← Book details Tarayya Part One Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 34 OF 51

Sashe 34

Tarayya Part One Complete Hausa Novel · about 8 min read

Lokacinda aka shigo aka sanarda ita zuwan ammy dubata bata motsaba saima rufe idanuwanta datayi hawayen ciki suka gangaro tunani abubuwa da dama na dawo mata,
"" mafita 'dayace karta haifi namiji idanma ta haifesa mutuwarsa itace mafita""
"" yaya kike tunanin zan fuskanci rumanah ranarda ta San cewar mune sanadin mutuwar iyayenta""
Rintse idanuwanta tayi da qarfi nauyi da zafin zuciyarta na qaruwa saidai batason barin zancen yashigeta a irin yanayin datake ciki yanxu sbd tanason tayiwa ammy fahimta mai kyau bazataso abinda kunnuwanta sukaji mata ba yazama gaskia.

Ammy kasa haquri tayi ta nufi dakin lokacin maheer yaje dubo suhailat.

Har ammy taqaraso gabanta bata motsaba daga inda take takure idanuwanta jajir.

Cikeda tsananin kunya da tausayinta murya na rawa tace,
Rumanah har abada bazan iya cire qaunarki arainaba sbd qaunace Allah yasakamin cikin raina Wanda kisani har abada bazan iya yin abinda nasan zan cutatardake ina fatar zaki riqe hakan aranki...Allah yaji qan abeel Hussain.

Juyawa tayi ta fice jikinta asanyaye sbd tana iya hasaso wasi wasi azuciyar rumanah.

Tana fita rumanar sulale ta kwanta agurin tasaki sabon kuka tana dafe qirjinta dake mata zafi da wata irin tafasa.

Cikin wata irin kaca mai tsananin nauyi da zafi aka na'do mamani da nauyin kacar yasata tafiya ahankali a duqe sbd ko qafarta daqyar take dagawa sbd nauyin kacar datake 'daureda ita.

Aka bude wani tsohon kurkukun dayafi shekara goma ba'a shigesaba aja jefata ciki da qarfi kanta ya bugu da bango take goshinta ya fashe da jini ta fitarda numfashi daqyar sbd azaba gashi batada hannun shafawa taji sbd irin 'daurin da'akayi mata ko numfashi daqyar take fitarwa.

Ta lumshe ido cikin azaba ta bude idon takalli qofar dishi dishi take gani sbd ba qaramar buguwa tayiba gashi anyi mata wani irin duka na rashin imani dan kariya biyu akayi mata a hannu 'daya.

Wani irin kwando aka bude tareda jeho abinda ke ciki aka rufe qofa
Wani irin baqin maciji tagani ya bude kansa yana fitarda huci.

Mummunar faduwa gabanta yayi wasu irin hawayen azaba da tsoro tareda baqin ciki suka gangaro mata jikinta ko qarfin dazaiyi rawa bashidashi sbd ti6is akayi mata.

Tana kallo macijin ya kwantarda kai yayi cikin wani qaton rami dake gurin Wanda shikansa ramin baza'a rasa wani macijin acikiba ko abinda yafisama.

Maganarta da adama ta tuno tana fargabar kar komai yaqi tafiya yanda suka tsara.

""" idan kikai nasarar basu wannan dafin suka sha zasu mutu atake kuma ki tabbatarda ankamaki duk wuya da azaba karki ce nice kice sultana ce Wanda kowa yasan hukuncinta na kisa ne kafin akasheta za'a bani matsayinta na sultana nikuma zanyi amfani da wannan matsayin na hana akasheki kuma daga lokacin namiki alqawarin matsayin Jakadiya kintashi daga baiwa har abada saidai kuma idan kika fadi sunana kisani babu 6ata lokaci dukkaninmu za'a kashemu amma idan kikace itace nizan kubutar dake kinga burinki na shekara da shekaru yacika ga 'yanci da dukiyar kanki dazaki tara""""
Numfashi tasaki a wahalce tana sake qarfafawa zuciyarta dan cika sauran aikin dan kuwa koda ta mutu tasan burinta akan zuriar bulama da asma'u yacika.

Suhailat data farfado ahankali hawaye kebin fuskarta suna sauka kan qirjinta idanuwanta arufe sbd ko hannunta daqyar take iya motsasa.

