Sashe 8
Kyautar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Zaruk ta hango da Hajiya Rahma zaune suna cin abinci, ta sakar masa murmushi. Karasawa ta yi ta zauna. Ba a jima ba Alhaji Usman suka shigo da Aazeen rike da ledoji a hannu, su ma joining suka yi zaman cin abincin.
“Yau Rangida babu korafi, da alama abincin ya yi dadi”.
Nurat ta dubi Zaruk ya sakar mata murmushi.
“No Dad, kawai dai ina jin yunwa ne”.
“Da ma ai ke ba a taba iya miki”. Hajiya Rahma ta ce da ita.
“Ladidi ta cancanci tukwici kenan?” In ji Zaruk yana kallon Nurat, ya faki idonsu a hankali ya dinga motsa baki yana nufin zai fada.
Ta yi saurin kada kai tana rokonsa. Mikewa ya yi tsaye.
“Ni zan wuce Ammi, a yi wa kuku godiya sosai”. Ya fada yana murmushi.
ABUJA
“Ummi ya kamata ki saba, na yi tafiya zuwa qasashen waje bila’adadin, na zaga duniya komai bai same ni ba, nan zuwa Kano tafiyar mintina ne, da zarar jirginmu ya sauka shi kenan an wuce gurin. Ko kina tsoro ne kada jirgi ya fado da dan lelenki?”
Deedat ya fada yana kokarin tallafo kuncinta da hannayensa biyu. Ta sauke ajiyar zuciya cikin damu
“Ba haka ba ne, kawai dai ina tsintar kaina cikin rudu duk lokacin da ka ambata cewar za ka Kano. Bana samun nutsuwa, ban san me ya sa haka ba”.
Ya yi murmushi cikin kokarin kwarara mata gwiwa.
“No, Ummina kada ki mance kirarina, in ka san ni ni ne, in ba ka sanni ba, ba ni ba ne. Ummina. Kowa ya san ba ni ba ne, kin ji sam ba ni ba ne babu wanda ya san ni, kuma ma ban da ke da abinki addu’arki fa na tare da ni, ba zan mutu
*💖💕KYAUTAR ZUCIYA💖💞*
*NA*
*BILKISU H.MUHAMMAD*
_(Matar Auwalu By fos zage)_
*Free page 5 6*
*_Wanan littafin na kudine akan 300 kacal in kinsan zaki biya don ki fitarmin dashi Dan Allah ki barmin kayana yar uwa_*
*Ga jerin sunayan litattafai na da zaku samu a kasuwa*
*1. IZZATU*
*2. MULKIN MALLAKA*
*3. KAUNA CE*
*4. DACEWA*
*5. RASHIN RABO*
*6.TARAIRAYA*
*7. JINI BIYU*
*8. AKWAI BAMBANCI*
*9. TSALAR KAUNA*
*10. YA YI SAKE*
*11. ILLAR SABO*
*12. SO DA SANKARA*
*13. RASHIN RABO*
*14. WATA RAYUWA*
*15. HUBBAN SHADIDAN*
*16. BAKIN K'AZAFI*
*17. MATSALAR KAUNA*
*18. KYAN KUSKURE*
*19. WA YAFI SONTA?*
*20. GABA DA SO*
_NOW_
*KYAUTA ZUCIYA*
```Duka wanan litattafan sunanan akasuwa zaku sameso a shagunan sai da litattafai inasha Allah```
*_Wanan littafin na kudi ne, Mai bukata karanta shi zai turo 300 ta wanan account number din_*
*_2277439558 UBA Bank_*
Bilkisu H Muhammad_* *_idan an turo sai a turawa wanan number alter 08031307884 domin tabbatar da an turo din idan kuma VTU za'ayi ita dai number za'ai da ita ko katin MTN na 300 din sai in saki a group paid insha Allah_*
*_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
*“N* o, Ummina kada ki mance kirarina, in ka san ni ni ne, in ba ka sanni ba, ba ni ba ne. Ba ni ba ne Ummina. Kowa ya san ba ni ba ne, kin ji sam ba ni ba ne babu wanda ya san ni, kuma ma ban da ke da abinki addu’arki fa na tare da ni, ba zan mutu ta hanyar da ki ke tunani ba, a kan gadonki zan mutu, a kan kafafunki, yanzu ki yi min addu’a zan tafi kwana bakwai kacal zan yi ai kamar yau ne ko Tawan?”
