← Book details Tarayya Part One Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 49 OF 51

Sashe 49

Tarayya Part One Complete Hausa Novel · about 8 min read

Khaleefa ne yakalleta cikin mamaki Dr Edward kuwa jinjina mata kai yayi alamar ta kula da maheer din yana buqatarta fiyeda koyaushe.

Shikuwa idanuwansa na ganinta baisan sanda ya sake fadawa jikinta yana qoqarin tsaida hawayensa saidai Sam basu tsaiduba saida suka zubo ya sake qanqameta yana cewa,
Suhailat please pray for me wlh zuciyata zafi takeyi I just can't live without her sbd wannan ma baida banbanci da mutuwa agareta.

Murmushin tausayinsa tasaki cikin sanyin murya tace,
Insha Allah zata warke
Nayi maka alqawarin zamowa majingini agareka duk lokacinda kake buqatata wannan alqawarin yananan haryanxu kuma nayi alqawarin cika makashi har qarshen rayuwata kuma zan tayaka jinyarta harta ji sauki sbd sonka shine qaddarata maheer abdulshams..

'Dagowa yayi kalleta da idanuwansa itama hawayen takeyi tana murmushi ahankali yaji wata irin soyayyarta mai tsafta tashiga zuciyarsa akaro na farko cikin wata irin rawar murya yace,
I love you suhailat sbd kece hasken rayuwata dakike tallafoni koyaushe.

Wasu hawayene suka gangaro mata ta rintse ido tana kwabar zuciyarta dake neman shegala da kamansa datasan ta samesune sbd nuna qaunarta ga rumanah saidai matuqar qaunarta ga rumanah zata jawo masa soyayyar mijinta to tabbas ta shirya samun soyayyar mijinta ta hakan.

Duk yanda ya 'daga hankalin likitocin asibitin akan abinda sukace dole ya dangana yadauki qaddara sbd result din dayane.

Ko ammy saidata kwana ta yini tana kukan halinda rumanar ke ciki da Wanda yashiga sbd gabaki daya ya birkice musu ko abinci sai ammyn tayi kuka yake iya shan abu mai ruwa ga suhailat data zamo batada wata hidima saita kula da dukkaninsu sbd sundawo gida.

Idan yazo ya zauna kusada ita haka zai riqe hannunta cikin nasa ya qura mata ido
Itadai hawayene kawai ke iya gangarowa ta gefen idonta musamman idan ammy tasata gaba tana kuka kokuma shi idan yazo ya zauna yasaka gaba ya qura mata ido tana iya hango mawuyacin halinda yake ciki.

Ranarda su hajiya yakurah suka iso aranar kuka yadawo sabo ganin halinda 'yarsu dasuke 'dokin gani take ciki...

Ko alhaji babaye dake dattijo saida ya zubarda hawayen baqin ciki da farin ciki.

Akwance take itama amma hawayene keta bin gefen fuskarta suna zuba Wanda hakan yaqara bawa kowa tausayi.

Duk da akwai Carolina sosai suhailat ke wahala sbd lalurar rumanah din.

Kusan satinsu alhaji babaye biyu kafin shi ya koma yabar haj yakurah dataqi dawowa tana jiran isowar mijinta dazasu tafi tareda rumanah sbd gwada nasu na addinin.

Satin alhaji babaye daya da tafiya alhaji mukhtar mijin haj yakurah ya iso kallo 'daya yayi mata yagano lalurarta Allah takeson akomawa sbd lalurace ta iska nan take suka yanke shawarar tafiya da ita maheer kai tsaye ya nuna rashin amincewarsa
Saidai ammy dataga yana mutuwar tsaye kullum sbd lalacewa da rayuwarsa ke nemanyi dan ko aiki bai taba fitaba koyaushe yana gida ga suhailat data zamto abar tausayi gurin qoqarin kulawa dashi da rumanah duk ta rame tausayinta da qaunarta yasa kai tsaye ta zaunar dashi cikin nutsuwa ta fahimtar dashi kuskuren dayake jefa rayuwarsa da iyalinsa ciki dan haka yabar rumanah aje da ita ya tsaya ya gyara mu'amalarsa da rayuwar aurensa da suhailat.

Sosai jikinsa yayi sanyi kuma yasan matuqar yanason gyara rayuwar iyalansa ta inganta saiya boye soyayyar rumanah kwata kwata dan haka zai danne Zuciyarsa yafara daga yanzu.

