da rai da lafiya"

Hidaya ta sauka online ta fara k'ok'arin d'aga wayar mijin ta……!


*****************

Bayan kwana biyu Abubuwa da dama sun faru,in da alak'ar Hidaya da Hassana D'an Larabawa tayi Girma,Marubuciya Hassana ta tabbatar da cewa Labarin Hidaya ya dace a Rubuta shi,musamman da ya kasance tsaftataccen Labari kuma duk wasu sharad'ai Hidayan ta cika su,bisa ga amincewar Mijin ta,a lokacin da Hidayan kuma ta bata Labarin ta shiga rud'ewa da k'ara jinjina Buwayar Ubangiji,Wanda shi ke yin komai da ya so a kuma lokacin da ya so,tabbas Labarin Hidaya wani Babban Jigo ne da idan mai karatu yayi nasarar karantawa zai sha Mamaki da Al'ajabi,Haka nan Labarin Hidaya ya tara komai,akwai nishad'i,Soyayya,bajinta,tausayi,fad'akarwa,wa'azantarwa,kulawa,sadaukarwa,jarrabawa,k'addara,aminci,da dai sauran su.

Kwana Hassana D'an Larabawa tayi tana jinjina Labarin Hidaya, tana jin Labarin a Zuciyar ta fiye da duk wani Labari da ta Rubuta,washe gari da safe kuwa bayan ta kammala komai ta fara k'ok'arin Rubuta Labarin Hidaya kamar Haka…..!


Comment
Share
Vote
pls


*TYPING*📲

✌️💔 *GARKUWA BIYU* 💔✌️

*TARE DA ALK'ALAMIN* ✍️

HASSANA D'AN LARABAWA

*MARUBUCIYAR* 👇

SANADIN HOTO
HASSANA DA HUSSAINA
CIN AMANAR RUHI
BAHAGON LAYI
BAHAGON LAYI (SABON SALO)

*DA KUMA*

GARKUWA BIYU


*BABI NA GOMA SHA UKU DA NA GOMA SHA HUD'U*


WATTPAD:Hassana3333


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️

🖊 *PEN WRITERS ASSOCIATION*🖊️


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️


______________________________________

*~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~*


_____________________________________


https://www.facebook.com/groups/1533639276725285/


*FARKON LABARI*


***Tana zaune a tsakar gida kan kujera Y'ar tsuguno,dankali ne na turawa a gabanta da wuk'a a hannun ta tana feraye wa,motsin da taji ya sa ta d'ago kai tana kallon bakin k'ofar parlour'n ta.

Tsaye yake ya d'aga labule yana kallonta,idanuwan sa da alamun bacci ya farka,yayi mik'a yana salati kafin ya sauke kallonsa a kanta,a hankali ya ta ko ya fito tsakar gidan ya nufo in da take,yayin da ta dakata da ferayar ta na kallon sa cikin kulawa da murmushi akan fuskarta.

Yana isowa gabanta ya tsuguna ya mik'a Hannu ya karb'i wuk'ar hannun ta,sannan ya d'auki dankalin ya cigaba da ferayewa,a lokacin ne kuma yayi magana.

"Haba Umma,maimakon ki tashe ni nayi Aikin da kaina,ai bai kamata ni ina bacci ke kuma kina aiki ba,ni ya kamata nayi aiki ke kuma ki huta,gashi ma har yamma tayi sosai ban san lokacin da baccin ya kwashe ni ba bayan na idar da sallar la'asar"

Umma tayi murmushi ta dubeshi da kulawa tace.

"Haba HAMZA!wannan ai Aikina ne ba naka ba,gani nayi yau kamar Azumin yana baka wahala shiyasa ma na k'yaleka ban tashe ka a baccin ba,saboda na san shi kansa baccin mai Azumi ibada ne,yanzu nake shirin da na kammala ferayar dankalin nan na taso ka domin kaje bakin titi ka samo mana kayan marmari da dabino da za mu yi bud'e baki da su".

Hamza ya jinjina kai yana cigaba da ferayar dankalin.

" To Umma,bari na kammala wannan sai na fita na nemo mana,ni na zaci ma akwai ragowar dabinon ai?

"Babu ya k'are wallahi,jiya da yara suka shigo wasa na rarraba musu ragowar"
Umma ta amsa tana k'ok'arin tattara b'awon dankalin za ta kwashe,ganin har ya kammala ferayewa.

Da sauri ya amshi tsintsiyar ya tattara,ita kuma Umma ta karb'i dankalin ta d'auraye ta nufi kitchen domin d'orawa.

Bayan ya zubar da b'awon a shara,ya nufi Famfon da ke tsakar gidan ya d'auraye hannayensa ,d'akin sa ya nufa ya cire jallabiyar jikinsa,sannan ya saka wani yadi na kufta me kyau da ya sake fito masa da asalin kyawun zatinsa,babu Wanda zai kalleshi yace bai haura shekaru Ashirin da wani abun ba,amma a lokacin yana da shekaru goma sha takwas kacal a duniya ne,tsantsar kamalar sa da haibarsa ke sawa Mutane na yi masa kallon Babban mutum.

Yana fitowa daga d'akin sa Umma na fitowa daga kitchen da flask d'in shayi a hannun ta,ta dubeshi tana jin dad'i a ranta sosai,har ta kasa had'iye wa sai da ta furta.

"Ka yi kyau Hamza,yadin nan yana yi maka kyau Sosai"

Yayi murmushi kansa a k'asa yace.

"Asalin kyan ai naki ne Umma,Hamza ke ya gado a fagen kyawu"

Tayi dariya tace.

"Anya kuwa?ai ni na tsufa,kyawun ya fara gushewa kwamanda"

Ya d'ago idanuwan sa ya kalleta da kyautatawa yace.

"Wai Umma menene kwamanda?wataran sai naji kina ambato na da kwamanda"

Ta sauke numfashi tace.

"Sunan ka ai sunan Kwamandan Yak'in uhudu ne,wato sayyadina Hamza,shugaban masu shahada na musulmai,shiyasa wataran nake maka alkunya da kwamanda"

Ya lumshe idanuwan sa ya bud'e yana jinjina kai,a hankali ya furta.

"Allah ya k'ara yarda da aminci ga sahabban manzon Allah (S A W)"

Umma ta amsa da "Ameen" sannan ta zarce da cewa.

"Bari na d'auko maka kud'in da zaka siyo kayan marmarin"

Da hanzari ya tare ta.

"Ki barshi kawai Umma,ina da kud'i fa"

Ta waiwayo ta k'ura masa idanu,kafin tace.

"Kana da kud'i ?ina ka samu kud'i?

Ya D'an Sosa k'eya yana murmushi,ya langab'e kai yana dubanta yace.

" Tun Wanda KHALEEL ya turo min ne fa,har yanzu basu k'are ba Umma akwai ragowa da yawa"

Umma ta girgiza kai tana murmushi tace.

"Ayya!Allah sarki Ibraheem,Allah dai ya saka masa da alkairi,Ubangiji ya bar amintarku har zuwa Aljanna,yadda yake taimakon ka Allah ya taimaka shi a dukkanin lamuran sa shi ma"

Hamza ya amsa cikin shauk'i.

"Ameen Umma,ai khaleel jinin jikina ne Umma,ni da shi tamkar Jini da hanta ne"

Sannan ya zarce da cewa.

"Bari naje nayi sauri na dawo Umma,yamma na dad'a yi bana son Magriba tayi ban dawo ba"

Yayi hanyar fita daga gidan,Umma nayi masa fatan alkairi da dawowa lafiya.


****************


A cikin wani kango suke zaune su biyu,wata mata me kyakkyawar sura tana kwance a k'asa tayi matashi da wata jaka, ga Yarinya da bata wuce shekaru takwas ba zaune a gabanta rik'e da hannayen ta,da doguwar Riga a jikinta Y'ar kanti mai d'ankaren kyau,kanta ba d'ankwali sai kalba da ta zubo har kafad'unta an mata adon duwatsu a kanta,yarinyar siririya ce k'warai,sai dai tana da kyawu dai dai gwargwado.

Yarinyar tana rik'e da hannun Uwar tana girgizawa da ambatar sunanta.

"Mummy!mummy!mummy ki tashi mu tafi daga nan,nan fa bashi da kyau,ki tashi mu koma gida kinji mummy…!

Uwar ta D'an bud'e idanuwanta da suka yi jajir alamun tana cikin tsaka mai wuya,da k'yar ta iya magana tana kallon yarinyar.

" Hidaya bamu da wata hanya da zamu fita daga nan!nan shine mafakar mu!nan shine rufin asirin mu!ko ni ban tsira ba ke ina son ki tsira Hidaya,rayuwar ki tana da amfani a gaba da yardar Allah!shirun nan da kika ga nayi addu'a nake yi Allah ya kawo Wanda zai taimake mu Hidaya"

Hidaya tayi shiru tana kallon mahaifiyarta,bata da wayo sosai da za ta gane maganganun mahaifiyar ta,ta k'urawa bakin ta idanu tana ganin yadda ya bushe da alamun tana buk'atar ruwa,ta kai Hannu ta shafa leb'en mahaifiyar ta ta,tayi magana cikin Yarin ta.

"Mummy kina jin k'ishirwa ko?za ki sha ruwa?

Tayi murmushi ta yi tari, sannan ta gyad'a kai tayi magana cikin nishi.

" Idan Allah yayi nufin shayar da ni zan sha Hidaya,idan kuma shan ruwa na na duniya ya k'are Allah ya shayar da ni na alkausara tare da Mahaifin ki"

Hidaya tayi kasak'e bata fahimta ba,kawai sai ta saki hannun mahaifiyarta ta ta mik'e tana cewa.

"Bari na samo miki Ruwa ki sha kinji Mummy"

Ta d'aga Hannu tana k'ok'arin dakatar da ita akan kar ta fita daga kangon,amma tari ya sark'afeta,ita kam Hidaya tuni ta zura da gudu ta fice daga kangon domin nemowa mummyn ta Ruwan da za ta sha.


*************

Sauri yake ta yi sosai ganin magriba ta kusa,hannunsa rik'e da ledoji da ya siyo kayan marmari,bai bi ta hanyar da ya bi da farko ba sai ya canja hanya,a ganinsa wannan hanyar da ya biyo za ta fiye masa sauk'i wajen isa gida tunda sauri yake yi.

Yana yanko layin da ke gaban sa yaji layin tsit babu hayaniyar mutane,haka nan babu yawaitar gilmawar mutane da yawa a layin,kansa a k'asa ya zo zai gifta ta gefen wani kango,kamar an ce ya d'ago kansa,karaf!ya ci karo da k'aramar Yarinya tsaye a bakin kangon sai zare idanu take yi tana kalle kalle,har zai wuce sai kuma ya D'an tsaya yana duban ta yana nazarin ta,kamar yadda yake kallonta haka ita ma ta k'ura masa idanu tana kallon sa,can kuma ta maida kallon ta kan ledar da ke hannunwan sa.
Har ya kuma juyawa zai wuce ganin Ummansa tana can jiransa,sai kuma wata zuciyar take k'issima masa me yarinyar take yi tsaye a gaban kango?kuma daga ganin ta kamar a tsorace take,ko d'ankwali babu a kanta ga magariba ta matso,in da take tsaye bakin kangon kuma duk bola ne.

Waiwayo wa yayi ya ta ko a hankali zuwa gabanta,ya tsaya suna kallon juna,ya D'an durk'usa gabanta ya kalli idanuwan ta yace.

"Ke!Me kike yi tsaye a bola kanki babu d'ankwali?maza ki tafi gida magariba tayi kinji ko"

Tayi shiru kanta a k'asa tana kallon ledar hannunsa.
Ya k'ura mata ido jin bata yi magana ba yace.

"Ba kya magana ne?

Sai ta girgiza kai,sannan ta cigaba da waiwaye tana kallon gefen ta da cikin kangon.

Yayi mamaki,amma ya shanye ya sake tambayar ta.

" me kike nema ne?

"Ruwa" ta ambata cikin k'aramar murya da yarinta.

Yayi shiru yana nazari,sannan yace.

"Ruwa?me za ki yi da Ruwa?

Tayi rau rau da ido tana murtsika idon da hannun ta.

" Mummyna zan kaiwa,tana jin k'ishirwa ne..!

"Ina mummyn ta ki?

Ya tambaye ta,haka kawai yaji ba zai iya tafiya ya bar yarinyar ba ba tare da ya ji dalilin tsayuwar ta a Gun ba duk da saurin da take yi,a yadda Zamani ya lalace abubuwan b'arna suka yi yawa akwai tsoro kaga Yarinya k'arama a bakin kango da magariba.

Hannu ta sa tayi masa nuni da cikin kangon tace.

" tana cikin nan..!

Gabansa ya fad'i!k'irjinsa ya buga!tsoro ya fara kamashi,ko dai yarinyar nan Aljana ce?daman gata kyakkyawa ga gashi mai tsawo!sannan ga idanuwan ta wasu iri!amma duk da hakan sai ya samu zuciyarsa da son shiga kangon domin ya ganewa idanunsa abin da ke ciki!

Hakan ya sa ya mik'e tsaye yana duban yarinyar yace.

"Muje ciki naga Mummyn ta ki,sai na bata Ruwan ta sha kinji"

Da hanzari ta saki murmushin murna har da D'an tsallen ta,tayi gaba da sauri,ya bita a baya zuciyar sa na dokawa,haka nan bakinsa na ambatar .

"حسبنا اللہ و نعمل وکیل"


Comments
Share
Vote
Pls


*TYPING*📲

✌️💔 *GARKUWA BIYU* 💔✌️

*TARE DA ALK'ALAMIN* ✍️

HASSANA D'AN LARABAWA

*MARUBUCIYAR* 👇

SANADIN HOTO
HASSANA DA HUSSAINA
CIN AMANAR RUHI
BAHAGON LAYI
BAHAGON LAYI (SABON SALO)

*DA KUMA*

GARKUWA BIYU


*BABI NA GOMA SHA BIYAR DA NA GOMA SHA SHIDA*


WATTPAD:Hassana3333


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️

🖊 *PEN WRITERS ASSOCIATION*🖊️


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️


______________________________________

*~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~*


_____________________________________


https://www.facebook.com/groups/1533639276725285/


**Tana tafe tana D'an tsalle yana bin ta a baya kamar rak'umi da akala!da bismillah ya saka k'afarsa cikin kangon da Y'ar ledar sa a Hannu,yana kallonta ta nufi wata mata da ke kwance tana ta d'ago Hannu tana magana cikin shak'ak'k'iyar murya ba a jin me take fad'a,har suka isa gaban ta yarinyar ta rik'o hannun ta ,a lokacin ne yaji muryar matar na ambatar .

"Hidaya,kina ina ne Hidaya?

" Gani Mummy,tashi na kawo miki wani zai baki Ruwa ki sha"

Idanuwan matar a rufe suke,amma jin maganar Hidaya sai ta fara k'ok'arin bud'e idanunta da sauri,ina tsugune a gefe mamaki ya cikani,har ta d'ago ta kalleni sosai muka had'a ido,ni na fara saurin magana da cikin tausayawa nace.

"Sannu"

Ta lumshe idanu ta amsa a hankali.

"Yawwa sannu D'an Samari,A ina Hidaya ta binkito ka?

Ya juya ya D'an kalli yarinyar da yaji a jikinsa ita ce Hidaya,sannan ya waiwaya ya dubi matar yace.

" Na zo wucewa ne naci karo d ita a bakin kangon nan,gashi naga magariba ta k'arato,shine na tsaya na tambayeta me take yi a nan?sai take fad'a min ruwa take so za ta bawa mamanta,dalilin da ya sa na biyo ta kenan domin naga me ke faruwa?saboda hankalina ya k'i kwanciya da ganin Yarinya a bakin kango,saboda yadda Zamani ya lalace"

"Ya sunan ka?
Abin da Maman Hidaya tace kenan idanuwan ta a kansa.

Kai tsaye ya bata amsa kansa a sunkuye.

" Hamza,suna na Hamza"

Ta lumshe idanu ta bud'e a hankali,ta k'ura masa idanu sosai,shi kam har lokacin k'irjin sa na bugawa amma yana k'ok'arin nuna jarumta,ta d'auke kallonta daga gareshi zuwa kan d'iyar ta,ta d'ago hannun ta ta shafa kan yarinyar idanuwanta suka ciko da hawaye,tace.

"Ina ganin ka naji hankalina ya kwanta da kai Hamza,k'ila kuma Allah ya amsa addu'ata ne akan rok'on da nayi masa,tabbas Allah ya turo da kai ne domin ka taimaka mana,domin ka zama kariya ga wannan k'aramar Yarinya me rauni,domin ka zama GARKUWAR ta a yanzu, kulawar da ka bata a lokacin nan ya tabbatar min kai mai hankali ne,kuma za ka iya kulawa da ita a kowane hali duk da dai kaima har yanzu baka kai minzalin girma ba,"

Hamza yayi shiru duk kansa ya kulle ya kasa gane abin da take nufi da maganganun ta,yayi kasak'e yana ta kallonta,sai kuma ya kama waige waige kamar me Neman wani abu.Ta lura da kamar yake a tsorace,shiyasa tayi hanzarin kau da tsoro daga fuskarsa ta hanyar canja magana da cewa.

"Aiken ka aka yi ne?naga kamar hankalinka baya nan kana sauri ko?

Da sauri ya gyad'a kai tare da magana.

" Eh!Umma na ce ta aike ni,gashi tana Azumi ne,ina sauri kar magariba tayi ban kai mata sak'on ba"

Tayi k'ok'arin mik'ewa zaune a hankali cikin dauriya,yayi kamar ya taimaka mata ganin sai nishi take,ta dai dai ta zaman ta yayin da Hidaya ta d'ane cinyar ta tana tab'a mata hanci tana wasa,ta rik'e hannun ta sannan ta dubi Hamza tayi D'an murmushi tace.

"Da kyau D'an Albarka!Don Allah Hamza ko za ka yi min wani taimako?

Duk da a tsorace yake amma hakan bai hanashi gyad'a kai ba,cikin k'arfin hali yace.

" Insha Allahu zan taimaka miki Mama,idan har ina da halin taimakawar"

Taji dad'i sosai har murmushi ya bayyana akan kyakywar fuskarta,tana duban sa ta fara magana.

"Zan ba ka wannan yarinyar ne domin ka tafi da ita a cikin duhun magariba,saboda fitar ta cikin haske akwai had'ari,kaje da ita gidan ku ta kwana,gobe da safe idan gari ya waye ka d'auketa ka kaita gidan Marayu,zan baka takardar da za ka basu idan kaje kai musu ita"

Tun da ta fara magana yake zazzaro idanuwa kamar za su fad'o k'asa,daman tubarkalla gashi da ido manya masu kyawu,bakin sa a sake k'irjinsa na bugawa da k'arfin gaske,ganin yadda ya kuma tsorata ya sa ta cigaba da magana.

"Na san za ka tsorata Hamza,gashi kuma lokaci ya k'ure mana balle na baka Labarin komai,ina so ka cire tsoro daga zuciyarka,ni mutum ce,kuma musulma kamar kai,Fatima(Hidaya)y'ata ce da na Haifa da cikina,marainiyace,me rauni ce,akwai k'addarori da suka sark'afe rayuwar ta,d'aya daga ciki Allah ya jarrabeta da ciwon( SIKILA),Akwai dalili mai k'arfi da zai sa na rabu da Hidaya a wannan lokacin ba da son raina ba,domin idan har ban rabu da ita ba rayuwata da ta ta suna cikin had'ari mai Girma,zan gaya maka sunan Gidan marayun da za ka kaita,daga baya insha Allahu idan komai ya warware zan je da kaina na d'auketa,don Allah kayi min wannan taimakon Hamza"

Kammala maganarta yayi dai dai da kiran sallar magariba da ya fara jiyo wa,ya runtse idanu cikin tashin hankali,ya san Ummansa tana can tana jiransa,ga kuma wata gingimemiyar magana da wannan matar ta zo masa da ita,ta ya ya zai iya d'aukar Yarinya ya tafi da ita,kuma har ta kwana da su?wane bayani zai yi wa Umman sa da za ta amince da shi?haka nan wane bayani zai wa mutane idan suka ganshi da yarinyar?haka kawai ace ma sato ta yayi!duk da yana jin tausayin su a cikin zuciyar sa amma ba zai iya wannan taimakon ba!domin akwai babban k'alubale a cikin sa.

Da Hanzari ya mik'e tsaye yana girgiza kai!ya sunkuci ledar da ke gaban sa ya juya da hanzari zai fice daga kangon,taku biyu yayi ya tsaya cak!ba wani Abu ne ya tsayar da shi ba illa tuno wani wa'azi da malamin islamiyyar su ya tab'a yi musu akan taimako,ya jaddada musu matuk'ar sun ga wani yana Neman taimako to su taimake shi,kuma su dinga taimakekeniya a junansu da tsoran Allah ,Alokacin ma har wata aya ya kawo musu,in da Allah (S W A)Ya ke cewa.

"و تعا ونوا علی البر والتقوی"

(Ku yi taimakekeniya akan aikin nagarta da tsoran Allah).

Tunawa da yayi da hakan ya sa jikinsa yayi sanyi,bai san wane irin k'alubabale za su fuskanta ba idan bai taimaka musu ba,a hankali ya waiwayo yana dubanta,tana zaunen tana ta kallonsa,Hidaya kam ta langab'e kan kafad'ar mahaifiyarta ta har ta fara bacci,ta ko wa yayi zuwa gabansu ya tsuguna ya sunkuyar da kai k'asa,a hankali yayi magana.

"Na amince zan taimaka muku"

Wani irin murmushi ta saki zuciyar ta ta cika da murna,Hawayen farinciki ya ratso idanuwan ta,tayi magana cikin d'oki.

"Allah yayi maka Albarka Hamza,Allah ya haskaka rayuwar ka,Allah ya taimake ka kamar yadda ka taimake mu"

Ta D'an muskuta ta janyo wata jaka da ta tada kai da ita d'azu,ta zuge jakar ahankali ta za ro wata takarda ta mik'a masa,ya kai Hannu ya karb'a yana buk'atar k'arin bayani.Ta fara magana idanuwanta a kansa.

"Wannan takardar idan kaje gidan marayu ita za ka basu,da zarar sun karanta abin da ke cikin ta za su karb'i Hidaya a hannun ka"

Ya gyad'a kai cikin Amincewa,ta kuma za ro wata takardar ta mik'a masa,ya kuma karb'a yana kallon ta,ta D'an sunkuyar da kai tana gyarawa Hidaya kwanciya akan kafad'ar ta,ta na Kore mata sauron da ya fara binsu saboda duhun magariba,sannan ta fara magana.

"Wannan kuma takardar ta Hidaya ce,amma ina rok'on ka ajiye mata a gunka,Idan Allah yayi dawowa ta a kusa to zan zo na d'auketa ba tare da ka bata takardar ba,saboda bana son ka bata har sai ta kai munzalin girma ta mallaki hankalin ta,a lokacin ne nake so ta karanta abin da ke ciki,to amma bani da tabbaci akan zan dawo a kusa ko ba zan dawo ba,shin zan sake ganin Hidaya a rayuwata ko ba zan sake ba?wannan duk Allah ne ya bar wa kansa sani,ni dai rok'ona a gareka ka ajiye wa Hidaya wannan takardar,idan idan Allah yayi girman ta a gidan marayu to inaso ka bata wannan takarda idan har ka samu dama,wannan ne taimakon da za ka yi min HAMZA"

K'arfin zuciya yaji sosai a lokacin,shiyasa ya bai wa Maman Hidaya tabbaci akan ya amince da dukkan abin da ta fad'a,a lokacin Hawaye ya zubo mata,ta shafa kan Hidaya ta dinga yi mata addu'a,yarinyar bata san me ke faruwa ba saboda baccin da take,a hankali ta d'ago Hidaya ta mik'a masa ita,ya sa Hannu ya karb'eta ya sab'a ta a kafad'ar sa shi ma,sannan ya mik'e ya d'auki jakar tare da ledar sa a Hannu,Zuciyar sa na ayyana masa taimako zai yi!har ya juya ya fara tafiya idanuwan sa cike da Hawayen tausayi,sai kuma ya juya ya dubeta ,ita ma kukan take yi,a hankali yayi magana.

"Ke kuma fa?anan za mu barki?dare fa yana yi"

Ta girgiza kai hawaye na malala tace.

"Kuje Hamza,kar ka damu dani,ni dai nafi damuwa da tserewar Hidaya cikin bala'in da ke shirin afka mana,ni ma nan da D'an lokaci k'ank'ani Allah zai taimake ni ,kamar yadda ya taimaki Hidaya,ku tafi Hamza,maza ku tafi"

Jin maganarta ya sa ya juya ya fara tafiya a hankali kamar Wanda k'wai ya fashewa a ciki,Hidaya na sharar bacci kan kafad'ar sa,yana jin sa wani iri kamar ba Hamza ba,a haka har ya kusa ficewa daga cikin kangon cikin wani yana yi da na zai fassaru ba,a lokacin ne ya jiyo muryar mahaifiyar Hidaya cikin kuka tana magana.

"Ka rik'e Hidaya Amana Hamza….Don Allah ka zama GARKUWAR ta a lokacin da ba na tare da ita…..,Hidaya bata da kowa a halin yanzu sai kai Hamza…...Don Allah Hamza….Don Allah Hamza….Don Allah Ham……

Bai k'arasa jin maganar ba ya fice daga kangon…maganar na yi masa kuwwa a kunnuwan sa…Hawaye na zubo masa suna sauka kan dokin wuyan Hidaya da ke kwance kan kafad'ar sa.…zuciyar sa tayi rauni k'warai da gaske,sosai yake kuka…ba kuma kukan komai ba sai na rabuwar Hidaya da mahaifiyar ta….!


Comment
Share
Vote
Pls


*TYPING*📲

✌️💔 *GARKUWA BIYU...!* 💔✌️

*TARE DA ALK'ALAMIN* ✍️

HASSANA D'AN LARABAWA

*MARUBUCIYAR* 👇

SANADIN HOTO
HASSANA DA HUSSAINA
CIN AMANAR RUHI
BAHAGON LAYI
BAHAGON LAYI (SABON SALO)

*DA KUMA*

GARKUWA BIYU


*BABI NA GOMA SHA BAKWAI DA NA GOMA SHA TAKWAS*


WATTPAD:Hassana3333


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️

🖊 *PEN WRITERS ASSOCIATION*🖊️


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️


______________________________________

*~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~*


_____________________________________


https://www.facebook.com/groups/1533639276725285/


*FAN'S INA GODIYA DA FATAN ALKAIRIN DA KUKE MIN A KULLUM,ALLAH YA SAKA DA ALKAIRI* 👏🥰


*** Umma ta na zaune a tsakar gida kan dadduma ta idar da sallar magriba,carbi ne a hannun ta tana salati da hailala,a gefe guda zuciyar ta cikin tsananin mamaki take sosai da rashin dawowar Hamza gida har magariba tayi,ta san halin Hamza duk wani Aike da za ta yi masa ya kan hanzarta yaje ya dawo akan lokaci ba tare da jinkirtawa ba,to menene dalilin dad'ewar sa haka?anya kuwa lafiya?duk cikin damuwa take jin ranta ta kasa ko da shan ruwa duk da lokacin shan Ruwan ma ya wuce,har lokacin da azumin ta a bakin ta na ranar Alhamis,kamar yadda suka saba yin Azumi a duk wata ranar litinin da Alhamis ita da Hamza.