Ta dinga murmushi a gefe daya kuma idanunta na fidda kwalla ta shafa sumarsa.
“Ka kula da kanka yarona, Allah ya yi maka albarka”.
Gaba daya suka dunguma har zuwa get inda ya shiga mota zuwa airport, ba ta bar get ba har sai da motar ta bace ma ganinta, ta juyo gida cike da kewarsa.
Hango shi ta yi zaune ya dora kafa daya kan daya yana kada su. Gabanta ne ya yi wani irin bugawa, ta shiga maimaita innalillahi…
Ya mike ya karaso gabanta yana tintsira dariya.
“Ya yi babar mai kudi, babar Richman da kyau”.
Ya sake tintsirewa da dariya.
“Da alama kina cike da kewarsa, kina tsoron kada ya mutu ko? To ai da saura, domin har yanzu ba wanda ya san shi ne da zarar an fahimci waye shi ina tabbatar miki ko awa daya ba zai kara ba, ni ne kuma zan tona masa asiri, ni din nan ni ne ajalinsa. Yanzu ki shiga ki debo min rabona in tafi, na sani ke ma saboda wannan din ki ke nuna mishi cewar kin fi kowa kaunar…”
Kyakkyawan marin da ta wanke shi da shi ne ya sanya shi kasa karasa maganarsa. daki ta shiga, sai ga ta da bandir din ‘yan dubu-dubu guda biyu.
Cikin muryar kuka ta soma magana, “Bana son ka kara minti daya a gidan nan, ka bace min da gani”.
Ya karbi kudin ya cilla su sama ya cafe, ya sumbaci kudin.
“Kin fanshi kanki, sai gani na biyu”.
Durkushewa ta yi ta dora kai a kujera, ta rushe da wani irin kuka.
“Yau Rangida babu korafi, da alama abincin ya yi dadi”.
Nurat ta dubi Zaruk ya sakar mata murmushi.
“No Dad, kawai dai ina jin yunwa ne”.
“Da ma ai ke ba a taba iya miki”. Hajiya Rahma ta ce da ita.
“Ladidi ta cancanci tukwici kenan?” In ji Zaruk yana kallon Nurat, ya faki idonsu a hankali ya dinga motsa baki yana nufin zai fada.
Ta yi saurin kada kai tana rokonsa. Mikewa ya yi tsaye.
“Ni zan wuce Ammi, a yi wa kuku godiya sosai”. Ya fada yana murmushi.
ABUJA
“Ummi ya kamata ki saba, na yi tafiya zuwa qasashen waje bila’adadin, na zaga duniya komai bai same ni ba, nan zuwa Kano tafiyar mintina ne, da zarar jirginmu ya sauka shi kenan an wuce gurin. Ko kina tsoro ne kada jirgi ya fado da dan lelenki?”
Deedat ya fada yana kokarin tallafo kuncinta da hannayensa biyu. Ta sauke ajiyar zuciya cikin damu
“Ba haka ba ne, kawai dai ina tsintar kaina cikin rudu duk lokacin da ka ambata cewar za ka Kano. Bana samun nutsuwa, ban san me ya sa haka ba”.
Ya yi murmushi cikin kokarin kwarara mata gwiwa.
