← Book details A Duniyata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 47 OF 84

Sashe 47

A Duniyata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

har yanzu tana fuskantar ragowa da kuma tasirin wannan dabi'ar tattare dashi da bata gama barin jikinss ba. Wani irin yanayi me ban tausayi da har yaso taba karatunshi.....boyayyen kuka duk dare da rashin bacci. Ta dauki dogon zango cikin musu addu'a da neman daidaitar rayuwarsu. Tofi rubutu da addu'a dukka kafin lamuransa su fara daidaita. Sai ta fuskanci kyara tsangwama ga duk macen da zata dososhi koda qanqanuwar yarinya ce. Bata fuskanci yadda abun yayi musu!mugun tasiri ba sai bayan wasu shakaru data haifa musu Aminatu amna me sunanta kenan.....haihuwar data tabbatar matsanancin rabo ne,don ko a wasa bata taba tunanin wai zata sake wata aba wai ita haihuwa ba. Da fari tsakaninsa da amna idanu ne kawai,baya ma zama.inda take bare daukarta,ta fahimci kaman wata kakkaifar gaba ce tsakaninsa da jinsin mata,ita kadaice mace cikin miliyoyin mata da take samun kulawa da qauna daga gareshi wanda ita dinma sai da suka debi shekaru yana dari dari da ita. Bata tsananta tuhuma ba,tasan incident din daya faru dashi a baya akan mariya da mariya sune suke hunting dinsa. Wannan abun bai karye ba tsakaninsa da amna din har sai sanda ta fara laulayin haqori. Kashin haqori matsananci daya sanya mata amai da zawo da yaso wucewa da rayuwarta. A ranar a kuma daren har sun fidda rai da ita,tayi wani suma a hannunsa. A ranar taga gigicewa mai tsanani a tattare dashi,shi daya ne yake da qwarin gwiwar daya dinga mata wasu abubuwa don dawo da mumfashinta,sai gashi cikin ikon Allah ta dawo. Tun daga wannan ranar kulawarsa a kanta ya zama na dabanne,sabo ya shiga tsakaninsu,ta tashi ta ganshi a matsayin yaya kuma uban da bata da kamarshi. "Kamar akwai inda zakaje ko?" Anni ta tambayi musaddiq da suke hira da farouq *SU SAKE DAWO MUKU DA WASU SABBIN LABARAI* *_BAYAN WASAN DA AKA BUGA GA WANI SABON WASAN_* *_MIQAQQIYAR TAFIYAR NISHADI_* *_KAFATAWA DA ZAFAFAN MUHAWARA_* *_LABARAI MASU DAURE KAI DA SANYA NISHADI A CIKIN ZUKATAN MASU KARATU_* *ZAFAFA BIYAR* *_MASUBURBUDAR LABARAI MASU CIKE DA HIKIMA DA DEBE KEWA DA WASA TUNANI TARE DA TSUMA ME KARATU DA TSUMAMMIYA KUMA TSAFTATACCIYAR SOYAYYA_* *Hanzarta shiga ayarin ZAFAFA FAMILY(WATO IYALAN ZAFAFA DA BASA GAJIYA DA KASANCEWA DA SU* _TA HANYAR SHIGA RUKUNIN MASU SIYAN LITATTAFANSU KAMAR HAKA_ _QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_ _K'ALBIM Mamuhghee_ _AJIYA A DUHU Billynabdul_ _DUNIYATA Huguma_ _Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_ *hudu 2k* *uku 1500* *Biyu 1k* *Daya 500* _YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_ *09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA* *IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA* *09033181070* *BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK* *ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171* *ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI* *AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA* 89825722 Nousaiba lawali maradi 1000cf *_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_* *_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_* *D U N I Y A T A* *_H U G U M A_* PAGE 46 ____________________________ https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX *_assalamu alaikum warahmatullah_* *_kina ta ganin kaya kala kala online?,kinason siya amma kina tsoron damfara?,tsada ko rashin ingancin kaya?