Sashe 13
Kyautar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*** *** ***
“Yaya Aazeen ana kiranki a waya fa”.
Sai da ta maimaita faxa kusan sau uku, sannan Aazeen ta yi firgigt.
“Mtsew! Qyale su”.
“Yaya Aazeen ba ki da lafiya ne?”
“Ina cikin damuwa ne kawai Nurat, tunanina da hankali gaba xaya sun koma ga mutumin nan, ina ji a jikina tamkar zai kusanto ni. Ina ji tamkar shi ne mijina, ban san shi ba amma kullum sai ya zo min cikin mafarkina. Wannan karon ne kaxai wani abun ke neman fin qarfina, amma ban tava neman abu na rasa ba, sai ya zamo mallakina ko da hakan zai zamo sanadiyyar rasa komai nawa”.
“Yaya Aazeen komai naki fa ki ka ce?”
“Eh mana, ban da abinki idan na rasa komai shi ne zai dawo min da ninkinsa. Ba ki san matsayinsa ba ne, har ma fa ya fi shugaban qasa kuxi”.
“To idan bai zama yadda ki ke so ba fa?”
“Kin ga Nurat, muddin yana da kuxi ko ya dai yake zan yi maleji, ai ba xaure shi zan yi a qafa ina yawo da shi ba”.
“To idan ki ka samu wanda ki ke so ba”.
Ta kai mata dukan wasa, “Allah ba zai sa in kamu da soyayyar wani ba, wannan zuciyar ba ta san so ba sai jin daxi da holewa, gwara ma idan na samu mai kyau na dinga kare yawa in mayar da shi fulawa kawai”.
“Yayata kina son mai kyau’.
“Eh mana, shi ya sa nake matuqar sonki”.
Nurat ta yi dariya.
“Yanzu idan ki ka haxu da mai kyau za ki so shi?”
“Mai zai hana?”
Wani daxi ya kama Nurat, tabbas haqanta zai cimma ruwa, ta fara samun yadda za ta villowa lamarin, ba za ta bari shaquwa da Adamu ya tashi a banza ba, sai sun zamo xaya.
Ji ta yi an zunguro ta. Ido biyu ta yi da Aazeen, Aazeen ta kanne mata ido xaya.
“Tunanin me ki ke yi? Gaya min, ko kin kamu ne?”
Ta yi murmushi, “Haba ‘yar maniniyata, kawai kina maganar maikyau na tuna da wani, ni ban ma tava ganin mai kyawunsa ba, za ku dace da shi”.
Tsaki Aazeen ta ja daidai lokacin wayarta ta sake xaukar ruri, ta miqe tana faxin, “Ke kin cika shirme’. Xaki ta shige.
Zuciyarsa tamkar ta faso qirji, son Nurat na neman halaka shi ta ina zai fara? Ya zai yi? Da sauri ya fito a xakinsa. Zainab matar yayansa na zaune a babban sitroom riqe da waya a hannu tana game. Kawai ya zube a kujera, ta xan dube shi, yadda yake ta faman huci.
“Man, waye ya tava mana kai?”
Kansa a qasa bai ce da ita komai ba, za ta sake yin magana ya yi saurin katse ta.
“Ban san haka nake sonta ba, ta yi tasiri a zuciyata, ba zan iya rayuwa ba tare da ita ba. lokaci ya yi da zan tinkari su Papa da maganar kada na mutu”.
‘Duk ita kaxai? Wace wannan haka?”
Ya furzar da huci.
“Nurat! Ina sonta, ina matuqar sonta. Ina jinta tamkar numfashina, ina jinta a can qarqashin zuciyata’.
Ta yi murmushi cikin sigar wasa ta dungure mishi kai.
“Da Allah can, sunan wacce ka ke ihun ita ce ruhinka ka mance Aazeen za ka ce”.
“Oh God! Kina tunanin mantuwa na yi? Nurat wadda na xebi shekaru ina dakon sonta, Nurat ita xin dai nake nufi”.
Ido buxe ta ke dubansa.
“Allah ba zai yi ma Nurat haka ba”.
A zahiri ta yi murmushi, “Haba dai, me za ka yi da wannan ‘yar mutsilar yarinyar da ba ta gama sanin ciwon kanta ba? Aazeen xin dai. Aazeen ita ce wadda za ku yi matching, gogaggiya kamar kai. Amma Nurat is too younger…”
“Stop Aunt! Kawai ki fito ki ce ni xin ban cancanci zama mijinta ba, saboda ni ban da kirki, ni ba na qwarai ba ne. To ina son ki sani zan sauya, zan iya yin komai a kan in mallake ta”.
