Sashe 22
Kyautar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*** *** ***
“Ba aiki ya kamata ki yi ba, hutawa za ki yi, ki bar ni da wannan uwar qwiyar”.
“Babu komai Anty, kin ga idan na saka hannu sai mu fi saurin gamawa”.
“Okey, shi ke nan tunda kin dage. Ga kaya can na xauko miki ki saka, kada ki vata na jikinki”.
“To Anti”. Nurat ta faxa.
Ta koma xaki ta sauya kaya. Kayan sun yi mata xas tamkar nata. Ba ta xaura xankwali ba, ta gyara tufkar gashinta ta fito. Kicin ta nufa inda ta samu Anti Aisha da qanwarta Yusra.
Anti Aisha ta bi ta da kallo, ba ta tava ganin Nurat ba sai yau, amma jinta ta ke yi kamar wadda suka shekara da ita. Wani irin qaunarta ce ta xarsu a zuciyarta. Ta sauke ajiyar zuciya.
“Kawai ki tafi da kayan, da ma ban tava saka su ba, tunani nake yi kamar sun yi min kaxan shi ya sa tuntuni na qi sakawa”.
Yusra ta ce, “Wallahi kin yi kyau”.
“Yanzu ki ci gaba da aikin, zan je na yi wanka, na san suna hanya kada su zo ban shirya ba. Oga ya yi min kashedin in yi kyau sosai, kada Ogansa ya raina shi”.
“Wai Yaya Aisha waye wannan xin?”
Yusra ta tambaya tana kallonta.
‘Shi xin na musamman ne. Takensa shi ne, in k sanshi shi ne, idan ba ka sanshi ba, to ba shi ba ne”.
“Okey, to me hakan ke nufi?”
“Ni kaina ban sani ba, a bakin Ogana nake jin wannan kirarin, na dai san mutum ne mai kirki. Da bazarsa muke rawa, ban tava ganin mutum irinsa ba, ya fi kowa kirki…”
Ringin xin wayarta ne ya katse ta. Ta zaro ido.
“Kada dai sun iso?”
Jiki na rawa ta xaga wayar.
“Da fatan kun gama shirya komai?” Deeni ya tambaya ta xaya vangaren.
Ta ce, “Sauran qiris”.
‘Okey, shi ke nan. Mu ma ga mu nan mun nufo gidan, abu mafi muhimmnci ki bar su Yusra su qarasa aikin ki je ki yi wanka”.
“An gama ranka ya daxe”.
Da gudu ta fice ta nufi bathroom.
“Tunda ki ka ga Yayata na wannan rawar qafar ba qaramin kuxi za ta shaqa ba, Deeni yana da son abin duniya, na tabbata ba qaramin samu yake a gindin wannan baqon ba. shi fa mijin Yaya idan ya raina ma qura ko kallo ba ka ishe shi ba. Yana da girman kai, ya fi mu’amala da manyan mutane…”
“Kin ga Yusra ki bar wannan gulmar mu yi qoqarin gama aikin nan tukunna’.
Sun gama komai, suna jidar kayan abincin zuwa dinning room, Aisha na can xaki tana shirya kanta, Nurat ta xauko jug na glass ta nufi dinning room. Ita kuma Yusra na moping xin kicin. Nurat ta duqufa tana shirya dinning table suka kutso kai. Sallama suka yi gaba xaya su ukun idanunsu a kanta, ba su tava ganin kyakkyawar halitta irinta ba.
Zo ka ga kunya da tashin hankali, qam! Ta qame a gurin.
“Subhanallahi! Ya Allah, na shiga uku, ta ya ya zan iya ficewa?”
Ba ta iya amsa sallamarsu ba.
Shi kam Deedat gabansa ne ya shiga bugawa.
“Ba kya jin ana sallama?” Deeni ya faxa.
