Sashe 22
A Duniyata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
din suna jin gidan kamar babu kowa a ciki saisu. Cikin jikinta ta rungumesu kaman yadda ta saba,sannan nadra din ta soma jan daya daga cikin ledojin. Duqawa haneefa tayi itama zata dauki guda daya nadra din ta tsaidata "Bafa zaki iya dauka ba" Cak ta tsaya tana turo baki "Anty wai da gaske bazan iya ba?" Murmushi ya qwace mata saboda hangen farincikin da tayi daga idanuwansu. "Zaki iya auta" Ta furta tana bude ledar,jakankunan maggi da suka qarawa ledar nauyi ta ajjiye a gefe sannan ta daure mata ledar tana cewa "Bismillah auta aiba raguwa bace" Hakan ya faranta mata rai,ta sukunya ta dauki ledar tana cewa "Ita yaaya nadra kullun komai sai tace bazan iya ba,batasan na fita qarfi ba" Daga sabreen din har nadra data riga tayi gaba suka saki dariya. Idonta a kansu har suka mata nisa sannan ta tsugunna a nutse ta kwashe maginta,ta fara takawa tana binsu zuwa Qofar da zata sadasu da babban tsakar gidan nasu. Zuciyarta a karye tana hangen haneefa daga nesa. Ta sake sakin boyayyen murmushi,akwai jarumta me yawa dangane da yarinyar,da alama zuciyarta dakakkiya ce kuma a tsaye take. Dab da zata shiga din su kuma suna yunqurin fitowa su biyu. A hankali taja da baya tana basu hanya bayan ta sauke idanunta qasa,saidai duk da hakan da tayi bai sanya ta tsira daga garesu ba. Qasan ranta akwai haushi takaici da kuma fushin rashin samun nasarar da batayi ba a safiyar dazu. "Ke ya kamata mu bawa hanya ta wuce ai......gagara" Ta furta tana qanqance idanu idanun nata fes akan Fuskarta da kuma abinda ta riqo a hannayenta. A hankali daada dake tsaye daga bayan bibo din ta gewayo ta gefanta tana cewa "Muje mana bibo,yamma tana sakeyi" "K'nnnn,gaskiya dai,fitar dare ai 'yan kwalta" Ta fada tana zakudawa tare da bin bayan daada bayan ta waiwayo ta ajewa sabreen wani kallo. Da kallon itama ta bisu,sam ko kadan daada bata nuna ta santa ko tasan da zamanta......nata da sauqi don kome za'ayi a kansu baka taba jin ta tofa nata........batasan wanne matsayi zata aje daada ba a kanta cikin gidan,ta bibo kuwa fitacciya ce ainun,muddin magana ce a kansu,Ala cuta ala magani har abada bare ya fiye mata su,koda kuwa wanne irin nau'in alkhairi zasuyi mata ko zasu kowa cikin gidan. Ajiyar zuciya ta saki tana ci gaba da kutsa kanta cikin gidan tana ta qoqarin kauda abinda takeji a yau yana taso mata qasan zuciyarta. Abune da take ganin bai kamata ta damu ba......ita din dai tasan kanta,ta yarda da kanta,sannan tasan wacece ita?,to me ya rage?,me take nema da shaidar mutumin yau?,mutanen dake rayuwar a DUNIYARta sam basu cancanci ta basu damuwarta ko tayi yunqurin gamsar dasu game da WACECE ITA?. Da sallama a bakinta ta sanya qafafunta cikin falon nasu,komai a tsaftace a kuma tsare,madaidaiciyar iska me dadi tana kai kawo tsakanin falon ta wutar sola dake maqale a dakin. Sanda take zubewa saman kujera daidai lokacin haneefa ke isowa gabanta da school bag dinta da wani.littafinta a hannu "Anty munyi C.A,a cikin talatin na samu ashirin da takwas......sannan an bamu assig....." "Kai haneefa haba" Nadra ta fasa tana hade fuska. Murmushi ta saki,saita dagawa nadra hannu "Qyaleta,zo.nan auta" Ta kirata sanda huda ke qarasowa ta aje mata ruwan pure water me sanyi guda biyu "Ki aje komai sai zuwa anjima zan duba,duka yau tare zamuyi assignment din kinji?" Kai ta daga tana murna ta cilla da gudu ta koma bedroom dinsu da jakar. Sai data bula ruwan sannan ta kalli huda "Me yasa baku wuce islamiyya ba?" Gyara zamanta