← Book details A Duniyata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 19 OF 84

Sashe 19

A Duniyata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

sawunki a likkafa.....ko kuma hukuma ta matsaki ki fito dasu" Idanunta ta watsa masa tana sakin murmushi "Kasan a inda kudadenka suke?,za kuma ka iya zuwa karba din idan na gaya maka?" A tunzure cikin fushi da yadda takeson maida maganar wata mara alfanu ko muhimmanci ya kalleta "Duk duniya akwai wanda ya isa ya hanani karbar haqqina?,akwai wanda ya isa ya cimin haqqina ban karba ba?" "Kwantar da hankalinka mana...." Tace dashi still tana murmushi,saita dafe kwandonta ta soma takawa tana nufar ficewa daga gidan kuma tana fadin "Gidan marayun nan......a wannan ranar kowanne yaro ya rabauta da duk wani abu na buqata da bashi dashi,suttura kayan ado na 'yanmatan da kuke sakawa ana musu dauki d'ai d'ai cikin dare ana kai muku su gidajen shaqatawarku da hotels kamar yadda ka gayyaceni nima zuwa naka dakin hotel din......kana iya zuwa ka karbi komai dake hannunsu ka sanyashi a kasuwa ka maido kudinka......muddin kuma ba zaka iya hakan ba,to ina baka shawarar ka fita daga rayuwar SABREEN......ka kuma daina bibiyarta......idan bakaji ba kuma......zan sake sakaka fidda wasu kudaden masu ciwo da baka shirya fitarsu ba kamar dai wancan lokacin" Ta qare maganar tana kaiwa qarshen wajen ta karya kwana tana niyyar bacewa ganinsa. Daya biyu uku yahada dukka yaga basuyi masa daidai ba. Wani sashe na zuciyarsa ya soma zugashi da "Ta yaya kana tsaye qaramar yarinya me qarancin shekaru zata nemi raina maka hankali?". Ya samu kansa da kansa da tuhumar kansa tare da ganin tsananin baike da wallensa. Wannan tunanin kadai ya qara masa qaimi,ya taka qafafunsa cikin azama da qwarin gwiwa ya soma rufa mata baya lokacin da takeji a ranta ta kammala siyan duk wani abu da suke da buqata ita da 'yan uwanta,wanann ya sanya ta nufi gurin biyan kudin kai tsaye "Inda zan baka shawara......zaifi kyau ka koma ka tafi sabgaka...." "Saboda ke kike nema na bani ke nemanki ba?,saboda nine mai laifi bake bace?" Hankali kwance ta maqale kafada tana sakin siririn murmushi "A'aha.....ba don dukka wadannan dalilan bane suka sanya ni na baka wannan shawarar ba......na baka ita ne don gudun kada ALLURA TA TONO GARMA" "Ni dake zanga wanda allurarsa zata tono garma......" "Ba laifilaifi malam naseer....." Abinda tace dashi kenan tana ci gaba da tattaki a bayanta. Yau yanason ganin qarshen gudun ruwanta......yanason yasan ita din wace?......da waye take tare?,su waye suka dauki nauyinta?. Waye ya turota?,maqarqashiya ce ko kuma hadin baki?. Hakanan yaci gaba da rufa mata baya tamkar me tsaron lafiyarta ko wanda aka bashi aikin kula da ita. Har cikin zuciyarsa yakejin yau zai nuna mata shi waye,zai kuma tabbatar mata tayi mahaukacin gangancin kuskure data shiga hanyarsa. Mutum biyu suka samu ana lissafa kayansu jikin qaramar na'urar dake da alhakin qididdige fitar kaya cikin katafaren shagon. A hankali ta tsaya daga bayan matar wadda bata iya ganin ainihin fuskarta,saidai shigar atamfar chiganvy gold mix match da wani irin danyen lafiyayyen lace da aka yiwa qawataccen dinkin buba da zani ya fito da kamalarta da kuma cikar siffarta. Tsaye yake daga gefanta,matashin da duka duka shekarunsa ba zasu haura ashirin da takwas ba. Ya bata dukka hankalinsa yana sauraren maganar da takeyi dashi cikin muryarta dake bayyanar da tsantsar kamalarta da cikakkiyar nutsuwar ruhi data halitta. Yanayin yadda ya rusuna ya bata hankalinsa yana saurarenta kadai zai bayyana maka zallar ladabi da kuma ganin girmanta da