“Amin”. Ta ce a taqaice. Da qyar ta ke xaga qafafunta ko gabanta ba ta gani saboda kunya. Juyawar da ta yi Salim da Deedat suka dubi juna. Da sauri ya voye kansa da wani irin sonta da ya shiga naso a dukkan sassan jikinsa. Ita xin ma duk da ba ta waye da ko su waye ba, ai hijabinta kawai ta xauka ta yi waje ba tare da ta yi sallama da su Yusra ba.
Aisha ta fita daga xaki cikin qayatacciyar shigar da ta sanya ma Deeni nutsuwa. Bayan sun zazzauna, Deeni ya dube ta.
‘Waccan baquwar muka yi?”
“Ni ma yau na fara ganinta, qawar Yusra ce. Yarinyar kirki ba ruwanta, komai nata abin burgewa ne”.
‘Yaya ban ga Nurat ba fa, ina ta shiga?” Yusra da ke qoqarin shigowa ta tambaya.
“Ki duba”.
Ta ce, “Ba ta nan, daga can nake”.
“To ina ta yi?” In ji Aisha.
“Shi ya sa ban so ta fio diining ba, ba ta son mutane. Ina zuwa”. Aisha ta ce.
Xaki ta koma, inda ta tarar da kayan ta zube a kan gado ta dawo gurinsu.
“Wallahi ko tafiya ta yi, hijabinta kurum ta xauka ko kayan nata ba ta canza ba”.
Yusra ta yi murmushi, “Da alamar kacivus ku ka yi da ita cikin rashin sani kuma babu hijabi a jikinta ko?”
Da sauri deeni ya kaxa kai.
“Tab! Yaya ai ko ke da ganin Nurat Usman a gidanki za ki rina, ita xin wata iri ce, kunyarta ta yi mata yawa, ai wannan xin ustaziyya ce, ni fa na yi mamakin da ta amince ta sanya wannan riga da wandon, Nana ta ce min, ko a gidansu ba ta zama babu hijabi, idan ma ba a yi sa’a ba ko gidansu Nanan ba za ta koma ba, qarshenta ma tana can tana kuka”.
“To ke ba ki san gidansu ba?”
“Ina zan sani, ni da ba ‘yar gari ba? Ni ma yau darajar Nanar ba ta nan ne ya sa ta shigo gidanmu. Ni kuma na rakito ta nan”.
Salim kam hankalinsa gaba xaya ya dawo kan Deedat, tsantsar sonta ya dinga hange a idanunsa. Tabbas wannan xin ce ta dace da rayuwar Deedat, ita ce macen da yake mafarkin mallaka. Da alamun an tada mishi mikin da ke kwance a zuciyarsa.
Gaisuwar Aisha ce ta katse masa tunani. Hira suka shiga yi tsakaninsu ban da Deedat, ba su wani damu da hakan ba sanin cewar shi xin ba mai son magana ba ne. Tashin hankalinsu xaya, ya qi cin abinci sai lemo kawai da ya sha. Qarshe ma miqewa ya yi.
Suka bi shi da kallo.
“Sai ina?” Deeni ya tambaya.
“Ku ba ni minti goma zan dawo”.
Bai jira amsarsu ba ya yi waje.
Duk inda yake tunanin zai ganta ya duba babu alamarta, dole ya koma gidan duk hankalinsa a tashe. Yana son zama da Yusra domin tambayar inda ta ke, to amman yana jin wani irin nauyi, ba zai iya tsayawa yana taxin budurwa da ita ba, yana jin hakan bai dace ba, ko ba ma haka ba, hakan ba girmansa ba ne.
Sai bayan magriba suka bar gidan, inda Salim ya ajiye ma Aisha dubu xari biyu gen-gen, ya bai wa Yusra dubu hamsin. Farin ciki a gurinsu tamkar za su shixe.
Bayan fitarsu Yusra ta dubi Aisha.
“Kin ga Nurat ta yi ma kanta, da tuni ta samu kuxaxen nan”.
“Amma dai ko ‘yar dubu goma kin ba ta?”
“Tab! Wai ma, wa ya ce ta tafi? Ko sisi ba zan ba ta ba”.