kadan tayi sannan tace "Jiran dawowarki mukeyi" Rabi tasha ruwan ta ajjiye tana sake karantar wani yanayi na daban daga huda din "Sai na dawo sannan zakuje Islamiyya huda?,yaushe aka fara wannan tsarin a dakin nan?" Tadan furta a zafafe tana dubanta. Qasa da kant huda din tayi,ba kasafai take ganin fushi ko fada dava Fuskarta ba,to amma duk sanda tayi din ya tabbata laifi sukayi mata babba. "Kiyi haquri.na tsaya dora abinci ne" Sassautowa tayi kadan tana sauke boyayyen numfashi. Bata qaunar abinda zai zaunar dasu cikin gidan ko kadan ballantana idanuwa ko kunnuwansu suji ko suga abinda rayuka zasu baci. Hakanan koda wasa bata qaunar suyi wasa da makaranta. Tana jin ciwo idan ta tuna iya inda matakin karatunta ya tsaya a shekaru ashirin da daya hudu da take dashi a duniya,wanda a yanzun kimanin shekaru hudu kenan rabonta da wata bawa wai makaranta. "Ku shirya ku wuce,duk da lokaci ya fita amma baiyi nisa ba ai" Ta fadi tana duba agogon hannunta sannan ta fara zareshi daga hannunta. Tana zaune dukansu suka gama shiryawa cikin fari qal din uniform da baqar doguwar riga daga sama. Hankalinta bai dawo daidai ba sai data tabbatar sun fita a gidan. Kai tsaye ta rage kayan jikinta ta zura sassauqar riga sannan ta wuce kitchen din dake falon tana duba girkin da huda ta fara yi. Komai yayi daidai,dole ta sanya huda ta koyi girki tun batakai minzali ba. Tana fita ta bar mata nadra da haneefa,tun bata san ya zata kula dasu ba har ta koya. Ko a yanzun idan huda tayi girki,itama tayi sai na huda ya dara nata. Sai data kammale komai sannan ta daura alwalar sallar la'asar,sanda ta idar idanuwanta sun fara nauyi,tana zaune daga saman abun sallar tana dan murxa idanunta. Ba baccin take buqatar yi ba a yanzu,tana son magana da jib ne. A yawancin lokuta a irin wannan lokacinne take samun tattauna maganganu ire iren wadannan,sam bata yarda tayi komai bisa idanunsu,bata taba bari ta rab'a lamarin rayuwarsu da nata rayuwar,komai tana tsaidashi ne iya muhallinsa. Hakanan tana hamma ta miqe ta koma daki. Locker gefan gadonta ta jawo,ta fidda madaidaiciyar baqar jaka dake dauke da mini laptop dinta,sannan ta zaro wayarta dake cikin jaka ta sake dawowa cikin falon. Kalmomin sirri ta sanya ta bude laptop din,sanna ta maida hankalinta akan wayarta tana barin laptop din ta daidaita. Maadanar lambobi ta shiga bincikawa har ta kawo kan sunanshi,ta danna masa kira tana aza idanunta akan screen na laptop din tana duban hoton daya mamaye fuskarta. Hoto ne da bata gajiya da kallonsa,duk sanda ta dubi hoton sai taji kamar tana tare da ita,kamar zata kirayeta ta amsa,kamar zata iya jin kadan daga radadin da take fuskanta,kamar zata damqi hannunta su fuskanci wannan JUYAYAYAR DUNIYAR su kuma kutsa cikin birkitacciyar rayuwarta su kawo daidaito. Daga wayar da akayi shi ya katse mata tunaninta,ta daidaita idanunta da suka fara zugi kadan kadan da alamun son tara ruwan hawaye "Aikin jeeb ya taso?" Boyayyen murmushi ta saki tana gyada kai "Sosai......ka zama kusa da na'urarka......inason sanin wayeshi" "An gama" Ya fada a taqaice "Aikin dazu fa?" Ta sake tambayarsa "Adda ya zama tsohon tarihi......bashi ba......ko bankinsa basu isa susan ya akayi kudin sukayi fiffike ba bare inda suka sauka" "Yayi" Ta amsa masa a taqaice tana sauke wayar daga kunnenta. Sake duba bagaren kira tayi a nutse har ta iso number wayarsa. Ta tsaya kadan tana kallon numbers din. Daga yanayinsa da yanayin shigarsa ta tabbatar ba qaramin mutum bane. Amma ko daya batajishi koda a gefan zuciyarta bama bare a