yakeyi,akwai kuma tag idan ka lura sosai daga gaban aljihunsa dake bayyanar da cewa shi din ma'aikaci ne a wani guri na daban. Mai matsakaicin tsaho ce,hakanan me jiki ce saidai ba qiba me yawa cancan ba,ta lullube saman kanta da 4D Vail me asalin kyau da aka zubawa duwatsu masu daraja akayi adon jiki dasu. Sassanyan qamshinta ya dinga tasowa a hankali daga jikinta zuwa hancin sabreen dake tsaye daga bayanta tana kallon tulin kayan siyayyar da aketa jera mata cikin ledar dake dauke da tambarin store din. Hannunta dake dauke da wasu kyawawan banguls masu sheqi ta miqawa ma'aikacin gurin tana cewa "Bansan me yasa suke son mu'amala da wannan katin bankin ba,duk sun lalace da lamarin cashless" Murmushi ma'aikacin ya saki cikin tsananin girmamawa "To ai hajiya yafi sauqin sha'ani ne" Kai ta gyada a hankali tana furta "To Allah ya kyauta". A nutse ta maida dubanta ga saurayin,tun kafin tace wani abu ya sake matsowa a ladabce yana bata hankalinsa "Ka kiramin wancan yawalen da kuma wancan acicin suzo mu wuce kafin rana ta sake dagawa" "Okay to in sha Allah" Ya amsa mata yana zaro wayarsa daga gaban rigarsa,yayin da ta fara takawa cikin nutsuwa tana ficewa daga gurin hadi da gyara yafen mayafinta dake qoqarin zamewa. Wucewar tata ya bawa sabreen damar matsowa gaba don a lissafa mata nata kayan "Ji mana.......zaki dawomin da duk abinda kika san kin sace ko kuma saimun dangana da hukuma?" Hannayenta ta goye a qirjinta tana kallon qofa yadda mutane ki shige da ficensu hankali kwance. Yana da ban mamaki......saidai ita din ta fishi abun mamaki. Inda yasan meta taka a kansa......inda tasan cewa kafataninsa.....zahirinsa da badininsa a tafin hannunta yake da baiyi gigin matsawa rayuwarta ba har ya matso gareta har haka ba. A nutse ta waiwayo ta zube masa farare tas din idanunta masu matuqar jan hankali da fusgar tunanin me tunani "Kana sha'awar yin gaba da gaba da hukumar ne?" Ta masa tambayar idanunta a tsaye car tsakiyar nashi. Idan ya kira kansa gogaggen cikin duniya baiyi qarya ba.....muddin kuwa ya kasance hakan yana ganin mugun ganganci ne zaiyi ya gaza samun fikirar karantar mutum daga yanayin kallo zuwa lafuzan bakinsa ba....... "Kina tunanin abune me wahala a gareni?" Ya amsa mata yana mamakin yadda wannan mugun kwarjinin nata yake taka masa burki,kaifin idanunta ke hanashi daukan mataki tare da aiwatar da abinda yayi niyya.......abinda zuciyarsa ke shawartarsa. "Ko daya....daidai ne kuma" Ta amsa masa tana dauke duba da hankalinta daga kanshi tana maidawa ga ma'aikacin wanda ya kammala lissafin yana gaya mata adadin abinda zata biya. "Okay" Ta furta hankali kwance tana maida dubanta ga daya daga cikin ma'aikatan dake taimakawa da wadanda sukayi siyayya me yawa kamarta "Ko zaka fitamin dasu gate na biyu?" "Okay hajiya" Ya fada yana ajjiye qaramar calculator dake hannunsa yana qarasowa gurin tare da jira a gama sanya dukka kayan cikin leda. Sake Waiwayowa tayi gareshi karo na biyu. Kallon da tayi masa ta fahimci yakai matakin qarshe a iya haqurinsa "Malam naseer......ka shirya biyan duka bill na siyayyar sabreen ko kuwa tunda kai ka kawo qafafunka duk da gargadinka da tayi?" "Sabreen?" Ya maimaita sunan yana kallon idanunta. Kiran sunan sabreen da tayi a maimakon basma shi ya batar masa da tunani cikin taqi qanqani. "Zai biya duka bill din.....na gode sosai" Ta fadiwa ma'aikacin "Naga uban wanda zai sakani biyan kudin nan......na fahimci na sakar miki fa da yawa" Ya furta da zafi sannan a zafafe ya biyo bayanta. Ya tsammaci zata nemi guduwa ko ta gudu dinma,amma ga tarin mamakinsa tun bai qarasa isowa gareta ba