“Shi ke nan zan ba ki dubu goma ki ba ta”.
“Wannan kam in ki ka ba ni zan ba ta”.
Aisha ta kai mata duka.
“Mara mutunci”.
*** *** ***
Ta rungume shi ta baya, “Daddy kana sona da yawa, ba ni da tamkarka. Ina yinka wallahi ka fidda ni kunyar qawayena, zan nuna musu taka kyautar’.
Ya mirgino da ita gabansa yana murmushi.
“Rangida zan iya yin komai domin farin cikinki. Ba ma haka na so ba”.
“Dad taho mu je ku yi sallama da su, suna xaki”.
Ta janyo hannunsa. Hajiya Rahma ta kawar da kai ba ta ma san suna yi ba, ita dai ko ba komai ta rabu da qaya.
Nurat ce ta shigo, ta bi ta da kallo.
“Ina kayanki?”
“Ammi na yi kyau ko? Kwata na faxa shi ne na saka kayan qawata, maqociyarsu ce, ina Yayata?”
“Tana can xaki ita da qawayenta’.
“Okey, bari in je na ci abinci, yunwa nake ji”.
Ta yi waje, ta bi ta da kallo.
“Aazeen ina ma za ki zama kamar Nurat?”
Ta kaxa kai kawai.
Washegari da sassafe su Zee suka wuce, ranar Hajiya rahma ji ta yi kamar an sauke mata dutsen dala daga kanta.
Alhaji Usman ne ya shigo sitroom yana faman cika da batsewa. Ta yi kamar ba ta ganshi ba, ya zauna xaya daga cikin kujerun.
“Sun tafi hankalinki ya kwanta, ban ce zan auri xaya daga cikinsu ba. Da sun ci gaba da zama ina jin sai kin qone su. Ni ban tava jin uwar da ke kishi da yaranta ba, ita kanta Aazeen kishi ki ke da ita, ko wata kyautar na yi mata sai kin nuna damuwarki. Wallahi sam ba ki da tunani”.
Ba ta so tanka mishi ba, sai dai a wannan gavar ba ta jin za ta iya yin shiru.
“Ko a tarihi ban tava jin inda aka ce ga wata uwa can na baqin ciki da abin da uba ya yi ma xiyarta ba, ballantana Aazeen wadda nake jinta tamkar numfashina. Aazeen na fara samu a duniya, ina sonta fiye da komai, duk son da za ka yi mata ba za ka fi ni ba. Don haka nake kiyaye duk abin da zai rusa mata tarbiyya, idan za ka siyi duk abin da ke duniyar nan ka ba ta zan fi kowa farin ciki, amma ka dinga yin abin da addininmu ya halatta”.
*💖💕KYAUTAR ZUCIYA💖💞*
*NA*
*BILKISU H.MUHAMMAD*
_(Matar Auwalu By fos zage)_
*last Free page 15*
*_Wanan littafin na kudine akan 300 kacal in kinsan zaki biya don ki fitarmin dashi Dan Allah ki barmin kayana yar uwa_*
*Ga jerin sunayan litattafai na da zaku samu a kasuwa*
*1. IZZATU*
*2. MULKIN MALLAKA*
*3. KAUNA CE*
*4. DACEWA*
*5. RASHIN RABO*
*6.TARAIRAYA*
*7. JINI BIYU*
*8. AKWAI BAMBANCI*
*9. TSALAR KAUNA*
*10. YA YI SAKE*
*11. ILLAR SABO*
*12. SO DA SANKARA*
*13. RASHIN RABO*
*14. WATA RAYUWA*
*15. HUBBAN SHADIDAN*
*16. BAKIN K'AZAFI*
*17. MATSALAR KAUNA*
*18. KYAN KUSKURE*
*19. WA YAFI SONTA?*
*20. GABA DA SO*
_NOW_
*KYAUTA ZUCIYA*
```Duka wanan litattafan sunanan akasuwa zaku sameso a shagunan sai da litattafai inasha Allah```
“Ba aiki ya kamata ki yi ba, hutawa za ki yi, ki bar ni da wannan uwar qwiyar”.