“No, Ummina kada ki mance kirarina, in ka san ni ni ne, in ba ka sanni ba, ba ni ba ne. Ummina. Kowa ya san ba ni ba ne, kin ji sam ba ni ba ne babu wanda ya san ni, kuma ma ban da ke da abinki addu’arki fa na tare da ni, ba zan mutu
*💖💕KYAUTAR ZUCIYA💖💞*
*NA*
*BILKISU H.MUHAMMAD*
_(Matar Auwalu By fos zage)_
*Free page 5 6*
*_Wanan littafin na kudine akan 300 kacal in kinsan zaki biya don ki fitarmin dashi Dan Allah ki barmin kayana yar uwa_*
*Ga jerin sunayan litattafai na da zaku samu a kasuwa*
*1. IZZATU*
*2. MULKIN MALLAKA*
*3. KAUNA CE*
*4. DACEWA*
*5. RASHIN RABO*
*6.TARAIRAYA*
*7. JINI BIYU*
*8. AKWAI BAMBANCI*
*9. TSALAR KAUNA*
*10. YA YI SAKE*
*11. ILLAR SABO*
*12. SO DA SANKARA*
*13. RASHIN RABO*
*14. WATA RAYUWA*
*15. HUBBAN SHADIDAN*
*16. BAKIN K'AZAFI*
*17. MATSALAR KAUNA*
*18. KYAN KUSKURE*
*19. WA YAFI SONTA?*
*20. GABA DA SO*
_NOW_
*KYAUTA ZUCIYA*
```Duka wanan litattafan sunanan akasuwa zaku sameso a shagunan sai da litattafai inasha Allah```
*_Wanan littafin na kudi ne, Mai bukata karanta shi zai turo 300 ta wanan account number din_*
*_2277439558 UBA Bank_*
Bilkisu H Muhammad_* *_idan an turo sai a turawa wanan number alter 08031307884 domin tabbatar da an turo din idan kuma VTU za'ayi ita dai number za'ai da ita ko katin MTN na 300 din sai in saki a group paid insha Allah_*
*_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
*“N* o, Ummina kada ki mance kirarina, in ka san ni ni ne, in ba ka sanni ba, ba ni ba ne. Ba ni ba ne Ummina. Kowa ya san ba ni ba ne, kin ji sam ba ni ba ne babu wanda ya san ni, kuma ma ban da ke da abinki addu’arki fa na tare da ni, ba zan mutu ta hanyar da ki ke tunani ba, a kan gadonki zan mutu, a kan kafafunki, yanzu ki yi min addu’a zan tafi kwana bakwai kacal zan yi ai kamar yau ne ko Tawan?”
Ta dinga murmushi a gefe daya kuma idanunta na fidda kwalla ta shafa sumarsa.
“Ka kula da kanka yarona, Allah ya yi maka albarka”.
Gaba daya suka dunguma har zuwa get inda ya shiga mota zuwa airport, ba ta bar get ba har sai da motar ta bace ma ganinta, ta juyo gida cike da kewarsa.
Hango shi ta yi zaune ya dora kafa daya kan daya yana kada su. Gabanta ne ya yi wani irin bugawa, ta shiga maimaita innalillahi…
Ya mike ya karaso gabanta yana tintsira dariya.
“Ya yi babar mai kudi, babar Richman da kyau”.
Ya sake tintsirewa da dariya.
“Da alama kina cike da kewarsa, kina tsoron kada ya mutu ko? To ai da saura, domin har yanzu ba wanda ya san shi ne da zarar an fahimci waye shi ina tabbatar miki ko awa daya ba zai kara ba, ni ne kuma zan tona masa asiri, ni din nan ni ne ajalinsa. Yanzu ki shiga ki debo min rabona in tafi, na sani ke ma saboda wannan din ki ke nuna mishi cewar kin fi kowa kaunar…”
Kyakkyawan marin da ta wanke shi da shi ne ya sanya shi kasa karasa maganarsa. daki ta shiga, sai ga ta da bandir din ‘yan dubu-dubu guda biyu.
Cikin muryar kuka ta soma magana, “Bana son ka kara minti daya a gidan nan, ka bace min da gani”.
Ya karbi kudin ya cilla su sama ya cafe, ya sumbaci kudin.
“Kin fanshi kanki, sai gani na biyu”.
Durkushewa ta yi ta dora kai a kujera, ta rushe da wani irin kuka.