Ta karyar da murya, “No, ba fa nufina kenan ba. Wai ni ina son in ce qarama ce ita”.
Tsaki ya ja ya miqe yana jin iya ci gaba da tsayuwa a gurinta zai iya marinta. Juyowa ya yi ya dube ta da idanun nan jajir, haka ne ya sa ta shiga hankalinta.
Ya tarar wayarsa na faman ruri, lambar Aazeen ya gani, da sauri ya xauka. Muryar Nurat xin ce ta ratsa kunnuwansa, wata irin ajiyar zuciya ya sauke.
“Yaya Zaruk”. Ta kira sunansa a can vangarenta, ta kuma rasa da me za ta fara, don haka ta yi shiru.
Ya katse shirun da faxin, “Gaya min, kina son ganina ne?” Ya faxa yana mai roqon Allah ya sanya ita ma ta jarabtu da sonsa.
“Nurat, gaya mini kada ki damu, kin ji?”
“Um-um… da man ce maka zan yi ina son kiran Adamu jiya mun fara hira da Yaya Aazeen, sai nake jin kamar zan dace, za ta iya amincewa”.
Ya cije leve, ji ya yi kamar wani tsini ya soke shi. Da qyar ya danne zuciyarsa.
“Ya kamata ki fara shawo kanta kafin ki jajibo shi”.
“Ai na ce da kai ta fara amincewa”.
“To shi kenan, ki bari gobe in na zo sai mu ga ya za mu yi”.
Ta yi murmushi mai sauti. Ba ta sake jiran me zai ce ba ta yi saurin katse wayar.
Ciki ya yi da wayar ya riqe kai yana faman huci.
“Zan nemo shi, ba zan amince ba. zan yi wani abu a kai, bana tsoron duk abin da zai faru. I don’t care, zan gaya ma Papana dole ne in tabbatar da za ki zamo tawa, kina wasa da rayuwa ta, ba zan tava amincewa da wannan ba, kullum ana raina min hankali da faxin ke xin qarama ce, da zarar na taso sai a danqwafe ni, an bar zuciyata da masifa, shekara da shekaru ina azabtuwa. Wallahi na yi alqawari ko kallonki wani ya yi da zummar so sai na vatar da shi, bana tsoro, ba zan xaga qafa ba, dole ne ki zamo tawa. Ni ne kaxai na san muhimmancinki ba zan yarda ba, ina! Haka ba za ta tava yiwuwa ba, kai xin ma sai na gano ko kai waye na sani duk da ba ka santa ba da zarar ka xora ido a kanta ba za ka barta ba”.
Ya ci gaba da sambatunsa kamar wani tavavve ko qaramin yaro.
Idan ta tuno hirarsu da Aazeen duk sai daxi ya kamata, yanzu ta ina za ta fara? Ta yi shiru cikin tunani. Ta yi murmushi, me ya sa ta damu da yawa? Me ya sa zuciyarta ta nace da son haxa dangantaka da Adamu?
Ta gyara zamanta, “Qila shi ne sanadin gyaruwarta, sai kun haxu zai gane wace ke na sani, ba zai guje ki ba a lokacin da ya san halayyarki, don haka nake son in kama zuciyarsa da zummar ke ce, kuma ai ni ma mace ce, zan iya har ma sai na jira Yaya Zaruk ya koyar da ni, mutumin da yake ta faman ja min rai? Zan ba shi mamaki, sai dai kawai ya ji ana yi”.
Ta miqe tsaye ta shiga zaryar yadda za a yi ta sato wayar Aazeen.
Da sauri ta yi sitroom inda ta riski Aazeen zaune sanye da wasu maqalallun kaya, ta xora qafa xaya kan xaya cikin duba novel book.
“Yayata, ko za ki ba ni wayarki zan kira Aisha?”
Ba ta yi magana ba, kawai ta yi mata nuni da wayar. Da sauri ta xauka ta koma xaki. Sai da ta kulle ta murxa key ta koma ta zauna a kan gado.
“Ke ce kuwa?”
“Mai ka gani?”
“Ba ki saba kira a irin wannan lokacin ba shi ya sa nake jin kamar ba ke ba ce”.