Ta na nan zaune taji Sallamar sa ya shigo gidan,da Hanzari ta waiwaya ta dubeshi tana amsa sallamar,kuma shigowar sa yayi dai dai da kawo wutar NEPA wadda ta haskake tsakar gidan sosai,Umma ta bi Hamza da kallo ganin sa da Yarinya akan kafad'arsa,ga k'atuwar jaka a hannun sa,kansa a sunkuye ya zo ya gifta ta gabanta ya shige cikin parlour'n ta,kan kujera ya nufa ya sauke Hidaya a hankali Dan kar ta farka,ya gyara mata gashin ta da ya ba zo ya rufe mata fuskarta,ta D'an motsa a hankali tana tura yatsanta guda d'aya a bakin ta tana tsotsa,ya sauke ajiyar zuciya yana kallonta,tausayin ta na ratsa shi,Yarinya k'arama amma har shafukan k'addararta sun fara bud'ewa,an ambaceta da marainiya mara Uba,ta rabu da mahaifiyarta a shekaru na yarinta,babu dangi na nesa balle na kusa!ga lalura me wahalar da Numfashi.


Hak'ik'anin gaskiya Hidaya ta cancanta a tausaya mata,ajiye jakar ta yayi a k'asa daga gefe,ya sake sunkuyawa ya tofa mata addu'o'i,ya rage yawan iskar fanka,sannan ya juya ya fito tsakar gidan jikin sa a sanyaye.


Umma na nan in da ya barta ko motsi bata yi ba,shi ma wucewa yayi zuwa kitchen ya d'akko wankakken plate,ledar sa ta kayan marmari na hannunsa,ya kwance ta ya juye kayan marmarin a cikin plate d'in,ya d'auka ya fito da su ya k'ara so gaban Umma ya ajiye,a hankali yayi magana cikin sunkuyar da kai.


"Umma ki D'an yi min Afuwa na gabatar da sallar magariba ,saboda kar lokacin ta ya tsere mini"

Yana fad'in hakan ya mik'e tsaye ya nufi toilet d'in tsakar gidan,ya d'auki buta da ke cike da ruwa ya shiga ya gabatar da tsarki,ya fito ya tsuguna ya gabatar da cikakkiyar alwala a nutse,Umma dai sai kallon sa take yi,har ya kammala ya kuma komawa parlour'n ya d'auko wata daddumar ya fito ya shimfid'a ya ta da sallah,kasancewar ko yaje masallaci tuni an idar,shiyasa bai fita ba yayi abarsa a gida,har ya idar yayi addu'oin sa sannan ya waiwayo ya dubi Umma,ganin kallon da take masa sai yayi Murmushi ya matso kusa da ita ya kamo hannun ta ya rik'e,yayi magana yana duban kayan marmarin da ke gabanta da ko kallon su bata yi ba.


"Umma ya ba ki sha ba?Bismillah ki sha mana"

Ya fad'a tare da k'ara turo plate d'in gabanta.

Tayi shiru bata tanka ba sai kallon sa kawai da take yi,haka nan bata da niyyar sha,fuskantar hakan da yayi ya sa ya kuma magana cikin tausasawa yana kallon ta da murmushi akan fuskar sa.

"Umma kiyi hak'uri banyi miki sannu da shan ruwa ba,dafatan kin sha ruwa lafiya?kuma kiyi hak'uri da b'ata lokacin da na yi ban dawo ba,abin da kika hore ni da aikatawa naci karo da shi a hanyata ,shine dalilin rashin dawowa ta akan lokaci"


"Me kenan Hamza?" Umma ta tambayeshi,karo na farko kuma da tun shigowar sa tayi magana kenan.

"Taimako Umma,wani taimako na tsaya yi"ya bata amsa cikin karsashi.

Tayi ajiyar zuciya idanuwanta a kansa tace.


"Wane irin Taimako ne Hamza,wacece wannan da naga ka shigo da ita har ka wuce d'aki da ita?wacece ?ina ka samo ta?

Ya sauke numfashi,cikin Y'ar fargaba yace.

" Wata baiwar Allah ce Umma,mai tsananin rauni da Neman taimako"

Umma tace.

"Mu ma bayin Allah ne Hamza,kuma masu Neman taimako a wajen Allah,kawai ka fayyace min wacece ita?"

Ya kuma sauke ajiyar zuciya sannan yace.

"Zan gaya miki Umma na ,amma don Allah kiyi min alfarma ki fara saka wani Abu a cikin ki kafin na sanar da ke komai,kinga Azumi kika yi,ya kamata ace zuwa yanzun kin ci wani Abu"


Ta yi Murmushi tana yabawa da kulawar da yake bata,ta mayar masa da amsa da cewa.


"Kai ma ai Azumin kayi,kuma har zuwa yanzun ba ka ci komai ba,ta ya ya zan ci alhali kai baka ci ba Hamza"


Yayi Murmushi mai k'ayatarwa har fararen hak'oran sa suka bayyana,cikin jin dad'i yace.


"To mu sha wannan tare Umma,idan muka kammala nayi alk'awarin sanar da ke komai da ya faru daga fita ta d'azu har zuwa dawowa ta".

Umma ta girgiza kai cike da gamsuwa,tayi bisimillah ta saka hannun ta ta fara d'aukar kankana ta kai bakinta,sai da yaga ta sha sannan shi ma yayi bisimilla ya d'auka ya kai bakin sa ya tauna,ya lumshe idanu a hankali yana jin dad'in yadda suke shan Abu a kwano d'aya shi da mahaifiyar sa.


******************


Umma ta jima cikin k'urawa Hamza idanu bayan ya kammala fad'a mata abin da ya faru!wani irin mugun tausayin Hidaya na ragargazar zuciyar ta,ka sa hak'uri tayi ta mik'e daga tsakar gidan ta shige parlour'n ta,taje dab da Hidaya da ke kwasar bacci ta tsaya ta tsura mata idanu,a hankali Hamza ya d'aga labulen parlour'n shi ma ya shigo,ya tsaya dab da Umma suka tsurawa Hidaya idanu suna ta kallonta ,Umma ta waiwayo fuskarta cike da alhini ta kalli Hamza,tayi magana a hankali gudun kar Hidaya ta farka.


" Yanzu duk abin da ka fad'a min akan yarinyar nan da gaske ya faru Hamza?"

Ya sauke numfashi ya jijjiga kai yace.


"Abin da mahaifiyar ta ta sanar da ni nima shi na fad'a miki Umma,gaskiyar faruwar abin ko akasin hakan wannan Allah ne masani,sai dai a iya kallon da na yi mata na hango gaskiya cikin idanuwan ta,kuma na kyautata mata zato"


Ta nemi kujera ta zauna,yayin da Hamza ya zauna a k'asa ya tank'washe k'afafuwan sa yana kallon ta,ta sauke ajiyar zuciya sannan ta yi magana.

"Wani kokonto ne ya shiga zuciyata Hamza,ka tara hankalinka guri guda ka hango abin da na hango,ta ya ya Uwa mahaifiya za ta bawa Wanda bata sani ba d'iyar da ta haifa?kuma har tayi masa umarnin kai yarinyar Gidan Marayu?ni fa zuciyata a tsorace take Hamza!na fara zaton wani mummunan al'amari akan hakan…..


Da sauri ya fara girgiza kai,fuskar sa cike da alhini ya fara magana.

" Ah ah Umma,kar kiyi mummunan zato akan lamarin wannan Yarinya,domin bamu san komai a kanta ba,abin da yafi gara mu kyautata zato a kanta,sannan yawaita zato babu kyau,musamman mummunan zato,ko domin fad'in Allah mad'aukakin sarki.

"یأیھا الذین ءامنوا اجتنبوا کثیرا من الظن إن بعض الظن إثم"

Ma'ana:(Ya ku wad'anda suka yi imani,ku guji yawancin zato,domin wani b'angare na zato zunubi ne).


Haka nan a wani Hadisi ,Annabi (S A W) yana cewa."ku guji zato ,domin zato shine mafi k'aryar zance"

"Dan haka Umma mu kyautata zato akan Hidaya da mahaifiyarta ,kar muyi musu mummunan zato"


Umma ta sauke numfashi ta k'urawa Hamza ido tace.

"Haka ne Hamza,tabbas ka tunasar da ni abin da na manta,shikenan babu komai,Allah ya kai mu goben da kaina zan shirya na raka ka gidan marayun domin mu kaita,Allah ya kyautata rayuwar ta".


" Ameen Umma"Hamza ya amsa yana murmushi.

Suka yi shiru suna kallon Hidaya,sai can Umma ta kuma cewa.

"Ya kamata a tashi yarinyar nan a bata abinci,dole za ta ji yunwa fa"

Ya jinjina kai ya D'an tara gira yace.

"Amma Umma ina tsoron a tashe ta bata ga mahaifiyarta ba tayi kuka! Tunda mu dai ba sanin mu tayi ba"


Umma ta D'an yi murmushi tace.

"Insha Allahu babu abin da zai faru,ba zata yi kuka ba,bai kamata a barta da yunwa ba Hamza,kuma ai kai ta riga ta sanka,tunda har ta nemi kaje ka bawa mahaifiyarta Ruwa"


Hamza ya D'an yi dariya yana sunkuyar da kai,yace.

"To babu laifi Umma,a tashe ta d'in ta samu ta ci abincin,ni fargabata ma ko ya ya mahaifiyarta ta take a yanzu?saboda gaskiya na barta cikin mawuyacin hali,ina jin tamkar na koma inga halin da take ciki a yanzu wallahi"

Fuskar Umma ta nuna Jimami sosai!tace.

"Insha Allah tana cikin Aminci,Allah ya dubeta ita ma,Zo ka tashe ta,bari na had'o mata tea da wancan dankalin da na soya,zai fi mata sauk'in ci"

Umma ta ambata sannan ta mik'e ta fice daga parlour'n.

A hankali ya rarrafa kusa da Hidaya da ke ta bacci hannun ta cikin bakin ta,ya rasa ta ya ya ma zai tashe ta,kawai ji yake k'irjinsa na bugawa fat fat,da k'yar ya iya d'aga hannunsa ya kai kan nata hannun ya zare daga bakin ta,yana zare hannun kamar wadda aka daka ta tsandara wani ihu tana k'ok'arin bud'e idanu,a gigice ya mik'e tsaye yana zare idanuwan sa saboda ihunta ya zo masa a bazata…….!


Ihunta ne ya shigo da Umma parlour'n da sauri,hannun ta d'aya rik'e da kofin shayi,d'ayan plate ne ta zubo dankali,tana shigowa Hamza ya dubeta a firgice yace.

"Wai fa Umma kawai hannun ta da ke bakin ta na cire mata,shine tayi wannan ihun"

Umma tayi murmushi ta ajiye kayan hannun ta,ta matsa kusa da Hidaya da take k'ok'arin komawa bacci bayan ta mayar da hannun ta cikin bakin ta,ta kai Hannu za ta d'ago ta,da sauri Hamza yayi magana.

"Umma ki k'yale ta kawai,kar ki tab'a ta ta sake yi mana ihu"

Umma tayi Y'ar dariya tace.

"Kai dai wani zubin matsoraci ne Hamza,yanzu D'an wannan ihun ne ya sa ka firgice haka?

Ya D'an Sosa kansa yayi murmushi yace.

" Allah Umma ihun ne ya zo min a bazata,kawai fa daga cire mata Hannu a bakin ta shikenan ta zunduma ihu"

Umma tace.

"Ai yara masu tsotsan Hannu ba sa son a na cire musu hannun idan suna tsotsa,kuma da alama tana da hak'uri,saboda yara masu wannan d'abi'ar ta tsotsan Hannu suna da hak'uri ,ba su cika rigima ba"

Umma tana kammala maganarta ta juya ta ciccib'o Hidaya ta d'ora ta kan cinyar ta,a hankali ta fara shafa fuskarta tana ambatar Sunan ta"Hidaya…ke Hidaya bud'e idanuwan ki kinji…"

Hamza yana ta kallon su yana son ganin yadda Hidaya za ta yi idan ta farka,Umma kuma na ta ambatar sunanta tana D'an jijjigata,sai Hidaya ta fara bud'e idanuwan ta masu cike da barci,Umma tana ganin haka ta mik'e tsaye ta dire ta,sannan ta ja hannun ta suka shige bedroom d'in ta,toilet d'in d'akin ta ta kaita ta tsugunar da ita tayi fitsari,tayi mata tsarki,ta wanke mata fuskarta da bakinta,sannan ta kamota suka sake fitowa parlour 'n.

Har lokacin Hidaya bata gama wartsakewa ba,Hamza na tsaye suka fito,Umma ta zauna ta jawo Hidayan jikinta,ta kalli Hamza tace.

"Mik'o min tea d'in nan ka wani tsaya k'erere a tsaye,ka nemi waje ka zauna mana"

Da hanzari ya d'auko kofin ya mik'owa Umma,sannan ya durk'usa gaban su,ta karb'a tana k'ok'arin bawa Hidaya a baki, babu musu Yarinya ta karb'a ta fara k'walk'wala saboda babu zafi,Umma ta fifita ya huce.


Sai da ta gama sha tas,Umma tace wa Hamza"Mik'o dankalin ka ga har ta shanye shayin,k'ila daman tana jin yunwa fa"


A lokacin ne Hidaya ta fara dawowa hayyacin ta daga sakin da bacci yayi mata,ta d'aga kanta ta k'urawa Umma idanu,Umma na yi mata murmushi,har Hamza ya mik'o dankali yana fad'in.


"Ga shi Umma" a lokacin Hidaya ta d'auke kallonta daga kan Umma ta mayar kan Hamza,k'ura masa idanu tayi,shi ma ya zuba mata ido,ta kuma mai da kallonta kan Umma,sai kuma ta mik'e da hanzari daga kan cinyar Umma ta nufi Hamza ta fad'a k'irjinsa ta ruk'unk'ume shi ta fasa wani gigitaccen kuka da kiran "Mummy naaaaaa……!


Comment
Share
Vote
Pls


*TYPING*📲

✌️💔 *GARKUWA BIYU* 💔✌️

*TARE DA ALK'ALAMIN* ✍️

HASSANA D'AN LARABAWA

*MARUBUCIYAR* 👇

SANADIN HOTO
HASSANA DA HUSSAINA
CIN AMANAR RUHI
BAHAGON LAYI
BAHAGON LAYI (SABON SALO)

*DA KUMA*

GARKUWA BIYU


*BABI NA GOMA SHA TARA DA NA ASHIRIN*


WATTPAD:Hassana3333


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️

🖊 *PEN WRITERS ASSOCIATION*🖊️


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️


______________________________________

*~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~*


_____________________________________


https://www.facebook.com/groups/1533639276725285/


Ya D'an runtse idanu saboda yadda kanta ya bugi k'irjinsa,a gigice ya D'an kauce yana niyyar janye ta,ta k'ara matsawa jikinsa tana ruk'unk'ume shi sosai tana kuka,ya rik'o hannun ta yana shirin b'amb'areta a jikin shi amma ta rik'e shi gam,mamakin k'arfin ta yayi duk da ta kasance siririya matuk'a,ganin yadda yake kokawa da ita tak'i tsayawa sai kuka take tana rirrik'eshi,Umma kam tsayawa tayi kallon ikon Allah ta kasa magana.

A hankali ya waiwayo a gajiye ya dubi Umma,ya narke fuska yace.

"Umma ki mata magana ta sakeni,kinga dai ba wani Abu naci ba duk ta sake gajiyar da ni"

Umma tayi murmushi tace.

"Ai yanzu fa dole sai kayi hak'uri domin kai ta sani,ba Lallai ta yarda da ni ba dole kai za ta mak'alewa Hamza"

Fuska cike da Alhini yace.

"To ni yanzu ya zan yi da ita Umma?ina so naje na ci abinci,Sannan na fita masallaci sallar isha'i,kuma kin san k'arfe Tara ina da waya ni da Khaleel"

Umma ta sauke numfashi ta na kallon Hidaya da ta lafe jikin Hamza tace.

"Lallab'ata za ka yi ta ci abincin,na tabbatar idan ta k'oshi da kanta za ta koma baccin'

Ya D'an girgiza kai,to shi ta ya ya ma zai lallab'ata?gaba d'aya bai ma san ya zai yi ba,ya kalli Umma duk a daburce yake,kukan Hidaya na damunsa duk ta jik'a masa gaban riga da Hawaye da majina,kamar me tsoran magana haka ya daure ya fara ambatar sunanta yana d'ago ta daga jikin sa.

" Hidaya…ke Hidaya tashi kiji wata magana kinji…za ki gun mummyn ki ko?"

Ta na ji ya ambaci Mummyn ta tayi sauri ta d'ago ta kalleshi tana jijjiga kai,har da murmushin ta,fuskarta duk zanen hawaye,ya kalleta yana rik'e hannun ta.

"Za ki je gun Mummy ko?"

Ta gyad'a kai.

Ya D'an sakar mata Murmushi yace.

"Mummy ta je unguwa za ta dawo,in kuma ba ta dawo da wuri ba zan kai ki gun ta,amma idan kina so na kai ki sai kin daina kuka,kuma sai kinje gun Umma na ta ba ki abinci kin ci kinji"

Ya nuna mata Umman,ta waiwaya ta kalli Umman,Umma tayi mata Murmushi, Hidaya ta kau da kai ta kalli Hamza ta mak'e wuya alamar ba zata ba,ya D'an dafe kansa,sannan ya d'ago ya kalleta yace.

"Ba za ki je gun Umman ba?"

Ta gyad'a kai tana k'ok'arin sake fashewa da kuka,da sauri ya girgiza mata kai yana k'ok'arin zaunar da ita kusa da shi,tak'i yarda sai nane masa take,yana ji yana gani haka ta matseshi kamar zata koma cikin sa,Umma dai ta na ta kallonsu ba tayi magana ba.

Janyo plate d'in dankalin yayi ya fara d'ebowa yana kai mata bakin ta,ba musu ta karb'a ta fara taunawa a hankali,ya sauke ajiyar zuciya ya dubi Umma yana marairaice fuska,Umma tayi masa alamar yayi hak'uri na D'an lokaci ne,ya jijjiga kai ya mayar da hankalinsa kan Hidayan yana bata dankalin,ba taci da yawa ba ta daina karb'a alamar ta k'oshi,Umma ta mik'e ta kawo ruwa,ya karb'a ya bata tasha,yadda ya lura ko kallon Umma bata son yi,da sun had'a ido sai tayi saurin kau da kai ta matsa jikin sa,ko me ya sa oho!ya D'an tab'e baki.

Kiran Sallah ya fara jiyowa a masallaci,yana mik'ewa sai ga Hidaya ma tsaye tana rik'o hannunsa,ya rasa ya zai yi,a lokacin Umma dariya ta fara yi masa ganin duk ya rud'e Yarinya ta nane masa,da k'yar ya zaunar da Hidaya ya fara share mata hawayen da yake zubo mata,ya tausasa murya yana kallon ta yace.

"Hidaya ki zauna wajen Umma yanzu zan dawo,masallaci zani in yi sallah,kuma zan yi addu'a Umman ki ta dawo da wuri ko?

Ta D'an yi shiru,sai kuma can tace" Eh".

Yaji dad'i har yayi Murmushi yace.

"Ko in baki waya ta kiyi game?kin iya game?"

Tayi magana da sanyin murya.

"Eh na iya,ina yi da wayar Mummy na"

Ya fara k'ok'arin zaro waya a aljihun sa yana dariya.

"Da kyau HIDAYA, bari na baki to kiyi,yanzu zan dawo ba zan jima ba,kar kiyi kuka kinji"

Ta girgiza kai,ya kamo mata game ya mik'a mata wayar,ta haye kujerar d'akin har da kashingid'a ta fara buga game tana dariya,mamaki ya kama shi,ya tsura mata idanu yana murmushi,haka kawai yaji dad'in ganin yadda take farinciki,Umma tayi sakato ganin yadda ya shagala da kallon Hidaya har za a ta da sallah a masallaci,sai da ta yi masa magana sannan ya Ankara,kunya ta kama shi,da sauri ya juya ya fice daga parlour'n domin tafiya masallaci,ya bar Hidaya na b'angala dariya ba ta lura da fitar sa ba.


*****************


Loakacin da ya dawo gidan sai ya tarar Hidaya har tayi bacci,ga wayar sa nan a gefen ta ita kuma sai bacci take,Umma na zaune tana cin abinci daga gefen ta,zama yayi kusa da Umma ya tsoma Hannu cikin kwanon suka cigaba da cin abincin tare, yayi loma d'aya sannan ya kalli Umma yace.

"Wannan Y'ar rigimar har tayi bacci kenan?"

Umma ta girgiza kai ba tayi magana ba,sai a sannan ya tuna da gargad'in Umma akan magana idan ana cin abinci,saboda za a iya k'warewa,hakan yasa yayi shiru,suka cigaba da ci,lokaci lokaci yana d'aga kai ya kalli Hidaya har suka kammala cin Wanda ke gaban su,Umma ta nemi a dad'o yace ya k'oshi ,ya tattara kwanukan ya fita da su ya wanko hannun sa.

Ya D'an jima suna hira da Umma duk akan Hidaya,sannan ya kalli Agogo yace.

"Umma bari na gudu d'akina,kar Khaleel yayi ta jirana ban kira shi ba"

"To Hamza Allah ya tashe mu lafiya,bari na kai Hidayan cikin bedroom, Allah dai ya sa kar ta farka cikin dare tayi kuka" Umma ta ambata tana niyyar mik'ewa.

Hamza ya amsa da "To ameen Umma".

Yana kallo har Umma ta ciccib'i Hidaya,duk da bata da wani nauyi saboda sirantakar ta,suka wuce bedroom, sai da yaga shigewar su sannan ya sauke numfashi ya girgiza kai,a salub'e ya fice daga parlour'n zuwa d'akin sa.


Sai da ya kammala komai na al'adar sa ,ka ma daga wanka zuwa shirin bacci da sleeping dress masu kyau,sannan ya nemi waje ya zauna ya lalubo wayar sa da Hidaya ta jefar a parlour'n Umma,sunan Khaleel ya kamo Wanda ya rubuta (JININ JIKINA).

flashing yayi a lambar,wadda ta kasance ta k'asar waje,minti biyu wayar sa ta fara ruri alamar Khaleel ya kira shi,yayi murmushi yana jin wani sanyi a kansa,sannan ya d'aga wayar yayi sallama da k'ayatacciyar muryar sa.

Daga can Khaleel ya sauke numfashi cikin marairaicewa ya fara magana.

" Wai yau ina ka shiga ne Aboki?saura kad'an fa na rusa kuka saboda rashin jin muryar ka akan lokaci"

Hamza ya k'yalk'yale da dariya yace.

"Wane irin kuka kuma Khaleel?wallahi wasu Abubuwa ne yau suka yi min rubdugu sai hamdala kawai,to ya kake? Ya karatu?"

Khaleel ya amsa cikin shagwab'a tamkar mace.

"Gani nan dai kawai Aboki,rayuwar da babu kai a cikin ta ai lami ce,nan d'in babu wani dad'i sai hak'uri kawai"

Hamza yayi murmushi yace.

"To ya za a yi?kowa da in da Allah yake ajiye shi ya tsara masa rayuwa,ba ya yiwuwa daman mutum ya samu duk abin da yake so Khaleel,ka k'ara hak'uri akan Wanda kake yi,gani na ne kawai baka yi fa,amma kullum muna jin muryar juna,kuma kullum kana raina dai dai da second d'aya bana mantawa da kai"

Khaleel yayi ajiyar zuciya har Hamza ya jiyo shi,a hankali yayi magana.

"Shikenan Aboki na hak'ura,tun da babu yadda zan yi da daddy,wai ina Umma ne?ko har ta kwanta?

Hamza ya amsa.

" Eh ta kwanta,da yake yau tayi Azumi duk ta gaji ne"

Khaleel yace.

"Aboki kuna ta Azumi kai da Umma kuna samun lada,ni kuwa na kasa daurewa na dinga na litinin da Alhamis d'innan,gashi yana da falala sosai ko?"

Hamza yayi murmushi yace.

"Sosai ma kuwa!da za ka daure ka dinga yi,yana k'ara lafiya sosai ga jikin D'an Adam,yana durk'usar da zuciya,domin yawan k'oshi da abinci ya kan gadarwa zuciya girman kai da tak'ama da gafala,amma zama da yunwa na wani lokaci kan haskaka zuciya ta zama mai taushi,gami da gusar da k'ek'ashewar ta,ta zama killatacciya da tunani da zikirin Ubangiji,sannan Azumi kan k'untata magudanar jini,wad'anda sune magudanar shaid'an a jikin D'an Adam,domin shaid'an yana gudana a jikin D'an Adam a magudanar jini,haka nan yana k'ara kusanci ga Allah"

Khaleel yana sauraran bayanin Hamza Zuciyar sa na k'ara k'aunar sa,babu ranar da zai yi hira da Hamza bai samu wani Abu da ya k'aru da shi ba,Hamza ai kyakkyawar zuciya ne,yana jin sa tamkar Wanda suka fito ciki d'aya,ya lumshe idanu ya k'ara k'ank'ame wayar yace.

"Nagode Aboki,hak'ik'a kai d'in wani b'angare ne na jikina,Allah ya barmu tare,Ina sonka Hamza"

Hamza ya gyara kwanciya yana runtse idanu,sannan yace.

"Na fi sonka Khaleel,ka yi min abin da na zan manta da kai ba,ka yarda dani ka amince dani,na zama wani sirrinka,kai na daban ne a rayuwata Khaleel, komai kake so idan har ina da shi zan maka"

Khaleel yayi murmushi yace.

"Ina jin bacci,duk da ban gaji da jin muryar ka ba,me za ka fad'a min Wanda zai haskaka zuciyata Aboki na gari?

Kai tsaye Hamza yace.

" Sai dai in maka Nasiha,Nasiha akan tsoran Allah,wadda aka yi mana ranar juma'a yayin hud'uba a masallaci"

Da sauri Khaleel yace.

"Eh ina so Aboki,nima kayi min….

Hamza yayi murmushi yace…….!

" Ina yi mana wasiyya da ni da kai da mutanen duniya a kan muji tsoron Allah,domin tsoron Allah shine matattarar dukkanin alkairi gabad'aya,babu wani alkairi na nesa ko na kusa face tsoran Allah yana zaburarwa a kansa,haka nan,babu wani sharri na kusa ko nesa,a fili ko a b'oye,face tsoran Allah yana ba da Katanga don kariya daga gareshi.
Kuma hak'ik'a tsoran Allah shine Abu na farko da Allah yayi wa mutane farko da k'arshe wasiyya da shi.Allah yana cewa:

"ولقد وصینا الذین أوتوا الکتب من قبلکم و إیا کم أن اتقوا اللہ "

(Hak'k'a mun yi wasici ga wad'anda a ka ba wa littafi gabaninku da kuma ku,a kan ku ji tsoron Allah)

Hakan nan y kamata mu san siffofin masu tsoran Allah,domin muyi k'ok'ari muyi koyi da su.Kad'an daga cikin siffofin sun had'a da:
Imani,da tsayar da Sallah,da ciyarwa domin Allah,da yarda da abin da Allah ya saukar,da sakankancewa da ranar Lahira.
Yana daga cikin alfanun tsoron Allah :Allah yana karb'ar aikin mai tak'awa ne,kamar yadda yace,

"إنما یتقبل اللہ من المتقین"

(Kad'ai Allah yana karb'a ne daga masu jin tsoron sa).

Yana daga cikin amfanin tsoron Allah,ubangiji zai ba wa mai shi kaso biyu na rahamarsa,kuma ya sanya masa haske da zai rik'a tafiya a cikin sa,kuma ya gafarta masa zunubansa,kamar yadda Allah yace,

"یأیھا الذین ءامنوا اتقوا اللہ و ءامنوا برسولہ یٶتکم کفلین من رحمتہ ویجعل لکم نورا تمشون بہ و یغفر لکمؒ واللہ غفور رحیم"

(Ya ku wad'anda suka yi imani ku ji tsoron Allah, ku yi imani da manzansa,zai Baku kaso biyu daga cikin rahamarsa ,ya sanya muku haske a cikin rayuwarku,ya gafarta muku,hak'ik'a Allah mai yawan gafara ne mai jin k'ai).