“Babu komai Anty, kin ga idan na saka hannu sai mu fi saurin gamawa”.
“Okey, shi ke nan tunda kin dage. Ga kaya can na xauko miki ki saka, kada ki vata na jikinki”.
“To Anti”. Nurat ta faxa.
Ta koma xaki ta sauya kaya. Kayan sun yi mata xas tamkar nata. Ba ta xaura xankwali ba, ta gyara tufkar gashinta ta fito. Kicin ta nufa inda ta samu Anti Aisha da qanwarta Yusra.
Anti Aisha ta bi ta da kallo, ba ta tava ganin Nurat ba sai yau, amma jinta ta ke yi kamar wadda suka shekara da ita. Wani irin qaunarta ce ta xarsu a zuciyarta. Ta sauke ajiyar zuciya.
“Kawai ki tafi da kayan, da ma ban tava saka su ba, tunani nake yi kamar sun yi min kaxan shi ya sa tuntuni na qi sakawa”.
Yusra ta ce, “Wallahi kin yi kyau”.
“Yanzu ki ci gaba da aikin, zan je na yi wanka, na san suna hanya kada su zo ban shirya ba. Oga ya yi min kashedin in yi kyau sosai, kada Ogansa ya raina shi”.
“Wai Yaya Aisha waye wannan xin?”
Yusra ta tambaya tana kallonta.
‘Shi xin na musamman ne. Takensa shi ne, in k sanshi shi ne, idan ba ka sanshi ba, to ba shi ba ne”.
“Okey, to me hakan ke nufi?”
“Ni kaina ban sani ba, a bakin Ogana nake jin wannan kirarin, na dai san mutum ne mai kirki. Da bazarsa muke rawa, ban tava ganin mutum irinsa ba, ya fi kowa kirki…”
Ringin xin wayarta ne ya katse ta. Ta zaro ido.
“Kada dai sun iso?”
Jiki na rawa ta xaga wayar.
“Da fatan kun gama shirya komai?” Deeni ya tambaya ta xaya vangaren.
Ta ce, “Sauran qiris”.
‘Okey, shi ke nan. Mu ma ga mu nan mun nufo gidan, abu mafi muhimmnci ki bar su Yusra su qarasa aikin ki je ki yi wanka”.
“An gama ranka ya daxe”.
Da gudu ta fice ta nufi bathroom.
“Tunda ki ka ga Yayata na wannan rawar qafar ba qaramin kuxi za ta shaqa ba, Deeni yana da son abin duniya, na tabbata ba qaramin samu yake a gindin wannan baqon ba. shi fa mijin Yaya idan ya raina ma qura ko kallo ba ka ishe shi ba. Yana da girman kai, ya fi mu’amala da manyan mutane…”
“Kin ga Yusra ki bar wannan gulmar mu yi qoqarin gama aikin nan tukunna’.
Sun gama komai, suna jidar kayan abincin zuwa dinning room, Aisha na can xaki tana shirya kanta, Nurat ta xauko jug na glass ta nufi dinning room. Ita kuma Yusra na moping xin kicin. Nurat ta duqufa tana shirya dinning table suka kutso kai. Sallama suka yi gaba xaya su ukun idanunsu a kanta, ba su tava ganin kyakkyawar halitta irinta ba.
Zo ka ga kunya da tashin hankali, qam! Ta qame a gurin.
“Subhanallahi! Ya Allah, na shiga uku, ta ya ya zan iya ficewa?”
Ba ta iya amsa sallamarsu ba.
Shi kam Deedat gabansa ne ya shiga bugawa.
“Ba kya jin ana sallama?” Deeni ya faxa.