Qunci ne arayuwarta da zuciyarta,
Rayuwarta ta lalace batada wani sauran farin ciki,
Ta rasa mijinta badan ya rasuba,
Ta rasa rayuwar aure mai farin ciki,
Ta rasa lafiyarta,
Ta rasa mahaifarta gurin haihuwa ga abinda ta haifa ta rasashi mai zaunawama ya rungumeta ya rarrasheta ta rasa
Wace irin rayuwace mai tattareda garari take ciki?

Wani irin kuka mai qaramin sauti tasaki zuciyarta na mata ciwo mai tsanani
Kewar iyayenta da 'yayanta takeji sbd sune kadai sukasan zafinta da damuwarta.

Qarasawa yayi bakin gadon tareda Rungumeta da sauri yana jin tausayinta fiyeda kansa sbd yasan tafi kowa cutatuwa sbd tafi rasawa tunda ba wata haihuwar zata sakeba.

Akaro na farko arayuwarta taji batason kusancinsa agareta sbd nauyi hakan ke qarawa zuciyarta saidai ko motsi sosai bata iyayi bare ta zame jikinta hakan yasa wani sabon kukan qunci zuwar mata ahankali.

Sosai ya lurada batai farin ciki ko jin sanyi da ganinsaba akaro na farko arayuwar aurensu daya hango wani yanayi daban akansa wanda ba sonsa bane atareda ita ya rufe ido cikin wata sabuwar damuwar yanajin tausayin kansama sbd wata jarabawace Allah yake jarabtarsa da ita akan rumanah wadda idan baiyi taka tsantsanba zai tashi da Rabin jiki ranar lahira saidai kuma baisan yaya zaiyiba sbd sonta yazama halitta ajininsa.

Ahankali ya furta,
Allah yaji qan jemaal.

Sakinta yayi ya miqe tareda ficewa batareda ya qara kalma 'daya ba.

A wannan daren mineelik ba kowa yasamu damar kwantawaba bare ya rintsa sbd dukkanin dole da masautar na cikin tasa kalar damuwar.

Rumanah dai duk yanda akayi da ita taci abinci ko motsi taqiyi daga inda take idanuwanta sun bushe sunyi jajir ko gani sosai batayi sbd kumburin idanuwanta.,
Suhailat kuwa har lokacin bata iya kwakwaran motsi sai hawaye da ciwon qirji dayake cinta ita kanta anyi anyi taci abincin amma ko bude ido taqiyi sai hawaye take zubarwa.

A rayuwarsa wannan ne karo na farko dayaji yayiwa sarauta da gidan sarauta wata irin muguwar tsana sbd yasan son mulkine yasa akai hakan,
Ya tabbatarda kisace ta tabbata akan baiwar datayi da wainda suka sakata saidai bayajin zai tsaya ganin hakan gobe zaayi hidimar radin sunansu a goben zasubi jirgin dare su koma dan idan yananan zuciyarsa zata bugane da halinda matansa suke ciki musamman suhailat datake buqatar kulawa sosai.

Ammy da jakadiya kusan a zaune suka kwana ko ruwan arziki babu Wanda ya iya sakawa maqoshinsa sbd tashin hankalin dazai iya faruwa gobe sbd duk Wanda sunansa yashiga koda misali ne cire kansa ya wajabta gashi a sashen ta abin yafaru shine babban tashin hankali da damuwar dasuke ciki musamman dasukasan wacece mamani.

Ayau mineelik acike takeda duk wata masarautar dake zagaye da maqwaftaka da ita tareda wasu sarautun wasu qasashen da dama sbd gabatarda sunan magajinnta dakuma miqawa uwar magajin mineelik kambun saukewa da 'dora sabon sultan.

Wannan matsayin daza'a bata ayau shine abu mafi ha'dari da tashin hankalinda yake ciki ayau
Ammy duk yanda taso daurewa kasawa tayi saida hawayen baqin cikin datake ciki suka gangaro mata tun a daren jiya ta hana su ganta bare ta sanarda ita hadari da kuma illar abinda zata fada.

Saidai alqawarine shi ya daukarwa kansa zai tabbarda ta miqa mulkin nan ga sultan ya dauketa sunkoma adaren yau din.

Lokacinda aka hallara dan qaddamarwa saqo ya isowa sultan uwar magaji batada lafiya bazata iya fitowa.

Kai tsaye aka fara qaddamar da komai aka radawa abeel Hassan sunansa tareda qaddamar da sunan ummu-rumanah acikin littafin tarihin mineelik amatsayin uwar magaji.

Nan take masu rubuta tarihi aka bude paging fara rubuta nata.