Sannan Allah yana sanya wa mai tsoron sa mafita daga duk wani K'unci da damuwa,kamar yadda yace,

"و من یتق اللہ یجعل لہ مخرجا"

(Duk Wanda yaji tsoron Allah,to Allah zai sanya masa mafita)

Dan haka ya kamata muyi guziri da tsoran Allah,domin mu rabauta a rayuwar mu ta duniya da Lahira,domin tsoron Allah shine mafi alfanun abin da bawa zai yi guziri da shi,saboda fad'in Allah ta'ala.

"و تزودوا فإن خیر الزاد التقویؒ واتقون یٰأولی الألبٰب"

(Ku yi guziri ,hak'ik'a mafi amfanin guziri shi ne tsoron Allah, kuma ku ji tsoro na ya ku masu hankula).

Khaleel babu abin da yake rik'e tsoron Allah ,ya kafe shika shikan sa a Zuciyar mumini sai yawan Ambaton Allah a kowane lokaci,a kowane hali,Dan haka babu makawa a dawwama akan zikirin Allah,da tasbihi,tare da godiya ga Allah,ko domin mutum ya samu ya murk'ushe abokan gabarsa guda biyu,(shed'an da son zuciya).

Ina fatan wannan wasiyya za ta shiga Zuciyar mu khaleel,kuma mu zama daga cikin masu aiki da ita.


Zuciyar khaleel tayi sanyi,hawaye ya zubo masa,sosai yaji maganganun Hamza sun ratsa shi,shiyasa ya dinga yiwa Hamza godiya mai tarin yawa,kafin suka yi sallama da juna Zuciyar su cike da kewa.

Hamza ya gyara kwanciyar sa domin ya D'an samu ya runtsa,ko domin ya samu tashi tsakar dare ya gabatar da ibadar sa kamar yadda ya sa ba…..!


Comments
Share
Vote
Pls


*TYPING*📲

✌️💔 *GARKUWA BIYU* 💔✌️

*TARE DA ALK'ALAMIN* ✍️

HASSANA D'AN LARABAWA

*MARUBUCIYAR* 👇

SANADIN HOTO
HASSANA DA HUSSAINA
CIN AMANAR RUHI
BAHAGON LAYI
BAHAGON LAYI (SABON SALO)

*DA KUMA*

GARKUWA BIYU


*BABI NA ASHIRIN DA D'AYA DA NA ASHIRIN DA BIYU*


WATTPAD:Hassana3333


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️

🖊 *PEN WRITERS ASSOCIATION*🖊️


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️


______________________________________

*~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~*


_____________________________________


https://www.facebook.com/groups/1533639276725285/


K'arfe biyu na dare ya farka,bayan ya shiga toilet d'in d'akin sa yayi tsarki sai ya d'auro alwala,sallolin Nafila raka'a goma sha biyu ya gabatar,bayan ya idar yayi karatun alk'ur'ani,sannan yayi addu'o'i masu tarin yawa,har ya samu kansa da yiwa Hidaya addu'a ta fatan alkairi da samun sassauk'ar Rayuwa a gidan Marayu,haka nan yayi wa Mahaifiyarta addu'a akan duk in da take Allah ya tsare gabanta da bayan ta,sai wajen k'arfe uku da rabi sannan ya koma barci,bai jima da kwanciya ba aka fara kiraye kirayen sallah,haka ya mik'e bacci cike fal a idonsa,ya d'aura alwala yayi raka'atanil fijri,sannan ya bud'e d'akin sa ya fito.

Har k'ofar Umma yaje ya D'an bubbuga mata,bai jima ba ta taso ta bud'e tana muttsika idanu,yayi murmushi ya kalleta yace.

"Umma barcin bai isheki bane?ga shi har za a ta da sallah a masallaci"

Tayi Hamma ta dubeshi tace.

"Ashe har lokaci ya tafi haka,bari to nayi hanzarin d'aura alwala,Masallaci za ka tafi ne?"

Ya amsa yana gyara zaman dadduma a kafad'ar sa.

"Eh Umma Masallaci za ni,dafatan dai Y'ar rigimar nan bata hanaki bacci ba?

Tayi murmushi tace.

" Wai Hidaya?Ai yadda kasan matacciya saboda bacci,ko motsawa bata yi ba baccinta take cikin kwanciyar hankali wallahi"

Ya jinjina kai yana jin dad'i sannan yace.

"Alhamdulillah naji dad'in hakan Umma,ina ta fargabar kar tayi miki kuka Ashe ita baccinta ma ta sha,Lallai ta kyauta da bata wahalar min da Umma na ba"

Umma tayi murmushi, Yayi mata sallama ya wuce masallaci,ita kuma ta koma bedroom domin sallatar Asubahi.

Ya dad'e a masallaci yana Lazimi,sai da gari ya fara haske sannan ya dawo gida,ya koma d'akin sa ya D'an kwanta, bai ma san lokacin da barci ya sake d'auke shi ba.

K'arar kukan Hidaya ne ya farkar da shi,ya mik'e yana salati da addu'ar tashi daga barci,da k'yar ya mik'e ya fad'a toilet yayi brush ya wanke fuskar sa sannan ya fito,bai zauna ba sai ya wuce tsakar Gidan in da yake jiyo kukan Hidaya.

Tana tsaye d'aure da tawul a jikinta,da alamun wanka Umma tayi mata,fuskarta ta k'ara haske sosai,sai dai idanuwanta sun sauya kala duk sun yi ja saboda kuka,sai shesshek'ar Kuka take yi,bata kula da shi ba har ya k'ara so bayanta,lokacin Umma ta fito daga parlour'n ta da man shafawa a hannun ta,tana ganin Umma ta fito ta kuma fasa kuka kamar wadda aka ciza,ta juya da sauri tana kuka,kawai sai tayi arba da Hamza yana k'arasowa,ta ja wata ajiyar zuciya ta tafi da sauri ta rik'eshi tana kwantar da kanta a jikinsa,ya tsaya sakato suna kallon juna shi da Umma.

Umma tayi murmushi ta nufo su tana cewa.

"Yawwa ai gara da ka ta so,tunda ta tashi take Neman ka tana kuka,da k'yar ta yarda nayi mata wanka,nayi nayi mu shiga ciki na shafa mata mai ma amma tak'i,shine na shiga na d'auko na shafa mata a nan kawai"

Yayi murmushi yana rik'o kafad'un Hidaya ya rabata da jikinsa,sannan ya tsuguna gabanta ya kai Hannu ya share mata hawaye,ita kam sai k'ok'arin b'oye fuskarta take a jikinsa,yak'i bata damar hakan,ya dubi Umma fuskar sa da jimami yace

"Na rasa yadda akayi yarinyar nan ta sanni haka Umma,daga had'uwa da ita jiya tayi min wani mugun sani kamar Wanda muka shekara"

Umma ta k'ara sakin murmushi ta jawo kujera Y'ar tsuguno ta zauna,sannan ta dubi Hamza da Hidaya ta lafe a gefen sa tace.

"Ai dole ne Hamza,kai fa kana da shiga rai,nan da nan da mutum yayi maka gani d'aya yake jin ka kwanta masa a rai,kuma ba wai don kai d'in d'ana bane nake fad'in hakan a kan ka,ah ah,kawai gaskiya na fad'a,kuma kai kana da farinjinin yara,kaga dai yadda yaran layin nan suke cika Gidan nan saboda kai,ko Dan Nasiha da tarihin Annabawa da kake musu kullu yau min,Hidaya kuma tilas ta mak'ale maka,tunda kai kad'ai ta sani a halin yanzu,Ni wallahi har tausayin ta nake yadda za ta yi Rayuwar Gidan Marayu, ga ta ba wata ishasshiyar lafiya ce da ita ba,Rayuwar Gidan Marayu kuma ba wata gamsasshiyar kulawa za ta samu ba,saboda ciwonta yana buk'atar kulawa gaskiya,na ga yadda Maman Salma take fama da Salma akan wannan cuta ta sikila,wallahi Hamza ina tausayawa wad'anda Allah ya jarraba da wannan cuta mai wahalar da Numfashi.

Ya sauke numfashi duk ransa a jagule,ba komai yasa hakan ba sai wata gingimemiyar kewar Hidaya da ya fara ji a ransa,sai yaji baya son rabuwa da ita kwata kwata,amma ya zai yi ?tilas ya rabu da ita ya cika umarnin mahaifiyarta ,tausayin ta yake ji sosai,jin ta yake a jininsa tana yawo tamkar wadda suka fito ciki d'aya.

Ita kanta Umma ta fuskanci halin da Hamza ya shiga,kuma ita ma tuni ta fara jin kewar rabuwa da Hidayan,duk da Hidayan ba wani sakin jiki tayi da ita ba amma tana jin ta a ranta sosai tamkar d'iyar ta,lokaci guda taji ta zauna a Zuciyar ta daram.

Da wayo da dabara sannan Hidaya ta yarda Umma ta shafa mata mai,sai da Hamza ya bata wayar sa yace ta rik'e masa zai je yayi wanka ya dawo,a haka Umma ta shirya ta,sai ta rasa kayan da za ta saka mata,hakan ya sa ta jira har Hamza ya kammala shiryawa cikin shadda fara tas me aikin blue d'in zare,ya taje sumar sa da ta D'an fara taruwa,ya fito sai k'amshi yake zubawa yayi fes da shi ainihin zatin kyawun sa ya dad'a fitowa.

Ko Hidaya sai da ta bishi da kallo k'uri har ya iso gabanta ya tafa hannayen sa dai dai fuskar sa,sai ta D'an firgita kad'an,sai kuma ta fashe da dariya har jerarrun hak'oranta suka bayyana,kawai sai shi ma ya tsinci kansa da dariya yana kallonta,lokacin Umma ta fito daga bedroom tana wa Hamza magana.

"Hamza ya za a yi ne?Hidaya tayi wanka babu kayan sakawa"

Ya d'ago ya dubi Umma har lokacin fuskar sa da walwala yace.

"Ai ina jin kayan cikin jakar nan fa kayan ta ne,amma dai duba ki gani Umma"

Umma ta girgiza kai tare da komawa d'akin ta sungumo jakar ta fito da ita,zama tayi ta zuge jakar tana duba kayan,sai ta tarar duk kayan Hidaya ne masu kyau sosai kuwa,yawan ci y'an kanti ne dogayen riguna da riga da siket,sai lace da atamfa da shadda har ma da material su kam basu da yawa,ga takalma wajen kala shida,sai yarirrika da sark'ok'i da abin Hannu da ribbons iri iri na gayu,ga k'ananan pant dai dai jikinta.

Umma ta tsurawa kayan idanu tana mamaki,gaskiya duk in da Hidaya ta fito to daga gidan arzik'i ta fito,domin a cikin sark'ok'in ta har da sark'ar gwal guda biyu,kuma manya ne ba laifi,hakan yasa ta tasa kayan a gaba tayi shiru kawai.

Shi kam Hamza yana can hankalin sa na kan Hidaya da ya kamo mata cartoon a wayar sa tana kallo tana dariya yana taya ta,sai can ya waiwayo ya dubi Umma ya ga tayi kasak'e da kayan a gaban ta,gyara zama yayi yace.

"Umma babu kayan ta a ciki ne?"

Ta sauke numfashi tace.

"Duk ma kayan ta ne a ciki fa"

"To Umma d'auko mata guda d'aya ta saka kawai,sai tayi break fast,kar tai ta zama da towel a jikin ta" ya fad'a a sanda yake k'ok'arin mai da hankalin sa kan Hidaya da take ta nuna masa wayar hannun ta tana cewa "kalli kaga".

Umma ta zaro mata wani d'an d'asheshen material ja mai duwatsu ,d'inkin doguwar riga ne mai kyau,da flowers milk a jiki,ta d'auko mata takalmi milk color da sarka,sannan tayi mata magana akan ta taso ta sanya kaya a jikin ta.

Ita kam hankalin ta na kan waya har sai da Hamza ya sake yi mata magana sannan ta waiwayo ta kalleshi ta k'ura masa idanu,ya sake mai maita mata maganar sa.

" ki tashi ki sanya kayan ki,ko ba kya so mu tafi na kai ki wajen Mummyn?

Sai ta jijjiga kai ta b'ata fuska,ya zaro idanu yace.

"Ba kya so?me yasa hakan Hidaya?"

"Ni ma ba zani ba tunda ta gudu ta barni" ta fad'a da shagwab'a.

Yayi murmushin yace.

"Ayya Hidaya ki mata Afuwa kinji,wani uzuri ne ya sa ta tafi ta barki,kiyi hak'uri"

Ta D'an yi shiru,sai can ta kalleshi ta rik'o hannun sa tace.

"Amma dai idan ka kaini kai ma za ka zauna a wajen mummy ko?"

Ya kalli Umma k'irjinsa ya buga,Umma tayi murmushi tana kallon su,sai ya girgiza wa Hidaya kai yace.

"Ah ah Hidaya,ni ma zan dawo wajen Umma ta ne mu zauna tare ni da ita"

Bai aune ba yaga hawaye ya fara sintiri a idanuwan ta,ta fara buga k'afa tana kuka wai ita in dai ba zai zauna gun mummy ba ita ma ba zata tafi ba,hankalin sa ya tashi ya rasa ya zai yi ,gashi baya son kukan ta,da ta fara kuka yake Neman nutsuwar sa ya rasa,ya kalli Umma idanuwan sa sun fara sauyawa yace.

"Ya zan yi Umma?"

Tayi ajiyar zuciya ta jawo Hidaya ta rungume ta,abin mamaki sai bata k'i ba,ta kwanta luf a ji kin Umma tana ajiyar zuciya da hawaye,Umma ta dinga Shafa kanta ta kalli Hamza tace.

"Hamza na lura yarinyar nan tana sonka,kuma ba ta son rabuwa da kai"

Ya shafa gashin kansa da ke kwance yana k'yallin gyara,fuska babu walwala yace.

"To ya za mu yi Umma?haka nan za ta yi hak'uri mu rabu……

Bai k'arasa ba yaji muryar sa tayi rauni,da sauri ya mik'e ya fice daga parlour'n hawaye na ciko idanuwan sa.

Umma da ta hango damuwarsa sai taji duk na dad'i,ita kanta ba ta son rabuwa da Hidaya ko kad'an,musamman yanzu da take kwance a jikinta sai take jin k'aunarta na ratsata,da k'yar Umma ta daure ta dinga lallashin Hidaya har tayi shiru,kayan da ta d'auko mata kam k'in sakawa tayi,wai ita irin kayan Ya Hamza za ta saka,Umma ta dinga dariya tace.

" To ban da abin ki Hidaya ina mace ina sa kayan maza?

Kawai sai Umma taji Hidaya ta fara koro zance.

"Ai Umma akwai kayana kalar na sa a nan,ni dai su zan saka muyi iri d'aya kinji"

Haka tilas Umma ta birkice jakar ,sai daga can k'asa ta ci karo da wasu y'an kanti riga da siket,rigar fara me tutoci blue,sai siket d'in kuma blue color, Hidaya ta dinga Murna ta d'auki kayan ta saka da kanta,Umma ta d'auko mata wata farar hula ta bata ta saka,jelan gashinta duk sun bazo kafad'un ta,sai tayi wani irin kyawu na ban mamaki.

Sai lokacin ta fara cigiyar Hamza,Umma tace .

"Yana d'akin sa k'ila,je ki ki kirawoshi ya zo kuyi break fast"

Hidaya tayi tsalle ta tafi da gudunta Umma tana nuna mata k'ofar d'akin,Umma tayi murmushin ganin yadda Hidayan ta fara sakewa,ta shige kitchen domin fito da kayan break fast.

Shi kam Hamza na kwance rigingine akan bed d'in sa,kan sa a sama ya fad'a cikin tunani,duk a jagule yake jin ransa,Zuciyar sa na k'unar Rabuwa da Hidaya,rabuwa ta biyu da yake jin tana tab'a ruhin sa,ya rabu da abin da ya fi so cikin rayuwar sa wato (Khaleel) da k'yar ya jure ya daure wa wannan rabuwa kafin ya samu Zuciyar sa ta sake,kullum yana kukan rashin (Khaleel) kusa da shi,to ga Hidaya ta shigo rayuwar sa cikin kwana d'aya tak!amma yana jinta a Zuciyar sa kamar wadda suka shafe tsawon shekaru da dama.…
Wani Hawaye mai zafi ya tsiyayo masa yana gangarowa ta gefen fuskar sa,tattausan Hannun Hidaya kuma k'arami,shi yaji akan fuskar sa tana goge masa Hawaye,cikin raunin murya kuma yaji tayi magana a shagwab'e..

"Ya Hamza me yasa ka ke Kuka…?"


Comments
Share
Vote
Pls


*TYPING*📲

✌️💔 *GARKUWA BIYU* 💔✌️

*TARE DA ALK'ALAMIN* ✍️

HASSANA D'AN LARABAWA

*MARUBUCIYAR* 👇

SANADIN HOTO
HASSANA DA HUSSAINA
CIN AMANAR RUHI
BAHAGON LAYI
BAHAGON LAYI (SABON SALO)

*DA KUMA*

GARKUWA BIYU


*BABI NA ASHIRIN DA UKU DA NA ASHIRIN DA HUD'U*


WATTPAD:Hassana3333


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️

🖊 *PEN WRITERS ASSOCIATION*🖊️


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️


______________________________________

*~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~*


_____________________________________


https://www.facebook.com/groups/1533639276725285/


Yana daga kwancen ya D'an waiwayo da kansa yana duban ta,ga mamakin sa sai ita ma yaga hawayen a idanuwanta suna shirin zubowa,ya yunk'ura ya mik'e zaune bakinsa d'auke da salatin Annabi,ya kai Hannu ya murje ragowar hawayen da ke fuskarsa,sannan ya dubeta da D'an murmushi yace.

"Ya dai Hidaya?

Ta kai Hannu ita ma ta goge na ta hawayen,ta turo baki gaba tace.

" Me ya sa ka ke kuka?"

Ya girgiza kai.

"Babu komai Hidaya,kawai na tuna wani abokina ne da yayi tafiya mai nisa,shine kewarsa ta saka ni Hawaye"

Ta rik'o hannun sa tana wasa da yatsun sa,ta kalle shi tace.

"Amma zai dawo ko Ya Hamza"

Ya jijjiga kai alamar eh,sannan ya zarce da cewa.

"Amma dai zai jima bai dawo ba,gashi bani da wani Aboki sama da shi,shi kad'ai me babban Aboki na"

Ta d'an yi dariya kad'an ta zura masa idanu tace.

"To ba gani ba Ya Hamza,tunda baya nan ai ni sai na zama k'awarka kawai"

Yayi murmushi yace.

"Hidaya kenan!ai babu abota ko k'awance tsakanin Namiji da mace,ai ni yayanki ne ke kuma k'anwata ce ko?"

Ta jijjiga tana kallon sa tace.

"Eh kuwa, shiyasama zan dinga ce maka Ya Hamza,shi kuma Abokin ka ya sunan sa?"

Kai tsaye ya amsa mata da cewa, "Khaleel".

Tayi tsalle tana cewa.

" Ya Hamza zan dinga kiransa Uncle Khaleel ka ji,Mummy na tace idan mutum ya girme ni na dinga ce masa Yaya ko Uncle, idan mace ce kuma Anty ko Adda"

Ya zame hannun sa cikin na Hidaya yana amsawa da.

"Hakan na da kyau yarinyar kirki,ke kuma k'awayen ki guda nawa ne?"

Ta d'aga kanta sama kamar tana tunani har da sa d'an yatsanta a hab'ar ta,ya bita da kallo cike da birgewa,sai can ta sauke kallonta kan fuskar sa ta kamo yatsun ta ta na k'irgawa da su,har ta k'irga guda uku,cikin murmushi tace.

"Ka ga k'awayena haka ne Ya Hamza,Amma na yi fad'a da guda biyu,saura d'aya nake kulawa?"

Ya d'an zaro ido yace.

"Fad'a kuma?Ashe k'anwar ta wa mafad'aciya ce kenan?me yasa kika yi fad'a da su?"

Ta b'ata fuska saboda tuno abin da suke mata tace.

"To Ya Hamza ba su bane sai su yi ta tsokana ta wai k'ashi da rai,ko su ce min k'anjamammiya me ciwon sikila,ko su ce min me idon mage"

Tausayin ta ya kamashi,ta tab'e fuska kamar za ta yi kuma,nan da nan ya fara lallashin ta da cewa.

"Rabu da su kinji my k'anwa,Ai Allah ne ya jarrabeki kuma zai yaye miki tare da duk wani mai ciwon,kuma ke ba k'anjamammiya bace,za ki yi k'iba nan gaba kad'an insha Allah"

Ta saki fuska sosai sannan ta dubeshi tace.

"Kuma idan suka sake tsokana ta za ka rama min ko?za ka doke su ko?"

Ya gyad'a kai yana murmushi yace.

"K'warai kuwa,insha Allah zan zama GARKUWAR ki,babu Wanda zan bari ya tab'a ki Hidaya"

Tayi wani irin tsalle da juyi na murna,bai aune ba yaji ta fad'o kansa tana tuntsira dariyar murna,shi ma sai ya samu kansa da dariyar,da k'yar ya b'anb'areta a jikinsa,sannan ya zaunar da ita kusa da shi suka cigaba da hirar su cikin farinciki.

Umma dai ta ji su shiru ba su tawo ba,amma tana jiyo hayaniyar su musamman Hidaya da take ta zuba masa hira kala kala da zance,shi ba gwanin magana ba ma amma haka ya daure ya biye mata,tana ta d'akko Abubuwa a d'akin tana masa tambaya a kai,shi kuma bai k'osa ba yana ta bata amsa da kulawa.

Sai da Umma ta k'wala masa kira sannan ya mik'e yana amsawa yayi hanyar fita,Hidaya ta cillar da tsintsiyar da ta d'auka wai za ta yi shara,ta bishi a baya da gudu har ta cimmasa ta rik'o hannun sa suka jera har gaban Umma da ke ktcheen ta kammala had'a break fast, ya d'an Sosa k'eya yana murmushi yace.

"Ayya Umma na kiyi hak'uri ban zo na tayaki aiki ba yau"

Tayi murmushi tana rufe flask d'in tea tace.

"Ina za ka tuna dani ka samu Hidaya?ai tun d'azu ina ta jiyo shewar ku,Aiken ta na yi fa tayi kiranka kuzo ku karya shine ta shantake a can"

Ya mik'a Hannu ya karb'i flask d'in,Hidaya kuma ta d'auki wani tire da aka jera cups guda uku a kai,Umma tana cewa "Ajiye Hidaya ba za ki iya ba" ita kuma Hidaya na cewa"Allah zan iya Umma,ni fa ina da k'arfi sosai"

Umma tayi dariya a ranta tana cewa.

"A wannan Lange langen jikin na ki ina wani k'arfi?"

A parlour suka baje suna karyawa su Uku,Hidaya na ta wasanni ta k'i maida hankali kan cin abinci,Hamza ta na fama da ita dai Umma na tayashi har suka Kammala,shi da Hidaya suka kwashe kayan suka fita da su,Hidaya tace alambur ita za ta yi wanke wanken cups da spoon d'in da suka b'ata,Dan kar tayi rigima Umma ta k'yaleta,ta had'a mata Ruwan kumfa ta barta a tsakar gidan ta dawo parlour gun Hamza.

Zaune ta tarar da shi yana danne danne da wayar sa,ta zauna ta dubeshi cikin kulawa tace.

"Ya kamata ka tashi kayi shirin da za ka yi,nima a shirye nake,domin mu wuce mu mik'a yarinyar nan yanzu ko?"

Da wani irin hanzari ya d'ago ya kalli Umma,fuskarsa cike da tashin hankali mara misali,ganin yadda Umma ta zubo masa idanu shiyasa yayi saurin waskewa ya sunkuyar da kai,a hankali yace.

"To Umma,bari na d'auko takardar da za mu kaita da ita,tana cikin aljihun wando na na ranar da na saka,tare da envelop d'in da mummyn Hidayan ta bani akan na ajiyewa Hidaya sai ta girma sai na bata"

A hankali ya mik'e,jikin sa a sanyaye ya fito daga parlour 'n,Umma ta bishi da kallo tana girgiza kai cike da damuwar rabuwa da Hidaya.

Hidaya na kallon fitowar sa ta fara d'aga Hannu tana yi masa magana.

"Ya Hamza zo ka tayani wanke wanke,sai kayi min d'auraya ko?"

Ya tsaya cak! ya waiwayo yana dubanta cikin wani yanayi,duk ta jik'a jikinta da ruwa,kumfar omo kuwa har a fuskarta tayi faca faca,ya k'ura mata idanu sosai,wata kewa ta mamaye ruhinsa,yaji tamkar ya rusa ihu,Hawaye ya ciko idanuwan sa,da sassarfa ya juya da hanzari ya wuce d'akin sa ko gabansa baya iya gani.


**************


Yana shiga d'akin sa ya kife kansa a bango yana sakin numfashi, idanuwan sa a runtse k'irjinsa na zafi sosai,ya rasa dalilin da ya sa yake jin wani matsanancin ciwon tafiyar Hidaya,bai santa ba !bai sa ba da ita ba!rana d'aya ta shigo rayuwar sa tana son hargitsa masa lissafi!Yarinya k'arama da ita!kuma ya san matsanancin tausayin ta ke d'awainiya da shi! Ya sake lumshe idanuwan sa hawaye na taruwa,a hankali bakinsa ya motsa yana addu'a domin nemawa kansa sauk'in da yake ji a fad'in k'irjinsa,domin ya tabbatar Allah ba ya nufin bayin sa da tsanani sai sauk'i,kamar yadda ya fad'a a cikin littafinsa mai Girma.

"یرید اللہ بکم الیسر ولا یرید بکم العسر"

(Allah yana nufin sauk'i gare ku,baya nufin tsanani)

Haka nan Annabi(S A W)Yana cewa sahabbansa:"Ku sassauta kada ku tsananta,kuyi bushara kada ku Kore" Bukari da Muslim ne suka rawaito shi.

Yana tuna hakan ya sauke numfashi da k'arfi,ya cigaba da addu'a sosai,sai yaji k'uncin Zuciyar sa ya fara yaye wa,musamman da ya tuna cewa,Allah yana sane da Hidaya,domin shine mahaliccinta,shine mai zab'a mata rayuwa a duk in da ya so,haka nan Allah yana jin sa da ganin sa,kuma yana da yak'inin zai amsa masa addu'ar sa wadda yayi Daren jiya,akan Idan zaman Hidaya gidan Marayu alkairi ne Allah ya tabbatar, idan kuma babu alkairi to Allah ya sauya mata da mafi alkairi a rayuwar ta,Ubangiji mabuwayin sarki shi yace mu rok'e shi zai amsa mana mu bayin sa,domin shi makusanci ne a garemu,kuma yana amsa addu'ar duk Wanda ya kira shi .Allah ta'ala yace.

"و إذا سألک عبادی عنی فإنی قریب،أجیب دعوة الداع إذا دعان،فلیستجیبوا لی ولیٶمنوابی لعلھم یرشدون"

(Kuma yayin da bayina suka tambayeka game da ni,to ni makusanci ne,ina amsa addu'a idan ya kirani).