“Ni kaina ban san lokacin da na kira ba, kawai ina wasa da wayar na ga kawai hannuna ya kai ga lambarka’.
“Amma kuma kin tava ce min ba ki yi saving ba…”
“Uhum”. Kawai ta yi.
“Lallai na qara matsayi, na ji daxin haka qanwata”.
“Ai da ma kana da matsayi”.
“Ok, yanzu ba ni labari”.
Ta xan yi jim kamar ba ta kan wayar.
*💖💕KYAUTAR ZUCIYA💖💞*
*NA*
*BILKISU H.MUHAMMAD*
_(Matar Auwalu By fos zage)_
*Free page 9*
*_Wanan littafin na kudine akan 300 kacal in kinsan zaki biya don ki fitarmin dashi Dan Allah ki barmin kayana yar uwa_*
*Ga jerin sunayan litattafai na da zaku samu a kasuwa*
*1. IZZATU*
*2. MULKIN MALLAKA*
*3. KAUNA CE*
*4. DACEWA*
*5. RASHIN RABO*
*6.TARAIRAYA*
*7. JINI BIYU*
*8. AKWAI BAMBANCI*
*9. TSALAR KAUNA*
*10. YA YI SAKE*
*11. ILLAR SABO*
*12. SO DA SANKARA*
*13. RASHIN RABO*
*14. WATA RAYUWA*
*15. HUBBAN SHADIDAN*
*16. BAKIN K'AZAFI*
*17. MATSALAR KAUNA*
*18. KYAN KUSKURE*
*19. WA YAFI SONTA?*
*20. GABA DA SO*
_NOW_
*KYAUTA ZUCIYA*
```Duka wanan litattafan sunanan akasuwa zaku sameso a shagunan sai da litattafai inasha Allah```
*_Wanan littafin na kudi ne, Mai bukata karanta shi zai turo 300 ta wanan account number din_*
*_2277439558 UBA Bank_*
Bilkisu H Muhammad_* *_idan an turo sai a turawa wanan number alter 08031307884 domin tabbatar da an turo din idan kuma VTU za'ayi ita dai number za'ai da ita ko katin MTN na 300 din sai in saki a group paid insha Allah_*
*_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
“Yaya Aazeen ana kiranki a waya fa”.
Sai da ta maimaita faxa kusan sau uku, sannan Aazeen ta yi firgigt.
“Mtsew! Qyale su”.
“Yaya Aazeen ba ki da lafiya ne?”
“Ina cikin damuwa ne kawai Nurat, tunanina da hankali gaba xaya sun koma ga mutumin nan, ina ji a jikina tamkar zai kusanto ni. Ina ji tamkar shi ne mijina, ban san shi ba amma kullum sai ya zo min cikin mafarkina. Wannan karon ne kaxai wani abun ke neman fin qarfina, amma ban tava neman abu na rasa ba, sai ya zamo mallakina ko da hakan zai zamo sanadiyyar rasa komai nawa”.
“Yaya Aazeen komai naki fa ki ka ce?”
“Eh mana, ban da abinki idan na rasa komai shi ne zai dawo min da ninkinsa. Ba ki san matsayinsa ba ne, har ma fa ya fi shugaban qasa kuxi”.
“To idan bai zama yadda ki ke so ba fa?”
“Kin ga Nurat, muddin yana da kuxi ko ya dai yake zan yi maleji, ai ba xaure shi zan yi a qafa ina yawo da shi ba”.
“To idan ki ka samu wanda ki ke so ba”.
Ta kai mata dukan wasa, “Allah ba zai sa in kamu da soyayyar wani ba, wannan zuciyar ba ta san so ba sai jin daxi da holewa, gwara ma idan na samu mai kyau na dinga kare yawa in mayar da shi fulawa kawai”.
“Yayata kina son mai kyau’.
“Eh mana, shi ya sa nake matuqar sonki”.
Nurat ta yi dariya.
“Yanzu idan ki ka haxu da mai kyau za ki so shi?”
“Mai zai hana?”
Wani daxi ya kama Nurat, tabbas haqanta zai cimma ruwa, ta fara samun yadda za ta villowa lamarin, ba za ta bari shaquwa da Adamu ya tashi a banza ba, sai sun zamo xaya.
Ji ta yi an zunguro ta. Ido biyu ta yi da Aazeen, Aazeen ta kanne mata ido xaya.