_* *_wannan tsoro da taraddadi ya yanke miki indai da HUGUMA CLOSET_* *_muna da nau'ikan kaya kala daban daban bisa farashin da ba kowanne dan kasuwa ke iya bada kayansa akan hakan ba_* Shadda Laces Atamfa Kayan yara English wears dana jarirai Qawatattun handbags Mayafai Abayas da jallabiyas Inner wears Huluna na maza da mata yara da manya socks Takalma na maza da mata yara da manya Lafayas Sarqoqi agoguna banguls da rings _kai komai daya danganci kayan ado na fita kunya wa dan adam_ _bisa farashin da zaiyi daidai da buqatarka_ *_Me kike jira sallah na gabatowa?,ana can ana ruwan suturu daidai da qarfin kowa?_* *_masu manyan qarfi da matsakaita?_* *_ki dinga siya da kadan kadan kina saka kudin kina tara abinki har sukai sanda zaki karba?,ko ki siya lokaci daya a kai miki_* *_muna aika kaya ko ina a duniya in sha Allah_* *MUNA BONONZA LOKACI LOKACI NA DUKA ABINDA RABO YA TSAGA* *_MASU REPOSTING DA MASU SARI DUKA BA'A BARSU A BAYA BA,KI SIYA KI SAIDA KI SAMU RIBARKI HANKALI KWANCE,BA TARADDADIN INGANCIN KAYA KO WANDA KIKA BAIWA KUDINKI_* *_KIYI JOINING KI TURAWA 'YAN UWA DA ABOKAN ARZIQI_* *_INGANCI RAHUSA GASKIYA DA AMANA SHINE TAKENMU_* _____________________________ Tana tsareshi da ido. Duba daya ya yiwa annin ya fahimci tambayar ta yita ne kawai bawai don tana son sanin amsa daga bakinsa bane....aah,ta yita ne don tanason tunasar dashi wani abu "Kamar zan fita din......amma kuma banason fitar" Ya fada yana kallon qatoton agogon dake manne a bango. "Amma dai ina fata kana sane da girman umarnin uwa ko?,sannan kana sane da girman alqawari......haka kuma uwa uba baka manta dashi ba?" Dukka jikinsa ne yayi sanyi,sai yadan sadda kansa qasa kadan. Lallai ba shakka inda ace dukka iyaye haka suke tamkar anni da zaiyi wuya.....za'a tirza,hakanan za'a sha fama kafin a samu baragurbin yara cikin al'umma. Kai ya jinjina,sai ya soma ture plate din gabansa,ya dauki wayarsa ya sanya gaban aljihunsa ya miqe yana fadin "Sai na dawo" "Allah ya kiyaye......" Anni ta bashi amsa tana satar kallonsa. Tako ta ina ba alamun jin dadin zuwan da zaiyin,ba wani sukuni walawala ko farinciki irin na da a sanda zai hadu da iyayensa. Da kallon tausayi ta bishi dashi har ya bacewa ganinta. Ta janye idanunta tana sauke zazzafar ajiyar zuciya,sai suka hada idanu da farouq dake zaune yana cin abinci a hankali. "Daga musaddiq har muhammad tausayi suke bani har yanzu,har yanzu wannan tabon da aka barwa rayuwarsu yana tare dasu bai goge ba". Kai farouq ke gyadawa yana duban anni "Gaskiya kika fada anni......musaddiq nashi me sauqi ne,ba wanda abun ya yiwa illa matuqa yake kuma taba halayensa da dabi'unshi har yanzu irin fu'ad......akwai fushi saurin daukan zafi da yawa cikin halayensa......shariya rashin son yin magana ko hira da kowa,wanda yawancin lokuta idan irin hakan ta faru nasan abinne ya motsa masa,shi yasa sau da dama nake maida kaina wani iri a wajensa saboda na sama masa farinciki duk qanqantarsa". Kai kawai anni ke jinjinawa,har cikin zuciyarta tana jin ba dadi,abun kuma yana tabata. Wani gauron numfashi ta sauke tana ajiye wayarta data dauko wadda ta kasa juriya tana shirin kiranshi kenan. Kacokam ta aza idanunta ga bakin qofa tana tsumayin qarasa shigowarsa tana jin yadda yake gaisawa da ma'aikatan gidan faran faran. Irin sakewa da ta tabbata idan ya shigo ciki baya iya irinta da ita. Da sallama ta yaye kakkauran curtain din dake bakin qofar ya shigo. Ganinsa kawai da tayi,zuciyarta kuma na ayyana mata cewa wannan din d'anta ne halak malak sai taji wata izza ta sake daduwa cikin kanta "Kina da wannan kadarar.....kina da wannan damar don me yasa