A take yayi Hamdala ga Allah,sannan ya k'ara da salatin Annabi,sai ya ji jikinsa yayi k'wari,Zuciyar sa cike da jarumta,k'afafuwansa da suka yi sanyi suka soma k'arfafa,ya ta ka ya nufi wardrobe d'in sa ya bud'e ya zaro wandon kuftar da ya sa ka jiya da k'addara ta had'ashi da Hidaya,ya zauna a gefen gado ya zira hannuwan sa cikin aljihun wandon da nufin zaro takardar,cikin ikon Allah ya zaro ta ya fito da ita,ga mamakinsa sai yaga iya envelop d'in ce kawai babu takardar da za a kai gidan Marayu, ya ajiye envelop d'in gefen sa ya juya wandon d'aya b'arin yana duba d'aya aljihun,amma sai baiji komai ba,haka yai ta caje aljihun yana zazzagewa amma takarda tace d'aukeni in da ka ganni,ya cika da matsanancin mamaki,saboda shi dai ya san lokacin da Mummyn Hidaya ta ba shi takardun da kansa ya cusasu cikin aljihun sa,to ya akayi yaga d'aya bai ga d'aya ba,wannan takardar kuma ita ce jigon kai Hidaya gidan Marayu, idan babu takardar bai san ya ya zai yi ba,tunda bai san komai ba,bai da masaniya akan abin da ke cikin takardar balle yayi musu bayani da baki,bayani da baki ma ba zai gamsar ba.

Haka ya mik'e yayi ta binciken takardar amma Allah bai sa ya ganta ba,har gwiwar sa ta sare ya fara gajiya,ya zauna bakin gado ya dafe kansa cikin tunanin in da takardar ta yi kamar wata aljana,ya jima a zaune har bai san lokaci na ta tafiya ba,kawai sai jin sallamar Umma yayi a kansa.

Ya d'ago yana amsa wa idanuwan sa sun sauya kala,Umma taji gabanta ya fad'i ganinsa cikin wannan yanayin,da hanzari ta matso ta zauna gefen sa tana kamo hannunsa,cike da kulawa take ambatar.

"Lafiya kuwa Hamza?me ya faru ne tun d'azu ina jiranka?

Bai san lokacin da ya d'ora kansa kan kafad'ar Umman ba,ya saki Numfashi a hankali yayi magana.

" Umma na an samu matsala ne….

Ta d'ago kansa da sauri ta dubeshi,suka had'a idanu,ta ga duk ya wani marairaice,ta k'ura masa ido tace.

"Matsala kuma?wace matsala kenan?"

Ya sunkuyar da kai ya fara magana cikin rauni kamar zai saka kuka.

"Wallahi Umma banga takardar da za a kai Hidaya gidan Marayu da ita ba,tun d'azu nake dubawa amma ban ci nasarar ganinta ba,na rasa in da ta yi,kuma fa a aljihuna na sakata,kuma wallahi Umma ita ce shaidar da za mu kaita da ita,idan babu ba zai yiwu mu kai Hidaya gidan Marayu ba"

Umma na shirin magana suka ji Hidaya a bayansu na ambatar.

"Ya Hamza ni za a kai gidan Marayu?Umma ina ne gidan Marayu kuma …?".


Comment
Share
Vote
Pls


*TYPING*📲

✌️💔 *GARKUWA BIYU* 💔✌️

*TARE DA ALK'ALAMIN* ✍️

HASSANA D'AN LARABAWA

*MARUBUCIYAR* 👇

SANADIN HOTO
HASSANA DA HUSSAINA
CIN AMANAR RUHI
BAHAGON LAYI
BAHAGON LAYI (SABON SALO)

*DA KUMA*

GARKUWA BIYU


*BABI NA ASHIRIN DA BIYAR DA NA ASHIRIN DA SHIDA*

WATTPAD:Hassana3333


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️

🖊 *PEN WRITERS ASSOCIATION*🖊️


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️


______________________________________

*~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~*


_____________________________________


https://www.facebook.com/groups/1533639276725285/


A hanzarce suka waiwayo suna duban ta saboda basu san da zuwan ta ba,ta na tsaye bakin k'ofar jikinta jagab duk ta jik'e da Ruwan wanke wanke,jikinta na D'an rawa kad'an alamar ta fara jin sanyi,Umma ta dubeta ta k'ak'aro murmushi tace.

"Yanzu haa kika jik'a jikinki da ruwa Hidaya?to muje na sauya miki kaya saboda naji ana cewa ba a son masu irin lalurarki suna zama da jik'ak'k'un kaya"

Mik'ewa tayi tana kama hannun Hidayan za su fice,ta waiwayo ta dubi Hamza da ke zaune kansa a k'asa tace.

"Ka dai cigaba da dubawa ko za a dace a ganta,bari na sauyawa Hidayan kayan jikinta"

Ya jijjiga kai ba tare da yayi magana ba,kuma bai d'ago kansa ba,har suka fice Hidaya na waiwayen sa tana kallon sa.

Kafin Umma ta sauyawa Hidaya kaya tuni Hamza ya birkita d'akin sa Neman takarda,amma ko mai kalarta bai gani ba balle ita,duk ya gigice ya rasa ya zai yi ma,haka ya tattara ya hak'ura ya nufi cikin gida parlour'n Umma domin a san mafita.

Yana sallama Hidaya na zurowa da gudu tana nuna masa kayan da aka sauya mata,tana tambayar sa wai tayi kyau?yayi malalacin murmushi yana jinjina mata yace.

"Kin yi kyau K'anwata sosai"

Ta fara murna tana biye da shi har ya zauna kan kujera,ta fara k'ok'arin hayewa cinyar sa,da hanzari ya hanata hakan ya nuna mata kusa da shi yace.

"Zauna a nan kinji Hidaya"

Ta yi shiru tana duban sa k'uri da idanu,ya sake magana babu walwala a kan fuskar sa.

"Ki zauna a nan nace ko"

Ta tafi a hankali ta zauna,tayi kasak'e duk ranta a jagule ganin babu fara'a a fuskar Ya Hamzan ta,ganin yadda tayi shiru har da D'an tagumin ta sai yayi murmushi ya kalleta yace.

"Hidaya…..

Ta d'ago ta kalleshi tana k'ifk'ifta idanuwa,ya karya wuya yace.

" Fushi kika yi da yayan ki ne?"

Girgiza kai tayi ,Hamza yace.

"To D'an yi murmushi na gani mana"

Aikuwa sai ta saki murmushi mai kyau da ya sa Hamza cikin nishad'i,har bai san lokacin da ya zaro wayar sa a aljihu ya k'yasa mata photo ba,ya d'auketa wajen kala shida,ita kam Hidaya sai canja salo take tana wani iyayi,shi kuma yana dariya.

A lokacin Umma ta fito daga bedroom tana kallon su,sun shagala cikin nishad'i sosai,sai da tayi gyaran murya sannan suka Ankara,Hidaya da tafi da gudu da wayar Hamza a hannun ta ta na nunawa Umma hotunan da ya d'auketa ,Umma ta karb'a ta na dariya tace.

"Iyen ba,Aikuwa y'ammatan nawa tayi kyau sosai"

Ta k'yalk'yale da dariya ta na zama a jikin Umma bayan Umman ta zauna,Hidaya ta maida hankalin ta kan wayar tana wasa,Umma kuma ta dubi Hamza tace.

"Ka ga takardar kuwa?"

Ya girgiza kai cike da damuwa yace.

"Banganta ba Umma,na yi iya duba amma ko k'yallinta ban gani ba,abin ya d'aure min kai sosai"

Umma ta yi shiru,sai can tace.

"To yanzu ya za a yi kenan Hamza….

Ya jefa hannuwa yace.

" Ban sani ba Umma,wallahi ni duk kaina ya kulle ma"

Tayi ajiyar zuciya da tunani iri iri a ranta,tun jiya take addu'ar Allah yasa Hidaya ta zauna tare da su,Hamza ne kad'ai rabon da ta samu a duniyar ta,Wanda ya kasance maraya tun yana cikinta D'an wata biyar,Hamza ne komai na ta kamar yadda ta zama ita ce komai na sa,Ruwa da iska,zafi da sanyi,bazara da damuna duk suna tare,komai shi yake mata,idan bata da lafiya shine mai lura da ita,wani abin ma bai kamata yayi mata ba a matsayin sa na namiji,duk da kasancewar sa D'an cikin ta,amma wani abin dole sai Y'ar uwarta mace,duk wata mace tana buk'atar Y'ar uwa mace ko d'iya mace domin tallafawa juna a bisa wasu larurorin,shiyasa taji a ranta tana buk'atar zaman Hidaya tare da su,haka nan tana tausayawa Hidayan a bisa rayuwar da ta tsinci kanta,ga lalura ga kuma rashin dangi,kulawar da za a bata a gidan Marayu ba Lallai ta gamsheta ba,duk da su d'in ma ba wani k'arfi ne da su ba,amma tana tunanin da taimakon Allah za su iya rik'e Hidayan domin ta rayu da su,bata sani ba ko Allah ne yayi nufin amsa mata rok'onta shiyasa aka nemi takardar aka rasa,wadda kuma tilas sai da ita za a kai Hidayan gidan Marayun,ba tare da b'ata lokaci ba kawai Umma taji Zuciyar ta ta yarje mata su zauna da Hidaya har zuwa lokacin da Allah zai bayyana gaskiya akan lamarin ta.

Hamza dai yana ta kallon Umma ganin ta yi shiru bata ce komai ba,hakan ya sa yayi magana cikin sanyin murya.

"Umma kinyi shiru baki ce komai ba,yanzu ya za mu yi kenan? Ko komawa kangon zan yi ma gani ko har yanzu Mummyn Hidayan tana wajen?

Umma ta sauke numfashi ta dubi Hamza,cikin karsashi tace masa.

" Ni fa ina ganin Allah yayi nufin bamu kyautar Hidaya ne domin mu rayu tare da ita na wani lokaci,abin da nake ganin zai fi kawai shine,mu rik'e Hidaya mu zauna tare da ita a gidan nan,duk ma Wanda ya tambayeni a kanta zan shaida masa cewar Y'ar k'anwata ce aka bani ita daga nesa domin na raineta,tunda dai bani da wasu y'an uwa a kusa sai na nesa,ko ya ya ma gani…?"

A razane Hamza ya d'aga kai ya dubi Umma jin maganganun ta,Abubuwa biyu suka had'e masa lokaci guda,tsananin fargaba!da kuma mad'aukakin farinciki!

Ya dad'e a haka Zuciyar sa na kai komo bisa ga zab'in Umma,cikar farincikin sa shine zaman Hidaya tare da su,amma kuma Alk'awari ya d'aukar wa mahaifiyarta cewa zai kai ta gidan Marayu,bai sani ba ko akwai babban dalilin da ya sa ta nemi hakan gareshi,idan har bai kai ta ba ya karya alk'awari kenan?shikenan ya shiga sahun munafukai?to amma idan maslaha da kyakkyawar rayuwa yake nemawa Hidaya an ya ta cancanta da za ma gidan Marayu?wad'annan tunane tunane su ne suka damu ran Hamza har ya ji kansa ya fara ciwo,amma da ya tuna Allah mai bada mafita ne akan komai sai ya sauk'ak'awa ruhin sa,yayi wa Umman sa kyakkyawan kalami ta hanyar dubanta da cewa.

"Hanzarin ki mai kyau ne Umma na ,Sai dai akwai k'alubale tattare da hakan,abin da nake gani zan yi istihara akan lamarin,duk abin da yafi alkairi Allah ya zab'ar mana,idan zaman ta alkairi ne a garemu da ita kanta Allah ya tabbatar, idan kuma babu alkairi Allah ya musanya da mafi alkairi"

Umma ta ji dad'in abin da Hamza yace,cikin farinciki tace.

"Ameen ya Allah Hamza,zab'in Allah kam shine zab'i mai kyau ba son zuciyoyin mu ba"

Da wannan suka rufe maganar.


**************


Kwanan Hidaya Uku a gidan,tuni ta sake tamkar gidan su tana walwala sosai,yaran layin da suke shigowa har sun zama k'awayen ta,mamakin su Umma bai wuce yadda Hidaya ta fara mantawa da zancen Mummyn ta ba,ba ta cika tunawa da ita ba.

Hidaya Yarinya ce mai hankali da nutsuwa,sai dai akwai yawan shagwab'a da son wasa,wani zubin Hamza har gajiya yake da wasan ta,in dai yana gidan
bata da abokin wasa sai shi,wani zubin ficewar sa yake ya gudu ya bar mata gidan,idan ya dawo kuwa ta dinga shagwab'a kenan har da kuka,sai ya sha aikin lallashi tukun take shiru.

A tsawon wannan kwanakin da Umma da Hamza suna ta addu'a da istihara,babu abin da zuciyoyin su ke kai irin k'ara jin son zaman Hidaya tare da su,shiyasa kawai suka barwa ransu cewar su cigaba da rik'on Hidaya a wajen su.

Umma bata da yara,amma kuma gidan ta akwai farinjinin yara ko Dan Hamza yana da son yara,kuma ita ma Umman haka,musamman da yake ta iya kitso,yara suna shigowa tana yi musu musamman na layin,kuma bata karb'ar kud'i,domin Umma akwai karamci da mutumci,hakan yasa take zaune da mutane lafiya a unguwar,kuma tana da jarinta a Hannu Wanda Khaleel ya bata,tana saro atamfofi da laces da dai kayan mata duk tana siyarwa,gidajen masu kud'in layin duk suna siyan kayan ta,hakan yasa asirin su yake a rufe.


Satin Hidaya biyu a gidan idan ka ganta za ka d'auka tayi shekara ne,matuk'ar Sabo suka yi ta yadda suke ganin ba za su iya rabuwa da ita ba,a lokacin Hamza ya samu Umma da zancen yana so ya nemarwa Hidaya School wadda za ta dinga zuwa saboda cigaban karatun ta,saboda ya lura yarinyar tana da k'ok'ari sosai,kuma kullum sai tayi masa maganar makaranta,musamman idan taga ya shirya zai tafi ta sa makarantar,lokacin Hamza yana jami'a level 100 yana karantar mass communication.

Lokacin da ya samu Umma a parlour'nta tana zaune tana ware wasu atamfofi da zata aiki Hamza ya kai mata tasha,za a tura su gurin wata Costomer d'in ta a Gombe state,sai da ta kammala sauraren sa sannan ta amsa masa da cewa.

"Hakan na da kyau,sai a nemi makaranta mai kyau a sakata,amma Mara nisa wadda za ta iya zuwa da kanta ta dawo da kanta ko?"

Ya jijjiga kai yana taya ta zura kayan a Leda.

Ta sake magana tace.

"To yanzu nawa kake gani zai isa ayi hidimar karatun ta da su?in yaso sai na ware kud'in na baka,domin babu laifi watan nan na samu riba da yawa Hamza"

Yayi murmushi yace.

"Alhamdulillah haka akeso Umma,Allah ya k'ara sakawa kasuwancin ki albarka,amma ki bar kud'in ki zan yi wa Hidaya komai insha Allah"

Ta tsare shi da idanu da kallon tuhuma tace.

"Me yasa baka son na dinga yiwa Hidaya Hidima ne?komai nace zan mata sai kace kai za ka yi?a sanina kai d'in karatu kake ba wata Sana'a ba,har yaushe za ka iya d'aukar d'awainiyar wani a kanka?"

Da sauri ya tare ta cikin tausasawa.

"Ba haka bane Umma na,bana son na yi ta saka ki kashe kud'i ne akan abin da bakiji ba baki gani ba,ni ne na d'auko Hidaya na kawota gidan nan,ni ya kamata naji da d'awainiyar ta kar na d'ora miki,amma kiyi hak'uri don Allah Umma"

Tayi murmushi tace.

"Ai duk abin da ka kawo tamkar ni ce na kawo Hamza,ka daina kokonto akan hakan,ni Hidaya jin ta nake a raina tamkar kai, babu abin da babu zan mata ba"

"Na gode Umma na" ya fad'i hakan cikin k'ayatacciyar fara'a da ta fito da kyawunsa fili,Sannan yace da Umman.

"Ina Hidayan ne na ji ta shiru?"

Ta nuna masa bedroom tana cewa.

"Tana ciki tana kwalliya,wai yau Hansa'u take partyn Y'ar tsanarta,shine take ta kwalliya wai don tafi kowa kyau….

Hamza yayi dariya yana mik'ewa da fad'in.

" Lallai Ashe yau za mu sha party kenan?bari na lek'a na gano kwalliyar y'ammata"

Umma tayi dariya tana cigaba da had'a kayan gaban ta,shi kuma ya nufi bedroom d'in Umma ya d'aga labulen yana sallama.

Can kan kujerar gaban dressing mirror ya hangota zaune tana kwalliya,ta damb'ara powder duk tayi dabbara dabbara,ga jambaki duk ya b'ata mata gefen baki,kwalli kuwa har k'asan idanuwa da gefe wai tayi hawayen masoya,tun shigowar sa bata lura da shi ba ta na ta sake lamb'ata Abubuwa a fuskar ta,kallon fuskar ta yake yi yana k'unshe dariya,kamar wadda za ta dandali gad'a,bai san lokacin da dariyar ta sub'uce masa ba,k'arar dariyar sa yasa ta waigowa a hanzar ce……..!


Comment
Share
Vote
Pls


*TYPING*📲

✌️💔 *GARKUWA BIYU* 💔✌️

*TARE DA ALK'ALAMIN* ✍️

HASSANA D'AN LARABAWA

*MARUBUCIYAR* 👇

SANADIN HOTO
HASSANA DA HUSSAINA
CIN AMANAR RUHI
BAHAGON LAYI
BAHAGON LAYI (SABON SALO)

*DA KUMA*

GARKUWA BIYU


*BABI NA ASHIRIN DA BAKWAI DA NA ASHIRIN DA TAKWAS*


WATTPAD:Hassana3333


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️

🖊 *PEN WRITERS ASSOCIATION*🖊️


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️


______________________________________

*~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~*


_____________________________________


https://www.facebook.com/groups/1533639276725285/


Ta sakar masa murmushi a sanda ya k'araso gaban ta ya tsaya yana dubanta,shi kam dariya yake yi,bata gane dariyar da yake ba shiyasa ta tambaye shi cikin zumud'i tace.

"Ya Hamza ka ga kwalliyata,na yi kyau ko?"

Ya girgiza mata kai alamar bata yi kyau ba,sai ta kwab'e fuska za ta yi shagwab'ar da ta saba tace.

"Kalla fa ka gani Ya Hamza,Allah kuwa duk sai na fi su Hansa'u da Maryam kyau,shine za ka ce wai banyi kyau ba?

Yayi murmushi cikin kulawa yace.

" To ai gaskiya na fad'a miki K'anwata,in dai ba so kike nayi k'arya ba to gaskiya ba ki yi kyau ba,wannan abin duk ya b'ata miki fuska fa"

Ta fara turo baki tana buga k'afa wai ita Lallai sai yace ta yi kyau,yayi dariya yace "wai so kike nayi k'arya ne Hidaya"

Ta kamo hannunsa ta rik'e,ta d'aga kanta tana kallon fuskarsa saboda ya kere ta a tsawo sosai.

"Eh Ya Hamza,ni dai kayi k'arya kawai ka ce nayi kyau"

Da sauri yace.

"Subhanallah!ai k'arya babu kyau Hidaya,kullum an fi so mutum ya kasance akan gaskiyar sa tun yana yaro har zuwa girman sa kinji,K'arya zagin Allah ce,Sannan kuma Allah ya tsinewa mai k'arya,domin a Alk'ur'ani mai Girma Allah yace.

"فنجعل لعنت اللہ علی الکٰذ بین"

(Sannan kuma mu sanya tsinuwar Allah akan mak'aryata)

Duk wani aiki da za ka yi idan babu gaskiya da tsoran Allah a ciki to shirme ne Hidaya,ki daina k'ok'arin ganin duk abin da kike so sai kin samu ko da ta hanyar k'arya ne,domin ba zai amfaneki da komai ba daga duniya har Lahira ,gaskiya ita ce tushen dukkanin wani alkairi,gaskiya ita ke sawa bawa ya zama mai hak'uri a kan jarraba,mai godiya yayin samun ni'ima,mai gaggawar aikata alkairi,babu wata halayyar imani da za ta tabbata face sai da tabbatar gaskiya,shiyasa Allah ya umarci bayinsa muminai da jin tsoron sa,da kuma shiga cikin masu gaskiya,sai yace.

"یأیھا الذین ءامنوا اتقوا اللہ و کونوا مع الصٰدقین"

(Ya ku wad'anda suka ba da gaskiyar,ku ji tsoron Allah,kuma ku zama tare da masu gaskiya).

Abin nufi masu gaskiya a imanininsu,da maganganun su,da ayyukansu,da alk'awuransu.

Dan haka a ko da yaushe ki kasance mai fad'in gaskiya da tsayawa a kanta Hidaya,za ki ci riba duniya da Lahira.

Duk da tana da k'arancin shekaru amma maganganun sa sun shigeta,tana kallon sa duk jikinta yayi sanyi tayi magana.

"To Ya Hamza na daina,zan dinga fad'an gaskiya a ko ina ne,kuma na daina k'arya,idan naga wani ma yayi zance ya daina Allah ya hana kuma baya so"

Ganin ta fahimceshi sai yaji dad'i,ya saka mata albarka,sannan yace ta je toilet ta wanke fuskarta,da sauri ta tafi ta wanko kuwa,yana tsaye har ta dawo tana goge fuskar,ya kalleta yaga tayi masa wani kyawu,shi sai yaga ma kamar a kwanakin an dad'a mata wani kyau ne.

Da ta saka shi gaba da rigima tilas shi ya shafa mata powder har da kwalli,yasa mata jambaki kad'an,sai gata ta fito ras,sai da ya kammala mata sai ta tsiro da tsirfa wai ya tsaya ya d'aura mata zanin ta,nan da nan yayi fuska yace.

"Kije Umma ta d'aura miki,babu kyau fa Namiji ya dinga ganin jikin mace,Allah ya haka hakan Hidaya"

Ta bishi da kallo tana cewa.

"To ai kai yayana ne"

Ya amsa mata yana mik'ewa tsaye.

"Duk da hakan,ai ni ba muharramin ki ba ne"

Da sauri tace.

"Muharrami?Ya Hamza menene muharrami kuma?"

Yayi gaba yana cewa.
"Zan gaya miki ko menene,amma sai kin k'ara girma kinji"

Kafin ma tayi wata maganar har ya fice daga bedroom d'in.

Kafin Hidaya ta gama shirin partyn Y'ar tsana ya fice daga gidan zuwa tasha kai sak'on Umma….

Kusan awa d'aya da rabi ya d'auka kafin ya dawo,da yake bayan sallar la'asar ya fita,lokacin da ya dawo kusan k'arfe shida na magariba yayi.

A k'ofar gida ya ci karo da Hidaya da zugar k'awayen ta kusan guda biyar an gama party,tana ganin sa ta kama murna tana nuna wa k'awayen ta shi,duk suka nufo shi suna masa sannu da zuwa,ya amsa musu da murmushi akan fuskarsa sa,ya wuce gaba suka bishi yuuu a baya har cikin gidan,Umma na zaune tana gyara salak za ta yanka ta gansu sun shigo,tayi murmushi a ranta tana cewa "Hamza mai jama'a kenan!

Hidaya da k'awayen ta suka zagaye Umma suna taya ta had'a salat suna bata tana yankawa,yayin da Hamza ke zaune daga gefe yana yiwa Umma bayanin Aiken da tayi masa,sai da ya kammala take ce masa.

" Ni yau sai naga ka dad'e baka dawo ba,ko dai baka samu mota da wuri bane?Insha Allahu dai na kusa siya maka mashin kai ma ka huta haka"

Yayi murmushi yana Sosa kunnensa jin yana k'aik'ayi,ya kalli Hidaya yace ta d'auko masa abin Sosa kunne a d'akin Umma na sa ya k'are,da hanzari ta tashi ta shige d'aki,shi kuma ya mai da hankalin sa kan Umma yana bata amsa da cewa.

"Ba rashin mota ba ne Umma,na dai biya kangon nanne ko zan ci karo da …….

Fitowar Hidaya ta sa yayi shiru,taje har gabansa ta mik'a masa abin da ya aiketa,ya karb'a yana goge kunnen sa da babu wata daud'a a jiki saboda yawan tsaftar sa,tana tsaye a gabansa da alamun da magana a bakin ta,ya dubeta yana cewa.

" Ya dai Hidaya?akwai wani Abu ne?

Tayi murmushi sannan ta zura hannun ta cikin Hijabin ta ta fito da wata farar Leda ta mik'a masa,ya kai Hannu ya karb'a yana kallo yace "menene wannan?

Kanta a k'asa tana Y'ar dariya tace.

" Biscuit da lemo ne da aka bani na partyn Y'ar tsana,shine na kawo maka nawa ka ci"

Sai yaji k'aunarta ta kuma ninkuwa a ransa,Hidaya duk abin da ta ci ko baya nan sai ta rage masa,wataran ma bata iya cin komai muddin baya nan sai ya dawo,Yanzu ga k'awayen ta nan da suka yi partyn tare kowa ya cinye nasa kayan partyn,amma ita ta kasa cin nata ta ajiye masa saboda k'auna,cikin farinciki babu gwasalewa yace.

"To Na gode Hidaya na,bari mu ci tare ko ?sai mu sanwa Umma"

Ta gyad'a kai tana dariya,yayin da Umma ke cewa "Ah ah ni dai na yafe ,ku ci abin ku"

Ya farke ledar biscuit d'in ya zaro guda d'aya yayi bisimillah ya gutsira,tana ta kallonsa bakin ta kamar gonar auduga don fara'a,ragowar da ya gutsira ya kai mata bakin ta,ta bud'e bakin ya saka mata a hankali ta fara taunawa tana kad'a kai alamar dad'i,sannan ita ma ta d'auko ta mik'a masa bakin sa,ya karb'a ya tauna shi ma yana kad'a kai tamkar yadda tayi,ta fashe da dariya tana nunawa k'awayen ta yadda yake yi,su ma suka fara dariya suna kallon sa.

Sai lokacin Umma tayi magana tana cewa k'awayen Hidaya su tashi su tafi gida magariba ta kusa,kowacce tayi sallah sannan su dawo domin ayi karatu,daman kullum bayan magariba Hamza yana Tara yaran mak'ota a tsakar Gidan yana koya musu karatu ko tarihin annabawa da sahhabai.

Duk suka tashi suka tafi,yayin da Hidaya tayi gefe ta fara dakan yajin barkono da Umma ta sakata,Wanda za a ci wake da shinkafa da shi,sai lokacin Umma ke bawa Hamza amsar maganar da ya fara d'azu cewar.

"Wato har yanzu baka hak'ura da zuwa kangon nan ba ko Hamza?in fa ba wani ikon Allah ba da wuya ka sake ganin mahaifiyar Hidaya a wajen nan,kana wahalar da kanka ne kawai,gara ma ka hak'ura duk lokacin da Allah ya nufa za a ganta to babu makawa sai an ganta"

Hankalin sa na kan Hidaya da ke dakan barkono tana y'an wak'e wak'en ta,ya d'auke kallonsa ya mayar kan Umma yana sauke ajiyar zuciya yace.

"To shikenan Umma,Allah ya tabbatar da alkairi,d'azu naji kina maganar siyen mashin ko?kamar kin san shekaran jiyan nan muka gama magana da Khaleel,wai shi da mota zai siya min a satin nan,na nuna ban amince ba shine yayi fushi da ni har yau ya k'i nema na a waya,Idan na kira shi ma baya amsawa"

Umma ta zaro idanu da fad'in.

"Mota kuma?wace irin mota ni Maimunatu ana zaune k'alau?


Ya sunkuyar da kai k'asa cikin sanyin murya yace.


"Haka dai yace Umma,ina ta cewa ah ah ya bari zuwa nan gaba ma amma ya k'i ganewa,shine yayi fushi dani"


Umma ta sauke Numfashi ta kira sunan sa.

"Hamza.....

Ya d'ago kansa ya amsa yana duban ta,ta k'ura masa ido tace.