“Tunanin me ki ke yi? Gaya min, ko kin kamu ne?”
Ta yi murmushi, “Haba ‘yar maniniyata, kawai kina maganar maikyau na tuna da wani, ni ban ma tava ganin mai kyawunsa ba, za ku dace da shi”.
Tsaki Aazeen ta ja daidai lokacin wayarta ta sake xaukar ruri, ta miqe tana faxin, “Ke kin cika shirme’. Xaki ta shige.
Zuciyarsa tamkar ta faso qirji, son Nurat na neman halaka shi ta ina zai fara? Ya zai yi? Da sauri ya fito a xakinsa. Zainab matar yayansa na zaune a babban sitroom riqe da waya a hannu tana game. Kawai ya zube a kujera, ta xan dube shi, yadda yake ta faman huci.
“Man, waye ya tava mana kai?”
Kansa a qasa bai ce da ita komai ba, za ta sake yin magana ya yi saurin katse ta.
“Ban san haka nake sonta ba, ta yi tasiri a zuciyata, ba zan iya rayuwa ba tare da ita ba. lokaci ya yi da zan tinkari su Papa da maganar kada na mutu”.
‘Duk ita kaxai? Wace wannan haka?”
Ya furzar da huci.
“Nurat! Ina sonta, ina matuqar sonta. Ina jinta tamkar numfashina, ina jinta a can qarqashin zuciyata’.
Ta yi murmushi cikin sigar wasa ta dungure mishi kai.
“Da Allah can, sunan wacce ka ke ihun ita ce ruhinka ka mance Aazeen za ka ce”.
“Oh God! Kina tunanin mantuwa na yi? Nurat wadda na xebi shekaru ina dakon sonta, Nurat ita xin dai nake nufi”.
Ido buxe ta ke dubansa.
“Allah ba zai yi ma Nurat haka ba”.
A zahiri ta yi murmushi, “Haba dai, me za ka yi da wannan ‘yar mutsilar yarinyar da ba ta gama sanin ciwon kanta ba? Aazeen xin dai. Aazeen ita ce wadda za ku yi matching, gogaggiya kamar kai. Amma Nurat is too younger…”
“Stop Aunt! Kawai ki fito ki ce ni xin ban cancanci zama mijinta ba, saboda ni ban da kirki, ni ba na qwarai ba ne. To ina son ki sani zan sauya, zan iya yin komai a kan in mallake ta”.
Ta karyar da murya, “No, ba fa nufina kenan ba. Wai ni ina son in ce qarama ce ita”.
Tsaki ya ja ya miqe yana jin iya ci gaba da tsayuwa a gurinta zai iya marinta. Juyowa ya yi ya dube ta da idanun nan jajir, haka ne ya sa ta shiga hankalinta.
Ya tarar wayarsa na faman ruri, lambar Aazeen ya gani, da sauri ya xauka. Muryar Nurat xin ce ta ratsa kunnuwansa, wata irin ajiyar zuciya ya sauke.
“Yaya Zaruk”. Ta kira sunansa a can vangarenta, ta kuma rasa da me za ta fara, don haka ta yi shiru.
Ya katse shirun da faxin, “Gaya min, kina son ganina ne?” Ya faxa yana mai roqon Allah ya sanya ita ma ta jarabtu da sonsa.
“Nurat, gaya mini kada ki damu, kin ji?”
“Um-um… da man ce maka zan yi ina son kiran Adamu jiya mun fara hira da Yaya Aazeen, sai nake jin kamar zan dace, za ta iya amincewa”.
Ya cije leve, ji ya yi kamar wani tsini ya soke shi. Da qyar ya danne zuciyarsa.
“Ya kamata ki fara shawo kanta kafin ki jajibo shi”.
“Ai na ce da kai ta fara amincewa”.
“To shi kenan, ki bari gobe in na zo sai mu ga ya za mu yi”.
Ta yi murmushi mai sauti. Ba ta sake jiran me zai ce ba ta yi saurin katse wayar.
Ciki ya yi da wayar ya riqe kai yana faman huci.