shiga wani batu na daban. Hasalima yadda yaso bata mata lokaci ne yafi bata haushi,kalaman bakinsa kuwa aqalla taji masu kamanceceniya dasu a bakin gomman maza......maza iri daban daban,masu mabanbantan halaye da dabi'u. Tana jan system din kira yana sake shigowa. Ta dora zagayayyun idanunta ga fuskar wayar tare da zubawa numbers din idanu kamar me nazari. Batasan wadanne irin zukata suke dasu ba.......a sanda sukaso abu suna zamewa tamkar wadanda ba zukata a qirjinsu,tamkar wadanda hankulansu ke zamewa daga gangar jikinsu,idanuwansu da dukka kunnuwansu suna rufewa ruf izuwa ga cikar muradinsu. Dukka layukan da tasan zasu zame mata damuwa ta ciresu kwanaki biyu kenan,ta kuma tabbatar akwai masu nemanta da yawa. Qaramin tsaki taja ta saka hannu ta jawo wayar,ta daga tana karawa a kunnenta *SU SAKE DAWO MUKU DA WASU SABBIN LABARAI* *_BAYAN WASAN DA AKA BUGA GA WANI SABON WASAN_* *_MIQAQQIYAR TAFIYAR NISHADI_* *_KAFATAWA DA ZAFAFAN MUHAWARA_* *_LABARAI MASU DAURE KAI DA SANYA NISHADI A CIKIN ZUKATAN MASU KARATU_* *ZAFAFA BIYAR* *_MASUBURBUDAR LABARAI MASU CIKE DA HIKIMA DA DEBE KEWA DA WASA TUNANI TARE DA TSUMA ME KARATU DA TSUMAMMIYA KUMA TSAFTATACCIYAR SOYAYYA_* *Hanzarta shiga ayarin ZAFAFA FAMILY(WATO IYALAN ZAFAFA DA BASA GAJIYA DA KASANCEWA DA SU* _TA HANYAR SHIGA RUKUNIN MASU SIYAN LITATTAFANSU KAMAR HAKA_ _QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_ _K'ALBIM Mamuhghee_ _AJIYA A DUHU Billynabdul_ _DUNIYATA Huguma_ _Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_ *hudu 2k* *uku 1500* *Biyu 1k* *Daya 500* _YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_ *09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA* *IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA* *09033181070* *BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK* *ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171* *ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI* *AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA* 89825722 Nousaiba lawali maradi 1000cf *_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_* *_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_* *D U N I Y A T A* *_H U G U M A_* *Arewabooks@:Huguma* https://www.arewabooks.com/book?id=675041625c3130f457519997 PAGE 24 ____________________________ *_ALBISHIR A GAREKU!!_* *_SHIN KUNSAN UMMUMAHNOOR LUXURIES TA TANADAR MUKU INGANTATTUN KAYAN ADO NA FITA KUNYA KUWA?_* *_KAMAR SU_* Atamfofi Laces Shadda Materials Takalma Jakunkuna Mayafai Trolley Sarka da dan kunne Oil perfumes *_karki tsaya sanya har ayi babu ke,maza garzaya ta nan_* Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries *_inganci da kwalliya shine muradinmu_* ________________ ____________ "Ranki ya dade.....girmanki ne ai" Idanunta ta lumshe sannan ta budesu,shima dai kaman sauran,gwanayen dadin baki da iya tsara mace,abinda basu da masaniya akai....ya zuwa yanzu babu wani d'a namiji da yake burgeta duk duniya. Sunan soyayya kawai da labarinta tana daukanshi a mazaunin wani wasa ne.....wasa da qwaqwalwa da wani salo na batawa kai lokaci. Ya'aqoub,daya daga matasan mazan dake sharafinsu,kuma giyar soyayya da ta sha'awar sabreen suka yiwa qawanya. Daya daga cikin mazan da sukejin zasu iya kashe komai......zasu iya bada komai,hakanan zasu iya salwantar da komai saboda ita "Ayimin afuwa nasan wataqila nazo da takura......ba wani abu nake bida ba illa a bani dama zan turo dan saqo da aike" "Ka wuni lafiya?" Ta katseshi ya hanyar tambayar lafiyarsa. Wani boyayyen numfashi ya aje,daya daga