Da haka ya amince aka tafida rumanah din amma hardashi suka tafi saidaya kwana biyu yadawo dan qoqarta gyara mu'amalarsa da suhailat.

Koda yadawo su ammy da jakadiya tareda abeel sun komawarsu Libya dan haka gidan dagashi sai suhailat sbd su amah ma suna Mali tabarosu dama itakadai tazo.

Aranar daya dawo lafiyayyan tarba tayi masa cikeda Dari darin yanda zai dawo yayi rayuwa a inda babu rumanah.

Ganin yanda take kama kanta dashi duk sai yaji ya muzanta ya tattaro jarumtarsa ya danne abinda ke ransa ya riqo hannunta ahankali tareda jawota jikinsa yana kallon fuskarta dake kallonsa yasaki qayataccen murmushi yajata suka zauna bakin gadon dakinta daya shigo yasameta hartayi shirin bacci zata kwanta.

Kallonsa takeyi tanason gano damuwarsa saidai takasa ganin komai sai murmushin dayake sakar mata
Wani irin sanyi da farin ciki taji na shigarta ahankali kenan kalamansa daga zuciyarsa suka fito lokacinda yafada matasu.

Rungumesa tayi da sauri tana sakin hawayen farin ciki ta murmushin jin dadi.

Dagota yayi tareda zare mata riga yana murmushi yace,
Banyi wankaba so yau kece zakiyi wannan aiki.

Noqewa taso yi tana murmushi yayi saurin riqeta yana kallon cikin idonta ya girgiza mata kai ahankali yace,
Don't make that mistake again suhailat.

Kallonsa tayi tareda jinjina kai takama hannunsa ta nufi hanyar toilet dinta dashi suka shige.

Aranar wata irin rayuwa suka gudanar data mantarda suhailat dukkanin damuwarta ta dah inda sukai alqawarin dora sabuwar rayuwar aure ta fahimta,soyayya qauna da aminci atsakanin su uku da 'yayansu daga yanxu.

Ahankali ake gudanar da adduoi da sauran abubuwan addini tareda sauke al-qur'ani da sadaka ana fatar samun sauqi.

Kulawa sosai da wata irin qauna da soyayya suke mata kaf zuriar banda zuriar gidansu aqeel data gama tarwatsewa babu wani nakamawa acikin zuriar gidansu shiyasa koda sukaji 'yarsu bulama tadawo kuma a nakashe kota kan zancen basubiba.

Su kuwa haj yakurah tamkar 'yar data haifa da cikin ta takejin rumanah duk wata kulawarta da dukkanin hidimarta takoma ta rumanah shima alhaji babaye kullum saiyazo gidan sbd yayi yayi tabari rumanah takoma gidansa taqi yarda tabari.

Watanta hudu a Nigeria yazo dubata babu adadi duk tareda suhailat suke zuwa Wanda itama tanajin farin cikin ganinsa da suhailat sbd ganin hankalinsa ya 'dan kwanta sosai duk sukazo idan zasu tafi daurewa kawai yakeyi yakoma sbd alqawarin adalci daya daukarwa kansa.

Ammy kuwa kusan tamafi maheer din zuwa kuma takan dade idan tazo.

Ahankali tafara samun sauqi sbd wasu gurare dasuka fara motsawa ajikinta Wanda hakan ba qaramin farin ciki da qwarin gwiwa yasakasuba nan aka sake maida himma ga sauke al-qur'anai da sadaka da adduoi.

Ba'a rufa wata biyu da fara motsinta ba tafara magana ahankali har tana iya tashi zaune da kanta ta tashi.

Lokacinda wannan saqon ya iso masa aranar suhailat harda hawayen farin cikin ganinsa cikin tsananin farin ciki mara misaltuwa tayi sbd Sam kasa boye farin cikinsa yayi.

Kafin sati biyu dukkanin kuzarinta sun dawo lafiya kalau saidai bata iya komai da sauri ko qarfi Wanda hakan shima ahankali zai dawo.

Washe garin ranarda umma yakurah da ammy suka fada masa samun lafiyarta yatafi wannan karon suhailat qin biyosa tayi sbd ganinta kusa zai hanasu nuna kewar junansu.

Sai dare sosai ya isa Wanda tareda khaleefa dazaije gurin nuratu sukayo tafiyar dole suka sauka masaukinsu kai tsaye sai washe gari suka nufi gidan guraren qarfe goma shima sbd khaleefa daya hanasu tafiya tunda safe.