“Amin”. Ta ce a taqaice. Da qyar ta ke xaga qafafunta ko gabanta ba ta gani saboda kunya. Juyawar da ta yi Salim da Deedat suka dubi juna. Da sauri ya voye kansa da wani irin sonta da ya shiga naso a dukkan sassan jikinsa. Ita xin ma duk da ba ta waye da ko su waye ba, ai hijabinta kawai ta xauka ta yi waje ba tare da ta yi sallama da su Yusra ba.
Aisha ta fita daga xaki cikin qayatacciyar shigar da ta sanya ma Deeni nutsuwa. Bayan sun zazzauna, Deeni ya dube ta.
‘Waccan baquwar muka yi?”
“Ni ma yau na fara ganinta, qawar Yusra ce. Yarinyar kirki ba ruwanta, komai nata abin burgewa ne”.
‘Yaya ban ga Nurat ba fa, ina ta shiga?” Yusra da ke qoqarin shigowa ta tambaya.
“Ki duba”.
Ta ce, “Ba ta nan, daga can nake”.
“To ina ta yi?” In ji Aisha.
“Shi ya sa ban so ta fio diining ba, ba ta son mutane. Ina zuwa”. Aisha ta ce.
Xaki ta koma, inda ta tarar da kayan ta zube a kan gado ta dawo gurinsu.
“Wallahi ko tafiya ta yi, hijabinta kurum ta xauka ko kayan nata ba ta canza ba”.
Yusra ta yi murmushi, “Da alamar kacivus ku ka yi da ita cikin rashin sani kuma babu hijabi a jikinta ko?”
Da sauri deeni ya kaxa kai.
“Tab! Yaya ai ko ke da ganin Nurat Usman a gidanki za ki rina, ita xin wata iri ce, kunyarta ta yi mata yawa, ai wannan xin ustaziyya ce, ni fa na yi mamakin da ta amince ta sanya wannan riga da wandon, Nana ta ce min, ko a gidansu ba ta zama babu hijabi, idan ma ba a yi sa’a ba ko gidansu Nanan ba za ta koma ba, qarshenta ma tana can tana kuka”.
“To ke ba ki san gidansu ba?”
“Ina zan sani, ni da ba ‘yar gari ba? Ni ma yau darajar Nanar ba ta nan ne ya sa ta shigo gidanmu. Ni kuma na rakito ta nan”.
Salim kam hankalinsa gaba xaya ya dawo kan Deedat, tsantsar sonta ya dinga hange a idanunsa. Tabbas wannan xin ce ta dace da rayuwar Deedat, ita ce macen da yake mafarkin mallaka. Da alamun an tada mishi mikin da ke kwance a zuciyarsa.
Gaisuwar Aisha ce ta katse masa tunani. Hira suka shiga yi tsakaninsu ban da Deedat, ba su wani damu da hakan ba sanin cewar shi xin ba mai son magana ba ne. Tashin hankalinsu xaya, ya qi cin abinci sai lemo kawai da ya sha. Qarshe ma miqewa ya yi.
Suka bi shi da kallo.
“Sai ina?” Deeni ya tambaya.
“Ku ba ni minti goma zan dawo”.
Bai jira amsarsu ba ya yi waje.
Duk inda yake tunanin zai ganta ya duba babu alamarta, dole ya koma gidan duk hankalinsa a tashe. Yana son zama da Yusra domin tambayar inda ta ke, to amman yana jin wani irin nauyi, ba zai iya tsayawa yana taxin budurwa da ita ba, yana jin hakan bai dace ba, ko ba ma haka ba, hakan ba girmansa ba ne.
Sai bayan magriba suka bar gidan, inda Salim ya ajiye ma Aisha dubu xari biyu gen-gen, ya bai wa Yusra dubu hamsin. Farin ciki a gurinsu tamkar za su shixe.
Bayan fitarsu Yusra ta dubi Aisha.
“Kin ga Nurat ta yi ma kanta, da tuni ta samu kuxaxen nan”.
“Amma dai ko ‘yar dubu goma kin ba ta?”
“Tab! Wai ma, wa ya ce ta tafi? Ko sisi ba zan ba ta ba”.