taja cak ta tsaya tana sauraron isowarsa. "Ka samu aminci game da haramtattun kayanka da aka aiko maka dasu ta cikin jirgin ruwan dake tsakanin River Benue da riba niger?.......ko kuma ka shirya aci kasuwar wannan sirrin da jami'an tsaron dake neman kayan tamkar yadda mutuwa ke neman ruhi?". Kamar wanda aka sanyawa sasari akan tsaida haka yaja wani wawan burki. Kallonta yakeyi da madaukakin mamaki. Wanne irin hadari ne da ita har haka?. Wanne nisan ji da gani ne da ita?,nisan binciken da ya bata damar gano birnannen sirrinsa da ko matarsa da suke kwana daki daya su tashi daki daya bata sani ba?. "Ka biyasu kudin siyayyarsu duk yadda suka buqata,na barka lafiya Alhaji Naseer" Ta qarashe maganar tana takawa hankali kwance tana fita kwata kwata daga wajen. "Malam qaraso ka bada kudin......ta atm ne ko cash zaka bada?" Muryar ma'aikacin ta katseshi daga bin burbushin hanyar data wuce da kallo ya juyo zuwa wajen biyan kudin yana sauke wani irin gauron numfashi me nauyi da zafi cikin tsananin mamaki da tsoro. *SU SAKE DAWO MUKU DA WASU SABBIN LABARAI* *_BAYAN WASAN DA AKA BUGA GA WANI SABON WASAN_* *_MIQAQQIYAR TAFIYAR NISHADI_* *_KAFATAWA DA ZAFAFAN MUHAWARA_* *_LABARAI MASU DAURE KAI DA SANYA NISHADI A CIKIN ZUKATAN MASU KARATU_* *ZAFAFA BIYAR* *_MASUBURBUDAR LABARAI MASU CIKE DA HIKIMA DA DEBE KEWA DA WASA TUNANI TARE DA TSUMA ME KARATU DA TSUMAMMIYA KUMA TSAFTATACCIYAR SOYAYYA_* *Hanzarta shiga ayarin ZAFAFA FAMILY(WATO IYALAN ZAFAFA DA BASA GAJIYA DA KASANCEWA DA SU* _TA HANYAR SHIGA RUKUNIN MASU SIYAN LITATTAFANSU KAMAR HAKA_ _QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_ _K'ALBIM Mamuhghee_ _AJIYA A DUHU Billynabdul_ _DUNIYATA Huguma_ _Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_ *hudu 2k* *uku 1500* *Biyu 1k* *Daya 500* _YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_ *09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA* *IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA* *09033181070* *BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK* *ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171* *ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI* *AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA* 89825722 Nousaiba lawali maradi 1000cf *_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_* *_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_* *D U N I Y A T A* *_H U G U M A_* *Arewabooks@:Huguma* PAGE 21 https://chat.whatsapp.com/DT97XBDyEfyEwniN0a09Cz __________________________ *_ALBISHIR A GAREKU!!_* *_SHIN KUNSAN UMMUMAHNOOR LUXURIES TA TANADAR MUKU INGANTATTUN KAYAN ADO NA FITA KUNYA KUWA?_* *_KAM AR SU_* Atamfofi Laces Shadda Materials Takalma Jakunkuna Mayafai Trolley Sarka da dan kunne Oil perfumes *_karki tsaya sanya har ayi babu ke,maza garzaya ta nan_* Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries *_inganci da kwalliya shine muradinmu_* ____________________________ Sanda take sallamewa saita samu kanta da zama sosai a inda ta idar da sallar tana irga tasbihi da yatsun hannunta,yayin da kunnuwanta kadan kadan ke jiye mata tasbihin matar dake yinsa can qasa qasa,saidai lokaci lokaci yana qwacewa ya fito,har zuwa sannan bata waiwaya ko sau daya ta kalli fuskarta ba,amma daddadan turarenta bai fasa silalowa zuwa cikin hancinta ba. Wayarta ta matsa haske ya bayyana ta duba lokaci. Tasan ko busari bai iso ba to dab yake da isowar,ta maida wayar ta ajiye tana kallon sararin cikin masallacin da babu kowa saisu uku. Daidai sanda zata dauke idanunta dai dai sannan taji matar dake gefan nata taja wani irin
Chapter 19 · 0% Book details