" Ina fatan dai ba kai kake rok'an Khaleel akan yayi maka wani abin ba ko?Saboda ina tsoran yadda yake maka Hidima sosai,abubuwan da yake maka sun yi yawa fa"


Hankalin sa ya tashi jin maganar Umma,da sauri ya janyo kujerar da yake kai ya matso dab da ita ya kamo hannun ta ya rik'e,fuska cike da jimami ya fara magana.


"Umma na ai kin san hali na,kin san tarbiyyar da kika bani ina kanta ban kufce ba,wallahi ban tab'a rok'on Khaleel yayi min wani abin ba,sau da yawa ma yana min kyautar Abu nak'i karb'a,haka kuma yana sawa yayi fushi da ni,kullum yana cemin wai duk abin da ya mallaka kamar nawa ne,amma ban tab'a yardar wa zuciyata hakan ba,don Allah Umma kar zuciyar ki ta zargi D'an ta da rok'o"


Sai Umma taji tausayin Hamza,hakan yasa tayi murmushi ta shafa kansa tace.


"Ba zargin ka nake ba,na fad'a ne dai don ka kiyaye Hamza,bana son ka zama mai kwad'ayin abin hannun mutane,hakan na jawo zubewar k'imar mutum,Khaleel kuma ka barni da shi,duk lokacin da ya sakko ya kira ka a waya ka bani shi za mu yi magana,ya kamata ya dinga sassauta Abubuwa kud'in da yake kashe maka sunyi yawa,kuma na san cewar duk ba da sanin mahaifinsa yake ba,saboda yadda Mahaifin sa ya tsani talakawa baya son D'an sa na alak'a da su,ka duba yadda dole Sai da ya raba Khaleel da k'asar nan duk don ya raba abotarku Hamza,na tabbatar idan ya san Khaleel yana yi maka Hidima to da matsala,gara ya dinga sassauta wa yayi wa Mahaifin sa biyayya ko ba haka ba?"

Yayi ajiyar zuciya yana kallon Umma yace.


"Hakane Umma,ni kaina abin da kullum nake nuna masa kenan,amma ya k'i ganewa,Sai ya dinga cemin wai ni jininsa ne,daddyn sa bai isa ya raba mu ba,Umma wallahi ba cin ina yiwa Khaleel nasiha akan kyautata iyaye da jin maganar su da tuni ya fand'arewa daddyn sa,kuma Dan yayi sa a daddyn na sa yana matuk'ar sonsa ne ma.......


Bai k'arasa magana ba suka ji Hidaya ta k'wallara ihu da k'arfi,saamakon yajin da ya shigar mata ido tana dakan Barkono.....


A rikice suka mik'e suka yi kanta,tana niyyar fad'uwa k'asa Hamza ya tarota ta fad'o jikinsa,ganin yadda take yi azaba ta ishe ta sai ya kuma rikicewa ya k'ank'ameta,Umma sai salati take yi,da sauri ta nufi kitchen Dan lalubo gishirin da za ta lasa mata a baki ko idon zai bud'e,shi kam Hamza har ya fara k'wallar tausayin Hidaya ganin yadda take tsalle a jikinsa idanuwa a manne.......!


Comment
Share
Vote
Pls


*TYPING*📲

✌️💔 *GARKUWA BIYU* 💔✌️

*TARE DA ALK'ALAMIN* ✍️

HASSANA D'AN LARABAWA

*MARUBUCIYAR* 👇

SANADIN HOTO
HASSANA DA HUSSAINA
CIN AMANAR RUHI
BAHAGON LAYI
BAHAGON LAYI (SABON SALO)

*DA KUMA*

GARKUWA BIYU


*BABI NA ASHIRIN DA TARA DA NA TALATIN*


WATTPAD:Hassana3333


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️

🖊 *PEN WRITERS ASSOCIATION*🖊️


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️


______________________________________

*~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~*


_____________________________________


https://www.facebook.com/groups/1533639276725285/


Sai da Umma ta fito da gishiri ta lasa mata a baki sannan ta fara mommotsa idanuwan tana san bud'ewa,da ta bud'e sai ta rufe ta k'ara fasa kuka,Hamza ya sake rud'ewa yana cewa Umma.


"Umma ko mu tafi asibiti ne?kar yarinyar nan ta makance fa"

Dariya ya bawa Umma,amma ta kanne tace.

"Wane irin Asibiti kuma Hamza?Dan kawai yaji ya shiga idanunta sai a ta fi asibiti,yanzu zai ware bari ka gani"

Yayi shiru yana ta kallon fuskar Hidaya har tayi ja,ya kira sunan ta a hankali.

"Hidaya….bud'e idonki kinji"

Cikin muryar shagwab'a tace.

"Idona zai cire ne Ya Hamza idan na bud'e"

Ya girgiza kai tamkar tana ganinsa yace.

"Ba zai cire ba,kiyi bismillah ki bud'e a hankali,zan sake bushe miki ma"

A hankali ta fara bud'ewa da rufewa har suka bud'e tas,abin tausayi duk sun yi jajawur sunyi k'ananu,ya sake jin tausayin ta ya tsirga masa,bakinsa ya sa ya bushe mata idanuwan yana ta jera mata sannu saboda tausayi.

Umma kam sai lokacin tayi dariya tana duban Hidaya tace.

"Raguwa kawai!don D'an yaji ya shigar miki ido kike wannan kwazozoton,ke fa macece Hidaya,in zaki koyi juriya da dauriya ma ki koya,nan gaba ma har girki za ki yi,zafin turiri ma kad'ai ya isheki,gashi in kika girma za ki yi Aure har ki haihu,dole ki zama jaruma Yarinya"

Hidaya dai tai shiru har lokacin bata gama dawowa dai dai ba,sai Hamza ne ya maida wa Umma amsa da cewa.

"Umma barkono ne fa ya shige mata ido,ai dole tayi kuka,ai tayi jarumta ma Dan idan nine sumewa ma zan yi Umma"

"Amma kuwa da anji jiki,yaji ya shiga ido an suma" Umma ta fad'a tana dariya,haka tai ta jan Hidaya da wasa Hamza na tare mata,Hidaya kam saboda Haushin yajin ko abincin cewa tayi ba zata ci ba,Hamza ya biye mata shi ma ya k'i ci,da daddaren ya fita ya sayo musu fura da Nama suka ci,Umma tana kallon su ta fita sabgar su,ta had'a abincin na su ta aika da shi mak'ota saboda kar ya kwana ya lalace…..


*************


Bayan sati d'aya duk wani shirye shiryen kai Hidaya makaranta ya kammala,tana ta murna da tsalle za a sakata makaranta,har da islamiyya Hamza ya nemar mata,babu b'ata lokaci ta soma zuwa cikin nasara da Sa'a.

Har zuwa wannan lokacin kuma cikin ikon Allah ciwon Hidaya bai tab'a tashi ba,don su har mantawa suke yi wai tana da lalurar sikila ma,Hidaya ta murje ta dad'a wani sihirtaccen kyau da girma,kamar ba Y'ar shekara Tara ba,sai dai bata k'i ba sai tsawo da murjewar jiki.

Tana jin dad'in karatun ta sosai,in da aka kaita primary 5 saboda k'ok'arinta,haka nan kullum a gida Hamza yana mata bitar karatu sosai tana kuma ganewa.

Shak'uwar su kuwa sai abin da yayi gaba,Hamza na son Hidaya ,Hidaya na son Ya Hamza,komai tare suke yi,suyi wanke wanke tare,suyi shara tare,Aiken Umma tare suke zuwa,har wanki wataran idan Hamza na yi zagewa take ta tayashi,tunda bai fiye kai wanki ba,rana yake warewa ya fitar da kayansa da na Umma da na Hidaya duk ya wanke.

Kowa a unguwar mamakin shak'uwar Hamza da Hidaya a ke,duk kuma Wanda zai tambayi Umma akan Hidaya ta kan sanarda shi cewar d'iyar k'anwarta ce da ke kano,shine aka kawota nan Kaduna ta zauna tare da su,y'an uwan Umma kuma da ke kano da suka ga Hidaya sai Umma tace musu ai Hidayan d'iyar k'anin marigayi Mahaifin Hamza ce,ta d'akko ta ne saboda tana son d'iya mace kusa da ita,har suka dinga yi mata tsiya da cewa to in dai Hakane tayi Aure mana,za ta iya haihuwar yara da yawa ma ba mace d'aya ba,ita kam Umma tsoron Aure take yi tunda mijinta ya rasu tana da k'arancin shekaru har yau bata yi wani Auren ba,haka nan Kaduna ta rik'eta ta kasa komawa asalin garinta wato kano,tana ji a ranta ko bata yi Aure ba za ta iya kare kanta,zaman ta da D'an ta k'waya d'aya JAL mai albarka ya fiye mata y'ay'a dubu marasa Albarka.


Da yake Hidaya ta kasance mai sakin fuska da fara'a kamar Hamza,sai tayi farinjini,ko ina sonta ake yi,kulawar da Hamza yake bata kuwa bata da misali,komai ya samu Hidaya,duk abin da ya gani ya burgeshi zai siya mata,sai ya koma hidimar Hidaya kawai,ya daina yiwa kansa duk wata Hidima,sai dai yayi wa Umma da Hidaya.


Abu d'aya ke matuk'ar damun Hamza,shine rashin jin Khaleel a waya,tun yana Neman sa ba a d'agawa har Idan ya kira sai a ce a kashe take,duk ya zama tamkar Mara lafiya bashi da walwala,hatta Hidaya ta fuskanci hakan,saboda baya sakewa suyi hira da wasa da karatu kamar da,shiyasa ita ma ta shiga cikin damuwa ta daina walwala sosai,Umma tana lura da su,sai dai bata ce musu kanzil ba,tana jira su bayyana mata damuwar da ke ransu da kansu, ne,musamman Hamza da ta lura har wata rama ya D'an yi……


*****************


Yana zaune a parlour'n Umma misalin k'arfe takwas da minti Ashirin na ranar Alhamis,ya zabga tagumi ya fad'a cikin tunani,babu abin da yake son ji sai muryar Khaleel,wane irin fushi Khaleel ya d'auka da shi Hakane?ko yayi fushi da shi baya iya kwana biyu bai nemeshi sun shirya ba,amma yanzu kusan sati uku ko hud'u ko muryar juna basu ji ba,an ya kuwa lafiya?ya tabbatar idan da lafiya Khaleel ba zai iya kaiwa wannan lokacin bai neme shi ba,duk kuwa da laifin da yake ganin yayi masa.

Hidaya ta d'aga labulen d'akin tayi sallama,da plate a hannun ta Wanda ke cike taf da abinci,shinkafa da miya da salad har da nama,ta zo ta dire a gabansa,ta bishi da kallo tana cewa.

"Ya Hamza ga abincin mu sauko mu ci"

Ya girgiza kai Yana gyara zama yace.

"Ki ci kawai K'anwata,ni bana jin yunwa ba zan iya ci ba"

Ta yi shiru tana duban sa ganin ya shareta ya d'aga kan sa sama ko dubanta bai sake yi ba,ganin haka ita ma sai taji abincin ya fice mata a rai,daman kuma ranar duk bata jin dad'in jikinta .

Umma ce ta shigo parlour'n,sai ta tarar da su kowa ya ja gefe ya zuba tagumi,ga abincin ta anyi gefe da shi alamar ba za a ci ba,ta kama hab'a tana salati sannan ta dubesu tace.

"Wai ku kwana biyun nan lafiyar ku kuwa?me yake faruwa ne da kuke cikin damuwa haka?na zuba muku ido ne daman naga iya gudun ruwanku,to dai naga tabbas abin naku azimun ne,haka kawai kun d'auki damuwa kun d'orawa ranku,idan d'aya na cikin damuwa sai d'ayan ma ya shiga damuwa,haka ake rayuwar duniya kenan?kai Hamza bud'e baki kayi min bayanin rashin walwalarka ,gashi nan har ita ma k'anwaraka ka sakata cikin rashin walwala…

Maganarta ta katse saboda ganin Hawaye a idanuwan Hamza,ta zaro idanu cikin tashin hankali tace.

" kuka fa kake Hamza?wai menene ya faru ne da na za ka bud'e baki ka gaya min ba?

Hannuwan Hidaya kawai yaji a fuskarsa tana share masa hawaye,yayin da na ta idanun suka cicciko sosai da hawaye,suka yi wani irin k'yalli suna shining, ya kautar da kansa daga gareta ya dubi Umma yace.

"Umma Khaleel……

Sai yayi shiru ya duk'ar da kai k'asa Zuciyar sa na harbawa.

Umma tace.

" Me ya faru da khaleel d'in…?

Yayi ajiyar zuciya,cikin rauni ya soma magana.

"Umma tun ranar da na fad'a miki yayi fushi da ni akan siyen mota har yanzu bai k'ara nemana ba,idan na kira wayar sa bana samu,ban san halin da yake ciki ba Umma,Zuciyata kullum cike da fargaba da tsoro,bana son b'ata masa rai saboda kin san lalurar sa shi ma bata son b'acin rai,ina son sanin halin da Khaleel yake ciki Umma,da ina da hali zan shirya ne na ta fi England domin gano halin da yake ciki,Umma ki tayani addu'a Allah yasa Khaleel Yana cikin k'oshin lafiya"

Ita kanta Umma sai da taji ba dad'i,domin tayi tunanin tuni sun shirya suna waya kuma,tabbas dole Hamza ya damu,domin bata tab'a ganin abokan da suka shak'u da juna kamar Hamza da Khaleel ba,bata manta ranar rabuwar su har suma Khaleel yayi don damuwa,Hamza kam yafi wata biyu kafin ya dawo nutsuwarsa normal,tarihin abotar Hamza da Khaleel babba ce,Wanda Abubuwa suka faru a tsakani da bata son tunawa da su,Allah ne yake rik'e da amincin su har yanzu,amincin da babbar katanga ta so ruwa shi tun suna yara,amma Allah bai nufa ba,ba kuma wata Katanga ba ce illa Mahaifin Khaleel.

Umma ta sauke numfashi ta dawo daga tunanin da Zuciyar ta ta fad'a,nan da nan ta shiga bawa Hamza baki tana fad'in.

"Kayi hak'uri ,insha Allahu babu wani abin da zai faru da Khaleel sai Alkairi,ka dinga yin addu'a in Allah ya yarda a kurkusa za ka ji ya neme ka Hamza,damuwar bata da amfani,sai ka jawowa kanka wata lalurar,kasa Allah a ranka ka dogara da shi zai isar maka kaji"

Ya jijjiga kai hawaye na k'ok'arin zubo wa da sauri ya mayar da su Dan kar Umma ta gani,babu Wanda ya san adadin yawan damuwar da yake ciki,amma zai dage da addu'a akan duk in da Khaleel yake Allah ya tsare masa shi.

Ya juya da nufin kallon Hidaya sai yaga tana hawaye,da hanzari ya rik'o hannun ta yana tambayar ta me ya saka ta kuka,sai kuma yaji hannun ta da d'umi,langab'ewa tayi a jikinsa ta fara murk'ususu tana rik'e ciki wai cikinta da bayan ta na ciwo.

Hankalin Umma da Hamza yayi matuk'ar tashi ganin yadda Hidaya ke malelekuwa,can ta fara wani k'udundunewa tana kukan ciwon k'afa,idan tace nan na ciwo sai tace can na ciwo,sai ga Hamza ya rikice da kukan tausayin Hidaya,musamman da yaji cikin kuka tana ta kiran sunan sa tana cewa.

"Ya Hamza ka taimaka min zan mutu !Ya Hamza cikin!bayana!k'afana!k'irjina!duka jikina ciwo Ya Hamza,wayyo Allah kace musu su daina buga min k'arfe a jikina!Ya Hamza…..Ya Hamza…Ya Hamza ka cire min ciwon zan mutu…….

Kafin wani lokaci Hidaya ta fita daga hayyacinta tana shirin suma!tsananin tashin hankalin da Hamza ke ciki baya misaltuwa,hatta Umma sai da tayi hawayen tausayin ta,ganin abin ya ci tura da sauri ta shiga d'aki ta d'auko hijabin ta ta fito ta tarar da Hamza rungume da Hidaya a jikinsa sai faman Kuka yake yana fad'in.


" Hidaya na don Allah ki tashi ,ina ne yake miki ciwo,tashi mu gani …tashi kinji Hidaya….

Da hanzari Umma tace ya d'auko Hidaya su wuce asibiti,sungumarta yayi tamkar jaririya daman gata shafal,ya rungume ta suka fice daga Gidan a gigice ganin Hidaya na sassank'amewa.


Har bakin titi suka fita sannan suka samu mota,suna tafe amma Hamza gani yake direban baya sauri,sai lokacin yaji sha'awar ina ma yana da motar sa shi ma,da duk wannan jinkirin ba za su had'u da shi ba.

Kafin su isa Asibitin har Hidaya ta suma,ta sank'ame a k'irjin Hamza,shi kam saboda kuka har idanuwan sa sun kumbura,Umma ke lallashin sa tana ta zabga addu'a.

Da gudu likitocin suka amshi Hidaya da ke sume,aka fara bata taimakon gaggawa domin ta farfad'o,Hamza da Umma na tsaye cike da tararrabi,kansa ciwo yake tamkar ya tsage,damuwa tayi masa yawa,ga damuwar Hidaya ga damuwar Khaleel….

Sai wajen goman dare tukun likita yayi musu bayanin ana buk'atar jini za a sakawa Hidaya saboda jinin ta ya fara k'onewa,a lokacin ma likitan fad'a ya dinga yi musu kan an dad'e ba a bawa Hidayan maganin ta na sikila ba,to su gabad'aya ma sun manta Hidaya na da wani ciwo na sikila,saboda bai tab'a tashi ba sai yau,Umma dai ta rasa bakin magana,balle Hamza da yake cikin tsananin tashin hankali.

Yana jin jiri sosai amma haka yace a gwada jininsa a d'iba a sakawa Hidaya idan zai yiwu,haka aka yi kuwa,aka gwada Sai a ka ga yayi dai dai,Umma ta fita Harabar asibitin gun masu siye da siyarwa ta siyo masa Maltina da madara,da farko k'in sha yayi,sai da Umma ta rufe shi da fad'a sannan ya karb'a ya runtse ido ya sha,d'aci kawai yake ji a bakinsa.

An d'ebi jinin Hamza da gaggawa sannan aka jonawa Hidaya da ke ta faman bacci,wajen sha d'aya da rabi na dare Umma ta cewa Hamza.

"Ka koma gida ka kwanta kar abar Gidan ba kowa,ni sai na kwana da ita,gobe sai ka kawo mana abubuwan da za mu buk'ata da wurwuri kaji"

Hamza da ke rik'e da hannun Hidaya ya kalli Umma cike da damuwa yace.

"Umma ki barni na kwana da ita mana,idan ma na ta fi Gidan hankalina yana nan ba zai kwanta ba wallahi"

Umma tayi murmushi tace.

"Hamza jinyar mace ai sai mace,ka daure ka koma,Idan ka kasa baccin ka tashi kai ta salloli ka nemawa Hidaya sauk'in wannan lalura da duk wani mai fama da ita"

Ya mik'e ba don ya so ba,ya sunkuya yana kallon Hidaya da ta zabge lokaci guda kamar wadda ta shekara tana ciwo,addu'a yayi mata sosai hawaye na ciko idanuwan sa,a hankali ya mik'e yana shirin fita sai ga likita ya kawo takardar magungunan da ake buk'ata zuwa safiya,Hamza ya karb'a ya cewa Umma zai biya pharmacy ya siyo da safe ya tawo da su,yayi wa Umma sallama ya fice yana waiwayen Hidaya da ke baccin wahala.

Yana fita bakin Asibitin yaga wani pharmacy daga gefe suna shirin kullewa,da hanzari ya nufe su ya roki'i alfarmar su duba katin da aka bashi,me pharmacy d'in ganin Hamza a rud'e sai ya karb'a ya duba,magunguna ne guda bakwai,yace wa Hamza suna da guda biyar babu guda biyu,sai dai idan guda biyar d'in za a bashi in yaso yaje wani gun ya siyo guda biyun.

Hamza ya nemi ya san kud'in guda biyar d'in ,a kayi lissafi Naira dubu talatin da bakwai,ya karb'i katin yace masa zai zo da safe ya kawo kud'in sai ya karb'i maganin.

Ya jima kafin ya samu abin hawa saboda dare ya fara sosai,lokacin da yaje unguwar su tsit kowane gida a rufe,amma da yake akwai wutar NEPA ko ina da haske tarwai,bud'e Gidan yayi ya shiga sannan ya kulle.

Kai tsaye ya nufi d'akin sa duk jikinsa babu k'wari,abin duniya duk ya taru yayi masa yawa,babu abin da ke d'aga masa hankali idan ya tuna bashi da wasu kud'i sosai,dubu ashirin ce ta rage masa cikin account d'in sa,gashi baya son takurawa Umma ,D'an jarin nata ba wani yawa ne da shi ba,kuma duk a ciki ake hidimar Gidan,Umma bata yarda yayi wani abin da kansa,haka ya kwanta cikin tunane tunanen yadda zai samu kud'in maganin Hidaya,da yaga ya kasa bacci tilas ya mik'e ya fad'a toilet ya d'auro alwala ya fito ya kalli gabas.

Nafiloli ya dinga zabgawa,bayan ya idar ya dinga sharara addu'a,ya d'auki tsawon lokaci kafin ya D'an jingina yana lumshe idanuwan sa da carbi a hannunsa yana ja,shi dai bai wani samu bacci ba a Daren,hankalin sa kaf yana Asibiti tunanin Umma da Hidaya.

Yana idar da sallar Asuba a masallaci ya dawo gida da zummar harhad'a kayan tafiya asibiti,yana shiga d'akin sa yaji rurin wayarsa ,shi gabad'aya ma ya manta da ita,kamar ya share sai kuma ya isa ya d'auka yana dubawa.

Sunan da ya gani ya matuk'ar girgiza Zuciyar sa…take Hawaye ya ciko idanuwan sa a lokacin da ya kai wayar kunnen sa domin amsa kiran………!


Comments
Share
Vote
Pls


*TYPING*📲

✌️💔 *GARKUWA BIYU* 💔✌️

*TARE DA ALK'ALAMIN* ✍️

HASSANA D'AN LARABAWA

*MARUBUCIYAR* 👇

SANADIN HOTO
HASSANA DA HUSSAINA
CIN AMANAR RUHI
BAHAGON LAYI
BAHAGON LAYI (SABON SALO)

*DA KUMA*

GARKUWA BIYU


*BABI NA TALATIN DA D'AYA DA NA TALATIN DA BIYU*


WATTPAD:Hassana3333


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️

🖊 *PEN WRITERS ASSOCIATION*🖊️


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️


______________________________________

*~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~*


_____________________________________


https://www.facebook.com/groups/1533639276725285/


Wata sassanyar ajiyar zuciya ya sauke jin muryar Khaleel na Sallama cikin sanyin murya,kasa amsawa yayi saboda hawayen da ya ratso fuskar sa,jikinsa har wata rawa rawa ya fara,daga can b'angaren Khallel yaji Hamza bai amsa masa sallamar sa ba,hakan ya sa yayi magana a hankali cikin k'ank'anuwar murya tamkar ta marasa lafiya.

"Aboki……kana tare da ni…..?

Hamza ya zame ya zauna bakin gado yana numfarfashi,duk da yaji matuk'ar farincikin jin muryar Khaleel amma cike yake da jin haushin k'in Neman sa da yayi,kuma shi ma idan ya nemeshi baya samun sa,da k'yar Hamza ya sauke numfashi yayi magana murya na rawa.

" Khaleel…! fushi nake da kai Khaleel"

Cikin rauni Khaleel yayi saurin tare shi da cewa.

"Bani da lafiya ne Aboki…..Kayi hak'uri..!?

Hamza ya lumshe idanu k'irjinsa na bugawa saboda tunowa da Hidaya da yayi,cikin alamun tausayawa yace.

" Laifinka ya k'aru kenan Khaleel,kayi fushi da ni kak'i fuskanta ta tsawon lokaci,kayi rashin lafiya ta tsawon kwanaki amma baka sanar da ni ba?ko da bana tare da kai ai zan iya yi maka addu'a Khaleel,me yasa hakan?ka san irin tashin hankalin da na shiga kuwa?ka san irin yadda zuciyata tayi rauni akan tunanin halin da kake ciki kuwa?ban ji dad'in abin da kayi min ba ko kad'an Khaleel, zuciyata tana fushi da kai "

Khaleel ya marairaice murya ya fara bayani .


"Tsaya kaji Aboki,wallahi a ranar da muka yi sa'insa ni da kai akan siyen mota,ka san na kashe wayar cike da b'acin rai saboda ka k'i yarda,to bayan na kashe ne naji k'irjina yana zafi sosai saboda b'acin rai,shine fa ciwon Zuciya na ya motsa,sai James ne da muke zaune gida d'aya ya kwashe ni muka tafi Hospital saboda na fara fita hayyacina,kwana na biyu ban san in da kaina yake ba,a lokacin ne aka nemi daddy na a waya aka sanar da shi yazo hankalin sa a tashe,a nan daddy ya nemi sanin abin da ya tayar min da ciwon,shine James yake fad'a masa cewar bai sani ba,shi dai kawai ya ji sanda nake waya,daga nan kuma sai tari na da nishi na ya jiyo,shine ya kawo ni asibiti,a lokacin daddy ya karb'i wayata ya kasheta ma gabad'aya ya b'oyeta,shine dalilin da ko ka kira ba zaka samu ba,kuma da na dawo hayyacina babu yanda banyi da daddy ya bani na kira ka ba amma ya k'i,wai sai na warware gabad'aya,har kuka nayi masa saboda na san na barka cikin damuwa ba ka jin murya ta,amma daddy ya k'i fuskanta ta,yau kwanana goma da fitowa daga Hospital amma daddy bai koma Nigeria ba sai yau,yana tare dani yana lura da ni har na murmure,yau d'in ma Anty Kubra ce ta ishe shi da waya shine ya tafi,shine fa na samu na kira ka yanzu…ka ji abin da ya faru Aboki,don Allah kayi hak'uri…….

Hamza ya sauke nannauyar ajiyar zuciya saboda jin bayanin Khaleel,tausayin sa ya kamashi sosai,wannan ciwo yana wahalar da Khaleel,Allah ya yaye masa,Hamza yayi magana cikin nuna kulawa.

"Ayya Khaleel ban sani ba ne,nayi kiranka sau ba adadi bana samun ka,nayi tunanin ko har yanzu fushi kake dani akan maganar shiyasa kak'i kulani,ni zan baka hak'uri Khaleel tunda b'acin ran da na saka ka a ciki ne har ciwon ka ya tashi….kayi min Afuwa ka yafe min Khaleel"

Khaleel yayi murmushi,ya mak'e wuya kamar yana gaban Hamza,yayi magana cikin shagwab'a.

"Ni ba zan hak'ura ba sai ka yarda da wata magana da zan fad'a maka yanzu…

Da sauri Hamza yace.

" Na amince Khaleel…idan har za ta sa ka yafe min laifina"

Khaleel ya D'an yi tsalle ganin ya ci gari ,yace.

"Maganar siyen mota tilas ka amince da ita,sannan shagon nan na Gidan ku da k'ofar sa ke kallon waje za a zo a gyara shi a zuba kantoci,na saro maka wayoyi na zamani sai ka dinga siyarwa,idan kaje lectures ka dawo sai ka bud'e ka zauna,lokacin da baka nan ka samu yaro ya dinga zauna maka,y'an kud'ad'en da zaka dinga samu za su to she maka wata kafar,bana son zaman ka haka babu sana'ar yi Aboki,wad'annan Abubuwa biyun idan ka amince da su to ni kuma zan yafe maka dalilin su"


Tunda ya fara magana Hamza ke jinjina lamarin ,da ya san abin da zai ce kenan da baiyi alk'awari ba sam,yanzu ya zaiyi kenan?hidimar ta yi yawa,Khaleel baya tausayawa kud'i idan yaso kashewa,ko Dan yaga Allah ya hore masa su?domin ko iya kadarorin da mahaifiyar sa ta mallaka masa kafin ta rasu suna da yawa,har da kamfanoni,bayan ta rasu kuma ya samu gado mai d'umbun yawa…..