Daga ammy har yarima maheer babu Wanda ya halarci taron kuma sarai sultan yagano manufarsu tayin hakan zasu fuskanci hukuncinsa daga baya ayanxu baiwa mamani ce agabansa zai bata wata irin mutuwa mai firgitarwa itada wainda suka sakata ga 'yan baya.

Koina yayi tsit jiran hukuncin sultan akeyi lokacinda mamani ta tabbatarda Jakadiya ce tasakata amatsayin itama sultana ce ta aikota.

Tsita akayi
kowa wuta ta dauke masa musamman sultan da mamakin baiwa mamani yakamasa sbd yafi kowa sanin sultanarsa bazata aikata hakanba,
Tabbas wannan baiwa mai taurin raice saidai ji da ganin hukuncin sultan kawai tajeyi batasan waye sultan ba.

Kallo daya yayiwa kaleeb cikin babbar murya yace,
Aje ajefawa zakuna ita su cinyeta da ranta akawo qashinta asa 'dakin kayan tarihin mineelik...

Da ido adama dake dake gefensa tayiwa sultan aqeel magana ya gyara zamansa tareda kallon sauran sarakunan dake Royal hall din yace,
Idan aka kashe wannan baiwa batareda ta fadi wainda suka sakataba baka kai qarshen matsalar a mineelik ba sbd gobe ko jibi magajin ne da kansa za'a kashe kuma hakan zaisakawa mutane wasi wasin hukuncinka tunda ta fadi wainda suka sakata anshare anyi kamar bata fadaba.

Ido cikin ido yakalli sultan aqeel yace,
Babu Wanda ya isa yayi wasi wasin hukuncina a qarqashin mulkina da ikona ko wanene batareda na ciyar da namansa ga dabbobinaba.

Murmushin mulki sultan aqeel yasaki yace,
Hakane kuma idan kanason hakan yacigaba da faruwa saika nunawa mineelik Kaine sultan kuma Kaine kake yanke hukunci kowane irine akan ko wanene.

Nan take sauran sarakunan suka marawa gaskia baya suka qalubalanci sultan akan adalci idan har sultana ce tasakata to ayi adalci ayanke hukunci daidai yanda yakamata.

Atake mutane suka fara kallon kallo da hayaniyar abinda aka fada nan mamaki ya kama sultan kenan har akwai wainda zasu iya tambayar hukuncinsa su qalubalanci yanayin mulkinsa
Atake yace aje a kama Jakadiya arufe ya 'daga hukuncin zuwa gobe duk me hannu aciki kafin faduwar rana baya duniya.

Lokacinda akaje aka kama Jakadiya aka rufe
Sultana kuwa rufe sashenta akayi tareda aje masu tsaron qofar da doka mai qarfi daga sultan babu Wanda zai shiga gurinta ajira hukuncinsa zuwa gobe.

Lokacinda zancen ya isa kunnen maheer kai tsaye gurin sultan yanufa akai masa iso lokacin anwatse sai gobe a shaida hukuncinda zai iya yankewa.

Kallonsa yarima yayi cikeda takaici da baqin cikin yanda yasan sultana bazata aikata hakan ga yayansa ba amma ya yarda haryana iya tunanin yanke mata hukunci
Kai tsaye yace,
Amatsayina na uban magaji zan kar6i mulkin mineelik har lokacinda zai girma ya karbi da hannunsa.

Wani irin murmushin takaici sultan yasaki batareda yakallesaba yace,
Mulkin mineelik da za6ar mai mulkin na mutum 'dayane yanxu dan haka ka rasa damarka,
Mahaifiyarka kuma koni bazan iya kubutarda itaba idan har bincike ya nuna da hannunta aciki.

Yana fadar haka ya shige tabarsa zaune idanuwansa na kadawa jajir.

Duk inda tashin hankali yake masarautar na ciki dan shi kansa sultan jinjina alamarin yake aransa yana jaddadawa yana kuma fatar bincike yasa kar asamu hannun sultana aciki.

Acikin daren babu kalar azabar daba'a bawa mamaniba tace Jakadiya tasaka ta.

Jakadiya aka hau bawa baqar azaba amma daqyar take iya furta babu saka hannunsu aciki.

Acikin daren saqon neman sulhu da sassaucin hukunci yazo daga masarautar Libya dakuma wasu masarautun duk sai alamarin yasake girmama ya sake cabewa sultan gashi komene adaren ne sbd gobe dolene zai yanke hukunci.
Chapter 34 · 0% Book details