“Shi ke nan zan ba ki dubu goma ki ba ta”.
“Wannan kam in ki ka ba ni zan ba ta”.
Aisha ta kai mata duka.
“Mara mutunci”.
*** *** ***
Ta rungume shi ta baya, “Daddy kana sona da yawa, ba ni da tamkarka. Ina yinka wallahi ka fidda ni kunyar qawayena, zan nuna musu taka kyautar’.
Ya mirgino da ita gabansa yana murmushi.
“Rangida zan iya yin komai domin farin cikinki. Ba ma haka na so ba”.
“Dad taho mu je ku yi sallama da su, suna xaki”.
Ta janyo hannunsa. Hajiya Rahma ta kawar da kai ba ta ma san suna yi ba, ita dai ko ba komai ta rabu da qaya.
Nurat ce ta shigo, ta bi ta da kallo.
“Ina kayanki?”
“Ammi na yi kyau ko? Kwata na faxa shi ne na saka kayan qawata, maqociyarsu ce, ina Yayata?”
“Tana can xaki ita da qawayenta’.
“Okey, bari in je na ci abinci, yunwa nake ji”.
Ta yi waje, ta bi ta da kallo.
“Aazeen ina ma za ki zama kamar Nurat?”
Ta kaxa kai kawai.
Washegari da sassafe su Zee suka wuce, ranar Hajiya rahma ji ta yi kamar an sauke mata dutsen dala daga kanta.
Alhaji Usman ne ya shigo sitroom yana faman cika da batsewa. Ta yi kamar ba ta ganshi ba, ya zauna xaya daga cikin kujerun.
“Sun tafi hankalinki ya kwanta, ban ce zan auri xaya daga cikinsu ba. Da sun ci gaba da zama ina jin sai kin qone su. Ni ban tava jin uwar da ke kishi da yaranta ba, ita kanta Aazeen kishi ki ke da ita, ko wata kyautar na yi mata sai kin nuna damuwarki. Wallahi sam ba ki da tunani”.
Ba ta so tanka mishi ba, sai dai a wannan gavar ba ta jin za ta iya yin shiru.
“Ko a tarihi ban tava jin inda aka ce ga wata uwa can na baqin ciki da abin da uba ya yi ma xiyarta ba, ballantana Aazeen wadda nake jinta tamkar numfashina. Aazeen na fara samu a duniya, ina sonta fiye da komai, duk son da za ka yi mata ba za ka fi ni ba. Don haka nake kiyaye duk abin da zai rusa mata tarbiyya, idan za ka siyi duk abin da ke duniyar nan ka ba ta zan fi kowa farin ciki, amma ka dinga yin abin da addininmu ya halatta”.
*💖💕KYAUTAR ZUCIYA💖💞*
*NA*
*BILKISU H.MUHAMMAD*
_(Matar Auwalu By fos zage)_
*last Free page 15*
*_Wanan littafin na kudine akan 300 kacal in kinsan zaki biya don ki fitarmin dashi Dan Allah ki barmin kayana yar uwa_*
*Ga jerin sunayan litattafai na da zaku samu a kasuwa*
*1. IZZATU*
*2. MULKIN MALLAKA*
*3. KAUNA CE*
*4. DACEWA*
*5. RASHIN RABO*
*6.TARAIRAYA*
*7. JINI BIYU*
*8. AKWAI BAMBANCI*
*9. TSALAR KAUNA*
*10. YA YI SAKE*
*11. ILLAR SABO*
*12. SO DA SANKARA*
*13. RASHIN RABO*
*14. WATA RAYUWA*
*15. HUBBAN SHADIDAN*
*16. BAKIN K'AZAFI*
*17. MATSALAR KAUNA*
*18. KYAN KUSKURE*
*19. WA YAFI SONTA?*
*20. GABA DA SO*
_NOW_
*KYAUTA ZUCIYA*
```Duka wanan litattafan sunanan akasuwa zaku sameso a shagunan sai da litattafai inasha Allah```