Jin Hamza yayi shiru yasa Khaleel ya sake magana.

"Karfa kace min ah ah Aboki,domin kayi alk'awari ya kamata ka cika,Idan kuma kana son kuma b'ata min rai ne na koma gadon Asibiti to shikenan "

Hamza ya sauke ajiyar zuciya, babu abin da yake tsoro irin daddyn Khaleel yaji wannan hidimar da zai masa,tunda ba k'aunar abotar su yake ba,haka nan ga Umma nan a gefe, ita ma ya san ba zata amince ba,hakan yasa yace da Khaleel.

"Ba k'i nayi ba Khaleel, amma Umma bai zata amince ba,hidimar tayi yawa Khaleel…sannan ka tuna daddy ma…

Ya katse shi da sauri.

" Babu abin da zan maka yayi yawa a rayuwa,Hamza baka san yadda kake da k'ima a tare da ni ba ne,ba kuma zaka gane ba,ni dai na san ina sonka Hamza,zuciyata kullum k'ara k'aunarka take,kai Aboki ne nagari,irin Wanda manzon Allah (S A W)ya kwad'aitar da mu akan mu samu,batun Umma ka jingine shi gefe,zan mata bayani da kaina yadda zata fuskanceni…ko ba kai ba ni na riga na saba da kyauta Aboki,in dai ina da shi nafi son nai ta bayarwa,hakan yana sa wa ina jin dad'i idan ina taimakawa Wanda bashi da shi,sannan ka k'yale batun daddy ,ba kud'in sa nake d'iba ina amfani da su ba,nawa ne,halal d'ina ne Aboki,ra'ayin daddy na k'in talakawa daban,ra'ayi na na son taimako daban,shi ma daddyn ina nan ina ta addu'a akan Allah ya shiryar da Zuciyar sa ya gane dai dai"

Hamza yayi shiru har ya kammala jin bayanin Khaleel, sannan yayi magana.

"Duk abin da ka fad'a Hakane Khaleel,na kuma gode da nuna k'auna,yadda kake jina a ranka haka nake jin ka a raina,fiye ma da hakan,na kuma yarda da abin da kake so,sai dai a bisa wani sharad'i guda d'aya"

"Menene sharad'in..?Khaleel ya tambaya.

Hamza yace.

" Na yarda da batun bud'e shago,amma duk ribar da za a dinga samu sai dai mu raba biyu,d'aya taka d'aya tawa,sannan kayan ciki da ka zuba suna nan a matsayin naka ba mallaka ta ba,kawai zan kasance kamar yaron gun mai lura da shi,sannan batun mota ka ajiyeshi gefe,ka sauya min da mashin,ban isa hawa mota yanzu ba,komai da limit d'in sa Khaleel, idan aka ganni da mota yanzu idanu za su yi yawa a kaina,tunda an san talaka ne ni,don Allah ka fahimce ni ka yarda dani da maganata"

Khaleel ya sauke numfashi yace.

"Na ji na amince Aboki tunda haka kake so…

A lokacin Hamza ya d'aga kai ya dubi Agogo,yaga lokaci ya ja sosai, ya san Umma nan can na jiran shi,ga maganin Hidaya da zai siya ya kai,da sauri yace da Khaleel.


" Khaleel muyi sallama haka,Umma na can asibiti ita da Hidaya suna jirana…"bai san lokacin da ya furta hakan ba.

Cikin mamaki Khaleel yace.

"Umma na asibiti?waye ba lafiya?wacece Hidaya Aboki?

Ya jero masa tambayoyi,sai lokacin Hamza ya tuna b'aranb'aramar da yayi,domin kwata kwata Khaleel bai san da maganar Hidaya ba,bai kuma da niyyar fad'a masa a tsukin har sai wani lokaci na daban,amma yanzu tilas ya sanar da shi komai,tunda bakinsa yayi azarb'ab'in furtawa.

Cikin wani irin yanayi Hamza ya fayyacewa Khaleel abubuwan da ya sani game da Hidaya tun daga ranar da ya fara ganinta har yau,da yake Khaleel yana da matuk'ar tausayi sai gashi yana hawayen tausayin Hidaya,ji yake a ransa ina ma yaga Hidayan da idanuwan sa,Aikuwa tilas insha Allah zai taimaki Hidaya,zai tsaya a kan al'amuranta ya zama GARKUWAR ta,zai to she mata duk wata k'ofa da zata wargaza rayuwar ta,haka kawai yaji a ransa yana son Hidaya,duk da bai tab'a ganin ta ba,Lalurar Hidaya ta tab'a ransa,saboda yana ganin yadda masu ciwon sikila suke shan wahala,nan Khaleel ya rok'i Hamza a kan idan yaje asibiti yayi masa flashing,shi kuma zai kira domin su gaisa da Umma,sannan yayi wa Hidaya ya jiki.

A haka suka yi sallama duk zuciyoyin su ba dad'i,sannan Hamza ya mik'e ya fara tattara abubuwan da ya san zai tafi da su asibiti…..


*****************


K'arfe Bakwai da y'an mintuna na safe mota ta sauke shi bakin Asibitin,ya waiwaya yana kallon pharmacy d'in da zai siyi maganin Hidaya,sai ya ganshi a kulle basu bud'e ba,ya fito da ledar da ya zubo kayayyaki da flask d'in Ruwan zafi, sannan ya sallami mai adaidaita sahun,da hanzari ya d'ebi kayan zuwa cikin Asibitin.

Ya tura k'ofar a hankali da sallama, Umma na zaune gefen gadon tana mammatsawa Hidaya k'afafuwanta da suke mata ciwo,Hidayan na kwance hankalin ta a kan k'ofar shigowa,tana ganin Hamza ne ta saki wani k'ayataccen murmushi da ya fito da asalin kyawun fuskar ta,cikin dasasshiyar murya ta marasa lafiya tayi magana tana k'ok'arin mik'ewa zaune.

"Oyoyo Ya Hamza na….."

Wani farinciki ya mamaye ruhin sa ganin Hidaya ta fara warwarewa,da sauri ya k'arasa ya ajiye kayan hannun sa,ya nufi bakin gadon ya sunkuya yana kallonta fuskarsa cike da murmushi yace.

"Sannu K'anwata…ya jikin na ki?

Ta rik'o hannunsa tana Murmushi tace.

" Da sauk'i Ya Hamza,ina ta Neman ka ban ganka ba,Umma tace min kana gida"

Ya amsa yana damk'e siririn hannun ta a na sa hannun.

"Eh ina can tunaninki ya ishe ni,Ashe har kin fara warwarewa?Alhamdulillah Addu'a tayi aiki kenan,to yanzu menene yake miki ciwo?" Ya zarce da tambayarta.

Ta amsa tana D'an yamutsa fuska..

"K'afata ne Ya Hamza,kamar ana tsira min allura,amma yanzu Umma ta na matsa min ina jin dad'i"

Ya girgiza kai cike da tausayi yana jera mata sannu ba adadi,ita kam sai amsawa take tana kallonsa,zuwan sa yanzu taji dad'in ganin sa,tunda ta farka take son ganin sa daman,ita dai tana son Ya Hamzan ta.

Waiwayawa yayi yana duban Umma da ke had'awa Hidaya tea a k'aramin Kofi,sai lokacin ya tuna Ashe bai gaisheta ba,duk hankalin sa ya tafi kan Hidaya,cikin kunya ya soma gaishe ta,ta yi murmushi tana cewa.

"Sai yanzu ka tuna da ni Hamza..?

Ya Sosa k'eya yana sunkuyar da kai,Umma ta cigaba da juya tea d'in yayin da Hidaya ke cewa Hamza ya cigaba da mammatsa mata k'afarta,haka ya zauna a gefenta ya kai Hannu yana mammatsa mata a hankali,sosai take jin dad'in hakan har da lumshe idanuwa.

Umma ce ta taimaka mata ta yi brush,sannan Hamza ya fara bata tea d'in da k'aramin cokali,tana sha tana shagwab'a shi kam sai biye mata yake,wai ita ya tsefe mata kanta sai Umma ta yi mata kitso,kan ya ishe ta haka,da k'yar ya lallab'ata akan ta bari su koma gida tunda yanzu bata da lafiya.

Yana kammala bata yace da Umma bari ya fita ya siyo maganin,ita kam Hidaya saboda son yawo wai zata rakashi,yayi dariya Yana cewa .

" Da wace k'afar za ki rakani?

Umma da yake ta san akwai kud'i a hannun sa sai bata tambaye shi yadda zai siyo maganin ba,kuma bata san maganin Yana da tsada ba,haka ya fita cikin tunanin yadda zai siyi maganin,dubu Ashirin d'in acc d'in sa ba zata isa komai ba,amma ya san Allah ba zai kunyata shi ba,ya rok'eshi ya hore masa,kuma ya san hanyoyin Allah suna da d'umbun yawa.

Babu abin da ya fad'o a ransa irin yayi maza yaje ya saida wayar sa,in yaso ko k'arama sai ya siya,hakan zai sa ya samu kud'in maganin.

Yana fitowa bakin Asibitin ya kalli pharmacy d'in ya ganshi a bud'e sun fito,Yana shirin tsaida mota domin tafiya kasuwar sayar da wayoyi kawai yaji wayar sa ta yi k'ara alamar shigowar sak'o,a hankali ya zaro ta daga aljihun sa ya duba,zaro idanu yayi k'irjinsa na bugawa saboda ganin alert d'in dubu d'ari cas an tura masa cikin acc d'in sa……!


Comments
Share
Vote
Pls


*TYPING*📲

✌️💔 *GARKUWA BIYU* 💔✌️

*TARE DA ALK'ALAMIN* ✍️

HASSANA D'AN LARABAWA

*MARUBUCIYAR* 👇

SANADIN HOTO
HASSANA DA HUSSAINA
CIN AMANAR RUHI
BAHAGON LAYI
BAHAGON LAYI (SABON SALO)

*DA KUMA*

GARKUWA BIYU


*BABI NA TALATIN DA UKU DA NA TALATIN DA HUD'U*


WATTPAD:Hassana3333


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️

🖊 *PEN WRITERS ASSOCIATION*🖊️


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️


______________________________________

*~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~*


_____________________________________


https://www.facebook.com/groups/1533639276725285/


Lumshe idanuwa yayi yana jin wani sanyi a Zuciyar sa,sak'on daga Khaleel yake,kamar ya san cikin buk'atar kud'i yake,godiya yayi wa Allah yana ta fad'in "Alhamdulillah" har bai san iya adadin da ya fad'a ba.

Da sauri ya nufi pharmacy d'in,me wajen ya gane shi,nan da nan ya tare shi cikin fara'a suka gaisa,Hamza yace yazo ne akan maganar maganin nan,sai dai bashi da kud'i Cash a Hannu,shin zai iya yi musu transfer ta bank?

Mutumin yace ba damuwa zai iya,ya bashi acc number nan da nan Hamza yayi masa transfer yana daga tsaye,mutumin yana jin shigar kud'in cikin acc number d'in sa ya had'awa Hamza maganin ya bashi,sai lokacin Hamza ke tambayar sa in da zai samu ragowar maganin,mutumin yace ya shiga cikin asibitin akwai wajen siyar da magunguna ya duba ba zai rasa ba.

Hamza yayi masa godiya sosai ya fito rik'e da ledar maganin,ya tsallaka titi ya shige cikin asibitin,bai sha wahala wajen gane pharmacy d'in asibitin ba,ya D'an tarar da layi kad'an,ya jira aka sallame su sannan ya mik'a na sa katin,cikin ikon Allah aka ce akwai maganin da yake ne ma guda biyun,nan ma ya rok'i alfarmar yayi musu transfer suka ce eh zai iya babu komai,nan ya tura musu kud'in dubu takwas da d'ari uku,aka bashi maganin ya had'a da na hannunsa ya fito .

Sanda ya koma d'akin Umma har ta taimakawa Hidaya tayi wanka ta sauya kaya,sai yaga tayi fari sai dai ta rame,ya dubeta yaga duk k'asusuwa a wuyan ta yace.

"An ya Hidaya za ki yi k'iba kuwa?irin wannan rama haka?"

Umma tace.

"Hmmmm!irin lalurar su ai bata barin su k'iba,sai dai su murmure"

Ita kam Hidaya murmushi ta yi tana shafa wuyan ta,ya mik'awa Umma ledar magungunan ,ta karb'a ta duba tana cewa.

"Duka an samu kenan?

" Eh Umma an samu duka,bari nayi wa likitan magana ko?"

Umma tace.

"To babu laifi,Allah yayi maka Albarka Hamza"

"Ameen Umma na"ya amsa yana k'ok'arin ficewa daga d'akin yaji muryar Hidaya ma cewa.

" Allah sarki Ya Hamza,duk ka kashe kud'in ka wajen siyo min magani ko?insha Allahu zan siyi banki idan na samu kud'i in ta tara maka kana amfani da su"

Murmushi kawai yayi ya fice bai ce komai ba,yana jin Umma nan dariya tana fad'in.

"Ah lallai su Hidaya Ashe za a tara kud'i da yawa".


************


Lokacin da likitan yazo ya dubata sannan ya bata magungunan tasha,sai da Hamza ya dinga lallab'ata sannan ta karb'a har da Kuka,saboda Hidaya bata son magani ko kad'an,likitan yana ta tsokanar ta yana dariya.

Nan da nan Hidaya ta ware sosai kamar ba ita ce ta lallank'washe jiya ba,likitan ya dinga bawa su Umma shawarwari akan yadda za su kula da lafiyar Hidaya,da yadda ciwon yake,ya fad'a musu a dinga bawa Hidaya kulawa sosai,saboda ciwon ta yana buk'atar kulawa,ya dinga fad'a musu yadda masu ciwon sikila suke jin azaba a jikinsu,yace musu shi kansa yana da sikila,kuma ba k'aramar wahala ya sha ba,yana kan sha ma,yace saboda hakan yayi karatun likita b'angaren cutar domin ya taimakawa masu ciwon,saboda duk yadda za a fasalta maka yadda suke shan wahala ba zaka gane ba in dai ba cutar gareka ba.

Nan Umma da Hamza suka sake tausayawa Hidaya da duk wani mai fama da lalurar,suka yiwa likitan godiya sosai da sosai,a ranar haka Hamza ya shashance a asibitin ko makaranta bai jeba,gashi karatu ya d'au zafi sun kusa fara exam.

Yana ta lallab'a Hidaya sai abin da take so yake mata,har da su tatsuniya sai k'yalk'yala dariya take yi,Umma dai na kallon su tana jin farinciki a Zuciyar ta ganin yadda suke kulawa da junan su,sai lokacin ya tuna da Khaleel yace idan yazo asibitin ya kira shi.

Da sauri ya gyara zama yana k'ok'arin zaro wayar sa cikin Aljihun wandon sa yace.

"Subhanallah,Umma nayi mantuwa fa,d'azu mun yi magana da Khaleel har yace min idan nazo asibitin na kira shi za ku yi magana ke da shi,sannan ya duba jikin Hidaya,shaf na manta sai yanzu,Ashe shirun da naji daga gareshi bashi da lafiya ne Umma,ciwon sa ne ya tashi wallahi"


Umma ta jinjina cike da jimami take nemar wa Khaleel sauk'i a wajen Allah,Hamza yayi masa flashing,cikin minti uku sai ga Khaleel ya kira Video call,Hamza ya amsa sai ga Khaleel zaune akan wata farar kujera a bakin beach,k'afafun sa zube cikin ruwan ,sanye yake da k'ananan kaya da suka yi masa masifar kyau tamkar D'an turawa,yayi haske sosai ga kwantacciyar suma da saje da ya k'a wata fuskar sa,fuskar sa d'auke da wadataccen murmushin da ya k'ara masa kyau,suka haske juna da murmushi shi da Hamza,Khaleel ya D'an harari Hamza,cikin muryar sa mai dad'i yace.

"Ni fa ba da kai zan yi magana ba Aboki,ka fara bani Umman mu naga mahaifiyata,daga nan sai na gaisa da K'anwar mu Hidaya"

Hamza yayi murmushi ya D'an tab'e baki yace.

"To ai ga Umman a kusa dani ….in kuma ka cika min baki sai na hanaka magana da ita malam"

"Afuwan Aboki…don Allah bani Umman mu,na jima ban ganta ba balle naji muryar ta"

Umma na daga gefe tana ta murmushi tana jin maganar Khaleel,Hamza ya kai mata wayar ya zauna ya jingina da kafad'ar ta ,Umma ta kalli fuskar wayar idanuwan ta suka yi arba da Khaleel,wani farinciki ya kamata,Khaleel ya harari Hamza cikin wasa yace.

"To ka kauce mana,ko a gabanka zan gaisa da Uwa ta?

Umma tayi dariya yayin da Hamza yayi masa gwalo ya matsa gun Hidaya,shi kuma Khaleel ya fara gaida Umma cikin tsantsar nuna kulawa da biyayya.

Umma ta amsa tana yi masa ya jiki,har tana k'orafin tsananin ramar da taga yayi,yayi murmushi kawai,a lokacin ya kwantar da murya ya fara tsara Umma da maganganu masu dad'i akan k'udurin sa akan Hamza,babu yadda Umma za ta yi saboda kwarjinin da Khaleel yayi mata tunda suna kallon juna,gashi sai magiya yake surfa mata,tilas Umma tace ta amince,sannan ta dinga yi masa godiya,amma tayi k'orafin ya dinga rage wasu abubuwan Hidimar tayi yawa,Khaleel farinciki tamkar ya zuba ruwa a k'asa ya sha,ya dinga godiya,a lokacin yake tambayar Umma jikin Hidaya,Umma tace da sauk'i,tana mamakin Ashe har Hamza ya bawa Khaleel Labarin Hidaya kenan?

Sun gama magana da Umma sannan Hamza ya karb'i wayar,suka kalli juna da murmushi akan fuskokin su,Khaleel na tsokanarsa wai ya yaga ya k'ara kyau?me Umma take bashi yana ci?Hamza yayi dariya yace" kai da kake k'asar turawa ai Kaine kayi kyau Khaleel, kalli fatarka fa,ni kuwa ina Nigeria jaga jaga muna fama,Khaleel ke k'orafin ai shi a dole yake zaune England, Dan dai babu yarda zai yi ne,amma yafi son zaman k'asar sa Nigeria,Nigerian ma kuma Kaduna kusa da Hamzan,domin baya son zaman Abuja gurin daddyn sa,shi dai Hamza dariya kawai yayi.

A lokacin Khaleel ke cewa Hamza ya bashi Hidaya ya ganta su gaisa,kuma yayi mata sannu,a hankali Hamza ya matsa kusa da Hidaya ya kalleta yana ce mata.

"Hidaya ga Uncle Khaleel za ku yi magana kinji"

Fuskarta na kallon Hamza tayi murmushi cikin zumud'i tace.

"Da gaske ya Hamza?don Allah da gaske ka ke?

Ya jijjiga mata kai yace.

" Eh da gaske!kin ganshi ma fa yana kallonki"

Duk tattaunawar da ake tsakanin Hidaya da Hamza khaleel na kallon su yana murmushi,a lokacin ne Hidaya ta juya a hanzarce ta kalli wayar cikin slow,idanuwan Khaleel da na Hidaya suka yi arba da juna….wata irin fad'uwar gaba Khaleel yaji wadda bai tab'a jin irinta a fad'in duniyar sa ba a lokacin da idanuwan sa suka sark'afe cikin na Hidaya,wani Abu yaji yana masa yawo a jikinsa yana zagayawa jini da tsokarsa yana huda shi,bai san ko menene ba!amma tabbas a lokaci guda yaji Hidaya ta gama zagaye jinin jikin sa.

Yadda yake kallon ta haka take kallonsa tana doka masa murmushi,tayi maza ta juya ta kalli Hamza tace.

"Wannan ne Uncle Khaleel Ya Hamza?

Gyad'a mata kai yayi yana murmushi, Khaleel kam wani sanyi sanyi yake ji a jikin sa,cikin wata irin murya da bai san yana da ita ba ya D'an d'agawa Hidaya yatsun sa guda biyu yace.

" Hi!K'anwar mu ya kike? Ya jikin na ki?

Tayi dariya cikin k'ank'anuwar murya tace.

"Jikina da sauk'i Uncle Khaleel, Ya Hamza yana ta bani Labarin ka ina so na ganka,kullum ina cewa ya nuna min hoton ka sai ya k'i,yau dai gashi na ganka ko?

Ya lumshe idanu yana kad'an kai yace.

" Aikuwa yau Hidaya taga Uncle d'in ta,shi kam Ya Hamza sai mun hukunta shi tunda ya hana Hidaya ganin Uncle Khaleel ko?"

Tayi dariya ta kalli Hamza da ke ta murmushi tace.

"Ah ah a k'yaleshi,bana son a tab'a min Ya Hamza na fa"

Hamza da khaleel suka yi dariya,suka cigaba da hira su uku,Umma kam toilet ta shige tana wanka,sai da Hidaya ta fara Hamma tana jin barci har tana langab'ewa kafad'ar Hamza,sannan Khaleel ya hak'ura yace zai sake kira da daddare suyi hira,yayi wa Hidaya fatan samun sauk'i,lokacin Hamza ya fara yi masa godiya kan kud'in da ya turo masa d'azu,Khaleel bai tsaya jin godiyar ba ya kashe wayar sa saboda baya son godiya.

Hidaya kam har tayi bacci,Umma ta fito daga toilet a dai dai lokacin da Hamza ke k'ok'arin ficewa daga d'akin ta ambaci sunan sa cikin wata irin murya,da hanzari ya juyo ya dubeta yana amsawa,yanayin da ya gani a fuskarta yasa k'irjinsa ya tsananta bugawa……..!


Comments
Share
Vote
Pls


*TYPING*📲

✌️💔 *GARKUWA BIYU* 💔✌️

*TARE DA ALK'ALAMIN* ✍️

HASSANA D'AN LARABAWA

*MARUBUCIYAR* 👇

SANADIN HOTO
HASSANA DA HUSSAINA
CIN AMANAR RUHI
BAHAGON LAYI
BAHAGON LAYI (SABON SALO)

*DA KUMA*

GARKUWA BIYU


*BABI NA TALATIN DA BIYAR DA NA TALATIN DA SHIDA*


WATTPAD:Hassana3333


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️

🖊 *PEN WRITERS ASSOCIATION*🖊️


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️


______________________________________

*~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~*


_____________________________________


https://www.facebook.com/groups/1533639276725285/


Jikinsa a sanyaye ya juyo ya dawo d'akin,Umma ta nemi gefen gado ta zauna,shi kam tsugunawa yayi a gabanta ya rik'o hannun ta yana kallon fuskarta da babu walwala ko kad'an,hankalin sa a tashe yayi magana.

"Gani Umma na…."

Ta k'ura masa ido ta ambaci sunan sa.

"HAMZA…

" Na'am Umman Hamza"ya amsa mata.

Ta sauke numfashi ta fara magana cikin wani yanayi.

"Khaleel ya sanar da ni abubuwan da kuka tattauna,amma me yasa baka fad'a min da kanka ba?me yasa ka saka shi ya gaya min da bakinsa?saboda ka san zan ji kunyar sa har na amince masa ko?to ai shikenan Hamza ka yi nasara,na amince masa ne saboda kwarjinin da yayi min,gashi sai magiya yake min,amma gaskiya hankalina bai gama kwanciya da hakan ba,mutane ba za su dubi domin Allah yake mana Hidima ba,za su dubi mune kwad'ayayyu da muka nace masa har yake kashe mana kud'ad'e da hidindimu,Hamza wannan rayuwar ta sauya,kiwon mutum ake ba dabba ba,ina tsoron kar a kaiwa Mahaifin sa gulmar hidimar da yake mana,kasan ba sonmu yake ba,babu abin da ya tsana irin alak'ar ka da D'an sa,ni tun farko ban so har ka amsa masa cewar ka amince da abin da yace ba Hamza,zuciyata tana kokonto akan hakan,bana son abin da zai zo ya tab'a mutuncin mu muna zaune lafiya Hamza"


Ya rud'e ganin damuwar Umma,da sauri ya sake damk'e hannun ta ya d'ora kansa kan kafad'ar ta ya fara magana a hankali cikin ladabi.

"Ki gafarceni Umma,wallahi na rasa yadda zan yi da nacin Khaleel ne shiyasa har na amsa,kuma shi yace zai gaya miki da kansa ba ni na yarje masa hakan ba,amma ni ma ba da son raina ba,kuma dalilin da yasa na amince masa saboda kar na kuma saka masa damuwa a ransa har ciwon sa ya tashi ne,kin san Khaleel da saka Abu a rai Umma,amma don girman Allah ki yafe min idan na b'ata miki rai,bana son ganinki cikin damuwa ko kad'an Umma,kuma insha Allahu babu abin da zai biyo baya sai alkairi"

Umma ta yi shiru ba tace komai ba,ganin yadda Hamza ya shiga damuwa har da k'wallarsa yana ta rok'onta Afuwa sai taji tausayin sa,tayi masa murmushi ta shafa kansa tace.

"Shikenan babu komai ya wuce,Allah ya tabbatar da alkairi"

"Ameen Umma na,Na gode Allah ya k'ara miki Lafiya da Nisan kwana mai amfani" ya fad'a cike da murna.


*********************


Kwanan Hidaya biyu a asibitin aka sallameta,cikin ikon Allah ta warware sosai,daman shi ciwon sikila haka yake,idan ya motsa mutum kamar ba zai rai ba,amma idan ya lafa sai kaga kamar mutum bai tab'a ciwon ba ma(Allah ka k'ara mana lafiya).

A wad'annan kwanakin Hidaya ta yi mugun Sabo da Khaleel ta waya,kusan kullum sai ya kira Hamza ko kuma video call domin su sha hira shi da Hidaya da Hamzan,sai Khaleel ya sake shiga Zuciyar Hamza sosai saboda nunawa Hidaya k'auna da yake yi…


Da aka sallamosu haka Gidan Umma kullum a cike da masu zuwa duba Hidaya,y'an unguwar sun yi matuk'ar Sabo da ita,k'awayen ta su Hansa'u kuwa suna manne da ita,hatta y'an uwan Umma daga kano sai da suka zo duba Hidaya.

Hidaya ta cigaba da zuwa makaranta,shak'uwar ta da Hamza na k'ara hab'aka,bata da abokin shawara sai shi,bata da wani makusanci da ya zarce Hamza,duk abin da ya shige mata duhu Hamza take fad'awa,ko Umma bata san wasu abubuwan game da Hidaya ba kamar yadda Hamza ya sani,Hamza shine sirrin Hidaya.


Cikin ikon Allah tuni har an kammala gyaran shagon yayi fes da shi,an zuba wayoyi da charger da condom da earpiece masu tsananin kyau da sauk'i,ga kuma gallelen mashin d'in Hamza Sabo dal na zamani,lokacin da aka kawo mashin d'in kamar Hidaya zata shid'e don murna,haka suka wuni yana zagaya unguwa da ita akan mashin,Hidaya an samu abin hawa,ko makaranta zata sai tace sai ya kaita,duk da makarantar babu nisa,haka zata haye baya ya kaita ya direta,in yana da lecture ya wuce makaranta,idan babu kuma ya dawo gida ya bud'e shago yayi zaman sa.

Sosai ciniki ya bud'e masa sai Hamdala,har da generator Khaleel ya siya masa,yana kunnawa ana kawo chaji sosai a wajen,da yake Hamza na mutane ne,akwai kuma abokan sa guda biyu y'an mak'otan su,Faisal da Anas,idan baya nan sune suke jire masa shagon sa.