A babban palo suka tararda su umma da ammy harmada Jakadiya da sabuwar mai rainon abeel suna ganinsa umma tayi murmushi sbd tanajin dadi da farin cikin yanda yake tsananin qaunar rumanah dinsu.

Ammy ma dariyar tayi masa inda aka gabatar musu da abincin breakfast saidai sunyi breakfast already.

Duk yanda yaso ganinta qin barin su kebe umma tayi qarshema anan palo tasa Nana aishat 'yar autarta taje kairawo rumanah din tajima kafin yafito sanyeda dogon hijabi har qasa daya matuqar yimata kyau sbd wannan ne karo na farko daya ganta sanye dashi itama anan din takoya sakashi sai tanajin dadinsa.

Kasa 'dauke mayun idanuwansa akanta yayi musamman yanda ta canza sosai takoma kamar ba rumanarsaba datasha wahalar rayuwa dan lokacin.

Wani irin murmushi yasaki Wanda shikadai yasan yayi abinsa sai ita data gani ta dauke kai tana gaidasu cikin yarensu sbd har gwara khaleefa yafara son koyar yaran Hausa sbd nuratu dayake yawan ziyarta shikuwa haryanxu yakasa koyan komai.

Koyaushe da turanci yake magana dasu umma da alhaji babaye hakama ammy.

Kwanakinsa uku amma Sam umma taqi barinsu kebewa hakan ya matuqar dama lissafinsa shiyasashi tattarawa yakoma gashi ko waya basayi bare yarage zafi.

Koda yadawo suhailat ta lurada bai cikin dadin rai da walwala saidai batai shishigin tambayaba tunda bai shiga haqqintaba.

Bayan sati biyu kai tsaye yakira alhaji babaye yasanardashi yanason rumanah tadawo tunda taji sauqi koda alhaji babayen yayiwa umma magana kai tsaye tace sai wani wata sbd zasuyi walima dakuma 'yan shirye shirye.

Baisoba amma sbd ammy data basa hakuri saiya bari din badan yasoba.

Hidima sosai da gyara irin nasu na asalin 'yan Maiduguri.

Taron biki sosai akayi tamkar yanxune zaa daura mata aure akai walima da yinin biki na alfarma inda ko nanma 'yan jarida basuyi qasa da gwiwaba sunxo ganawa da tsohuwar sarauniyar qasar Ethiopia saidai maheer daya bada gargadi mai qarfi akan karta kuskura barin kowa yadauki hotonta ko fira da ita.

Lokacinda nuratu ta iso gurin bikin sosai sukayi farin cikin ganin juna dakuma auren nuratun da khaleefa keson yi.

Irin gyaran da akai mata da shirin da akai mata ita kanta burge kanta takeyi ga wani irin qamshi daya kama jikinta.

Dukiyarta kai tsaye tace suci gaba da kulawa da ita tabar musu halak malak bata buqatar komai.

Ranarda zasu tafi ammy ce da jakadiya sai umman da matar alhaji babaye da yaransu 'yan mata da nuratu suka rakasu har Libya tareda dukiyar aure mai tarin yawa inda sukai kwana biyu suka juyo suka barota.

Sabuwar rayuwa ta bude a Libya inda nanma ammy wani gyaran ta dora ranarda tacika kwana shida cif aranar aka sai mata ticket ta wuce batareda abeel ba.

Qarfe uku na yamma jirginta ya sauka suhailat ce tazo daukarta sbd ogan na hospital gurin aiki baimasan aranar zata dawoba ammy suhailat kawai tafadawa shiyasa tazo daukarta.

Cikeda farin cikin ganin juna suka rungume juna suhailat na mata sannu da zuwa da cewa,
Where is my abeel?
cikin farin ciki ta amsa tana cewa,
Ammy ce ba ruwana.

Wani gida na daban taga sun nufa Wanda yafi nada girma sosai tun a harabar gidan ta fahimci kowaccensu nada wadataccen gurinta yanxu.

Da gudu su amah suka fito suna mata oyoyo ta riqe hannun fammah data fara mantata tayi kissing goshinta tana cewa,
Famman mum 'dinta.

Babban lafiyayyan qaton palonsu suka shiga nan suhailat ta rakata da luggage dinta har cikin dakinta dake daukeda parlour da two bedrooms aciki ga komai nata is white.
Chapter 49 · 0% Book details