zaki bari a qwace miki su cikin sauqi haka?" Ta yiwa kanta da kanta wannan tambayar. Gyara zamanta tayi sosai sanda ya iso ciki,ya zauna saman daya daga cikin kujerun yana dan tsagaita dubansa daga inda take "Barka da dare" Ya furta a nutse,har yanzun baya jin wani sabo shaquwa ko soyayya nata a tattare dashi,yana jinta kamar kowacce baquwa......yana kuma jinta kamar kowanne baqon abu na rayuwarsu. Qoqarin wadata fuskarta da fara'a tayi kaman yadda zuwaira ta shawarceta don samun isa ga burika da muradanta cikin sauqi "Ai na cire tsammani da zuwanka musaddiq......wai dama haka duniya take?,......na zaci komai girman laifin uwa d'a yana iya yafeshi ko?" Ta fada murya a sanyaye. Idanunsa kadan ya daga yana kallonta,ya kasa gamsuwa da ita har yanzu,yana jin inama ace yadda ta furta wadannan kalaman a bakinta haka suke har cikin zuciyarta?. "Kibar wannan maganar maamah,abune daya riga ya shude,kin wuni lafiya?" Ya maida maganar da tambayar lafiyarta "Alhamdulillah.....saidai yayanka ya watsar dani musaddiq,ya barni cikin buqatar rayuwa da abubuwan da a zahiri ya cancanci ace nafi qarfinsu amma suna neman fin qarfina" Ta fada a karye. Mamaki sosai ya sake lullubeshi har ya gaza jurewa sai daya daga idanunsa ya qarewa suturar jikinta da kuma falon da take ciki kallo. Tana cikin ni'ima da wadatar da babu abinda ta nema a rayuwarta ta rasa amma tana kiran abubuwa da dama sunfi qarfinta?. Anya kuwa da kyakkyawa da kuma tsakakkiyar zuciya ta dawo cikin rayuwarsu?,anya wannan tsohon maqalallen halin baya tare da ita?. Shine mutum na farkon da yafi kowa sanin cewa hammansa baya wasa da ci sutura sha muhallinta da lafiyarta,bayan ya dauke duka wannan kuma da wani ajiyayyen salary na dubu dari duk wata,duk da aqa'ida ba wata qwaqwarar buqata guda daya da ashekarunta ta yima rayuwarta saura. Hatta da man fetur da ake zubawa motocinta guda biyu bai daukewa kansa ba,to me take nema sama da wannan cikin dukiyar da aka sameta a sanda ta nisancesu?,cikin dukiyar da aka sameta a sanda ta gujesu?,cikin dukiyar da aka sameta a sanda take can cikin duniya tana kalar rayuwar data zaba?,kalar rayuwar data fifita sama da ta rayu dasu?. "Bana jin akwai sauran abinda hamma ya rageki dashi maamah" Ya gaza jurewa sai daya fadi mata idanunshi tsar a kanta zuciyarsa kuma cike da mamakin furucinta. Idonta itama takai kansa tana kallonsa "Yanzu a naka tunanin a matsayina na mahaifiyar mutumin da ya mallaki kamfanin sarrafa diamond......mutumin da yake da harqalla da manyan kamfanoni da suke a qasashen waje.....qasashen wajenma manyan qasashen da suka tumbatsa ta fannin tattalin arziqi da qarfin mulki da iko.....mutumin da yake noma kaso mafi tsoka na dukka abincin da Nigerian dama Africa gaba daya suke ciyar da al'ummarsu amma ace abinda zai iya cira ya bani na zallar kudi shine dubu dari?" Ta aje masa tambayar ranta yana fara mata zafi amma tana danneshi. Ci gaba yayi da kallonta yana fahimtar abubuwa da dama tattare da ita,a yau kuma a yanzun sai yaji shima ya shirya tambayarta "Idan har ya miki kadan kuma hamma bai kyauta ba......wacce buqata kike da ita da zakiyi da kudi?" Tambayar sak irin ta dan uwansa kenan......amsar kuma da ba zasu taba samunta a bakinta har abada "Musaddiq......yanzu bayan ci sha sutura da biyan duka sauran buqatu da zasu taso Shikenan iya abinda nake da buqata a matsayina na 'yar adam?,bayan ina da d'an da a kullum idan zai bani kyautar million daya bazaiji komai ba a jikinsa daga abinda ya mallaka?" "Maamah......kin taba zuwa da wata buqata kinaso ayi
Chapter 47 · 0% Book details