Wata uku da bud'e shagon wata ranar lahadi bashi da lecture,Hidaya ma babu makarantar boko,misalin k'arfe sha d'aya na safe bayan ta kammala taya Umma aikin gida tayi wakan ta fes da kwalliya,ta k'ara girma kamar ba ita ba,ta dubi Umma da ke zaune parlour tana hutawa tace.

"Umma ina Ya Hamza ne?

Umma tayi Hamma saboda gajiya tace.

" Yana shago,bai jima da fita ba kina wanka"

Hijabin ta ta d'auka ta saka tayi hanyar fita tana cewa.

"Umma bari naje na goggoge masa kantocin shagon nan,naga jiya duk sunyi k'ura da yawa"

Umma ta d'aga murya tace.

"Kinyi wanka fa,amma zaki kuma shiga aikin k'ura?

Ta fice da sauri tana cewa.

" Na sake wani wankan idan na gama"

Umma ta girgiza kai ta maida kanta ta kwanta gyangyad'i na d'iban ta.


Bakin shagon cike da mutane masu kawo caji da masu siyen abubuwan da suke so,suka matsa mata suka bata hanya,ta d'aga kantar da ta kare tsakanin Hamza da mutane ta shige cikin shagon,Hamza na tsaye yana d'aukowa wani mutum condom da yazo siya,ya waiwayo ya kalleta yayi murmushi yace.

"Har kin shirya?na neme ki ai Umma tace kin shiga wanka"

Ta jijjiga kai tana murmushi tace.

"Eh Ya Hamza, yau fa sanitation zan wa shagon nan duk yayi k'ura"

Ya D'an zaro ido yace"Ayya Hidaya ai zaki b'ata wankan ki"

"Babu komai sai na canza wani Ya Hamza"

Haka ya k'yaleta ta d'au daster ta fara goge goge,shi kuma ya cigaba da sallamar mutane,sai dai Abu d'aya ya dame shi ganin yadda mazan da suke zuwa suka ishi Hidaya da kallon k'urilla,nan da nan yaji ransa ya b'aci, ko me suke kallo oho musu.

Ita kam bata san ma suna yi ba,hankali ta na kan aikin ta tana zubawa Hamzan surutu,ba kuma hirar komai take masa ba sai ta khaleel,yana jinta yana bata amsar maganar da take masa.

Fitsari yaji ya matse shi,Dan haka yace da Hidaya ta bar goge gogen ta kula da shagon zai shiga cikin gida ya fito yanzu,ta amsa da to ,shi kuma ya d'aga Kantar ya fice daga shagon.

Yana shiga ya wuce d'akinsa da sauri,toilet ya shiga saboda jin fitsarin ya matse shi sosai kamar ya zubo a wando,bayan ya gama uzurin sa sai ya fito,ya lek'a d'akin Umma ya ganta kwance a parlour bacci ya kwasheta.


A dai dai wannan Lokacin wata dank'areriyar mota me azabar kyawu ta tsaya dai dai k'ofar Gidan,driver'n motar yana tsayawa ya fito da hanzari ya zagayo ya bud'e k'ofar Gidan baya,wani Hamshak'in mutum ya sako k'afafuwan sa ya fito,jikinsa sanye da kaya na alfarma,daga ganinsa kasan naira ta zauna,ALHAJI MUDASSIR Kenan,Mahaifin Khaleel.

Babu Neman izini ko sallama haka ya taka cikin izza da gadara ya kutsa kansa cikin Gidan,driver kam tsayawa yayi a gindin motar yana jiran sa.

Ita Hidaya bata lura da zuwan su ba ma,hankalin ta ya d'auke kan sallamar mutanen da suke zuwa.

ALHAJI mudassir yana kutsawa tsakar Gidan ya ci karo da Hamza yana k'ok'arin fitowa,da sauri Hamza yayi baya yana duban daddy k'irjinsa na wani irin bugawa da tsananin k'arfi, fuskar daddy tamkar gobara saboda fushi,zubewa Hamza yayi a gaban daddy cikin rawar baki yace.

"Barka …da zuwa daddy…ya …ya hanya..?

Wani matsiyacin kallo daddy ya watsawa Hamza,cikin kakkausar murya ya fara magana da k'arfi yana nuna Hamza da Hannu.

" Kai ka kiyaye ni?bana buk'atar gaisuwar ka,matsiyacin yaro D'an Gidan talakawa jikan mayu,so nawa zan gargad'eka akan mak'alewa yarona ne,wai kai maye ne?nace kai maye ne?haka kawai ka mak'alewa d'ana sai zuk'e masa jini kake,D'an arzik'in da yake da shi wato sai ka k'arar da shi ko?wai kai baka da zuciya a cikin k'irjinka ne?wane irin jarababben yaro ne kai?me za a yi da halin talaka a rayuwa?talaka shegen kansa ne,na tsani talakawa a rayuwa ta domin bak'ar Zuciyar su,ba zan tab'a sonka ba Hamza,idan ka cika D'an halak cikin uwarka da uban ka ka rabu da d'ana,ka fita daga rayuwar d'ana,ka barshi ya sake yayi min biyayya,kai warware asirin da kayi masa,idan ba haka ba wallahi sai Na d'auki mummunan mataki a kanka, asararre kawai……

Hamza kansa a k'asa yana jin duk cin mutuncin da daddy ke masa,K'unci ya mamaye ruhinsa,idanuwan sa suka yi jajir,a dai dai lokacin hargagin daddy ya tashi Umma daga baccin da ta fara,ta taso da sauri ta d'aga labulen parlour'nta tana duban daddy tsaye yana zazzagawa Hamza cin mutunci,Hamza durk'ushe kansa a k'asa Hawayen sa na d'isa,daddy ya waiwaya ya dubi Umma,suka had'a idanu a lokacin da daddy ya cigaba da magana yana mata kallon banza.

"Yawwa fito kiji da kunnuwanki kema,d'anki ya zama kaska rab'i mai jini,to ki ja masa kunne ya fita daga harkar d'ana,ya daina mak'ale masa,bana buk'atar sa a cikin rayuwar d'ana,idan ba haka babu sai na mayar da shi abin kwatance a garin nan,talakawan banza talakawan wofi,na d'aukeshi ma daga k'asar amma kuna bibiyarsa kamar mayu, wannan shine gargad'ina na k'arshe a gareku,Idan kunne ya ji jiki ya tsira…….

Yana kaiwa nan ya saki mugun tsaki ya juya zai fice daga Gidan,yana kaiwa soro suka yi kacib'us shi da Hidaya da ke k'ok'arin shigowa soron a dai dai lokacin,sakamakon man inji ya k'are ta rufe shagon ta shigo ta kirawo Hamza domin a zuba wani,tun daga waje take jiyo hargagi da masifa amma bata san ko muryar waye ba,bangaje Hidaya daddy yayi ya wuce a fusace,Hidaya ta tsorata saosai ta kauce,ta bi k'eyarsa da kallo saboda bata yi nasarar ganin fuskar sa ba,a hankali ta tab'e baki ta nufi cikin gidan.

Hamza ya d'ago yana duban Umma da ta yi mutuwar tsaye,irin wannan ranar take gudu daman,ranar da Mahaifin Khaleel zai sake yi musu tijara a karo na barkatai,shin wai menene laifin su ne?Khaleel ne ya mak'alewa Hamza ba Hamza ne ya mak'alewa Khaleel ba,amma me yasa Mahaifin Khaleel ya kasa gane hakan?shin menene laifin talaka a rayuwa?talaka da ya kasance bawan Allah…!

Hawaye mai zafi ya zubo mata,a dai dai lokacin da Hamza ya d'ago ya kalleta,k'irjinsa ya buga ganin Umma na kuka,ya nufeta hankali a tashe kamar ya kifa,zubewa yayi a gabanta ya rik'e k'afafuwanta ya fashe da kuka mai cin rai yana magana cikin rauni.

"Ki yafe min mahaifiyata,fushin ki gareni babbar masifa ce umma na,nine na jawo miki,daman an ce D'an kuka mai jawa uwarsa jifa,da banyi abota da Khaleel ba da ba a zo an ci mutuncin ki ba,don Allah ki yafe min Umma na,hawayen ki ya bar zuba a kaina,ban san me zan fad'awa ubangijina akan hakan ba,ina kwad'ayin samun aljanna Umma,idan hawayen ki yana zuba a kaina ba zan tab'a samunta ba Umma,don Allah ki yafe min Mahaifiyata"

Kuka sosai Hamza yake mai cin rai,ita ma Umma hawayen ta na d'isa,cikin wata irin Murya a shak'e ta kirayi sunan Hamza.

"HAMZA…..

Ya kasa amsawa saboda kuka sai kallonta da yake yi kawai yana shesshek'a da nishi,ta runtse idanu tace.

" Idan har da gaske ni ce Mahaifiyar ka,ni na tsuguna na haifeka,ni ce na raineka,nice na shayar da kai,ni ce na d'auki d'awainiyar ka tun daga haihuwarka har zuwa girman ka,ni ce uwarka ni ce ubanka,to ina so a yau kayi min alfarmar cire Khaleel daga ranka,ka shafe babin tarihinsa a rayuwar ka,ka manta da shi da duk wani Abu da ya shafe shi,ka mayar masa da duk wani Abu na sa da ke wajen ka,ina so abotarku ta zo k'arshe a yau ba gobe ba……

A dai dai lokacin da Hidaya ta k'araso kalaman Umma na shiga kunnuwan ta,a gigice ita da Hamza suka dubi Umma…k'irjin su ba bugawa,Kansu kamar ya fashe saboda razanar jin kalaman Umma…….!


Comments
Share
Vote
Pls


*TYPING*📲

✌️💔 *GARKUWA BIYU...!* 💔✌️

*TARE DA ALK'ALAMIN* ✍️

HASSANA D'AN LARABAWA

*MARUBUCIYAR* 👇

SANADIN HOTO
HASSANA DA HUSSAINA
CIN AMANAR RUHI
BAHAGON LAYI
BAHAGON LAYI (SABON SALO)

*DA KUMA*

GARKUWA BIYU


*BABI NA TALATIN DA BAKWAI DA NA TALATIN DA TAKWAS*


WATTPAD:Hassana3333


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️

🖊 *PEN WRITERS ASSOCIATION*🖊️


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️


______________________________________

*~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~*


_____________________________________


https://www.facebook.com/groups/1533639276725285/


Umma ta juya a fusace ta shige parlour'n ta,bata tsaya a nan ba sai ta wuce bedroom ma ta kullo k'ofar ta gabad'aya.

Hamza kam bai san lokacin da ya sake fashewa da kuka ba,Abubuwa da yawa sun tarar masa,ga fushin Umma,ga ciwon rabuwa da abin da yake so wato Khaleel, kuma dole ne ya bi abin da Umman sa take so yayi mata biyayya,domin kaf duniya ba shi da kamar ta,babu kuma Wanda yayi wahala da shi tamkar ta,haka nan ya zama tilas idan d'a yana son zama na gari to ya kyauta tawa iyayen sa,musamman ma Mahaifiya,hak'k'in iyaye a musulunci ,hak'k'i ne mai girma,saboda haka ma Allah mad'aukakin sarki ya had'a shi da hak'k'in sa a wurare da dama a cikin alk'ur'ani mai girma,kamar fad'in Allah:


"و اعبدوا اللہ ولا تشرکوا بہ شیـٸا،وبالوٰلدین إحسـٰناوبذی القربیٰ والیتـٰمیٰ والمسـٰکین"


Ma'ana:(Ku bautawa Allah kada kuyi shirka da shi da wani Abu,Sannan ku kyautata iyaye da makusanta da maraya da miskinai).

Haka nan a wata ayar Allah ya sake cewa:


"ووصینا الإنسـٰن بو ٰلدیہ حملتہ أمہ وھنًا علی وھن وفصـٰلہ فی عامین أن اشکر لی ولوٰلدیک الی المصیر"


Ma'ana:(Mun yi wa mutum wasiyya da iyayen sa,mahaifiyarsa ta d'auketa shi rauni akan rauni,d'aukan cikin sa da yaye shi shekara biyu,ka gode min da iyayen ka,gareni makoma take).

Ko ba a k'ara ba iya wad'annan ayoyin ma sun isa a gane darajar iyaye da k'imar su ta wuce duk yadda ake tunanin ta,shi yasa Hamza yaji a Zuciyar sa ranar rabuwa da Khaleel ta zo,domin ba zai iya k'etare maganar Mahaifiyar sa ba.

Yadda hawayen sa ke shatata tamkar za su k'are yasa jikin Hidaya wani irin mugun rawa,bata tab'a ganin Ya Hamzan ta cikin wannan halin ba,take ita ma ta fara kuka duk da bata san cikakken abin da ya faru ba,sai dai Umarnin da Umma ta bawa Hamza akan khaleel, ita kanta Umarnin yayi mata tsauri ba ma Hamza ba,duk da bata yi tsawon zama da Hamza ba a D'an tak'aitaccen lokaci ta gane matsananciyar k'aunar da take tsakanin abokan guda biyu,to me ya faru haka da Umma take son datse wannan alak'a mai girma da kyawu?an ya kuwa Umma bai ta zafafa ba?.

A hankali ta ja sanyayyun k'afafuwan ta ta isa in da Hamza ke durk'ushe yana zubar da hawaye,tsugunawa tayi dab da shi hawaye na malala a idanuwan ta,a hankali ta kira sunan sa cikin siririyar murya.

"Ya Hamza…..

Ya d'ago idanuwan sa da suka yi jajir tsabar kuka da tashin hankali,ganin yadda Hidaya ke kuka sai ya k'ara raunata Zuciyar sa,da hanzari ya girgiza mata kai sannan ya mik'e ya wuce ta ba tare da yace mata uffan ba,ya fad'a cikin d'akin sa cikin wani yana yi mara fassaruwa.


Hidaya ta jima a wajen cikin tashin hankali da Hawaye,a rayuwar ta bata son ganin damuwar Hamza,Zuciyar ta ciwo take muddin ta ganshi cikin damuwa,Ya Hamzan ta yana da wata k'ima ta musamman da babu wani namiji da yake da k'imar a tare da ita,haka ta mik'e jiki a sanyaye ta shige parlour'n Umma,ta tarar Umman ta kulle kanta a d'aki,haka ta dawo kan kujera ta lafe ta kwanta tayi lamo kamar mara lafiya,lokaci lokaci hawaye na ziraro mata akan fuskarta.

Gabad'aya sai Gidan yayi wani shiru ba dad'i ko kad'an,kowa babu walwala,ko k'awayen Hidaya masu shigowa su taya ta wasa ranar babu Wanda ya shigo,kamar sun san Gidan babu lafiya,tana nan kwance har azahar ta yi aka fara kiran sallah,tana jin motsin Hamza sanda ya fito ya d'aura alwala ya fita masallaci.

Ita ma ta mik'e kanta na matsanancin ciwo,ta fito ta d'aura alwala,tana dawowa ta tarar Umma ta bud'e k'ofar d'akin,a hankali ta shiga da sallama,sai ta tarar Umman na sallah,da alamun a bathroom d'in d'akin ta ta yi alwala,hijabin ta ta saka ta matsa kusa da Umma ta ta da sallah ita ma,har Umma ta idar ta zauna tana Jan carbi,ita ma Hidaya ta kammala ta zauna tana addu'o'i,ta D'an sa ci kallon Umma,tana so tayi mata magana amma babu fuska,har lokacin Umma a turb'une take,suna nan zaune suka ji sallamar Hamza,Hidaya ta amsa cikin bugun zuciya tana kallon Umma,ya shigo kansa a k'asa salo salo har ya k'ara so gaban Umma ya tsuguna,ya zura hannunsa a aljihu ya fito da mukullai guda biyu ya zube a gaban Umma,kansa a k'asa ya fara magana cikin rawar murya.


"Umma na ina mai k'ara Neman afuwarki a bisa sab'a mikin da nayi,kiyi min Afuwa Ya mahaifiyata,Hamza D'an ki ne mai biyayya a gareki da bin dukkanin abin da kike so matuk'ar bai sab'awa Allah da manzon sa ba,A yau zan bar Khaleel kamar yadda kika umarceni,wad'annan mukullayen mallakin Khaleel ne,d'aya na mashin d'in da ya siya min,d'ayan kuma na shagon da dukiyarsa take ciki ne,akwai cinikin da aka yi daga lokacin da aka bud'e shagon har zuwa yau,zan ware uwar kud'i na mayar masa,zan raba ribar da aka samu na bashi hak'k'in sa na rabin riba,nima na d'au na wa rabi,kamar yadda muka yi alk'awari ni da shi,ina so kibar mukullayen a wajenki,zan tattaro duk ragowar abin da ya dangance shi na kawo miki,zan aika masa da sak'o ta waya sai ya turo a karb'a kawai Umma,ina fatan hakan yayi miki…!?

Umma ta cigaba da Jan carbinta hankali kwance,sai can ta jijjiga kai tayi magana a tak'aice.

" Ya yi,madalla,Allah yayi maka Albarka "

Hamza ya amsa,sannan ya cigaba da tsuguno,amma Umma ko kallon sa bata sake yi ba,Hidaya kam sai kallon sa take cike da tausayin sa,kansa a duk'e,ganin Umma bata sake magana ba sai ya mik'e ya fice daga d'akin a sanyaye.

A lokacin ne Hidaya ta ji ba zata iya daurewa ba,cikin marairaicewa ta dubi Umma tace.


"Don Allah Umma kiyi hak'uri ki sassauta wa Ya Hamza…kar ki raba shi da Uncle Khaleel, saboda……


Kallon da Umma tayi mata shi ya katseta daga maganar,cikin b'acin rai Umma tayi magana.


" Idan na sake jin bakin ki akan maganar nan idan ranki yayi dubu sai ya b'aci Fatima…..kinji ni ko baki jini ba…?

Hidaya ta jijjiga kai alamar ta ji,sosai ta tsorata da yanayin Umman,tunda har Umma ta kira sunanta na gaskiya tabbas tana cikin b'acin rai,domin bata fiye Kiran ta da Fatima ba ,shiru tayi har sai da Umman ta sake magana.

"Ki tashi ki je kitchen akwai taliya da miya ki zuba ki ci,sannan ki zo ki saka uniform d'in islamiyya ki ta fi "

Hidaya ta girgiza kai a hankali.

"Ba na jin yunwa Umma"

Umma ta harareta ta tab'e baki.

"Kar ki ji d'in…cikin ki ne ai ba na wani ba"


Hidaya ta mik'e a hankali ta bud'e wardrobe ta Ciro kayan ta na islamiyya ta sauya da na jikinta,ta sanya hijabin ta sannan ta d'auki jakar makarantar ta ta rataya,ta dubi Umma murya a sanyaye tace.

"Umma na shirya …zan tafi"

"Allah ya tsare hanya ya bada ilimi mai amfani"

Abin da Umma tace kenan ta cigaba da Jan carbin ta.

Hidaya ta kad'a kai tana amsawa,ta fice daga d'akin jiki ba k'wari.


A tsakar gida ta tarar da Hamza,yana zaune kan kujera Y'ar tsuguno kansa a sunkuye a k'asa,sai tsinken tsintsiyar kwakwa da ke hannunsa yana za na shi a k'asa kamar me wasa,amma kamar ba a hayyacinsa yake ba,tausayin sa ya sa Hidaya taji hawaye ya cicciko idanuwanta,a hankali ta k'ara so gabansa ta tsaya,amma duk da hakan bai ji motsinta ba hankalin sa ya tafi wani wajen,har sai da ta ambaci sunan sa sannan ya d'ago da sauri ya dubeta,yayi murmushi mai kama da yak'e,idanuwan sa duk sun wani shanye,a haka yake dubanta sannan yayi magana.


"Wai har kin yi shirin tafiya islamiyya?to ai kamar ba ki ci abincin rana ba ko?"

Ta girgiza kai a hankali tace.

"Eh na yi shiri Ya Hamza zan tafi,bana jin yunwa ne shiyasa ban ci abincin ba"

Zaro idanuwa yayi yana b'ata rai yace.

"Ba zaki tafi makaranta baki ci abinci ba Hidaya, maza ajiye jakar kije ki zubo ki ci a gabana sannan ki tafi"

Ta k'ura masa idanuwa sannan tayi magana a shagwab'e.

"To ai kaima baka ci ba,kuma ni ba zan iya ci ba idan baka ci ba,sai dai idan ka yarda na zubo mana tare sai mu ci,kaji Ya Hamza,na zubo mana tare don Allah?"

Yayi kasak'e yana duban ta,shagwab'ar ta na tab'a Ruhin sa,sai kawai yayi murmushi yana jin wani Abu na tsirga masa,ya kuma tabbatar in dai bai ci ba to ba zata ci ba,shiyasa ya jijjiga kai yace.

"Zan ci …jeki ki zubo"

Ta saki murmushin da ya k'ara fidda kyawunta har da tsalle,ta cire jakarta ta dire,har da zare hijabin ta ta d'ora kan igiyar shanya,sannan ta nufi kitchen da saurin ta,ya bita da kallo idanuwan sa kamar su zagwanye,sai da ta shige sannan ya kau da kai yana D'an murmushi.

A plate d'aya ta zubo musu,ta d'auko wata kujerar ta zauna ta saka abincin a tsakiyar su,cokali mai yatsu guda biyu ta d'auko,ta bashi d'aya ta d'au d'aya,ya karb'a yana saka mata Albarka, suka fara cin abincin a hankali,shi kam Hamza ba wani ci yake ba,wasa da cokalin kawai yake,idan ya fuskanci Hidaya zata gane sai yayi sauri ya d'iba ya kai bakinsa,shi gabad'aya ma d'aci abincin yake masa,saboda Hidaya ta ci shiyasa kawai yake cuccusawa.

A haka suka kammala cin abincin, ta d'auko musu ruwa suka sha suka wanke bakin su,Hidaya ta mayar da hijabin ta ta d'auki Jakarta tana yiwa Hamza sallama,har ta kai bakin k'ofar soro taji muryar Hamza na cewa.

"Yau ba kya buk'atar rakiyata kenan?

Ta D'an juyo ta kalleshi,sai ta sunkuyar da kai ta rasa abin cewa,kullum shi take d'anewa ya kaita a mashin,to yau kuma babu mashin,ta ya ya zata ce ya kai ta?

Murmushi yayi ya nufo ta yana cewa.

" Ko babu mashin ai ina da k'afafu Hidaya,muje na rakaki da K'afafuwana kinji Y'ar K'anwata"

Ta saki murmushin murna,ya k'araso ya karb'i jakar makarantar ta ya rik'e,sannan suka jera suka fice cike da annashuwa da k'aunar juna.

Umma da ke tsaye ta tagar bedroom d'in ta ta bi su da kallo tana lumshe idanuwanta, wani Abu na tab'a ranta,kawai sai ta girgiza kai ta bar gurin.


A wannan Daren Hamza ya rubutawa Khaleel zungureren sak'o cike da kalamai masu tab'a zuciya,ya kuma rok'eshi akan ya turo a karb'i komai na sa da ke hannunsa,sai dai bai fad'a masa cewar ga abin da daddy ya zo yayi musu ba,ya shaida masa kawai lokacin rabuwarsu ne yayi,kuma kar ma ya nemeshi a waya domin jin ba'asi,Dan ba zai d'aga ya saurare shi ba,sannan yayi masa fatan alkairi da godiya a bisa taimakon sa da yayi tun daga lokacin da Allah ya had'a su har zuwa yanzu.

Hamza ya rubuta wannan sak'o ne cikin kuka da kewar Khaleel, yana turawa ya kashe wayar sa ya zare sim card d'in ya jefar….ya kwanta ya dafe kansa da ke barazanar tarwatsewa….Hawaye na malala har cikin kunnuwan sa,bakinsa na furta"Hasbunallahu wa ni'imal wakeel"


Lokacin da Khaleel ya ci karo da sak'on Hamza ya fito daga wanka ne d'aure da towel a k'ugun sa,yana goge Ruwan jikinsa da wani towel d'in,shigowar sak'o yaji,k'arar wayar kawai yaji ya tabbatar Hamzansa ne,saboda komai na sa daban ya sa masa a wayar sa,da hanzari ya d'auki wayar yana murmushi ya soma karanta sak'on.

Tamkar Wanda aka bugawa guduma haka yaji,kansa ya sara,k'irjinsa ya dinga tsananin bugu tamkar ya fad'o k'asa,ya dafe saitin Zuciyar sa bakinsa na rawa,Allah ya taimake shi kusa da bed yake,shiyasa ya fad'i zaune ya yarda wayar a k'asa,bai tab'a jin tashin hankali irin na ranar ba bayan ranar mutuwar mahaifiyar sa,da ranar da daddy ya raba shi da Hamza ya kawo shi England da sunan karatu,sai kuma wannan rana da ta zama ta uku a jerin ranakun bak'incikin sa,tamkar Wanda zai zauce haka Khaleel ya riski kansa a wannan rana,duk da maganar da Hamza ya fad'a akan ko ya kira shi ba zai sameshi ba amma bai lamunci hakan ba,wayar da ya jefar ya d'auko hannunsa na rawa ya fara daddanawa don Neman Hamza,idanuwan sa ma basa gani tsabar shiga rud'u,da k'yar ya gano lambar ya soma kira a gigice,amma baiyi nasarar samu ba,kawai sai khaleel ya fashe da wani irin kuka,nan da nan Zuciyar sa ta fara ciwo,ya kira wayar Hamza ya fi sau d'ari a wannan dare amma bai samu ba,haka ya kwana cikin kuka da kewa kamar yadda Hamza ya kasance.


***************


A wannan tsakanin lokacin ne kuma ciwon Hidaya ya matsa sosai,jininta ya dinga k'onewa,ciwo tamkar Hidaya zata mutu,hankalin Hamza da Umma ya tashi,in kaga Hamza sai kayi hawaye saboda tsananin ramar da yayi,idanuwan sa sun zurma saboda tashin hankali ,duk wani tanadin sa na ribar da ya samu sai da cutar Hidaya ta cinye shi,haka nan D'an jarin Umma duk ya tafi,har ta kai Hamza ya soma zarar kayansa da sutturun sa yana siyarwa duk don ya ceci rayuwar Hidaya.

Har kuma zuwa wannan lokacin Khaleel bai turo ya karb'i dukiyarsa ba,shi kuma Hamza duk da yana cikin buk'atar kud'i bai tab'a kud'in Khaleel ba,yana fatan ya cika alk'awarin da ya d'aukar wa Umma,ba zai sake cin abin Khaleel ba,ba zai yadda wani Abu ya sake had'a shi da shi ba,duk da har lokacin k'aunar Khaleel bata gushe a ransa ba,illa ma dad'uwa da tayi,kullum sai yayi kuka idan ya tuna da Khaleel, ga lalurar Hidaya,Abu ya zame masa goma da ashirin.

Akwai lokacin da ciwon ya sake motsawa gashi basu da kud'i,sun rasa ya za su yi,Umma ta bada shawarar a d'auki sark'ar gold d'in Hidaya a siyar domin a siya mata magani,amma Hamza ya k'i yarda,yace hak'k'in sa ne ya nemarwa Hidaya magani da kud'insa da k'arfinsa,haka Hamza ya dinga fita yana aikin k'arfi yana samun y'an kud'ad'e yana siyawa Hidaya magani,ga maganin masu ciwon sikila da tsada.

Wani dare da ciwon ya matsa wa Hidaya har da suma,suka rikice suka gigice,da ta farko ta dinga kuka tana rik'e k'irjinta,cikin zafin ciwo ta rik'o hannun Hamza tana kuka da nishi tace.