“Zan nemo shi, ba zan amince ba. zan yi wani abu a kai, bana tsoron duk abin da zai faru. I don’t care, zan gaya ma Papana dole ne in tabbatar da za ki zamo tawa, kina wasa da rayuwa ta, ba zan tava amincewa da wannan ba, kullum ana raina min hankali da faxin ke xin qarama ce, da zarar na taso sai a danqwafe ni, an bar zuciyata da masifa, shekara da shekaru ina azabtuwa. Wallahi na yi alqawari ko kallonki wani ya yi da zummar so sai na vatar da shi, bana tsoro, ba zan xaga qafa ba, dole ne ki zamo tawa. Ni ne kaxai na san muhimmancinki ba zan yarda ba, ina! Haka ba za ta tava yiwuwa ba, kai xin ma sai na gano ko kai waye na sani duk da ba ka santa ba da zarar ka xora ido a kanta ba za ka barta ba”.
Ya ci gaba da sambatunsa kamar wani tavavve ko qaramin yaro.
Idan ta tuno hirarsu da Aazeen duk sai daxi ya kamata, yanzu ta ina za ta fara? Ta yi shiru cikin tunani. Ta yi murmushi, me ya sa ta damu da yawa? Me ya sa zuciyarta ta nace da son haxa dangantaka da Adamu?
Ta gyara zamanta, “Qila shi ne sanadin gyaruwarta, sai kun haxu zai gane wace ke na sani, ba zai guje ki ba a lokacin da ya san halayyarki, don haka nake son in kama zuciyarsa da zummar ke ce, kuma ai ni ma mace ce, zan iya har ma sai na jira Yaya Zaruk ya koyar da ni, mutumin da yake ta faman ja min rai? Zan ba shi mamaki, sai dai kawai ya ji ana yi”.
Ta miqe tsaye ta shiga zaryar yadda za a yi ta sato wayar Aazeen.
Da sauri ta yi sitroom inda ta riski Aazeen zaune sanye da wasu maqalallun kaya, ta xora qafa xaya kan xaya cikin duba novel book.
“Yayata, ko za ki ba ni wayarki zan kira Aisha?”
Ba ta yi magana ba, kawai ta yi mata nuni da wayar. Da sauri ta xauka ta koma xaki. Sai da ta kulle ta murxa key ta koma ta zauna a kan gado.
“Ke ce kuwa?”
“Mai ka gani?”
“Ba ki saba kira a irin wannan lokacin ba shi ya sa nake jin kamar ba ke ba ce”.
“Ni kaina ban san lokacin da na kira ba, kawai ina wasa da wayar na ga kawai hannuna ya kai ga lambarka’.
“Amma kuma kin tava ce min ba ki yi saving ba…”
“Uhum”. Kawai ta yi.
“Lallai na qara matsayi, na ji daxin haka qanwata”.
“Ai da ma kana da matsayi”.
“Ok, yanzu ba ni labari”.
Ta xan yi jim kamar ba ta kan wayar.
*💖💕KYAUTAR ZUCIYA💖💞*
*NA*
*BILKISU H.MUHAMMAD*
_(Matar Auwalu By fos zage)_
*Free page 9*
*_Wanan littafin na kudine akan 300 kacal in kinsan zaki biya don ki fitarmin dashi Dan Allah ki barmin kayana yar uwa_*
*Ga jerin sunayan litattafai na da zaku samu a kasuwa*
*1. IZZATU*
*2. MULKIN MALLAKA*
*3. KAUNA CE*
*4. DACEWA*
*5. RASHIN RABO*
*6.TARAIRAYA*
*7. JINI BIYU*
*8. AKWAI BAMBANCI*
*9. TSALAR KAUNA*
*10. YA YI SAKE*
*11. ILLAR SABO*
*12. SO DA SANKARA*
*13. RASHIN RABO*
*14. WATA RAYUWA*
*15. HUBBAN SHADIDAN*
*16. BAKIN K'AZAFI*
*17. MATSALAR KAUNA*
*18. KYAN KUSKURE*
*19. WA YAFI SONTA?*
*20. GABA DA SO*
_NOW_
*KYAUTA ZUCIYA*
```Duka wanan litattafan sunanan akasuwa zaku sameso a shagunan sai da litattafai inasha Allah```
*_Wanan littafin na kudi ne, Mai bukata karanta shi zai turo 300 ta wanan account number din_*
*_2277439558 UBA Bank_*
Bilkisu H Muhammad_* *_idan an turo sai a turawa wanan number alter 08031307884 domin tabbatar da an turo din idan kuma VTU za'ayi ita dai number za'ai da ita ko katin MTN na 300 din sai in saki a group paid insha Allah_*
*_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*