"Ya Hamza zan mutu!ko ina a jikina ciwo yake wallahi!kamar ana sassarani da gatari!Ya Hamza ina son na rayu da kai amma na san mutuwa zan yi,Umma kuyi min addu'a na daina jin ciwon da nake ji,Ya Hamza ka cire min ciwon nan …don Allah ka cire min …

Hamza ya damk'e hannuwanta sosai,Umma tana hawayen tausayin Hidaya,cikin dauriya Hamza yake magana cike da tauhidi da iklasi.

" Hidaya ki yi hak'uri da k'addarar da Allah ya d'ora miki ta wannan cuta,ba ni da ikon yaye miki domin babu Wanda ya isa ya yaye wa wani bawa cuta sai Allan da ya k'addara masa,kamar yadda ya fad'a a cikin suratul An'am.


"و إن یمسسک اللہ بضر فلا کاشف لہ الا ھو،و إن یمسسک بخیر فھو علی کل شیء قدیر"


(Idan Allah ya same ka da wata cuta babu mai yaye ta sai shi,idan ya same ka da alheri shi mai iko ne a bisa kowane Abu).

Ki mik'a lamarin ki ga Allah Hidaya,domin duk wani al'amari na Allah ne.

"إن الاُمر کلہ للہ"

(Dukkanin wani al'amari na Allah ne).

Allah zai yaye miki wannan cuta da izininsa,da ke da duk wani mai fama da ita,haka nan Allah baya d'orawa bawansa abin da na zai iya ba,kiyi hak'uri,wannan lalurar ibada kike yi….

Haka Hamza ya dinga tausarta da yi mata nasiha,cikin ikon Allah sai ta fara jin rangwami akan azabar da take ji a jikinta,har bacci yayi nasarar kwashe ta.

A hankali kuma sai jikinta ya warware,har ma ta cigaba da zuwa makaranta,Hamza yafi kowa murna,kullum addu'ar sa Allah ya bawa Hidayan sa lafiya.


*****************


Wata biyu bayan hakan Hidaya ta k'ara murmurewa,tayi wani girma ta k'ara kyau,shak'uwar ta da Hamza sai abin da yayi gaba kam.

Zaune take a tsakar gida bakin rariya tana wanke wanke,Hamza ya fito daga d'akin sa yana mik'a alamar ya tashi daga barci,lokacin misalin k'arfe d'aya ne na ranar Asabar,ta kalleshi tana dariya tace.

"Ya Hamza kana jin dad'in ka,wato ma baccin rana kake yi ka barni da aiki,don Allah zo ka tayani d'aurayar kwanukan nan mana."

Ya nufo ta ya tsuguna dab da ita,ya kalleta lokacin da yake tsoma hannun sa cikin Ruwan wanke wanke yana d'auraye wa,yayi magana cikin k'aramar murya.

"Ban ma fa san lokacin da baccin ya kwashe ni ba wallahi,ina karatun exam kawai naji ina gyangyad'i…kuma na san ba komai ke d'awainiya da ni ba sai gajiya."

Ta mik'a masa wani cup yana d'auraye wa, yayin da take cewa.

"Allah sarki Ya Hamza na,insha Allahu bayan wuya sai dad'i,ni fa har na k'agu ka kammala karatun ka ka zama cikakken D'an jarida,wayyo Allah randa na jika a redio kana karanta labarai wane irin dad'i zan ji Ya Hamza?"

Ta wani lumshe idanu har da dafe k'irji irin tana tsumayin ranar ta zo,yayi murmushi kawai,ya juya yana duban d'akin Umma yace.


"Wai Umma fita tayi ne?ban ji motsin ta ba"

Ta jijjiga kai tace.

"Eh ta fita Gidan Maman salma,Salma ce ciwonta ya tashi shine ta shiga duba ta"

Ya jijjiga kai cike da jimami yana wa Salma addu'ar samun sauk'i,a dai dai lokacin suka kammala wanke wanken,Hamza ya d'ibi kayan ya shiga kitchen da su,ita kuma ta sunkuya tana d'auraye wajen da ruwa da tsintsiya.

A hankali ta d'ago kai jin ana wata murya sassanya me tsananin dad'i tayi sallama,ta bud'e baki za ta amsa amma ta kasa saboda razanar da tayi da Wanda ke tsaye a bakin k'ofar shigowa tsakar gidan,ko daga bacci ta tashi zata shaida wannan k'ayatacciyar fuskar,domin duk da bata tab'a ganin ta a fili ba ta sha ganin ta a waya da hoto,ba kowa bane face Khaleel.

Sanye yake cikin wasu k'ananan kaya bak'ak'e masu matuk'ar kyau da d'aukan hankali,da takalmi sau ciki Wanda ya rufe k'afafuwan sa,kalar ja,sai wata jibgegiyar rigar sanyi me gashi gashi ita ma ja da ya d'ora saman kayan sa,wani sihirtaccen kyau yayi ga k'amshi da ke tashi kamar an yi b'arin turare…

Bayan sallamar da yayi babu abin da ya fara cin karo da shi sai Hidaya,wadda suke kallon kallo a tsananin su,ita fuskarta na bayyana tsoro da mamakin ganin sa,yayin da ta sa fuskar ta bayyana Abubuwa da yawa masu wuyar fassaruwa,sai dai fuskar na d'auke da wani irin murmushi na kammala,idanuwan sa sunyi narai narai wani irin ruwa ya kwanta a cikin su.

A dai dai lokacin da ya nufo Hidaya da ke sank'are a tsaye,a lokacin ne Hamza ya fito daga ktcheen hannun sa da Kofi cike da ruwa yana fad'in.

"Lokacin shan Ruwan ki yayi zo ki sha,kin san dai likita yace ki dinga yawan shan ruwa a kowace rana Hidaya…...

Maganar ta mak'ale sanda idanuwan sa suka yi arba da Khaleel,ya saki kofin a k'asa cikin wani yana yi na matuk'ar razana,a kuma wannan lokacin Umma ta shigo gidan tana sallama……


Comment
Share
Vote
Pls


*TYPING*📲

✌️💔 *GARKUWA BIYU...!* 💔✌️

*TARE DA ALK'ALAMIN* ✍️

HASSANA D'AN LARABAWA

*MARUBUCIYAR* 👇

SANADIN HOTO
HASSANA DA HUSSAINA
CIN AMANAR RUHI
BAHAGON LAYI
BAHAGON LAYI (SABON SALO)

*DA KUMA*

GARKUWA BIYU


*BABI NA TALATIN DA TARA DA NA ARBA'IN*


WATTPAD:Hassana3333


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️

🖊 *PEN WRITERS ASSOCIATION*🖊️


✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️


______________________________________

*~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~*


_____________________________________


https://www.facebook.com/groups/1533639276725285/


Kallon kallo kawai aka tsaya yi tsakanin su,kowa Zuciyar sa na tsananin bugu,wata gingimemiyar Soyayya da kewa suka tasowa Hamza a lokaci guda,Soyayyar Khaleel da kewar sa,idanuwan sa suka cicciko da hawaye,k'afarsa ta fara rawa tamkar ba zata d'auki gangar jikinsa ba,Zuciyar sa na ingizashi akan ya je ya tari Khaleel ya rungume shi a jikinsa ko zai samu sauk'in damuwar da yake ji,amma inah!idanuwan Umma sun masa Katanga da aikata hakan,ba zai iya karya alk'awarin ta ba!shiyasa ya zab'i ya wuce d'aki domin ya kaucewa kallon Khaleel da ke tsaye yana duban sa cikin rauni,ya tabbatar idan ya cigaba da tsayuwa tilas sai Zuciyar sa ta ingiza shi akan kula Khaleel, Wanda kuma hakan babban laifi ne da zai aikatawa mahaifiyar sa.

A hankali ya juya baya ya soma tafiya domin shigewa d'aki,a lokacin har hawayen idanuwan sa sunyi nasarar fara zubowa,Hidaya tana fuskantar nufinsa ta yi hanzarin dakatar da shi wajen kiran sunan sa da rawar murya.

"Ya HAMZA…!

Ya tsaya cak ba tare da ya juyo ba yana sauraren ta,ta cigaba da magana tana kallon kwantacciyar sumar k'eyar sa.

" Wannan fa Uncle Khaleel ne…kuma na tabbatar wajen ka ya zo…amma me yasa za ka tafi ka barshi?ko baka ganshi ba ne…!?

Bai waiwayo ba yayi magana cikin raunin murya.

"Na ganshi Hidaya…amma bani da iko wajen kula shi,har sai mahaifiyata tayi min umarnin aikata hakan"

Shi kam Khaleel tsaye yake cikin wani yanayi,kansa duk'e a k'asa,Abubuwa da yawa sun cika rarraunar Zuciyar sa wadda bata da k'oshin lafiya,a hankali ya d'ago kansa ya dubi Umma,wani irin hawaye ya zubo masa,kawai sai ya nufi Umman da ke tsaye kamar an dasa ta ,ya tsuguna gaban ta,yayi iya k'ok'arin sa na ganin maganar da yake son yi ta fito amma ya kasa,wani tuk'uk'i yake ji a k'irjinsa,hakan ya sa kawai ya dinga girgiza kai yana hawaye.

Matsanancin tausayin sa ya kama Umma,wace irin k'auna Khaleel yake wa Hamza da har yayo tattaki tun daga England ya tawo domin Hamza?ga wata irin rama da ya kwantsama duk dalilin tashin hankalin rabuwa da Hamza,ya baro karatunsa da komai nasa domin Hamza kawai !Anya kuwa idan ta raba wannan Abotar tayi adalci kenan!?

Ganin yadda Khaleel ke faman had'iyar zuciya yana kuka ya kasa magana sai hakan ya tsorata Umma sosai,kar taje wani abun ya faru da D'an mutane !hakan ya sa cikin wata irin murya tayi hanzarin magana,musamman da taga Hidaya ma ta tsura mata idanu,cikin wani irin kallo mai kama da tuhuma ko Neman agaji.

"Hamza kazo gun Khaleel na amince kayi magana da shi" Tana fad'in hakan ta wuce d'akin ta da sauri.

Sai lokacin Hamza ya juyo cikin farinciki,a maimakon hawaye masu d'umi sai hawayen sa ya fara sanyaya,ya k'araso inda Khaleel ke tsugune ya dafa kafad'ar sa,Khaleel ya d'ago idanuwan sa da suke zubar hawaye a hankali ya dubi Hamza,a yayin da Hamzan ya rik'o kafad'un sa ya mik'ar da shi,suka zubawa juna idanu cike da wata irin k'auna,da hawaye a idanuwan su amma Zuciyar su k'al da farinciki,da murna ta ishi Khaleel kawai sai ya afka k'irjin Hamza suka rungume juna suna wata irin dariya,ga kuma hawaye na malala,sai lokacin Khaleel ya samu yin magana ,cikin muryar shauk'i ya ambaci.


"Abokinahhhhh…..!

Hidaya da ke tsaye tana kallon su farinciki ya isheta,ga tausayin su da ita ma ya sakata k'walla,bata san lokacin da dariya ta kufce mata ba,ta d'aga hannuwanta tana tafa musu tana k'yalk'yala dariya.

A hankali suka saki juna suka waiwayo a tare suna duban Hidaya fuskar su d'auke da mad'aukakin farinciki da murna.


***************


Bayan komai ya lafa,Khaleel ya samu tarba ta musamman cike da farinciki,suna zaune gabad'ayan su a parlour'n Umma bayan sun kammala cin abinci,nan Khaleel ke bawa Umma hak'urin duk abin da ya faru har da kukan sa,ita kanta Umma tayi mamakin yadda akayi Khaleel ya san Mahaifin sa ya zo ya ci musu mutunci,sai lokacin Khaleel ke sanar da su cewar sai da ya tsaurara bincike sannan ya gano hakan ta hanyar driver'n daddy,domin shine ya sanar da shi tabbas ya kawo daddy Gidan su Hamza,yace hankalin sa yayi matuk'ar tashi har ciwon sa ya kusan motsawa,yace baya iya bacci saboda tunani,shi abotar sa da Hamza Allah ne ya had'a ba wani mutum ba,Dan haka ba zai iya rabuwa da Hamza ba,kuka sosai ya dinga yi har Zuciyar Umma ta lafa ta tausaya musu,ganin shi kansa Hamzan kuka yake,a lokacin Umma tace ta amince su ci gaba da abotar su,amma bata yarda Khaleel ya cigaba da kashewa Hamza kud'i ba,hakan na janyo wa a dinga zargin wani abin,tilas Khaleel ya hak'ura da hakan,sai dai ya kafe ba zai karb'i abin da Hamza yayi niyyar dawo masa da shi ba,Umma kuma tace dole sai ya karb'a,nan take Khaleel ya yanke hukunci akan cewa ya mallaka wa Hidaya komai kyauta,a matsayin ta na marainiya,a cigaba da kula da rayuwar ta da karatunta da lafiyar ta da wannan jari na shagon da aka bud'e.

Umma ta so yin gardama amma ya kafe ya nace akan hakan,tilas ta hak'ura ta zubawa sarautar Allah idanu,lokacin Hidayan ma bata nan ta ta fi islamiyya,Dan haka ba komai aka tattauna akan idanunta ba.

Kwanakin Khaleel uku a Gidan su Hamza,wad'anda yayi su cikin farinciki tamkar ya dawwama a haka,babu k'yama babu komai ya baje tamkar Gidan su,yana manne da Hamza da Hidaya,Hidaya har fashin makaranta ta dinga yi kullum suna tare suna hira,kulawar da Khaleel yake bawa Hidaya har mamaki take bawa Hamza,lokaci d'aya sun saba da juna bashi da zance sai na Hidaya,haka nan ko band'aki ta shiga Khaleel ya dinga Neman ta kenan kamar wadda ta b'ata,sosai dai Sabo ya shiga tsakanin su.

Sati d'aya cif yayi shirin komawa England, Wanda ko Mahaifin sa bai san yazo ba,kuma ta Abujar ya sauka amma baije gida ba,saboda yasan ba za su kwashe da dad'i ba,kullum dai zancen Hamza baya wuce yiwa Khaleel nasiha akan yiwa Mahaifin sa biyayya,duk da Mahaifin na sa ya kasance wani baud'ad'd'e mai bak'in hali.

Ran da Khaleel zai tafi tamkar marasa lafiya suka zama,suka rungume juna shi da Hamza tamkar ba za su rabu ba suna kuka,Hidaya na gefe ita ma tana na ta hawayen,tana ji a ranta bata son rabuwa da Khaleel saboda yana da kirki,ga dad'in zama ,kuma masoyin Ya Hamzan ta ne,Dan haka take d'aukar sa da k'ima,sai da Umma ta dinga lallamin su sannan suka hak'ura,in da Khaleel zai wuce abuja domin samun jirgin da zai Lula da shi England.

Suka yi wata irin rabuwa Mara dad'i mai cike da kewa da zubar hawaye,Khaleel yana ji a ransa zaiyi duk mai yiwuwa domin ganin ya k'auracewa zaman England zuwa k'asar sa Nigeria.

Hamza da Hidaya sun fi sati d'aya kafin su dawo hayyacin su kewar Khaleel ta sake su,kullum ba su da zance sai na sa,duk da suna waya har ma da video call.


*****************


*BAYAN SHEKARA BAKWAI*


Abubuwa da yawa sun faru cikin wad'annan shekaru,na farinciki da akasin haka,na farincikin bai wuce kammala karatun da Hamza yayi ba,Wanda ya zama cikakken D'an jarida,sai dai har zuwa lokacin bai samu Aiki ba,haka nan shagon siyar da wayoyi ya bunk'asa sosai,Hamza yana tarawa Hidaya dukiyar ta kamar yadda Khaleel ya mallaka mata wajen,duk da cewar har lokacin bata san wajen mallakinta ba ne,a zatonta mallakin Ya Hamza ne,da kuma wasu Abubuwa makamantan hakan.

Na bak'inciki kuma ba zai wuce rashin lafiyar Hidaya ba,wadda take matuk'ar shan wahala idan ta motsa,dan ma cikin ikon Allah ba sa rasa kud'in siyen magani,daga baya ma sai Khaleel ya had'a su da wani babban likitan ciwon sikila,wanda komai Khaleel d'in ne ke biya,sai kuma bak'incikin rashin Khaleel a kusa,Wanda har zuwa wannan lokacin bai dawo Nigeria ba,domin Mahaifin sa ya dage akan sai yayi karatu mai zurfi,a kullum Hamza na tausar sa akan yayi hak'uri komai yayi farko zai k'arshe har ya zama Labari ,a kwana a tashi tilas wataran zai dawo,yayi hak'uri kuma ya dage da addu'a.

Zuwa wannan lokacin Hidaya na da shekaru goma sha shida cif!ba kuma lallai ka shaidata ba saboda wani irin girma da tayi na fara cikar budurci,sai dai har lokacin bata da k'iba,sai dai cikar baya da mazaunai,kyawun ta kullum k'ara fitowa yake yi sosai da sosai,haka nan Hamza,wanda ya zama cikakken saurayi mai ji da wani sihirtaccen kyau da haiba,ga nutsuwa da hankali ,uwa uba Addini,tsafta da kamala.


Har zuwa wannan lokacin kuma babu Wanda ya tab'a fitowa ko ya furta cewa yana son Hidaya,saboda yadda ake rad'e rad'in Hidayan Y'ar tsuntuwa ce,da yake zancen duniya baya b'uya,haka nan duk yadda mutum ya kai da son rufe wani Sirri idan Allah yayi nufin tonuwar sa sai ya bayyana.

Wannan wani k'alubale ne ga rayuwar Hidaya,duk da Hamza ya kanyi k'ok'ari wajen ganin ya hana hakan tasiri,da gaske yake son zama GARKUWAR Hidaya,baya barinta tayi kuka idan aka ci mutuncinta a waje,ya kanyi duk yadda zaiyi domin ya kareta,an sha fad'a da Hamza akan Hidaya,Hamza ya sha dukan mutane akan Hidaya.

Wataran ta kanyi kuka idan ta tuna rayuwar ta,wadda kullum Hamza ya kan d'aurata akan ta dinga yiwa mahaifiyarta addu'a,Allah ya kareta a duk in da take,kuma Allah ya bayyana ta.

Sai dai Hidayan jinsa kawai take,amma a ranta bata fatan taga mahaifiyarta,wadda ta gudu ta barta tun bata da wani wayo,babu wani uzuri da zata yi mata akan hakan,domin tsakanin d'a da uwa sai Allah amma har ta iya gujemata shekaru da dama ba tare da waiwayenta ba,ita kam Umma da Hamza sun fiye mata komai a rayuwar ta,mutanen da suka rik'e ta bisa Amana suka lura da rayuwar ta da tarbiyyarta,suka gwammace su kwana basu ci abinci ba akan ceton rayuwar ta,suka kareta ga duk wani Abu mara kyau,kullum burin su ta samu kyakkyawar rayuwa,suka tsaya akan ilimin ta Wanda yanzu haka tana shekarar k'arshe ta kammala secondary school,ta sauke alk'ur'ani mai girma da wasu litattafai, a yanzu hadda take yi har tayi nisa,wai shin me zata cewa wad'annan bayin Allah da suka tallafi rayuwar ta alhali basu da wata alak'a ta jini da ita….?


***************


Cikin cikakkiyar muryar sa mai d'auke da wani amo mai Jan hankali ya shigo tsakar gidan da sallama,Umma da ke zaune tana ninke wasu kaya ta amsa sallamar sa tana masa sannu da zuwa,ya amsa yana zama kusa da ita cikin gajiya,sai dai fuskarsa d'auke da tarin farinciki take.

Umma ta dubeshi tana fad'in.

"Daga ganin fuskar ka ina zaton an dace ko?"

Ya gyad'a kai yana tayata ninke wata riga yace.

"K'warai kuwa Umma,addu'ar ki gareni ta yi tasiri,yau dai na samu an d'aukeni aiki a gidan redion jihar Kaduna,da matsayi babba da albashi mai kauri"

Umma ta washe baki cike da murna take fad'in.

"Alhamdulillah ala kulli halin,ina taya ka murna Hamza,Allah ya sanya alkairi ya baka damar sauke nauyin da ke kanka,yau ina cike da farinciki wallahi,kai Allah abin godiya"

Shi Hamza yawan farincikin da Umma take shine musababbin jin na sa farincikin ya ninku sau ba adadi,haka Umma tai ta sakawa aikin Albarka cike da jin dad'i,ya dinga amsawa da "Ameen Umma na"

Har suka kammala ninkin bai ga Hidaya ba,hakan ya sa ya tambayi Umma ina Hidayan take.

Umma ta tab'e baki tace.

"Ta na d'aki ta k'unshe kanta ni ban san me yake damunta ba tun d'azu,nayi tambayar duniya amma tak'i magana sai hawaye take,kuma yanayin ta bai nuna min ko bata da lafiya ba,kawai miskilancin ta ne ya matsa,sai kaje gareta kaji abin da ke damunta,Dan kai kad'ai take gayawa damuwarta ko abin da ya shafe ta"

Ya girgiza kai nan da nan yaji damuwa ta mamaye k'irjin sa,shi fa Sam baya son damuwar Hidaya,ya kan fita shiga damuwa idan tana cikin damuwa.

Mik'ewa yayi a hankali ya nufi parlour'n Umma, bai ganta anan ba,hakan ya sa ya wuce bedroom kai tsaye ya d'aga labulen had'e da sallama.

Tsayawa yayi cak yana duban ta,ta na kwance rub da ciki da wata doguwar riga a jikinta duk ta d'ame ta halittun ta sun bayyana a fili,yaji wani yammm!a jikinsa,ya runtse idanu yana fad'in "A 'uzu billahi minash shaid'anir rajeem" Saboda wani Abu da yaji Wanda bai tab'a jin irin sa ba,shed'an na k'awata masa surorin Hidaya,Hidayan da ya d'auketa tamkar ciki d'aya suka fito,bai tab'a jin hakan ba kuma sai yau,to me yasa yau yaji hakan?

A hankali ya fara takawa domin isa gareta,motsin sa yasa ta mirgina ta tashi tana goge hawayen idanuwan ta,yana kallonta yayi maza ya kau da kai saboda yadda k'irjin ta ya fito a cikin rigar sosai,Zuciyar sa na wani irin bugawa ya wuce wardrobe in da kayan Hidayan suke a jere reras suna k'amshi,ta bishi da kallo lokacin da ya bud'e ya saka Hannu ya zaro wani dogon hijab d'in ta,kansa a k'asa ya nufo ta har ya isa dab da ita ya mik'a mata hijab d'in,ta karb'a fuskar ta cike da alamun tambaya.

"Ki saka a jikin ki" abin da yace kenan,sannan ya jawo kujerar dressing mirro ya zauna yana fuskantar ta,har lokacin kuma ya kasa d'aga ido suyi four eyes da juna,domin ba zai iya jure hakan ba.

Bayan ta saka ta sunkuyar da kai ta cigaba da goge hawayen da yake zubo mata,a hankali ya d'ago kai ya dubeta,har lokacin bata sauya a idanuwan sa ba,gabad'aya Hidayan ta sauya masa kamar ba Hidayan sa ba,wadda ya raineta tun da k'ananan shekaru har zuwa girma,hawayen da take fitarwa yana tab'a ransa,idan yaga tana kuka sai yaga kamar ya Gaza a kan amanarta da ya d'auka.

Cikin sanyin murya ya ambaci sunan ta.

"Hidayahhhhh…..!

Yadda ya ja sunan ita kanta sai da tsigar jikinta ta tashi,cikin wani slow ta d'ago shanyayyun idanuwan ta masu sirkin ja saboda lalurar ta,suka had'a idanu,a tare suka yi saurin kau da kai saboda sak'on da ya shiga jikin su mai kama da shocking.

Ya sake kiran sunan ta a karo na biyu da rawar murya,ta amsa ita ma cikin rawar muryar.

" Me ya same ki kike kuka?baki da lafiya ne..!?

Kamar ya to no hawayen ta,nan da nan ta kuma b'allewa da hawaye har da shesshek'ar kuka,hankalin sa yayi matuk'ar tashi,a rikice yace.

"Kin san dai kukan ki ba k'aramin tashin hankali yake sakani ba,ki fad'a min abin da ya saka ki kuka kafin ni ma ki sakani kukan…!


Ta san tabbas zai iya yin kukan,domin ba yau ya fara sakata a gaba yayi kuka idan tana yi ba,cikin rauni ta d'ago tayi magana a hankali kuma a tak'aice.

" Ya Hamza jini…..!

Ya ji maganar wata iri,ya kasa gane abin da take nufi,iya hangensa bai gano ba saboda a tak'aice tayi maganar kuma babu ma'anarta a bayyane,shiyasa ya D'an tara gira yana duban ta yace.

"Jini kuma?jini a ina….!?

Ta sunkuyar da kai ta fara yi masa bayani a hankali cikin k'aramar murya.

" D'azu ne da na shiga toilet zan yi fitsari,shine na…na…naga… jini …naga jini a pant d'i na yana fita ta jikina…"


Wata gingimemiyar kunya ce ta taso ta rufe Hamza,domin shi mutum ne mai tsananin kunya,yayi shiru kansa a k'asa,Hidaya ta girma kenan,domin a yadda tayi bayani tabbas al'ada ce ta zo mata,k'ila rud'ewar da tayi ne ya saka bata fahimci hakan ba.

To amma me yasa ta kasa fad'awa Umma amma shi ta fad'a masa?ko Dan ya kasance shine abokin shawarar ta kuma sirrin ta?ya rasa ma mai zai ce mata,a hankali ya jiyo muryar ta cikin kuka tana fad'in.

"Shikenan wata lalurar ta sake shiga ta kenan Ya Hamza…!?

Da sauri ya katseta cikin girgiza kai.

" Ah ah Hidaya,kar ki rud'a kanki mana,girma ne yazo miki fa,ko baki karanta a islamiyya ba?ai kin san Haila ko?abin da mata suke yi idan sun girma?

Hidaya tayi shiru tana tunani,sai lokacin ta gane yanayin da ta shiga,Ashe haila ce ta zo mata bata gane ba har tayi b'aramb'ara ma,wata dank'areriyar kunya ta rufto mata,ta fad'i kwance a kan gadon tana cukuikuye kanta cikin hijab d'in ta,ji take tamkar ta nutse a k'asa don kunya,ita kuwa me ya shiga kanta har ta kasa ganewa?bayan sun karanta a makaranta sau ba adadi?

Murmushi kawai Hamza yayi ya mik'e tsaye ya fice daga d'akin,har lokacin Umma nan zaune tana jin redio,tana ganin sa ta kalleshi tace.

"In ce ko ta fad'a maka abin da take wa kuka..!?

Yayi k'asa da kai yana fad'in.

" Eh Umma….am…ina zuwa dai "yana fad'in hakan yayi sauri ya fice daga gidan.

Umma ta bishi da kallo kawai cikin mamaki.

Tana nan zaune minti bakwai da fitar sa sai gashi ya dawo da bak'ar Leda a hannun sa,ya zo ya tsuguna gaban ta kansa a sunkuye ya kasa had'a idanuwa da ita,a hankali ya mik'a mata ledar yana fad'in.

" Umma ga sak'on Hidaya,ayi hak'uri a nuna mata yadda zata yi amfani da shi…yarinyar ta cika rud'ewa da yawa ne,ummmm…bari in je waje Faisal na jira na"


Kafin ma Umma tayi wani yunk'uri tuni Hamza ya fece da saurin sa,tayi sakato da bak'ar Leda a Hannu,sai da ya fice sannan ta sauke numfashi a hankali ta kwance ledar Dan duba abin da ke ciki…zaro idanuwa tayi ganin Audugar mata wadda ake tare jinin al'ada da ita wato (Always)…….!


Comment
Share
Vote
Pls

*GARKUWA BIYU*


BY HASSANA D'AN LARABAWA ✍️
Chapter 1 · 0% Book details